Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(π•Žπ”Ό 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 π”Ήπ•Œπ•‹ π•Žπ”Ό'ℝ𝔼 π”Έπ•ƒπ•Žπ”Έπ•π•Š, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 π•†π•Œβ„ π”Ήπ”Όπ•Šπ•‹ 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ π•†π•Œβ„ β„π”Όπ”Έπ”»π”Όβ„π•ŠπŸ’ͺ)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️

PART 2
_PAGE 4️⃣6️⃣99

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724



_MY FIRST NOVEL _



Hannah gaba daya kanta ya kwance bata taba tsammanin abubuwa zasu kwabe mata haka ba, wai me yakawo Jalila a gabar da takeso kulla wannan gadar Zaren, da komai ya tafi dai2, Jalal baze taba tsallake shirinta ba, wayarta ce ta fara ringing amma Hannah tayi biris da ita, an kirata ya kai sau shida sannan ta dauka a fusace tace
"dalla waye haka?"

"ke dalla zizo ne, za'a miki abun Arziki amma kina wa mutane hauka, ki tattara kayanki tun wuri kisan inda dare yayi miki wallahi"

"kamar yaya? Saboda me?"

"Allah ne yake sonki da rahama, Wallahi Jiya na raka wani me gidana Unguwa, ya tsaya gurin wani me gidansa dan sanda ne babba, naji me gidannan sa yana waya, bayan ya gama yake gayawa maigidana, wai wani yabada izinin a kamo masa wata yarinya a ajiye masa ita har seta haihu, ta yaye yaron ya shekara biyar sannan a saketa, idan kuma ba tada ciki aita ajiye ta kar a saketa, kuma yadda mutumin nan yake kwatantawa na gano kaman kece, ban gasgata hakan ba se jiya da naje palace, wallahi cikin dare 'yan sada sukazo nemanki, dan haka in kin san da wata cakwakiyar da kika kulla tun wuri ki kama gabanki wallahi "

Hannah ta hadiyi wani mugun miyau ta ce
"Shikenan nagode sosai zizo"

Ta katse wayarta ta mike tsaye tareda fadin
"kan bala'i banga ta zama ba, ni Jalal zewa haka? Wallahi yadda ya fada din nan aka kamani kashina ya bushe, Amma wallahi in yasan besan wata besan wata ba, ni zesa akama, nizewa hauka? Banga ta zama ba"
Ta mike da sauri ta janyo Akwati tafara zuba kayanta tanayi tanayin surutai.




Jalila tattar komai ta ajiye a gefe ta maida hankali akan karatunta, dan yadda takeji in bata dena yawan damuwar nan ba zuciyarta zata iya bugawa, sosai Maama ta rage wannan gabar da takeyi da Jalila, tana dan sakewa da Jalila har suyi hira, suna shirye shiryen yadda biki ze kasance, Jalila bata taba nuna mata tana fushi da ita akan abubuwan da tayi mata a baya ba, Maama har mamaki takeyi, wani lokacin yanayin halinta daya da Jawwad, ka musu laifi amma su nuna basu san kanayi ba, ita kanta Nana tayi mamakin yadda Maama tayi saurin karaya da Al'amarin da yafaru.


Jalila tana kitchen tana aiki Nana ta sameta
"sannu da aiki Jalila, har tausayi kike bani, ke ba kya gajiya da aiki, da ke zaki rigani Aure ai ban san ya zanyi da aikin gidan nan ba, dan ma su Yaya Jawwad basa nan, aikinsu sam baya karewa"
Jalila tai murmushi tace "Nana uwar son jiki, keda zakiyi Aure ai son jiki banaki bane, madam get ready to face the challenge, Ba sauki a Aure"
"Nasani amma gaskiya bazan iya yadda kikeyi din nan ba, tabdijan shikenan kai bawa baka da hutu"

"Aikuwa mukayi miki aure kikaje kikayi shirme, in yace ze kar Aure Addu'a zamu taya shi, mu fidda anko mu sha biki"
"Kan bala'i ji muguwa, to ta Allah bataki ba"

"Kai Nana sarkin kishi"

"ke ba dole inyi kishin sa ba, ke har mamaki kike bani, ainaga kokarin ki da zaki auri Ahmad din nan, inajinki Hanan tana gaya miki matarsa bata da kirki"
Jalila ta murmusa tace

"Nana kenan, macen da ta amsa Sunanta mace, wadda ta yadda da kanta bata batawa kanta lokaci akan wani kishi, duk rashin kirkin matarsa ai ba akanta zan zauna ba, zan maida hankalina ne akan mijina, zanyi kishine da matar da nasan ta fini Ilimi, kyau, dukiya da asali, se matar data hada wannan abubuwan lokaci daya itace watakila zan kalleta a matsayin kishiya"
jinjina kai Nana tayi tace
"Sannu Jalila, Aini ko Kaza za'a aajiye ace kishiya ta ce to hankalina baze kwanta ba, yaushe zan kashe kaina, ke masu irin wannan zuciyar taki bau da yawa"
A tare sukayi dariya, Sannan Nana tace
"Yawwa Jalila nikam nace ya akayi kika amso qur'anin nan daga hannun Ilham? Na ganshi a karamin drwower"
Dan murmushi Jalila tayi tace "Nawane ai ba nata ba, dan haka tunda ya tafi dole ya dawo"
"Amma dagaske yaya Jalal ne ya baki shi? Kamar yadda Ilham ta fada?"
"watakila shi yabani dan bani da tabbas" Jalila ta fada ba tareda ta kalli Nana ba
"Kamar Yaya baki da tabbas?" Nana ta tambayeta cike da mamaki
Jalila ta juya ta cigaba da aikinta sannan tace
"Kamar yadda nagaya miki mana, bani da tabbas na shi yabani koba shi bane ba"
Nana tace "Kai Jalila kin fiye rainin hankali, mutum yayi miki magana ki raina masa hankali, in tai wari dai maji, Ke Jalila ban gaya miki ba"
"Ina jinki hajiya Nana jarida"
Nana ta dan hade rai tace "kefa 'yar wulakanci ce, wace irin Jarida kuma?"
Jalila tayi murmushi tace "Allah yabaki hakuri"
Nana Ta dan saki fuskarta tace "Wai bakiga kwana biyun nan Maama duk tayi sanyi bane"
Cikin ko in kula Jalila tace "Ban lura da hakan ba, tana komai nata kaman yadda take a baya"
"Shikenan tunda haka kika ce amma Anjima zaki rakani wani guri"
"Ina kenan?"
"In munje zaki gani, saura daga baya kice min bazaki ba"
Jalila tace
"zan raka ki Insha Allah, Amrya ba kya laifi"
"kai Jalila har kinsa naji dadi" Nana takarasa fadar hakan tareda fita daga kitchen din.
Koda Jalila ta kammala aikinta ta koma daki, ta tarar da missed calls a wayarta, ta dauka ta bude don duba waye ya kirata haka? Kiran na Jawwad ne da kuma Ahmad, tana kokarin kiran Jawwad ne kiran Ahmad ya shigo wayarta, dan haka ta fasa kiran Jawwad ta amsa kiran Ahmad, Jalila ta shafe lokaci me tsawo suna waya da Ahmad, Sosai Ahmad yake bawa Jalila kulawa, dan tana iya shafe lokaci me tsawo suna waya ba tareda ta kosa ba, sukanyi kwanaki basuyi waya ba, saboda yanayin Aikinsa, dan haka duk lokacin da suka samu dama suna daukar dogon lokaci suna tare a waya, tana cikin wayar ne kiran wayar Jawwad ya dinga shigowa, dan haka sukayi sallama da Ahmad, ta kira Jawwad, tana bugawa ya daga

Jawwad yace "Baby dawa kike ta waya hakane? Da farko na kira baki daga ba, Nakuma kiranki busy busy, for more than hour"
"Am sorry Yaya Jawwad , Ahmad ne ya kirani, shine.. sekuma tayi shiru
Jawwad yace
"Hmmm to shikenan nagane, dama munyi magana da Hanan tace; zasuyi magana da Nana irin kayan da zasu saka na dinner, za'a turawa Abba, A dakko musu, kayan sun iso, ta kira layin Nana baya shiga"
Dan zumbura baki Jalila tayi kaman yana ganinta tace
"suka dai za'a siyawa nikuma fa? Ko tun yanzu anfara ware ni"
"Waya isa ya wareki babyn Abba, A sekin zaba sannan za'a basu su zaba suma"
"to shikenan zan musu magana Insha Allah, ya Aikin kuma?"
"Aiki Alhamdilillah gashi muna ta fama"
"To Allah yabada sa'a"
"Ameen Babyn Abba"
"Ina Jalal? Ya nasa Aikin?" Jalila taji tayi maganar ba tareda ta shirya yinta ba.
Jawwad yace "Kinfara missing dinsa ne?"
Sekuma taji gaba daya ta dirirce tarasa me zatace
"Amm a'a kawai na tambaya ne, don't mind me, yaushe zakazo"
Jawwad yace
"A'a tsaya, naji dadi da kike tambayarsa, dama be kamata ya samu aiki ta hanyarki, yakama hanya ya tafi nesa da gida kuma ace bakya bincikar ya yakeba, Jalal dai yana nan lafiya, kuma yadda yake nunamin yana jin dadin Aikin nasa, Alhamdilillah ana samun cigaba a rayuwarsa, muna godiya kanwar mu, Allah yabiya ki ladan wannan dawainiya damu da kike"
"Ameen Yaya, to shikenan, naji kaman Maama tana kirana"
Jawwad yace "to shikenan munyi waya da Maaman dazu da safe, Amma in cewa Jalal kina gaisheshi?" ya tambayet cikin zolaya
Da sauri tace
"A'a karka fada, ni bana gaisheshi"
Jawwad yai murmushi yace "Shikenan se anjima"
sukayi sallama, ta danyi Ajiyar zuciya, sannan ta mike, ta tafi bandaki dan daura Alwala anata kiran sallar Azahar.

Da la'asar Nana ta uzzurawa Jalila suka dau mota fita, seda suka tsaya a kasuwa sukayi siyayya, Sannan Nana tace ta rakata Asibiti dubiya, Sam Jalila bata kawo komai a ranta ba ta raka Nana Asibiti, suka shiga female ward, Nana ta tambayi wani daki, aka nuna musu, Seda suka shiga dakin sannan Jalila ta lura da suwaye a dakin, Su Yaya mairo ne a dakin, se Naja dake kwance kaman gawa, ana samata ruwa,
da Jalila tasan gurinsu Nana zata janyo ta, da bata biyota ba, Amma me sukeyi a Asibiti? Ta tambayi kanta, Sallamar dasu Jalila sukayi ne yasa su juyowa suga su waye, Ganin Nana da Jalila yasa su hade rai, Jalila ta samu guri ta tsaya, Nana ta karasa ta zauna, tace
"Yaya Mairo ina wuni"
Rai a hade yaya mairo tace "lafiya"
"Yame jiki kuma?" Nana ta kuma tambaya
A fusace Yaya mairo tace
"ban sani ba gulayya, uwarki ta gaya miki shine kikazo ganin kwaf, hadda dakko wannan annamimiyar shedaniyar, to da dan uwanki ya fasa Auren Naja bata mutu ba tana da rai, sannan ki gaggauta dauke wannan tsinanniyar yarinyar ku bar gurin nan, dan na tsani yarinyar nan bana kaunar ta, Yarinya sekace mayya, wayasani ko bayan Kafirci ta gaji maita, kila ta sha a Nono, kiri2 tana kokarin rabani da 'yar uwata, za' ayi Auren nan amma ta shiga ta fita ta hana, makira sedai kici kanki wallahi, kurwarmu tafi karfinki"

Jalila dake gefe tace "kinga nifa ban san nan zamuzo ba, dana san nan zamuzo da bazan biyota ba, ni ban san Naja bata da lafiya ba, dan haka kidena zagina, wallahi kika kuma zagarmin uwa sena rama, ko ina maita zanci naman kune? Me zan ci ajikinku jikin matsiyata, Azzalumai"

Sa'adah ta taso a fusace tazo gaban Jalila ta nuna ta tace "ke karki kuskura ki zagarmin uwa"
"in aka zagetan me zakiyi?"
Jalila ta tambayeta tareda sauke hannun sa'adah tace

"uwata da aka haifa a cikin Arna, da ita nake Alfahari, dan haka duk wanda ya kuma Yunkurin zaginta se inda karfina ya kare"
Nana ta mike da sauri taje tsakaninsu ta tsaya tace
"haba dan Allah, nifa ban kawo Jalila gurin nan dan kuyi rigima ba, nazo in duba Naja ne nace ta rakoni, me yakawo zancen maita, yaya Jalila tayi hakuri a lokuta da dama da kuke cin mutuncin ta, Yaya mairo a rayuwa mussaman idan kanada 'ya' ya bakayi wa dan wani gori, kokuma mummunan baki, ......

"rufemin baki ko in gaureki da mari, kema ta shanye ki, shine zakizo kimin rashin kunya, na rufe kofa in muku dukan tsiya a gurin nan"
Jalila tace

"Wallahi babu matar da ta isa in tsaya ta dakeni, wallahi Nana dana san nan zaki kawoni bazan biyoki ba, kuma ki kyalesu karsu fasa zagina, bacin ranki akan an fasa aurar 'yarkine, badan anyi yunkurin likawa Yaya Jawwad ita ba ba abunda zesa in fadi wani abu a kanta, tunda tun ba yauba nasan halin yaranki kaf, nasan Naja tana shaye2, an gayamin Sa'adah na bin maza kuma kowanne inada tabattaciyar hujja akan hakan, kuma bari kiji ni ce nan nagayawa Abba yayi bincike akan Naja, kuma bincike ya tabattar masa da ba mutuniyar kirki bace, nan gaba in zakiwa dan wani gori ki duba gaba da bayanki ki tabattar bakida abun gorin tukuna, Allah ne ya sa kamin cin mutuncin da kikemin nida uwata, kuma kadan kika gani wallahi, kekuma Nana ingo key din motar kya taho, ni zan hau ta haya in koma gida"
Jalila tayi ficewarta, da sauri Nana ta biyo bayan ta, da kyar ta lallaba Jalila ta hau motar suka nufi gida, harsuka je gida Jalila bata kula Nana ba ta cika tayi fam, suka shiga da kayan siyayyar da sukayi daki, Jalila ta hade rai sosai Nana ta nisa ta zauna a kusada ita tace

"Jalila nasan zakiji ba dadi abunda nayi miki, na kawoki anci mutuncinki, Jalila nasa ki rakoni ne dan kiga sakayyar hakurin da kikeyi, Jalila me hakuri ba a taba ganin bayansa, duk takurar da sukayi miki abaya zagi da cin mutuci, Amma abun Allah agaban Maama cikin jikin Naja ya zube, Jalila sadaukarwarki da jajircewarki akan samarwa wasu farinciki, Allah baze taba barinki ki wulakanta ba, Jalila duk lokacin da naga hawayenki ina shiga matukar damuwa, amma dayawa kikanyi kukane idan kika kasa samarwa wani farinciki, kokuma wani yayi hurting dinki, amma hakan baya hanaki kokarin ganin kinsa nakusa dake farinciki, shiyasa na kaiki kiga sakayyar da Allah yayi miki akan makiyanki, masu saki zubda hawaye, Jalila ina sarawa kokarin ki, masu irin zuciyarki kadan ne a cikin al'umma, Allah ya dawwamar da haske a cikin rayuwarki"
Jalila ta rungume Nana, tana zubda hawayen da bata da tabbacin na farinciki ne kona bacin rai, tace "Nana nagode da addu'ar da kikayi min, dukda kasancewar su yan uwan mahaifiyarki baki juyamin baya ba, Amma Nana har cikin zuciya ta bana murna da abunda yasamu Naja, duk abunda yafaru da mace daya a society makamancin wannan, gurba cewa ce ta al'umma, da Yaya mairo tayi musu tarbiyya me kyau, Allah ka dai yasan mutanen dazasu amfana dasu, kuma da bazan taba adawa da Aurenta da Yaya ba, Amma ina fatan Allah ya shiryesu, yabasu mafita "
"Ameen Jalila "





Tunda Jalal yayi wannan tafiyar be kara dawowa ba, sedai suyi waya da daddyn sa ko Jawwad, Amma Jawwad yaje sau biyu lagos gurin Jalal, dukkan wani shirye2 suna yinsa ne ta waya shida Jawwad, tunda sukayi wannan rabuwar da Jalila basu kara haduwa ba.
Jalal yayi kalau dashi, bashi da tension sosai, sena tunanin irin missing din Jalila da yayi, 'yan kwanakin da yayi tareda ita, suna shiri ya tsaye masa, amma da zarar ya tuna maganar ta na babu shi babu ita gaba daya se yaji abun duniya ya dame shi, shi kansa yasan Jalila halitta ce me matukar mahimmanci a rayuwarsa, a yanzu yana kokarin yin salloli biyar a rana, dukda ba kowane lokaci yake yinsu akan lokaci ba, yana kokarin yaki da zuciyarsa yaga yayi salla. Amma duk lokacin da yaji abubuwa sun da meshi, yana zama yayiwa kansa caji da giya yadda yakamata.
Sannan Jalal yasaka a nemo masa Hannah duk inda take, se yaga waye gatanta, dan yayiwa kansa alkawarin se yasa an ladabtar da ita, seta gane shiba sa'anta bane da zatayi masa hauka.



Bangaren Jalila ma tana son sanin halin da Jalal din yake ciki, tana son sanin ko har yanzu yana shaye2? Wace irin rayuwa yakeyi zamansa a lagos? Tana tausayin Jalal sosai, musamman idan ta tuna da labarin rayuwarsa da kuma amanar da Antynsa ta bata, ko ba komai dukda fadan da sukeyu takan tuna Alkhairan sa, Amma da ta tuna abunda Mummy da Ilham sukayi mata, gaba daya se ranta ya baci, se taji bata sha'awar kuma shiga shirgin rayuwar Jalal, dama saboda Jawwad suke haduwa, in Jawwad yayi Aure ko ganinta baze kara yiba balle mahaifiyarsa ta zargi wani abu.



Rana bata karya, sedai uwar diya taji kunya inji hausawa, Duk abunda aka sama sa rana inda rai da lafiya zezo, Shirye2 sunyi nisa game da wannan bukukuwa da wadannan iyalai ke tun kara, Jawwad yayiwa Hanan saiti uku na kayan lefe, be cika mata tarkace ba, sedai yazuba mata kaya masu matukar tsada da kyau, haka Nana ita set hudu mahmud yayi mata, itama an zuba mata dukiya (kunsan family su Jalal akwai masu gidan rana) gaba daya kayan lefen bauchi aka kaisu, a can aka karba kayan, na Abdallah ma aka kai kaduna gidansu siyama, gaba daya Basa zama, koda yaushe Hanan tana yawan zuwa kano saboda siyayyar biki.
Duk wani shirye2 Jalila ce kan gaba gurin tsara yadda abubuwa zasu gudana, An shirya gaba daya bikin zasuyi shi a garin bauchi ne.
Saura sati daya a fara biki, su Nana suka tafi garin bauchi inda acan za'ayi dukkan wata hada2 ta biki,

Jawwad da Jalal tare suka je har maiduguri suka kai musu katin bikin Jawwad, dama ga abun dai2 da bikin Nana, rabon da Jalal ya taka kafarsa garin maiduguri har ya manta, Amma bisa ga mamakinsu sega Jalal, dangin Daddy sunyi matukar farincikin ganin Jalal, ya nutsu ba kamar da ba, yasa manyan kaya hada hula, gashi suka samu labarin har aiki yake, sunyi farincikin ganin sa, sun samu kyakyawar karba daga dangin Jalal, dama Jawwad ma dan gida ne, seda suka kwana biyu a garin maiduguri suka wuce bauchi shida Jawwad, sam Mummy bata san batun Jalal yaje maiduguri ba.





Ayi hakuri yau typing babu yawa, nayi busy sosai ne

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
πŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈ

What's app only 07063065680.
Watpad @Ayshercool7724

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

*ABDUL JALAL*

_Story, writing and edited _

By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(π•Žπ”Ό 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 π”Ήπ•Œπ•‹ π•Žπ”Ό'ℝ𝔼 π”Έπ•ƒπ•Žπ”Έπ•π•Š, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 π•†π•Œβ„ π”Ήπ”Όπ•Šπ•‹ 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ π•†π•Œβ„ β„π”Όπ”Έπ”»π”Όβ„π•ŠπŸ’ͺ)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️

PART 2
_PAGE 4️⃣7️⃣100

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724



_MY FIRST NOVEL _


Shirye2 sunyi nisa sosai ana ta hada2, za'a shiga satin biki, Jawwad da Jalal sun kwana biyu a bauchi suka koma kano domin rabon invitation ga abokan Jawwad, Amma har suka tafi Jalila basu hadu da Jalal ba, duk inda amare suka shiga Jalila na biye dasu, tare sukaje gyaran kai, da kunshi na amare, hatta gyaran jiki da Jalila ake, se sheki take kamar itace Amaryar, in kaga yadda take zakewa kai kace itace amaryar, Ana gobe za'a fara bikin 'yan uwansu Jalal daga maiduguri suka zo (dangin su Mahmud) lokacin da suka zo su Jalila sun tafi gurin kunshi, tunda suka zo Antyn Jalal ke cigiyar Jalila, Amma aka sanar da ita sun tafi gurin kunshi, guri na mussaman aka tanadarwa dangin mijin Nana. Ana gobe a fara bikin su Jawwad suma suka dawo shida Jalal, duk inda zashi kafarsa kafar Jalal.

'yan uwa wanda sukazo daga wasu garuruwan, Inna ta dinga nuna musu Su Jalila Da Nana, tana gaya musu ga' ya'yan da jikokin kanwarta.

Yaya mairo kam da zuri'ar ta kaf babu wanda yazo taron nan, sedai sauran 'yan uwa da abokan Arziki.

Se dare su Jalila suka dawo daga gurin kunshi, kallo daya zakayiwa fuskar amaren zaka gane yadda suke cikin farinciki, gashi sun dau kyau Masha Allah, suka tafi part din Anty fido a can suke kwana saboda estate din ya fara daukar harami da baki, kasancewar daddyn Hanan babban mutum ne asanshi sosai. Hakama Abba yanada mutane sosai, ga dangin su Jalal, dan haka estate din cike yake da mutane.
Koda su Jalila sukayi sallar magariba, Hanan tace
"gaskiya sena kira Haidar yazo ya ga kunshin nan"
Jalila tace
"ke zumudin me kikeyi? Kwana nawa ya rage?"
"dan kwana nawa ya rage, se indena kula dashi? Se yaga kunshin nan, in yamasa ayi biki da shi, in yace be kyau ba a dirje shi a daren nan"
Gaba daya sukayi dariya, Nana tace

"ni dama muna gurin kunshi Mahmud yacemin; sunzo dazu suna tareda su Yaya Abdallah, ina son mu hadu da shi, inji ko yaci Abinci?"

Jalila kallonsu kawai take tana murmushi, tana mamakin ya sukeji a ransu game da soyayya haka? Ita dai tasan tana son Ahmad, Amma bata tunanin zata iya wannan rawar kafar akansa kamar yadda su Hanan sukeyi, ko lokacin da take son Yaya Jawwad bata tunanin zata iya abunda su Nana sukeyi, tana kallonsu suka canza kaya, sukayi waya da su Yaya Jawwad suka fice babban palourn part din.

Itama sallolinta tayi, tai wanka ta canza kaya, ta samu ta nutsu tana cin Abinci, ta nayi tana chatting da Ahmad, yana ta mata magiya akan ta fito yana son su hadu amma taki, se wasa take masa da hankali.

Maama ta kira Jalila a waya tace taje main part ana neman ta, haka ta tashi ta tafi, da ita so take ta samu ta kwanta ta dan huta, ta fita ta kofar kitchen yadda su Hanan bazasu ganta ba.
Koda taje, da kyar ta gano Maama saboda cikar da akayi a gidan, Maama tace
"dangin mijin Nana ke nemanki, Antyn Jalal tunda sukazo take cigiyar ki fa"
Jalila tace "Ai ban san sunzo ba, suna ina?"
Maama tayi mata Jagora har masaukin da aka basu, Jalila na shiga Antyn Jalal ta fadada murmushinta tace " 'yar halak taki ambato, tun dazu nake cigiyarki"
Cikin fara' a Jalila tace
"Anty sannunku da zuwa, munje gurin kunshi ne shiyasa, ya kukazo? Ya hanya?"
"Alhamdilillah Jalila, Allah yasanya Alkhairi, ya kaimu lokacin naki Auren, kalli yadda kike sheki kamar Amarya"
Sunkuyar da kai Jalila tayi, alamun kunya, ta gefen Antyn ce tace
"Masha Allah itace Jalila kenan, kai Jalila Allah yasaka miki da Alkhairi, muna godiya da nuna kulawarki ga danmu, last week sega Jalal a maiduguri, babban farinciki danayi, wai aikin dayake ta silarki aka same shi, mungode Jalila"
Gaba daya Attention din sauran da suke dakin ya dawo kanta, wasu suna magana da hausa wasu nayi da yare, suka dinga yi mata Addu'a, tarasa Addu'a mema suke mata haka? Kamar wadda ta basu wata gagarumar kyauta.
Dangin Jalal suna da matukar kirki da karamci, nan Antyn Jalal ta dinga nuna mata dangin Jalal, tana gaya mata kowacce mecece a gurin Jalal, 'yan gayune, kuma kallo daya zakayi musu kasan suna hutawa, gasu kyawawa abunda ta lura da shi shine, gaba dayansu babbar shedar da zaka gane family dinsu da shi, shine wannan dogon hancin irin na Jalal, mazansu da matansu haka suke kayan dogon hanci, Kamar sun saba da Jalila suka dinga yi mata hira, gaba daya Jalila jinta take a takure, Anty ta lura da hakan dan haka tayiwa Jalila sallama, tace seda safe.
Jalila na fitowa tana sauri takoma part dinsu ta hadu da Yusuf

Please Login or Register in order to submit comment