Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

qulluwar zuciyoyin wanda ba tsaran rayuwa bane ballanatana aure😮? Tab Shin ya kuke ganin wannan ruguntsumin zai kaya? Dr Falal Rabiu mai Mai wani sanannen billionaire ne wanda keda rijiyoyin mai a fad'in Najeriya, yana taimakon talakawa amma shi kam baya son talaka ya rab’e shi. Taya za’ai Muhammad Mahboub ya zamto siriki agare shi? Kai abin da kamar wuya. Mahboub *ANNURIN ZUCIYAR* Suraidah ne. Da sonshi ta rayu ya rene ta ya girmama a zuciar ta. Shin ko Suraidah zata iya bijerewa mahaifin nata? Tab! dankari Makari. Akwai cakwakiya fa, kun ta6a ganin talaka mai tsattsauran ra'ayi? Ku biyoni muje dan kuji me za'a kulla a tafiyar. Wannan labarin yasha banban da sauran rabarai na, zai ta6a zuciyoyin masu karatu, sannan zai fad'akar daku masu karatu, insha Allahu zai sanyaku nishad'i. Akwai zazzafar soyayya da kuma zazzafar kiyayya, akwai jarumtaka, sadaukarwa ta fannoni da dama, *ANNURIN ZUCIYA* daban yake a cikin sauran labarai. Domin mallakar ANNURIN ZUCIYA na marubuciyar MUSAYAR ZUCIYA (HAJJAH CE) ku tuntubi lamba kamar haka akan nera dari biyu kacal: +234 706 528 3730_


_*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER_

_07067124863_

*_Ko kuma*_

_09032345899_


_BAMUB💕_

_52_

Inayi jiki na na amsa min, Gaba d’aya ciwo yake kota ina, Ina kallon yadda shima ya kudundune a bargo yana rawar sanyi. Can ya d’au waya ya daddana da alamun sak’o ya tura. Ni dai ina zube akan sallaya ina sakin numfarfashin ciwo Jannat tai knocking, Mik’ewa yai ya karbo wasu kwalayen magani ya ajiye a bedside drawer,

“Taso musha magani Fateemah!”

Ba musu na mike dakyar domin Ina buk’atar maganin ina cije lebe na karasa na zauna akan gadon can nesa dashi ina rike hijabin jiki na, Matsowa yai kusa da ni na shiga ja da baya, Da karfin tsiya ya janyo ni ya sanya ni a kirjin sa. Cikin kunne na ya shiga radamin,

“Hak’ik’a nayi dace da samun kyakkyawar mace abar kwatance. Zan kasance tare dake a duk inda kike, cikin mafarkinki, cikin tunaninki, cikin farinciki da bak’in ciki. Zan kasance mai share maki hawayen ki, ya ma za’ai in bar idanuwanki su zubar da hawaye ? sam sam!.

“Zan kasance mai tarairayar ki tamkar kwai a tafin hannu. Fata na ki kasance cikin farin ciki da annashuwa, fata na ki zamto tauraruwar dake haske duniyar masoya. Ke ce tawa har abada Fateemah, Kin zarce sauran mata Ina neman wata kalma wadda babu wanda ya santa. Ina neman wata kalma da zan furta miki cewa…..ke ta daban ce, ke kyakkyawa ce, kin zarce sauran mata. Zuciya ta da taki ba za su ta6a rabuwa ba har abada. Ina son ki....”

Gaba d’aya jikin sa rawa yake, Ni kuma zazza’bi ne yake neman kwantar dani, Amman saboda tsabar mugunta bawan Allahn nan sai ya shiga ko’karin zare hijabin jiki na,

“Ya haka.. Dan Allah kayi hak’uri.”

Na fada hawaye d’aya nabin d’aya. Mubeen ya girgiza kai kawai ya cire hijabin ya cillar,

“Ba nace miki idan mu kadai bane basai kin saba?”

Ya rad’a min a kunne na, Hannun sa d’aya kuma yana karakaina a jiki na. Ina ji ina gani ya ragemin sauran kayan jiki na daga ni sai zani ya lullube mu da bargo, Daga nan salo ya canza. Bidirin sa yake sosai yana hawaye ina hawaye. Ni hawayen ciwo nake wallahi na bakar zalunta irin tasa, Shi kuma bansan hawayen me yake ba. Tun ina bashi hak’uri har na dena baki na ya mutu numfashi kawai nake fitarwa. Gaba d’aya sarrafa ni yake tamkar wata kayan wanki. Naci azaba iya abaza. Da kansa ya tsaftace mana jikin mu, Sannan ya barni a bandakin na kara yo wani wankan.

“Allah ya isa wallahi..”

Na fada a hankali ina goge hawaye. Murmushi naga yayi yana yafito ni da hannu,

“Zo kiji..”

“Wayyo Allah na! Dan Allah kayi hak’uri.”

“Matsoraciya! Ni ba abinda zan miki.”

Rungume ni yayi bayan munsha magani. Duk minti sai ya sumbaci goshi na, Baki na, da gefen kumatu na. Ni kam na shiga uku! Hawaye ne naga sun shiga yar tsere a fuskar sa. Kankame ni yayi ahankali cikin wata irin murya ya fara cewa,

“SO shi ne abun da ya dun’kule zuciyoyinmu waje guda har muka tsinci kanmu a cikin soyayya, Duk kuwa da dai ni kadai ne ke wahala akan kaunar ki. ina fatan ba za ki bari wani d’an ‘karamin abu ya zo ya raba tsakaninmu ba? Ina son ki. Ke tamkar gishiri ce a cikin rayuwa ta, idan na rasa ki zan yi rayuwa ne da babu armashi a cikinta,

“Fikre! Da akwai wasu lokuta da nake zubar da hawaye saboda ke, na san za ki ce saboda me?…..Da akwai wani lokaci da yake zuwa na ji tamkar na yi fikafikai na tashi sama…..Kin kuwa san duk saboda mene ne? Saboda motsawar sonki a cikin zuciya ta da tsintar kaina a cikin matsanancin shau’ki a dukkan lokacin da na ji muryarki ko na tina da ke…..Ina fatan za ki amince mu rayu a tare har abada. Ina son ki fikre,

“Bazan iya rayuwa babu ke ba, A mafarki da kuma a cikin soyayya babu abun da ba zai iya faruwa ba. Ina son ki sosai hakan ya sa nake ji tamkar ba zan iya rayuwa idan ba tare da ke ba. Ba na fatan rasa ki a rayuwa ta, domin kuwa a dukkan lokacin da na rasa ki, na tabbatar da rayuwa ta za ta shiga garari. Ina Son Ki kuma ba zan taba denawa ba.

“Hakika kin shayar dani zumar da ban taba sha ba, Kin kai ni garin dadin da ban taba mafarkin zuwa ba. Na kuma same ki cikakkiyar yar mutinci, Lallai agaida Innar mu da dawainiya. Kalmomi sunyi Kadan wajen kwararo godia ta agare ki.... Kina jina kuwa?”

Sake kasa nai da idanu na ina cije lebe, Hannun sa yasa ya dago hab’a ta yana kallon cikin idanu na, Ai kuwa da sauri na rufe su ruf, Sumbatar idanun yai daga nan ya koma kan baki na, Dakyar na kauda fuska ta,

“Ya kamata ace kin fara daukar darasi awajen dan karamin Malamin nan naki, Jia munyi darasin...”

Saurin rufe masa baki nai da tafin hannu na,

“Ya isa haka dan Allah! Kaji?”

Mirgino ni yayi, Ina ‘kasan sa yana sama. Ya sake narke min idanun sa masu rikitar wa,

“Mah!!!! Our marriage is our sacred bond–one that symbolizes love, hope, and the strength to overcome any obstacles. My unending love for you is my vision, my hope, my goal, and my soul. You’re my Goddess, my hope, my joy, and my life. Please be with me forever, my love. I love you more than life itself Fateemah na!”

Bawan Allah ya bani tausayi matuka ganin yadda yake ta zayyana min can cikin zuciyarsa. Na kuma gyara kaina a jikin sa sai dai fadin rai ya hana na nuna masa komai sai lumshe ido dana sake yi. Hannunsa yana saman kai na sai faman zuzzura yatsunsa yake yi a cikin, ba karamin dadi nake ji ba hakan ne kuma yasa na koma bacci ba tare da na sani ba.

Saukar numfashi na da yaji ne ya tabbatar masa da cewar nayi bacci, ya tashi ya koma saitin fuskata yana kare min kallo tamkar wanda yaga wata sabuwar halitta. Yatsunsa guda biyu yasa yana jan hancina tare da shafar gashin girata, duk da yana cikin halin zazzabi hakan bai hanashi janyoni zuwa kirjinsa ba, ya makale min tamkar wanda ya samu sakon cewa idan ya barni za'a sace ni. Lebansa yasa a saman nawa ya sumbata tare da lumshe idanu shima bacci ya dauke shi.

Mutanen gidan kuwa tunda suka ji mu shiru babu wanda yaje yaga halin da muke ci, daman Jannat ta sanarwa da Mammah cewar Yaya Mubeen yasa ta kaimasa magani bata sani ba ko jinsa ne kona matarsa. Jin haka ne kuma yasa Mammah Ahlaam hana kowa zuwa dakin dan dama taga take-taken Mubeen akan Batoul d'in tun kwanaki biyu yana ta karakaina a kanta.

Bamu muka farka ba sai wajan karfe goma na safe shima nice fitsari ya dameni shine na tashi da ban san lokacin da zamu tashi ba. Kasa hada ido nayi dashi ya kamo yatsuna yana matsawa tare da sanya tafukan hannunsa a wuya na, jin babu zafi yasa ya min magana a hankali kamar baya so.

"Fikre kin warke? Yanzu ina ne yake miki ciwo?"

Ban kalleshi ba na dai kawai girgiza kai na sannan na yi kokarin kwatar hannuna zan tashi, ya yi azamar rigani yana yaye min bargon da muka lulluba.

"Ina kuma zaki je?" Murya a dashe nace.

"Sauka zanyi.." Ya janyo ni na kwace saboda ya matse ni idan ya rike ni ji nake kamar zai zubo.

"Zaki je toilet ne?" Kai na kawai na mirgina ba tare da na ce komai ba.

"Okay tashi na kai ki." Na kasa yi masa musu haka na mika mishi hannu ya tasar dani saboda har lokacin jikina a tsamama yake.

Muna zuwa bakin band’aki na cije alamun ya barni daga nan, sai naji ya yi murmushi tare da sake damke min hannu tare da murda kofar ya bude. Ciki ya jani muka shiga tare, ya nuna min inda ake fitsari da kuma inda ake tutu na kalleshi cikin son jin karin bayani dan ban bahimce shi ba, ya daga min girarsa tare da makalo ni ta baya yace.

"Wanne zaki amfani dashi?" Na yi saurin kwace jikina na juya muka hada ido, harara na watsa mishi ina turo baki tare da hade rai nace.

"Ina ruwan ka da ni, ka tafi mana." Wajan sink ya nufa tare da daukar brush ya waigo ya kalli ne, nima a lokacin shi nake kallo.

"Guri daya zaki bari nima zanyi amfani dashi dan duk abinda kike ji nima shi nake ji. Yo banda abinki my Fikre jiya meye ban jinba bare gani? Kefa matata ce duk abinda muka yi tare lada za'a baki, idan na kalli wani abu a tattare dake naji dadi za'a rubuta miki lada ko so kike na kalli na wasu a rubuta miki alhaki saboda kin hanani yin wasu abubuwan da Allah ya halatta min.?"

Jikina ya yi sanyi, ni kaina na rasa me yasa nake masa hakan, amman dai nasan ina jin kunya gaskiya sannan ba wani sabawa nayi da yin hakan bare yace dama na kware. Babu yadda zanyi gashi kiris ya rage nayi a tsaye sai kawai na nufi gurin da aka tanada dan yin fitsari na tsugunna bayan duk na jajjanyo zanin jikina na bazashi daga baya. Shi kansa yasan cewar ya takura min hakan yasa shin murmushi yaje ya ajiye brush d'in ya fita, ina jin ya fice na sauke ajiyar zuciya fitsarin da ya makale shima ya karasa yowa waje.

Sai da na gama abinda zanyi sannan na fito, baya cikin dakin hakan ya bani damar cire zanina da ruwa ya jika shi na canza kaya zuwa wani hadaddan material orange color riga ne da skirt wadanda suka yi min das a jikina. Ina cikin daurin dankwali ya shigo hannunsa dauke da tray nayi saurin barin daurin na nufi wajan shi da nufin karba sai ya tsaya yana kallo na tamkar yaga sabuwar halitta.

“Wow wow wow my Fikre, iyeeee kullum sararin samaniya cike take da kyawawan taurari masu haske ta cikin hasken farin wata, amma kuma haske mafi kyawu da gani yana cikin idanuwanki my Fikre zo na sake ganinki.”

Ya karasa maganar yana karasawa wajan gado ya dire tray din. Kafin ya juyo tuni na karasa wajan madubi ina gyara daurin da nake yi, ya zo bayana tare da sanya hannayensa ya riko min kuguna yana kallo na sosai.

“Kinyi kyau my beloved wife.”

Nayi murmushi ina lumshe ido dan yanzu naji wani shauki akan yadda yake min magana, na samu kai na da cewa.

“Na gode.”

Ya jani jikinsa sosai, naga alama yana matukar jin dad'i idan ya rungume ni.

“Zo muje kiyi feeding d'in mu ina jin yunwa sosai, duk kuma kece silar ta.”

Tsabar mamaki ban san lokacin da ce.

“Ni kuma?”

“Kwarai da gaske kin san wannan abun idan aka yi shi yunwa yake karawa.”

Shiru nayi dana gano abin da yake nufi, wallahi bansan gayen nan haka yake ba, yaro a fuska sai kace idan kasa masa yatsa a baki ba zai ciza ba, ashe shima lamba d'aya ne. Yana rike dani har muka karasa ya zaunar dani wajan bedside carpet ya koma ya dakko tray din ya ajiye a gabana yana so mu hada ido naki.

“Bari naje na dawo.”

Yayi maganar yana riko hab'ata nayi saurin rintsa idanuwansa. Ina jin shi yana murmushi har ya fita, ni kuma na bude kwanukan ina ganin ko menene a ciki. Mayarwa nayi na rufe sai gashi ya kuma shigowa hannunsa rike da kwando mai dauke da tea flask da kayan shayi yazo ya dire tare da zama a kusa dani.

Kansa ya kwantar a kafada ta yana bude baki, na fahimce shi so yake na hada komai na bashi a baki, wannan gayen tabararsa tayi yawa na ayyana hakan a cikin zuciyarta tare da mika hannu na ciro flask d'in. Hadawa nayi shi kuma yana faman shafar bayana, har sai da na kammala hada mana sannan na ce dashi.

“Bismillah.”

“Hahh.”

Ya bude min bakin sa alamun na bashi, samun kaina nayi da sunkuyawa na leka fuskar shi tamkar ya san zanyi kafin nayi magana naji ya sakar min wani zazzafan kiss a saman lips dina. Nayi saurin kawar da kai ina dan murmushi zuwa lokacin Mubeen ya dena bani mamaki dan naga shi din mutum ne mai san soyayya yana kaunar pure love wato irin wanda yake min har cikin zuciyarsa.

Sannu a hankali na dinga gutsuro funkason da hannuna bawai cokali nasa ba, ina hadowa da ƴan cikin da aka yi miyar dasu ina bashi a baki yana ci, sai da naga yaci da yawa har ya fara kawar da kai tamkar ana bawa yaron goye sannan ne nima na fara cin nawa. Kansa ya dora akan cinya ta ya kura min ido yana kallon yanayin yadda nake ci yana murmushi.

“Fikre komai naki daban yake, ban san menene yasa nake ganin kin banbanta da duk sauran mata ba. Na godewa Allah alhamdulillahi da ya bani ke a matsayin matata wacce nake saka ran wata rana zata haifa min quadruplets”

Ban san lokacin da na kalleshi na zabga masa wata uwar harara ba, cikin subutar baki nace dashi.

“Waye yace maka zan haihu bare har nayi biyu-biyu sau hudu sai kace kaza?”

Hannunsa yasa a saman cikina yana shafawa, ya dago narkakkun idanunsa tare da daga min gira.

“Yarinya mun yi magana da Mammah tace honeymoon zamu tafi, wace kasar kike so muje my love.?”

“Wace yarinyar.?”Na tambaya cikin mamaki.

“Oh sorry Mrs Mubeen.”
Yatsina fuska nayi ina dauka kofin shayi na shiga girgiza masa kai.

“Ni babu wani honeymoon da zanje saboda Fadeelan Yaya Najeeb ta kusa haihuwa”

“Karki saka ran za'a yi a gabanki, kema shiryawa zaki muje yawan bude idanu idan mun dawo sai muje barka, haka ake cewa ko? Barka.”

Na zabga masa harara ya kai hannu zai ja min hanci naki yadda.

“Fishi kike yi? Yarinya na cewa Papa Paris zamu je garin masoya garin da suke tsaga soyayya su baje ta a fili, ina son ki tanadar min kalolin love, romantic abubuwa dan idan mukaje baki min ba ba zamu dawo ba kuma babu ke babu lecturing."

A zabure na janye kafafuwa na ban sani ba wallahi na manta jin ya ambaci komawa gurin aiki yasa murna ta rude ni, kanshi ne ya bada wani irin k'um.... ! Duk da naji bugun amman ban kula ba, baki na yana rawa fuskata cike da fara'a nace dashi.

“Da gaske kake zan koma gurin aiki na?!”

Yatsan sa da naga yasa a baki yana cizawa gashi sai wani irin kallo yake min ashe wai harara ce shine yasa na ankara da abinda nayi masa, yace dani.

“Ban miki alkawari ba, kina ganin ma yadda kika fasa min kai. Zoki duba min ki gani ko yayi jini.”

Harara na zabga masa ba tare da ya kalleni ba, kan nasa ya zuro min har sai da ya mai da shi yadda yake sannan ya juyo min da keyarsa ya takura min sai na duba mishi gurin.

Hannu nasa tare da fara bubude kanannad'add'an gashin kan nasa, babu komai ko alamar kumburi amman dana tabo fatar kanshi zai fara cewa.

“Ashh... ! Ahhhh.. Ohhh..! Zafi my Fikre.”

“Wai kai dan Allah baka jin kunya ne, kayi ta abu irin na babies?”

Na fada ina murgud'a baki ba tare da yasan nayi ba. Tashi ya yi daga kan kafar tawa ya janyo ni gabaki daya zuwa jikin sa, wuyan sa ya zuro a nawa yana fadin.

“Baki sani ba? Ke tunda kika zo gidan nan kinga su Mammah sun min abun da zai nuna miki cewar ni gardi ne?”

“Sau nawa ina gani.” Nayi magana ina kawar da kai.

“Okay haka ma zaki ce ko, muje zuwa ke da kanki zaki kuma maida ni baby boy yarinya. Taso muje mu kwanta.”

“Ni bana jin baccin kaje kayi kawai.”

“Haba my Fikre da ne ai nake kwana ni kadai, amman banda yanzu, zo muje kan gadon kisani nayi bacci idan ke bakya ji.”

“Ohh Mubeen.”

“Ahhhh Fikre please mana.”

Yayi hakan yana sake narkewa a jiki na, ya zanyi haka aure yake dole nabi umarninsa muka hau gado, gashin kansa na dinga yamutsawa a hankali wai dan ya yi baccin amman gayen nan yaki yi, sai ma ni da ya juyo yana jijjagawa tamkar wata baby girl, ai kuwa tuni nayi bacci shi kuwa bansan lokacin da ya yi nasa ba, kawai dai na bude ido nagan shi sakale dani baccinsa abin sha'awa har wani murmushi yake kona Meye oho.

***Ganin yana bacci yasa na zare jiki na na shirya cikin wata atamfa ruwan hoda da zani tasha aikin stones, Na yafa mayafi na na nufi sashen su mamma Ahlaam. Ina tafiya ina gyara tafiya ta azato na zasu gano wani abun. Ina shiga kuwa suka fara nannan dani tamkar zasu hadiye ni dan so. Ni dai kai na a kasa na zauna ina wasa da wayar hannu na. Ashe Mubeen canxa min waya tayi. Tayi kyau sosai da tsada kuma.

“Kawo mata abinci Jannat..”

A koshe nake amman ba zan iya musa mata ba. Gaba na aka cika da cima kala kala. Sai ga Mubeen ya shigo a hargitse, Idanun sa akai na.

“Ashe nan kika taho..? Mamma barka da safiya ..”

Yana kallo na yana gayda mahaifiyar sa. Wallahi bashida ta ido. Kada kai nayi kawai na cigaba da shan juice dina. Gaba na ya zauna yana cin chips din da nake ci,

“Shine baki tashe ni ba..”

Ya nai min wani kallo na cikin idanu, Kasa amsa masa nai, Matsowa ya kara yi yana janye warmers din gaba na. Ai kuwa na mike da sauri na nufi wajen wanke hannu. Mamma Ahlaam ta tashi tana waya Jannat na biye da ita. Nasan kuma bamu waje su kai,

“Meye haka Mubeen?”

“Tashi fa kikai ki kai tahowar ki, Kinsan neman da na miki kuwa? Ko wanka banyi ba. Amma ke kinyi.”

“Toh kayi hak’uri..”

Na fada ina rintse idanu na saboda yadda kai na yafara ciwo lokaci d’aya. Cikin rawar jiki da baki ya shiga tambaya ta,

“Menene? Ina ne yake miki ciwo? Ko wajen ne? Zo muje na duba..”

Wata uwar harara na dankara masa ina janye hannun sa dake kan goshina,

“Ka duba ina? Matsa dan Allah”

“Wajen mana.... Wuri ne mai matukar martaba da mutinci. Ko muje asibiti uhm?”

“Wai bakajin kunyar su Mamma ne?”

“Kunyar me? Matata ce kefa ta sunnah! Halaliyata kuma. Tukunna ma mena ce miki akan mayafi da jambaki?”

Ya fada yana tsare ni da kallo, Ban bashi amsa ba na cigaba da yatsina fuska. Mik’ewa yai ya janyo hannu na. Ina tirjewa ina komai haka ya daga ni,

“Mamma mun tafi..”

Ya dan d’aga murya da karfi yana gayawa mahaifiyar sa,

“Tsaya na mata sallama..”

“Babu inda zaki muje ki karba hukuncin ki.”

Yana gaba yana janye da hannu na haka muka koma sashen mu ina kukan zuci. Naki shiga ina tirjewa a bakin kofa. Jina nai a sama ya dago ni ya ajiye ni akan gado yamin rumfa,

“Mena ce miki akan sa hijabi da jambaki?”

Ckkin rawar murya na shiga in’ina,

“Kayi hak’uri na rigada na saba ko agidah ne, dole sena sa jambaki. Hijab kuma ban cika amfani dashi ba, Kuma naga duk gidah ne ko?”

Birkito ni yai muna kallon juna,

“Ya zanyi da son ki uhm? Abinda kake so shi kake wa kishi. Zawjati ina sonki so mai tsanani. Amma ya zama dole ki karb’a hukunci.”

Ni dai rufe idanu na nai ina jin saukar numfashin sa akan fuska ta mai dauke da flavor din mint. Lebe na ya kamo cikin wata siga ya shiga lashe jambakin kai daga nan wasa ya canza. Sai ga hannun mutumi acikin rigata. Yanason tab’o inda nake ganin girman sa ajiki na. Ya gama kashe ni da wani irin salo na tafiyar tsutsa. Ji nai kawai kofofin jiki na na maraba da amsar sak’on sa. Fashewa nai da kuka alokacin da naji sabon abinda yake min tamkar karamin yaro da ake shayar dashi. Ina kasa ta tsage haka naji. Hawayen takaici kawai nake, Ina jinsa ya zare sauran kayana ya shiga babban aiki ko gajia bayayi. Wallahi nagaji matuka. Kuka sosai nake ya hanani ta hanyar rufe bakin mu.

“Ina kaunar ki Fateemah na! Dan Allah ki so ni ko kadan ne, Ki karb’e ni a matsayin mijin ki, Ki dena kallo na amatsayin karamin yaro da kike koyarwa, Kinji dai yadda tawa qaddarar tayi da ni da tuni na zamto wani abu a rayuwa nima.. Ki saki jikin ki dani na miki alk’awarin shayar dake zuma mai dadin gaske... Ina kaunar ki Zawjati Fateemah”

Haka yai ta sumbatun sa yana aikin gaban sa. Ni kuwa banda zirarar da hawaye babu abunda nake, Ina jiyo sautin radar da yake min a kunne,

“Ni fa malamin ki ne, Ki saki jikin ki sosai domin naga alamun kofofin jikin ki na kar’bar sak’o na. Amman saboda kafiya irin taki kin ki bani hadin kai! Ni fa mubakaci ne. Kiyi hak’uri dani kinji? Ki tallafamin muyi ta raya sunnar ma’aiki..”

“Ciwo.. Dan Allah ka bari..”

Be amsa ni ba ya cigaba da harkar gaban sa, Ranar nasha azaba da radadi ga ciwon kai. Wallahi dakyar nake daga yatsa na, Bandaki ya kai ni ya tara ruwan zafi, ‘sit bath’! Inayi yana hucewa yana canza wani. A ranar dai bayan mun sha fada sai da yamin wanka tatas ya cude ni da soso da sabulu,

“Dama kinada tawadar Allah akan nan?”

Ya fada yana mai nuni da kirji na na hagu. Na dankara masa harara ina cije lebe,

“Ka fita zanyi wankan tsarki...”

Sumba ya sakarmin a goshi na yana murmushi,

“Wane dare ne jemage bai gani ba? Uhm? Komai fa nagani Fateemah na..”

Ya sakarmin gwalo ya fice da sauri, Wankan tsarki na shiga yi ina zubar da hawaye, Sekace inji ko gajiya bayayi akan abu d’aya. Gaba d’aya naji na takure bazan iya ba wallahi.

Muhammad Mubeen kuwa na komawa daki ya tsaya a gaba drawer Batoul yana karewa kayanta kallo. Wasu shegun kaya ya ciro gaba d’aya bana mutunci. Yai murmushi yana hango yadda zasu kwashe da Batoul. Ajiye su yayi akan gado ya koma wajen pantries da bras yana kallan su idanun sa awaje. Ina fitowa na hango shi ya ciro brazier ya kura mata idanu,

“Ya haka...?”

Juyowa yai yana murmushi yana kallon beriziyar yana nuna ta,

“Gani nai ta miki kadan fa, kalla fa.”

Na kauda fuska ina jinjina kokari irin nasa,

“To ajiyemin kaya na..”

Mayawa yai ya kamo ni a hankali muka zauna akan gado,

“Ga kaya nan kisa..”

Nabi shegiyar rigar da take a ajiye gaban ta shara shara kamar abun tatar koko da kallo. Ita yake nufi nasa? Tab lalle ma.

“Banason wannan zan sauya wata.”

“Toh ni inaso.. Ki saamin naga yadda zata miki. Itama fa kamar zata kamaki da alamu.”

Gaba d’aya dai halittar jiki na yake nazarta kome? Na danne bacin raina Ina zura rigar hade da dora zani akai. Gefen drawer na janyo na dakko hair dryer na jona a socket,

“Kawo na taya ki..”

“A’a..”

“Wallahi sai na yi, Ai dole na busar miki dashi ni ne sila.”

Da k’arfi ya janyo ni ya dora akan cinyar sa, Kaman kujera. Haka ya shiga busar min da kai

Please Login or Register in order to submit comment