Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ze samawa aiki, Jalila ba karamin birgeta family din nan suke ba, kansu a hade yake haka aka gama hira aka watse.
Jalila kullum tana tareda Inna, sannan Mummy Hanan duk ta dena mata wannan wulakanci datake mata abaya.

Jalila suna chatting da suleiman yake gaya mata, an tabattar da Alhaji Kabiru yana saida makamai da kwayoyi shida Jeje, ranar litinin za'a kaisu kotu, Jalila ba karamin farinciki tayi ba, taitayi masa godiya. Ta zauna tayi shiru tayi wani tunani, amma bata gayawa Hanan ba tasan damunta zatayi da tsokana dan haka tabar abun a ranta

Da safe Jalila bayan sungama breakfast taje tasamu Mummyn Hanan tace "Mummy dan Allah kan daddy ya fita inason inganshi"
Mummy tace "to shikenan zan masa magana" Hanan tace "queen me zakicewa daddy ne? Ina fatan bawata matsala?"
"Ba wata matsala inason inganshiine"
"to shikenan"
Mummy taiwa Jalila iso, taje palourn daddy , ta shiga suka gaisa yanata tsokanarta tana murmushi, se bayan sun gaisa tace
"babana gurinka nazo kamin wata Alfarma"
"Ina jinki 'yar Baba fadi komene? Insha Allah in zan iya sena miki shi"
Jalila ta kwashi kusan Awa guda a gurin daddy sannan ta fito, ko Hanan bata gayawa Abunda ta tattauna da daddy ba.

Har yanzu Jalal baya walwala sosai, daddynsa yadawo Nigeria, yakan shiga cikin gida gurin daddynsa, amma babu ruwansa da Mummy balle wata Ilham, Iyakar Jalal dakinsa, sedai wani lokacin yakan fito amma baya nisa sosai, Jawwad ne ke takuramasa yadan fita dashi suzaga gari, Jalal yadena zuwa club amma yana shaye shayensa a dakinsa be denaba.

Hannah duk yadda zatayi taga Jalal abu ya gagara, dan haka ta yankewa kanta shawara ta karshe, ta shirya tsaf ta tafi gidansu Jalal, Jalal na cikin dakinsa a kwance besan me akeba, daddy yana gaggawa ze fita da yamma motar Hanna tai parking a kofar gidan, ta fito daga motar da wata irin shiga da bata kamaci dan musulmi ba, da sauri takaraso gaban daddy tace "barka da yamma"
Yace mata "yawwa barka" ya dauke kansa yana kokarin bude motarsa tace "Amma dan Allah Jalal fa?" seda gaban daddy ya fadi, kaddai ace Jalal yafara neman matane ya dake yace mata "lafiya me Jalal din yayi miki?"
"meyema bemin ba? Amma dan Allah yana cikine gurinsa nazo, inason ganinsa" kaidajin yadda Hannah ke magana kasan babu Alamun tarbiyya a tareda ita daddy yace
"Meye alakarki dashi dakike nemansa, baki bani amsa ba"
"Akwai alaka me girma tsakanina da Jalal, sanin Alakar bata da amfani a gareka, babu abunda sanin Alakar ze kara maka banda bacin rai da tashin hankali, dan haka bekamata ayi tone tone ba, amma ina neman Alfarmar ka dan girman Allah kasaka baki Danka ya Aureni, hakan ne kadai hanyar tsira da mutuncina"
Mummunar faduwar gabace takama daddy, hasashensa yazama gaskiya kenan, yanzu lalacewar ta Jalal harta kai ga fara neman mata Innalillahi wa inna ilaihi raji un juyawa daddy yayi da sauri ya rike kansa ya shige cikin gida yana hada hanya.
Hannah kam murmushi tayi tace "koda banganka ba Jalal, nayi abunda nasan dole ka nemeni, na fuskanci bakajin rarrashi kafiye taurin kai, gara in fito maka a Hannah ta.
Ilham na palour tana harabar gidan tana waya daddy yazo ya wuce rike da kansa, mamakine yakamata, yanzun nan fa yake sauri ze fita to shida waye, sauri tayi ta nufi gate ta leka, amma taga anja mota batagane waye ba.
Gida ta dawo taje tagayawa Mummy, da sauri Mummy ta fito ta nufi part dinsa yana zaune ya dafe kai akan kujera, zama tayi kusada shi tace
"meyasameka hakane? Habibi lafiya kuwa yanzufa kake cikin walwala kafita meke damunka ne?"
Dagowa yayi idonsa jawur yace "Khadija Jalal"
"meyasami Jalal din? Bashida lafiya ne?"
"ba wannan ba, ina kyautata zaton Jalal yafara neman matan banza" dan zaro ido tayi "Kamarya ya'akayi kasan haka? Kodayake ba abun mamaki bane ba, tunda duk wanda yake shan giya koya kwana a club ba abun mamaki bane amma gaskiya bana zaton Jalal yana neman mata amma"
"Enough!!! Baze yuwu ba khadija, iya sanina ďana ba manemin mata bane ba, ban san ya'akayi haka zata faruba, kinga yarinyar datazo gurinsa yanzu kuwa? Kinsan metace min ne? No baze yuwuba dole in dau mataki, Zina bala'i ce, dole inyiwa tufkar hanci"

Ilham dake labe a kofar dakin sedata kusa rusa ihu, da gudu ta tafi dakinta ta rufe kofa tana sintiri, nashiga uku idan Dagaske Jalal yafara neman mata ina na kama, menene makomata? Kan bala'i hakan na nufin lalacewar komai fa? Amma wacece tazo gurin nasa? Ina baze yuwu ba, idan har Jalal yafara neman mata bazamu samu komai ba gaba daya shirinmu ze lalace ne, dole inje inga umma a yau din nan jakarta ta dauka ta zuba kudi tayi waje da sauri tafita ta tari napep ta nufi gidansu.

A sukwane Ilham taje gidansu, ta tarar da mamanta a tsakar gida tana tankade, "Umma akwai matsala ajiye tankaden nan ki tashi"
A sukwane tace "ke lafiya kike wannan rawar jikin?"
"nikam ki ajiye tankaden nan kitaso akwai matsala"
Jan hannun mamanta tayi sukayi daki ta zauna a gefen gado tace "Umma akwai gagarumar matsala, mahaifin Jalal yace yafara neman mata, wai wata yarinya tazo neman Jalal, be fadi me tace masa ba, amma yace yana zargin yafara neman mata, idan haka ta faru mu menene makomarmu?"
"ki kwantar da hankalinki kitashi kikoma tun kafin su gane wani abu, ki bar komai a hannuna gobe da kaina zanje gidan malam, ya bincikamin tsawon shekaru mutumin nan yana mana aiki, bamu taba samun matsala ba dan haka bana tunanin za'a samu wannan matsalar "
" gara dai kije da gaggawa kar asamu matsalar wannan karon, dan ina cikin matukar tashin hankali "
" bakomai ki tashi ki tafi"
Sukayi sallama Ilham ta taho.

Gaba daya hankalin daddy yagama tashi, yarasa nutsuwa gaba daya, yana murna yana ganin Jalal yafara rage wasu abubuwan amma kawai ace wannan mummunan tashin hankali da abun kunya na gabato family dinsu. Ganin duk ya tashi hankalinsa yasa Mummy tasame shi tace
"Hayatee wannan damuwar ba iyace mafita ba, nasha gaya maka abaya Yakamata ayiwa Jalal Aure, Namiji ne me cikakkiyar lafiya dole ya bukaci abokiyar rayuwa, amma wakake tunanin zebawa Jalal Auren 'yarsa a wannan halin nasa, shiyasa nace tunda Ilham ta nuna tana sonshi a haka kima' yar uwassa ce, kayadda a hada Auren nan, shine rufin Asirin mu, kila ma kaga ya dena abunda yake"
Daddy yai ajiyar zuciya yace "bakin Auren Ilham da Jalal nake ba, ina gudun abunda ze biyo baya ne, kinsan halinsa inbayason abu, yace baya son yarinyar nan, tunda yace bayaso ko anyi Auren nan wahala zata sha"
"Haba Hayatee kafison yadakko maka magana atukuna, a wajene yake cewa bayaso, da anyi abun zakaji shiru sun zauna lafiya amma kayi tunani, ina tunanin ayiwa Jalal Aure shine mafita, tunda banajin ma yanada wata wadda yakeso giyarsa ce kawai ta dameshi, inaga yiwa Jalal Aure shine mafita"
"to shikenan zanga abunda Yakamata nayi, Amma hankalina tashi sosai".

Bayan sallar magariba Jawwad yasa Jalal agaba da mita
"Gaskiya Jalal bana son wannan zaman gidan da kakeyi kadena walwala, kadena farinciki kullum a daki, bana son hakan, inaga zan duba mana wani business mufara kadena wannan zaman, dan haka zanyi tunani business zamu fara"
Jalal yai murmushi yace "Dama ina son yimaka magana, Daddy yacemin yasamomaka aiki amma kaki yadda katafi, karka damu dani Jawwad ka karbi aikinka ka tafi senafi kowa murna, Saura kuma muzo musha bikinka da Hanan, ko angon Hanan?"

Ajiyar zuciya Jawwad yayi yace "Jalal nina rasa mekemin dadi ma, Maama ta matsamin akan Auren Naja, kullum yarinyar nan setayi abunda zatajamin fada a gurin Maama, narasa yadda zanyi da ita"
"Kaine bakayi maganinta ba"
"Kamar yaya kenan?"
"Keje kasamu Abba ka gayamasa yanema maka Auren Hanan mana"
"Taya Jalal? Jalila tana sona idan na Auri Hanan ban kyauta ba Jalal"
"kana maganar kana son ta tana sonka amma meye makomarta agurin mahaifiyarka da danginta?"
Jawwad yai ajiyar zuciya yace
"Kasan wani abu makuwa?"
"A'a seka fada"
"Hanan tace min wai soyayyar 'yan uwantaka ce tsakanina da Jalila, Akwai wani a zuciyar Jalila, amma kana ganin hakan ze iya yuwa?"
Jalal ya dan kalli Jawwad yace
"Hmm Maybe, nidai fatana kaje ka karbi aikin nan kawai da daddy yasamo maka in bahakaba nida kaine"
Jawwad yai murmushi yace "Jalal kenan sedai mutafi tare".

Abbaa ya kira Jawwad dakinsa, gashi ga Mummy Jawwad ya shiga ya zauna yana fatan Allah yasa ba wani laifi yayi ba.
Abba yace
"Yayana na kaina, Maamanka tazomin da wani batu, shine nace yakamata ingaya maka kafin in aiwatar"
Jawwad yace
"to Abba na ina jinka"
"Yawwa Jawwad, Maamanka tace tanason hada Aurenka da Kanwarka Naja, kuma nan da sati biyu takeso akai kudin Auren, sannan ka karbi aikin da'aka sama maka, in anyi Auren se ku tafi can tare"
Duk wata jijiya ta jikin Jawwad seda ta dan tsaya na wucin gadi, gaba daya jikinsa yayi shock, cikin dakiya yace
"To Abbana, Allah ya tabattar mana da Abunda yafi Alkhairi gaba daya"
Maama tayi murmushi tace
"in ankai kudin banason asa fiye da wata shida"
Jawwad yace "to Maama Allah ya temakemu"
Abba yace "ina fatan dai ba'a matsa maka ba, inkana da magana ka fito kayi"
Jawwad yace "A'a Abba babu wata damuwa"
"to shikenan Allah yamaka Albarka"

Haka Jawwad yafito daga dakin jiki ba kwari ya tafi dakinsa ya kwanta

Jalal yayi mamaki jin shiru Jawwad bezoba yau, dan haka ya mike domin yaduba Jawwad, daddy ya kirashi a waya yace yana son ganinsa a cikin gida.
Cikin gidan ya nufa, ya nufi palourn daddy amma yana zuwa ya tarar da
Daddy, Mummy, dakuma Ilham turus yayi ya tsaya yana kallonsu daya bayan daya, yasan akwai wata kulalliya




Ina yinku ABDUL JALAL group irin sosai din nan fa 😍😍😍 inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing duk bayan kwana biyu, kuna bari ina lalaci posting duk sati 😜😜😜


Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
πŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈ
What's app only 07063065680.



. 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹

_ABDUL JALAL (2020)_

_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)

PART 2
_PAGE 3️⃣3️⃣86

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]






_MY FIRST NOVEL _

Kara hade rai yayi ya shiga palourn ya zauna becewa kowa komai ba ya zauna, daddy ya kalleshi yace "son ka tashi lafiya"
"Alhamdilillah" daddy yai murmushi yace "Masha Allah, kayi breakfast ne?"
"A'a ina jiran Jawwad ne kuma bezoba"

"bari a hada maka anan kaci" daddy ya kalli Ilham yace "Ilham hadawa yayanki Abinci mana"
Jiki na rawa ta mike ta nufi dining din daddy ta hado masa kayan breakfast ta kawo ta ajiye, shidai be kulata ba ya zauna yafara cin Abincin sa, daddy suka cigaba da hirarsu shidasu Mummy, shidai Jalal bece musu uffan ba, yana kammala cin Abincin sa ya mike ze fita, daddy ya dakatar dashi ta hanyar cewa "Ina kuma zakaje? Zamuyi magana ne ai"
Dawowa yayi ya zauna yana kallon daddy, daddy yace "Jalal kaga zamanka haka baze yuwu ba, tunda ansamu degree daya da kyar, kaga shekarunka sun fara Ja daga kai har Jawwad zuwa yanzu yakamata ace ansama maka abokiyar rayuwa a matsayinka na namiji, amma bantaba jin kacemin ga budurwarka ba, ko akwai wata bansaniba "
Wani irin kallo Jalal yayiwa daddy sannan yace" dan Allah adena wannan zancen, in lokacin Auren yazo za'ayi, amma dan Allah for now a kyaleni"
"A'a Jalal babu batun a kyaleka, banason cigaba da ganinka a haka ba Aure, bakasan Aure shine cikar mutum ba, inma baka da budurwa ne ga Ilham tace taji ta gani tana sonka a haka, meye laifin Ilham? Dan haka nakiraka tunda kaida Ilham duk dayane"
"A zato na a baya munyi wannan Maganar ta wuce? Wannan tamkar maida hannun agogo bayane, nace bana sonta, bana sonta akan me za'a takuramin, kuma ai naga Aure ba wajibi bane, balle ace in banyiba nayi laifi, dan haka a kyaleni bana sonta bazan Aureta ba"
A fusace Mummy tace "Baka isa ba wallahi, da abun kunyar da kake shirin jawomana gara aimaka Aure, kokana so kobakaso Aure se anyi shi"
"Abun kunya na nawa kuma? Koke har yanzu abubuwan da nakeyi basu isheki kunya ba? Nagama magana ba wanda ya isa yamin Auren dole wallahi, duk duniya natasani wannan yarinyar natsani duk wani abu da yashafeta, Aurene bazan Aureta ba"
Ilham ta rushe da kuka tace "Nashiga uku Mummy, menayiwa Yaya Jalal haka?"
Mummy tace "rabu dashi, Aurene babu fashi, tunda yasan yafara biye biyen mata, har karuwai sufara biyoshi gida, rashin mutuncin sa ya wuce yaje ya samesu a can, se yafara kawosu gida, ai dole a dau mataki akansa"
daddyn Jalal yaso ya hana Mummy karasa maganar amma seda ta karasa, Jalal dake shirin fita ya tsaya cak ya juyo
"Niza kiyiwa sharri dan nace bana son wannan shashashar, Nine nakebin mata, kirasa dame zaki alakanta ni se wannan mummunan Aiki, to wallahi da in Auri Ilham gara a dauramin Aure da Akuya, Nagode da sharrin da kika yimin a matsayinki na uwata"
"Ba sharri tayi maka ba Jalal, gaskiyane" juyowa yayi inda daddy ke magana, nan da nan idonsa ya canza ya harzuka matuka yace
"daddy da bakinka? Kaima ka yadda zannemi matan banza? Ka yadda ni Jalal zan kawo karuwa cikin gidan nan? Ka yadda ni Jalal ina neman matan banza, lalacewata bata kai haka ba" daddy yace
"Ya isa Jalal, ba sharri akayi maka ba, ni yarinyar tasamu a waje tace gurinka tazo, ita tacemin Akwai alakar dake tsakaninku wadda bata kamata inji ba, kuma lallai insaka Aureta shine kawai hanyar tsira da mutuncinta da naka, ka gayamin meye hakan inba neman mata kake ba?"
Shiruu Jalal yayi ya marasa meze ce, mamaki gaba daya ya kamashi, a iya tunaninsa babu wadda zatayi masa haka, su Jeje ne kuma zuwa yanzu suna hannu kodai duk shirin Mummy ne haka? Amma a tunanin sa be cancanci daddy yayi masa wannan mummunan zargin ba, ba tareda yayi bincike ba ana alakanta shi da dabi'ar dayafi tsana a rayuwarsa wato zina.

"Shikenan daddy naji na gode, Jalal danka mashayi kuma manemin mata,
Daddy da ina neman matan banza da lalacewar da zanyi tafi haka, da ba tun yanzu ba matan banza sun dade suna zarya a gidan nan, dukda Jawwad yana rufamin asiri a abubuwa da dama bana tunanin ze yadda ya zauna da mazinaci, shikenan nagode amma kusani Wallahi bazan Auri wannaan shedaniyar yarinyar ba"
Mummy tace "dalla rufemin baki, kai har kanada bakin dazakace bakason Ilham? Ba rufamaka asiri zatayi ba, kanada bakin kiranta shedaniya ka.....
"Enough Mummy!!! Karki kara zagina waye silar komai, natsani Ilham natsani me sonta" yakarasa yana Zazzare ido, daddy yace "Jalal ya isheka haka, danme zaka dinga cewa ka tasani yarinya metayi maka haka? Lokaci yayi dayakamata kadinga dagawa mahaifiyarka kafa"
"Daddy kayanke min hukunci bakayi bincike ba, kasan bana maka karya, nidai fatana kayi bincike kadena zargina, daddy kanamin uzuri a abubuwa da dama ban taba zaton haka daga gareka ba, sannan maganar Ilham wani abune daba lallai in gaya maka meyasa nace bana sonta ba, duk ku kwantar da hankalinku Insha Allah a satin nan zanbar muku gidanku, in bar muku kasarma gaba daya ku huta"
Ya juya a mugun fusace yafito daga part din daddy, gaba daya jikin daddy yayi sanyi tausayin Jalal ya kamashi, ya juya ya kalli Ilham yace "Ilham mekika yiwa Jalal ne yake miki haka?"
Ilham cikin kuka tace "daddy ni bansan menayi masa ba, yakemin wannan muguwar kiyayya"
Mummy ta dinga rarrashin Ilham.

Jalal kam tunda yafito yaji wani abu ya tokare masa kirji, dakin Jawwad ya tafi yana zuwa yatarar da Jawwad kwance akan gado ido a rufe, Jawwad yana kwancene zuciyarsa ba dadi yarasa yadda zeyi da matsalar ke damunsa, jin Jalal ya shigo ne yasa Jawwad ya bude ido, ya tashi zaune ya dake ya boye tasa damuwar ya kalli Jalal yace "Lafiya kuwa naganka haka meya farune?"
Kasa magana Jalal yayi, sedai jijiyoyin kansa da suka mimmike idonsa jawur, se huci yakeyi kai dagani kasan akwai damuwa sosai.
Jawwad yace "ka gayamin mana meke faruwa?"
"Jawwad zan nemi visa, dole zan bar Nigeria a satin nan, kuma wallahi na tafi bazasu kara ganina ba"
"meyasa Jalal, meyasa zakace haka?"
"Jawwad nagama yanke hukunci, wannan karon karka cemin komai dan mutuwa ce kawai zata hanani tafiyar nan, zan bar Nigeria idan na tafi wallahi bazan kuma dawowa ba".
A kwanakin nan sam Jawwad be gayawa Jalal shikuma tasa damuwar ba, sedai kokarin lallaba Jalal dayake yayi hakuri ammma fafur yaki se shirinsa yakeyi, sannan sam yadena shiga gidansu ya kashe wayoyinsa dan karma anemeshi.

Hanan da Jalila suna zaune suna hira da Inna a dakinta, Hanan tanata chatting ta dan dago ta kalli Jalila tace
"queen Haidar baya daga waya lafiya kuwa?" tai maganar a shagwabe
Jalila tace "kunfi kusa ai, nima bamuyi waya ba"
"nifa duk na damu a satin nan sam banji muryarsa "
Inna tace "waye kuma haidar, da kike kula dashi haka"?
"Sirikinki ne, kwanan nan zezo kiganshi kyakyawa dashi in gayamiki yafi mijinki Alhaji kyau, kai kaf family dinku babu me kyansa"

Inna tace "ke tafi can, anya akwai me kyan mijina, ai Imamu mijin Mairona ce kawai na yadda yafi mijina kyau"
Jalila da sauri tace "Imamu kuma, shine mijin kanwartaki?"
"Eh shine shima dan uwanane, dan Autan su Imamu shine baban Hanan"
Jalila tace "Inna to wai ina suke yanzu ita kanwartaki"
Inna ta danyi shiru tace "bari yarinya ta, Mu ukune a gurin babanmu nida mairo da yayanmu magaji, ni na Auri Alhaji dan yayar Innarmune, itakuma mairo ta Auri Imamu, dan kanin babanmu ne, yana son mairo sosai, 'yan fashine suka addabi garinmu, watarana suka shigo suka harbi wasu, sukayi Garkuwa da wasu, akayiwa wasu daga cikin matan fyade aka kora dabbobinmu sannan aka sakawa bukkokinmu wuta, kafin hakan tafaru yayanmu magaji ya saida wasu daga dabbobin gadonmu nida mairo yarabamana kudin, to lokacin da 'yan fashi suka shigo garin mairo da mijinta basu dawo daga kiwo ba, A wannan harin aka kashe yaya magaji, nida Alhaji da matar Yaya magaji, da yaranta da nawa yaran muka gudu abun be ritsa damu ba, haka muka baro garinmu muka taho nan bauchi, lokacin duniya na kwance akabamu masauki, muka cigaba da rainon yaranmu, bayan wasu shekaru A hankali bayan wasu shekaru muka dinga haduwa da wasu daga cikin 'yan uwanmu, duk inda mukaa hadu sesu sedawo nan gurin mu su zauna, a haka har mukayi wannan yawan, Amma har yanzu danake miki wannan zancen bansan inda mairo da imamu suke ba, ni ko bangansu ba inga zuri'arsu, Hanan tana matukar kama da ita, amma dana ganki senaga kunfi kama da ita, komai naki irin natane, Allah yasa ke irin zuri'arta ce" Inna ta fashe da kuka,
Jalila tace "Allah sarki inna, kiyi hakuri kinji Insha Allah zaki ganta ko 'ya' yanta, amma ni ban san kakannina ba inada kanan shekaru suka rasu, maybe da Yaya Jawwad ne ze iya sanin wani abun amma ni bansan komai akansu ba"

Suna cikin maganar Yusuf yayi sallama ya shigo, su Jalila suka gaiaheshi ya amsa, ya nemi guri ya zauna ya kalli Jalila yace "'yar Baba kije palourn kasa, second floor kinada bako" gaban Jalila ne yai mummunar faduwa da sauri Hanan ta mike zaune tace "Bako kuma?"
"Kece Jalila?" Yusuf ya tambayeta shiru Hanan tayi tana tunanin waye wannan kuma, ya biyo takan Yaya Yusuf, jiki a sanyaye Jalila ta mike, Hanan ma mikewa tayi zata biyo Jalila, Yusuf yace
"ke dawo nan ki zauna, koke nace kije?"
Hanan tadawo ta zauna ta zumbura baki, tana nazarin waye kuwa wannan"
Jalila taje daki ta dakko hijjabinta har kasa tasaka, ta tafi a hankali ta tura kofar palourn ta shiga kanta a sunkuye tayi sallama.
"wa'alaikum salam warahmatullah" dan daga kai tayi ta kalleshi ido hudu sukayi tai sauri sunkuyar da kanta
Yace "karaso mana queen" Jalila a ranta too queen kuma iyayi, ta karaso ta zauna a kujerar da take facing dinsa,
"barka da dare"
"yawwa barkanki dai my queen fatan kina lafiya?"
"Am not queen Jalila sunana"
Murmushi yayi yace "to ai duk daya, koba haka Hanan take ce miki ba, kuma aini ya cancanta in fadi wannan sunan koba hakaba?"
Shiru Jalila tayi, "to ya gajiyar biki?"
"Gajiya tabi lafiya Alhamdilillah"
"Masha Allah, ni sunana Ahmad nasan kinganni a bikin Yusuf, kobaki ganni ba nina ganki kuma kinyimin Jalila, nagayawa Yusuf ya nemamin izinin zuwa gurin ki a gurin daddy, daddy yabani damar inzo, sannan yace inmuka cika wasu sharuda sannan kin amince ze bani ke" ya danyi shiru sannan yace "Jalila harga Allah kinyimin inasonki Aurenki nakeson yi tsakanina da Allah, amma bazan miki doleba se abunda kikace"
Shiru Jalila tayi tana wasa da yatsun hannunta
"queen kice wani abu mana" still ahiru tayi
"ko banyi miki bane? Ki gayamin ba komai, bazan miki dole ba"
Girgiza kai tayi alamar A'a yace "to gayamin abunda ke ranki"
Fafur Jalila taki magana yai murmushi yace "dago ki kalleni"
Noke masa kafada tayi kaman yanda yara sukeyi sannan tace "to ni me zance?"
"wow muryar ki da dadi Jalila, gaki shagwababbiya" murmushi ta danyi
Wayartace tafara ringing, ya kalleta yace "daga wayar mana"
Ta daga wayar tasaka a kunne Nanace tace "Baby ya kike dan Allah yaushe zaki dawo"?
"kai Nana wai yaushe zan dawo ba rana sena gama hutawa" Nana tace
"department dinku sukoma tun last week, nai shiru ban fadawa Abba kun koma ba, karyayi miki fada, sannan an kafe exams dinku yau"
"dagaske menasamu?"
"nidai nasamu upper credit, but Baby wallahi you are the most luckiest girl i ever seen in my life, kaf department dinku babu me points dinki, se zancenki ake, wasu sun sanki wasu basu sanki ba, lectures sunata a nuna musu ke"
"Alhamdilillah yanzu ina Yaya Jawwad kwana biyu baya daga waya?"
"Baby da banyi niyyar gayamiki ba, shiyasa naketa damunki ki dawo, Abba ya yadda Naja ta Auri yaya Jawwad, memakon yaya Jawwad yace masa bayasonta amma yayi shiru kinsan halinsa nan da kwana tara za'a kai kudin Auren sa gidansu Naja"
Jalila ta manta da wani Ahmad a gurin a razane tace "What, Nana dagaske kike dan Allah"
"Wallahi Baby dagaske nake, gashi yanata fama da Yaya Jalal shima wai ranar Asabar ze bar kasar nan, da se wani satin ze tafi, amma wani abun akayi masa a gidansu, yace wallahi inya tafi bazasu kuma ganinsa ba, ke yaya Jawwad yana cikin damuwa, gashi kusan kullum se Naja tasa anyi masa fada"
Mikewa Jalila tayi ta dafe goshinta tace "Nana am coming back this week Insha Allah, Idan har Abba yabari akayi Auren nan an rusa Rayuwar Yaya Jawwad gaba daya, kuma ina tausayin Hanan, zan dawo a satin nan Insha Allah, dole afasa Auren nan"
Sukayi sallama da Nana ta mike zata koma cikin gida Ahmad yace "Jalila lafiya kuwa? Naga kin shiga wani yanayi ko akwai damuwa ne?"
"A'a bakomai"
"Bari in kyaleki, nadawo na karbi lambarki zamuyi waya" gyada masa kai tayi ta fice da sauri.

Please Login or Register in order to submit comment