Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Abada!!!
Khadija kam ko a jikinta, Murna ma tayi tace zata cigaba da rayuwarta yadda takeso, dama kishi da ita se wadda tayi gagarumin shiri, ganin yadda Habib yatada hankalinsa yasata tayi duk yadda tayi ya manta da babin Salma suka cigaba da Rayuwarsu.
Ba karamin kaduwa Saudat tayi ba dataji labarin Salma ta bar gidan Habib, bata taba tunanin hatsabibancin khadija ya kai taraba Salma da Habib ba. Dan haka abun yakara yiwa Saudat ciwo, yanzu duk wannan uban gidan da uwar dukiyar ita kadai ce matar gidan. Nan take taji Ranata yakara baci, "zaki gane baki da wayo khadija wallahi sena miki Abunda ga dukiya amma seta gagareki ci cikin kwanciyar hankali"
Haka khadija tacigaba da rainon cikin da tayi kokarin yafita amma yaki.
Wata tara labour yazo amma bazata iya haihuwa da kanta ba se cs akai mata aka ciro mata da namiji kato kaman Habib yayi kaki ya tofar saboda kama.
Seda akayi sati biyu ta warke saboda cs din da aka mata sannan akayi gagarumin shagalin suna, sam be gayawa khadija sunan dazesawa jaririn ba se ranar suna, ya sanar da sunan yaron ABDUL JALAL, sunan mahaifin Salma kenan!!!!

Tabdijan da alama Habib ya debota da zafi sunan baban Salma fa yasakawa dan khadija.




A ko yaushe ina alfahari daku masoya wannan Novel ina godiya da addu 'oinku
Sannaan masu rokon adinga posting a Facebook insha Allah za' a fara posting din Littafin ABDUL JALAL Facebook tundaga farko
Insha Allah, za'afara posting a group din
AISHA HUMAIRA NOVEL FANS (Daddy's girl) dakuma sauran groups nagode sosai ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹

_ABDUL JALAL (2020)_

_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)

PART 2
_PAGE 2️⃣3️⃣76

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]





_MY FIRST NOVEL_



Saudat ta danyi shiru sannan tace "kumafa hakane amma tayaya kenan?"
"bari muje gida zan gayamiki meyakamata kiyi"

Watarana Khadija ta shirya da dauki Jalal taje gidansu, suka wuni acan se magariba suka koma gida a hanyarsu takomawa ta hadu da Kabir, amma ta dauke kanta kaman bata sanshiba ta zuge glass din motarta tai tafiyarta, Kabir yayi mamakin girman motar da khadija take ja, kana ganinta zaka san tana cikin daula da jin dadi, gefe ga danta kaman ba dan hausawa ba kyakyawa dashi. Taja motarta tabar gurin ya dubi shikuma irin rayuwar dayakeyi ta wahala, ya gyada kai yace "wallahi khadija senayi silar kin fito daga wannan daular dan bazaki yaudareni a banza ba"
Haka Rayuwa tacigaba da gara Kabir wanda hakan yasa yafara shaye2 miyagun kwayoyi.

Bayan Rabuwar Salma da Habib an takuramata a gida akan lallai setayi Aure, wani Ambassador yafito yana sonta, akayi bikinsu, abun Allah ko wata guda batayi a gidansa ba Allah yasa ta samu ciki, Masoya da yan uwa sun tayata murna sosai har Allah yasa ta sauke lafiya ta haifi namiji akasamasa Mahmud, bayan mahmud ta haifi Yusuf da Yasmin, Mahmud shine wanda mukazo dashi, zakiga yana kama da Jalal. Amma Allah yayiwa Ambassador Ahmad Rasuwa shekaru biyar dasuka wuce. Dan haka tai zamanta a England.

Khadija ta karbi makudan kudi a hannun Habib tafara kasuwanci, tana zuwa kasashe daban2 tayi sarin kaya ta sayar, tana da manyan shaguna a fadin kasar nan, wanda dukkansu mallakinta ne.
Saudat ta haifi diya mace, bayan danta munir, wadda itace Ilham, khadija taita zaryar Asibiti akan tanason takuma samun ciki, amma abu ya gagara har wasu kasashen sukaje da Habib amma aka sanar matada bazata kara samun ciki ba, Mahaifarta tasamu matsala sakamakon rauni datayi saboda yawan shan abortion pills datai tayi, khadija ta damu sosai har tagaji ta hakura.
Saudat ta nunawa khadija komai ya wuce, Khadija ta dinga mata barin kudi baji ba gani, Khadija tagayawa Saudat halin da take ciki
"Saudat naso ace nakuma samun haihuwa, ko mace in haifa, Jalal yasamu dan uwa"
"tunda Allah yabaki Jalal dinma ai ki gode masa, dan wani har ya mutu bazega kwansa a duniya ba"
Gefe guda Saudat tayi farinciki jin cewa khadija bazata kuma haihuwa ba, hakan yasa takara kudurcewa ranta seta Rama abunda Khadija tayi mata akan Jalal.

Ummi ta dade bata haihu ba, sunyi girma lokacin da Allah yabata haihuwa, Tunda Allah yasa Ummi ta haifi yarinya mace, hakan yakara saka Jalal zaunewa a gidansu Jawwad, kullum suna tare suna Rainon Kanwarsu, Jalal yaitabin Uncle Aliyu kanin mahaifin Jawwad yana cemasa dan Allah asakawa jaririyar nan sunansa wato Jalal. Aliyu yabiye masa yace Jalal sunan mazane amma insha Allah zanmaka takwara, karka damu, Ranar Suna yasamata Jalila, yace yayiwa Jalal takwara, Habib yaji dadin karar da Aliyu yai masa, yadda suke nunawa dansa soda kauna, duk rikicin da Jalila takeyi intaji muryar Jalal yanzu zata fara murna, gaba daya Jalal jiyake Jawwad da danginsa sune komai nasa.
Fafur khadija tahana adinga kai Jalal dangin mahaifinsa, acewarta tunda basa kaunarta danta ma basonshi suke ba, Amma a haka Habib yake zuwa yakaishi ko a ranar ne su juyo, duk dangin Habib sunsan Jawwad, Jawwad yanajin yaren kanuri kaman yadda Jalal ma yafara jin fulatanci saboda kauna da shakuwa.
Jalila na karama sosai Mahaifinta yanemi Aiki a garin kaduna yatafi da Ummi da Jalila, saboda yawan tsangwama da iyalannasa ke fuskanta, dukda lokacin Jalal da girmansa yashiga secondary, amma haka ya dinga rikici yana kuka, Shi be yadda a tafi da Jalila ba ya saba da ita. Tare yake cin Abinci da ita, komai yagani na wasa se yace ita ze kaiwa, komai yaci seya ajiye nata. Jalal ya dade yana damuwa akan barin gari da uncle Aliyu sukayi, Abun har yafara bawa khadija haushi, yadda ya tashi hankalinsa akan wanda ba dangin iya ba na baba sun bar gari. Ummin Jalila seda tayi kuka lokacin dazata bar kano, saboda ta riga ta shaku da yaranta Jalal da Jawwad
Bisa ga Shawarar zulaiha, Saudat seta dakko Ilham tace ga Ilham nan tabawa khadija ta dinga debewa Jalal kewa ze manta da waccan yarinyar, khadija tayi murna da wannan kyauta da Saudat tayi mata, lokacin Ilham nada shekara takwas khadija ta karbeta, amma sam Ilham basa shiri da Jalal dan sam bata da kunya shikuma ga son girma, dan haka har dukanta yake, Jawwad yaita masa fada yace Ilham kaman Jalila takefa itama kanwarmuce, Jalal yace "Jalila ba mara kunya bace, ni Jalila ce kawai kanwata ba wannan ba"

Har yanzu khadija bata fasa yawace2 kasuwanci ba, Jalal ya tashine a tsakanin kwararo ba bu shakuwar uwa a tareda shi, Allah ne ya dubi Jalal ya hadashi da mutanene kirki irin dangin Jawwad.

Jalal yanada matukar kwakwalwa, sarrafa abu da haddace shi baya masa wahala, dan suna Jss2 suka Sauke Al'qur'ani, suka juya hadda, wanda wannan nasara tasu da taimakon Allah da taimakon Ummine da mijinta, Saboda itake tsayawa taga sun iya dukkan wani karatu dasuka koyo a makaranta, sunyi nisa sosai a haddarsu dan sunkai izufi Arba'in Rayuwar Jalal tafara samun matsala, Jalal yana SS2 a secondary komai nasa yafara lalacewa, sakamakon haduwa da miyagun abokai dayafarayi, Jalal yanada kyauta ga faran faran da mutane, ba babba ba yaro kowa nasane, duk wanda yakeda bukata Jalal ze dauka yai masa, hakan yasa har manya suka fara girmama shi suna gaisheshi.
Jalal lokaci daya ya canza watarana khadija bata kasa tana can harkar kasuwancinta daga Daddy se Jawwad da Jalal a gidan Ilham kuma tana gidansu, 'yan fashi suka shigo cikin dare, suka kama masu gadi suka kullesu, suka shiga cikin gidan, Habib yace su dauki duk abunda sukeso a gidan amma karsu taba masa yaransa, suka sakasu kneel down, sannan tattara abunda suka samu a gidan har zasu tafi dayan ya juyo ya saita Habib da bindiga, gaba daya yaran suka fara kuka, dan fashin ya musu tsawa amma suka ki yin shiru, dan fashin ya saita Jawwad yace "bari in kashe tilon dannaka dan yafiye maka komai a duniya kuma da alama yana sonka sosai" zatonsu shine Jalal, dan haka ya saita Jawwad da bindiga, Habib yace dan Allah karku kashemin shi, gaba daya yaranane, tunda kun samu abunda kuke so dan Allah ku kyalesu garani kukasheni, dan fashin nan yamasa banza ya dan kunamar bindigarsa, kawai Jalal ya mike tsaye, bullet din ya shigeshi a gefen kirjinsa, yan fashin na ganin haka, suka kwashi abunda suka kwasa suka gudu. A gigice Habib da Jawwad sukayi kan Jalal amma yana kwance kaman ba rai jini nata malala a kirjinsa, hakan ya firgita Jawwad kwarai shima ya suma a gurin, misalin karfe uku na dare haka ya daukesu ya tafi dasu Asibiti.
Da kyar aka cire bullet din a kirjin Jalal, ya galabaita saboda a gefem zuciyarsa bullet din yasameshi, shima Jawwad da kyar aka samu ya farka. Wannan fashi ana kyautata zaton dasa Hannun Kabir a ciki, amma ba'a tabattar da hakan ba. Seda Habib ya kai su Jawwad Dubai aka dubasu acam sannan hankalinsa ya kwanta, seda akayi kwanaki sannan khadija tasan meyafaru.
Akaita zuwa duba Jalal, Allah yatemakshi ba'a dadeba ya warke suka koma makaranta.

Mahaifin Jalal ya hada mahaifin Jawwad da manyan mutane akan harkar kasuwancinsa, wanda silar hakan Allah yasawa mahaifin Jawwad nasibi a kasuwancinsa, yasai gida a Sharada NNDC, suka koma, Jalal yasamu daddynsa yace masa dan Allah yanaso yasaimusu gidan dayake makawabtaka danasu Jawwad sukoma, haka kuwa akayi suka tattara suka koma kusada juna, ga gida ga gida.
Har yanzu babu jituwar Arziki tsakanin Jalal da Ilham, ba Ilham bama kawai hatta mamanta Saudat basa shiri saboda hakanan Allah be hada jininsuba, wataran Saudat tazo gidan, tabawa Jalal kyautar turare, da yanuna baze karba ba, Amma Jawwad yasashi ya karba, yace masa ba a haka mutum yamaka kyauta ka gwaleshi, Tunda Saudat uwace a gurinsa, Ranar suna kwance cikin Dare, Jawwad yaji kaman ana jijjiga gadon dasuke kwance dan haka ya tashi da sauri ya kunna fitila, yaga Jikin Jalal yanata Kakkarwa, abun yabashi tsoro sosai, ya tattaba Jalal yace "Dan uwa meyasameka kobaka da lafiya ne" Jalal ya masa shiru, koda Jawwad ya cigaba da magana se Jalal ya bude idonsa seda Jawwad ya firgita wani irin Green yaga kwallarsa tayi, ga jijiyoyin kansa sun tashi sunfito sosai har goshinsa, Jalal ya rike Jawwad yace "Jawwad wani hayaki ya shiga jikina, kamin Addu'a amma karka gayawa kowa, ka dauki turarenda Maman Ilham tabani ka jefar dashi, daga ciki hayakin yake fitowa" Jawwad yadinga karanto masa duk abunda yazo bakinsa a haka har bacci ya dauke Jalal, sannan Jawwad ya dauke turaren ya boyeshi, Jawwad beggayawa kowa ba kaman yadda Jalal ya bukata.
Tundaga nan Jalal yafara zama wani iri, Suna SS2 Jalal yafara haduwa da miyagun abokai, ciki hada wani hatsabibi waishi Jabir Junaid, suna ce masa Jeje, gaban Jalila seda yafadi jin an ambaci Jeje,
"tunda Jeje ya shiga Rayuwar Jalal komai nasa yafara lalacewa, ya koya masa shaye2, Jawwad yai kokarin ya raba Jalal da Jeje amma abu ya gagara, Jawwad be gayawa kowa Jalal yafara shaye2 ba, yayai2 amma Abun na Jalal kullum gaba yakeyi, a haka har mutane suka fara ganewa. Habib yashiga tashin hankali daya fuskanci Jalal yafara shaye2, ya shiga dakin Jalal ya tarar dashi a kwance ga kayan shaye2 Jawwad na gefensa yayi tagumi, hankalin daddy ya tashi, ya tambayi Jawwad me yake faruwa haka, nan Jawwad yaiwa daddy bayanin komai, amma be gayamasa tun asalin meya faruba, ya dai ce masa shima kawai gani yayi Jalal yana shaye2, yayi2 ya dena yaki Habib yashiga tashin hankali jin tilon dansa yafada mummunar Rayuwa, A lokacin khadija kusan watanta guda bata Nigeria, Bayan Jalal yadena maye ya zaunar dashi yaita masa nasiha yana masa fada, amma Jalal fadan nan ko a jikinsa.
Bayan dawowar Mummy Habib ya dinga yi mata fada yana cewa "Khadija a sanadin rashin kulawarki, da sakacinki Rayuwar dana ta tasamma rugujewa, Jalal yakama hanyar lalacewa, wace irin uwace ke"
A fusace tace "Nifa baangane inda maganganunka suka dosa ba, da can bakasan inada sakacin ba se yanzu?"
"ABDUL JALAL yafara shaye2, shaye2 yakeyi" Zare ido tayi "Kamar ya shaye, ni dana baya shaye2, Jalal baze hakaba"
"koki yadda kokarki yadda yarage naki, sekije ki bincika" a gigice ta fita tanufi dakin Jalal, aikuwa tana shiga ta tarar dashi yanata busa hayaki, cikin tashin hankali ta karasa cikin dakin
"Jalal mekakeyi haka? Shaye2 fa kakeyi"
Banza yamata yacigaba da abunda yakeyi, ta karaso ta nufo inda yake amma ya dakamata tsawa "Karki sake kizo inda nake tunda ba kyason bakya kaunata, bakida wata magana dazaki gayamin lokaci yariga ya kure, Mummy da hannunki kika rusa Rayuwata, kin fifita son zuciyarki akan Rayuwar danki, kifita ki barmin dakina, bana kaunar ganinki"
"Amma Jalal........
Jifa yafarayi da duk abunda yaci karo dashi cikin tsawa yake cewa" Kifita Nace bana son ganinki, kije kudi su baki farincikin da duk kike bukata, kifita kibani guri, Jawwad ne yashigo dakin da Sauri yaga abunda Jalal yake da sauri yaje ya rikeshi, Mummy ta juya cike da damuwa tabar dakin.
Tundaga wannan lokacin Rayuwar Jalal tashiga rudani, yadena jin magana ibada ma baya iyayi, yadena ganin girman kowa, yadena ganin mutuncin kowa, kowa ya janye dansa daga shiga huldar Jalal, Jawwad ne kawai be barshiba, da mahaifiyar Jawwad ta fuskanci Halin da Jalal yafada setayi kokarin ta rabasu, saboda kar itama nata dan ya lalace. Amma abu ya gagara mahaifin Jawwad yace indai tai kokarin raba Jawwad da Jalal batayi adalci ba Addu'a yakamata tayi musu gaba daya, wasa2 abu yafara shafar kwakwalwar Jalal ya manta abubuwa saboda shaye2, a haka suka gama secondary suka shiga jami'a, Jawwad na mechanical engineering, shikuma Jalal yana karanta civil engineering, shima a university din haka yakara lalacewa da shaye2, kullum Jawwad kokari yake yaga Jawwad yadena abunda yakeyi amma abu ya gagara.
Suna level 1 kakar Jalal mahaifiyar khadija ta rasu, Jalal yazama rikakken dan shaye2, yazamana in har Jawwad bega Jalal ba to a Club ze tsintoshi. Dukdahaka lokaci zuwa lokaci Jawwad yana raka Jalal maiduguri su gaida dangin mahaifinsa Khadija tacewa Jalal bata yadda yakuma zuwa maiduguri ba, inyakuma bata yafe ba tunda dangin mahifin sa basa sonta shikuma Jalal yace sedai katta yafe, ita mutum nawane sukace basu yafe mataba, Jawwad yace masa be kamata yadinga zuwaba tunda tace bazata yafeba hakkinta ze iya kamashi, dama dangin Habib tuni suka dena zuwa saboda wulakancin Khadija.
Jalal yana shekararsa ta karshe a Jami'a abun nasa yakara ta'azzara, da yana iya karatu dukda yana shaye2, yana da kwakwalwar sosai dan yana daga cikin wanda ake ji dasu ga barin kudi dayakeyi, amma a final year kwakwalwar Jalal takara birkicewa, yakasa karatun ga mantuwa, makarantarma gaba daya yadena zuwa, se yawon club, abokansa yan iska suka kara like masa saboda yadda yake sakar musu kudi, gaba daya iyaye suka hana yaransu shiga harkarsa, suka shiga tsangwamarsa da an ganshi se a tashi abar guri yazama abun kyama, kowa ya gujeshi se Jawwad, hakan yakara tunzurashi yafara rashin mutunci yadena ganin girman kowa, memakon amasa nasiha ko Addu'a se akaita Allah wadaran da halinsa, hatta dangin Khadija basason yaje inda suke bayan abaya harsosuke yaje saboda sunsan indai yaje seya musu barin kudi, ana cikin wannan halinne Ilham ta nuna tanason Jalal a haka, hakan ya tabattar da akwai abunda Ilham suke shiryawa dan daukar fansa akan Khadija da danta, Amma hankalin khadija be kaiba itama ta goyi bayan hakan tana ganin tahaka ne zata wanke zuciyar Saudat akan abunda taimata, har zuwa wannan lokaci ake wannan turka turkar.

Kakar Jalal mahaifiyar Habib tayi kuka lokacin data samu labarin yanda jikanta yakoma, gashi kiri kiri an hanashi zuwa inda take da wannan bakincikin takoma ga Allah, tanawa jikanta fatan shiriya, amma ranar dasukazo gaisuwa suka juya, Mummy tahana Jalal kwana, wannan abun yakara bakantawa danginmu Rai, muka dauke kafarmu daga gidan Habib tsawon shekaru. Babban abun godiya ga Allah shine Jalal baya neman mata ba ruwansa da mata, ko a makaranta ko a club ba ruwanshi dasu, ze sha giya yayi askin banza, yayi rashin mutunci, baya ganin girman kowa musamman Mummynsa dayake ganin sam batayi masa adalci ba a matsayinsa na danta, tunda ta goyi bayan ya auri Ilham, da nufin ta wanke laifinta na baya yakara jin haushin mahaifiyarsa.

Antin Jalal ta kamo Hannun Jalila da fuskarta ta jikebda hawaye tace "Jalila nagaymiki iya abunda nasani gameda rayuwar Jalal, wani abun nima har yanzu ban saniba, nasan zanbarki cikin dunbin tunani, amma Jalila bantaba zaton Akwai wanda ze iya karkata hankalin Jalal ba, duk lokacin daka dakko yimasa Nasiha ko ransa yabaci sekaga yafita hayyacinsa idonsa ya canza kala yafara jifa da abubuwa, kin dakko hanyar daidaita Rayuwar Jalal amma bata sigar dakika fara ba, duk lokacin dakika batawa Jalal rai seya gayamin, Jalila akwai abubuwa da bangayamiki ba saboda ba'a bakina yakamata kijiba, wannan tarihin danabaki nagaya mikine bisa Amincewar Jalal, yanzu mu tashi kinga azahar tayi wanka zanyi inyi Salla zamu juya.
Jiki a sanyaye Jalila ta mike suka nufi cikin gidan, Jalila kam waje tayi, ta tafi gida, tana zuwa gida ta tarar da Nana a harabar Gidan, Nana tana ganinta tace "Jalila ina kika shiga ne? Tun dazu nake nemanki nakira layinki amma wayar na daki"
Jalila batace uffan ba ta wuce daki, tana zuwa ta zube akan Gado, ta fashe da kuka
"ban kyautaba, Mummy meyasa? Meyasa kikayi haka, Ashe shiyasa Jalal yake cewa Kinfiye sonkanki, Saboda kudi da son zuciya kin bata farincikin mutane da dama, kinyi sanadin Rayuwar danki, Jalal ka yafemin bansaniba" takara fashewa da kuka



A ko yaushe ina alfahari daku masoya wannan Novel ina godiya da addu 'oinku
Sannaan masu rokon adinga posting a Facebook insha Allah za' a fara posting din Littafin ABDUL JALAL Facebook tundaga farko
Insha Allah, za'afara posting a group din
AISHA HUMAIRA NOVEL FANS (Daddy's girl) dakuma sauran groups nagode sosai ❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹

_ABDUL JALAL (2020)_

_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)

PART 2
_PAGE 2️⃣4️⃣77

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]





_MY FIRST NOVEL_



Sosai Jalila take Hawaye, tareda surutai a hankali, Nana ce ta shigo dakin, da sauri Jalila ta goge hawayenta, zuwa tayi ta zauna ta kalli Jalila
"Jalila lafiya kuwa, meyasameki? Meyasaki kuka kuma ina kika shiga tun dazu nake nemanki" Jalila bata san wace tambayar yakamata ta fara amsawa Nana ba, Jalila ta dan girgigiza kai tace "Bakomai karki damu"
"Yazakicemin ba komai, kuka fa kikeyi"
"Nana bakomai"
"Shikenan tashi muje, Bakin su Jalal zasu tafi, taso Anty Amina tace inkiramata ke" se yanzu Jalila tasan sunan Antin Jalal dinma, ba musu ta mike suka fito tare, suna shiga gidan suka tarar dasu sunfito zasu tafi, Mahmud ya kalli Nana yace "Nana gashi zan tafi bangama ganinki ba" murmushi Nana tayi "Nima bangama ganinka ba, kaje kayi zamanka a England, memakon kadawo Nigeria muma mu amfana da iliminnaka, kaje se wani uban kumatu kakeyi"
"Allah hajiya Nana, ke bakiga yadda kikakoma bane, kinzama wata madam, yanzuma Anti Amina mukayi waya, zasu zo nan kano, shiyasa nadawo nace nima suzo dani zan dade a Maiduguri kafin inkoma England" ya kalli Nana yayi kasa da muryarsa yace "Nana wannan ce Jalila ne?"
"itace kasanta ne?"
"A'a na tambayekine kawai, naga tana kama da wata ne, just forget, bani lambarki"
"Seka biya tukuna" murmushi Mahmud yayi, "Yimata kudi ko nawane imbiya" Nana tai dariya ta karbi wayarsa tasamasa lambarta, Suna tsaye suna jira Jalal yafito suyi Sallama amma tunda Jalila taimasa abun nan da safe, ya shige daki yaki fitowa ko sallama suyi, Jawwad yanata masa magiya amma yaki bude kofar nan.
Anti Amina takamo hannun Jalila tayi gefe da ita, ta kalleta tace "Jalila kuka kuma? Meyasa? Munasa ran samun nasarar daidaita rayuwar Jalal ta hanyarki amma muga karaya a taredake, karkimana haka Jalila, banbaki labarin Jalal dan isaki damuwa ba" kaman ta ziga Jalila takuma fashewa da kuka, Rungumeta Anti Amina tayi tana sharemata Hawaye cikin kuka Jalila tace
"Anty dana san haka Rayuwar Jalal take daban zama daya daga cikin masu kara rusa farincikinsa ba nasan na dade ina bata masa Rai amma.......
" Jalila kina yimasa hakane dan inyaji haushi ya dena abunda yake nasani karki damu kinji kidena kuka"
Jalila ta jinjina kai, suka musu rakiya har mota suka daga suka tafi.
Jalila jikinta a sanyaye takoma gida, daki takuma komawa ta kule akan gado tayi shiru nan ta shiga tunani daban2,
"Kenan Kabir shine Oga Kb? , Jeje yataka Rawa gurin lalacewar Jalal, menen alakar Kabir da Jeje?" dafe kanta tayi tai tagumi hannu bibiyu tai shiru sekuma wani abu yakuma fadomata a rai
"Saudat tabawa Jalal turare, aranar yadinga karkarwa cikin dare yana firgita, kenan Saudat ma wani abun tayi masa kokuma mene? To wa zangayawa? Mema yakamata inyi ne? "
"Yasalam" Jalila ta furta da karfi tareda dafe kanta, da Hanzari Nana ta shigo dakin ta tarar Jalila ta dafe kai tana kuka
"Jalila lafiyarki kuwa? Tun dazu nake tambayarki meyasameki amma kinki gayamin se kuka kike kinga yadda idonki yayi Ja kuwa?"
Murmushin dole Jalila ta kakalo, "Karki damu kaina namin ciwo sosai, allow me to rest" ta ture Nana ta kwanta, Nana ta dade tana mamakin meyake damun Jalila haka?
Yadda Jalila taga Rana haka taga dare, banda zunzurutun tunani da tambayoyi ba abunda ke kai komo a zuciyarta, ga wani irin tausayin Jalal dake ratsa zuciyarta, antarwatsa Rayuwarsa akan abunda lokacin da ake laifin baya duniyar, gaskiya Mummy bata cancanci zama uwa ba, ta fifita duniya akan Rayuwar danta. Har gari ya waye Jalila idonta biyu,
Halima da Nana ne suka hada breakfast, nanma sukayi sukayi taci Abinci takici, Abun yafara bawa Nana tsoro, dan haka taje tagayawa Maama halin da'ake ciki
"Nono kikeso inkamota in bata ko goyata zanyi inta jijjigata?"
"Maama bahakaba, at least yakamata musan meyake damunta, kartayiwa kanta illa, tun jiyafa bataci Abinci ba tanata kuka, kinsan batada cikakkiyar lafiya fa?"
A fusace Maama tace "fita kibarmin daki, kar Allah yasa taci, inta kashe kanta aita huta"
"Amma Maama....
" Bazaki fita ba sena makeki" ba shiri Nana ta fito, ta nufi part din

Please Login or Register in order to submit comment