Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register



Jalila na zuwa Hanan tafara yimata tambayoyi "Jalila wai waye Yaya Yusuf yace kinyi bako?"
"ke kyaleni dan Allah wani ne nina manta sunansa ma, Hanan satin nan, maybe nan da kwana uku zankoma Kano"
"Jalila meyasa? Saboda Yaya Yusuf?"
"A'a Hanan Akwai matsala ne, dole inkoma"
"Matsalar mene haka? Jalila kar mutan gidan nan su zargi ko wani lefi sukayi miki"
"bahaka baneba Hanan, Ankoma makaranta sannan ina bukatar zuwa gida"
Hanan tace "hmm ko dai saboda Jalal ne? Gayamin wani abune yafaru dashi ne?"
Cikin damuwa Jalila tace "Hanan dagaske Jalal yake in yabar kasar nan baze dawo ba, wai anyi masa wani abu a gidansu, fitarsa kasar waje hatsari ne" Jalila ta boyewa Hanan batun kai kudin Auren Jawwad kar Hanan ta damu.
Hanan taso ta tsokani Jalila amma ganin ta in serious mood yasa ta fasa tace "gaskiya yakamata kikoma bari daddy ya dawo se muyi masa magana"
Yusuf ne yayi knocking kofar dakin nasu sannan ya shigo da sallama ya kalli Jalila yace "Jalila yaya kun gaisa da Captain Ahmad?"
"Eh yaya Mungaisa"
"to bazamuyi miki dole ba, kigaya masa abunda ke ranki, inkinada wanda kikeso kigaya masa tun wuri"
"tana da wanda takeso fa, tana jin nauyin kane bata fada ba"
Yusuf yace "inkika kuma magana sekinyi tsallen kwado sau sittin a gurin nan, dake nake magana?"
Shiru Hanan tayi yacigaba da cewa "Jalila banason mu cutar dake gidan nan ba'ayi wa kowa dole, nayiwa daddy maganar, in ba kyasonsa ki gaya masa kinji"
Jalila ta gyada kai, yace to seda safenku.
Yusuf na fita Hanan tace "ke Jalila captain Ahmad ne dama, to tun wuri kice masa bakya sansa, har sunkai magana gurin daddy Yaya Yusuf baya wasa, wallahi dagaske suke, in Baba ya tambayeki kice be mikiba ba kya sonsa, kinada wanda kike so"
"Haka nace miki bana sonsa? Wanake dashi a yanzu danake so? To ni yayi min"
"karya kikeyi wallahi, Jalal shine kike so, ba wani aranki seshi"






Ina yinku ABDUL JALAL group irin sosai din nan fa 😍😍😍 inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing duk bayan kwana biyu, kuna bari ina lalaci posting duk sati 😜😜😜

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹

_ABDUL JALAL (2020)_

_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)

PART 2
_PAGE 3️⃣4️⃣87

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]






_MY FIRST NOVEL _

Tsaki Jalila tayi, taje ta dakko trolley tafara zuba kayanta, A daren Jalila taje tasamu dadyn Hanan tace masa zata koma gida jibi saboda sunkoma makaranta, daddy beji dadi ba yacewa Jalila da kansa ze maida ita gida.
'yan gidansu Hanan sunji babu dadi batun tafiyar Jalila, sun mata Alheri sosai, Inna ma taji babu dadi, tace itama wataran zatasa akaita kano gurin Jalila, ranar da Jalila zata koma tun safe tagama shirinta tsaf, karfe goma na safe daddyn Hanan da kansa yasa Jalila a mota ya tafi kai Jalila gida, suna tafe suna hira.

Jawwad yayi duk yadda zeyi ya hana Jalal tafiya amma wannan karon Jalal ya dage, yayi rantsuwa yace seya tafi sannan yaki gayawa Jawwad hakikanin abunda akayi masa a gida, Jawwad ya tafi gidansu Jalal yasamu daddy bayan sun gaisa yace
"daddy me akayiwa Jalal ne yace in yatafi baze sake dawowa ba, bansan me akayi masa ba"

Nan daddy yagayawa Jawwad abunda yafaru. Jawwad yace
"Amma daddy meyasa kake zargin Jalal akan wannan, daddy zan iya rantsuwa da Alqur'ani Jalal baya neman mata, koma wacece sharri take masa daddy"

"Jawwad se daga baya naga nima ban kyauta masa ba, ka bashi hakuri, yadena fushi da daddyn sa, amma kokana da masaniyar dalilin dayasa Jalal ya tsani Ilham, ko tayi masa wani abun ne?"

Jawwad yayi Jim sannan yace "A'a daddy nima bansaniba, ban san metayi masa ba"
"Anya kuwa Jawwad zan yadda bakasan komai ba?"
"daddy dagaske nake bansan komai ba"
"to shikenan, amma Jawwad dan Allah kahana Jalal tafiyar nan, nasan yana fushi dani, amma karya tafi ya bar daddyn sa"
"Insha Allah daddy zanyi kokarin yin hakan"

Jawwad ya tashi ya fita, tun lokacin da Abba yayiwa Jawwad zancen kai kudin Auren Naja yake rashin lafiya amma be gayawa kowa ba, ga kuma tension din Jalal, yakoma daki ya tarar Jalal yanata hada kaya, ya zura masa ido, yarasa mema zece masa, kansa ne yake sarawa sosai ya kwanta akan doguwar kujera ya lumshe ido, yanata sakawa yana kwancewa.

Nana tasan da dawowar Jalila dan haka tanata murna, tana shirye2 itakuma Naja so take Jalila ta dawo ta kuntata mata rai.
Karfe biyu na rana Su Jalila suka iso kano, Nana ta fito ta taresu ta rungume Jalila suka dinga murna, Abba baya gari, ya tafi da Maama lagos, kwanansu uku da tafiya, dan haka Jalila ta budewa daddy sitting room ya zauna.
Nana ta dauki kayan Jalila ta shiga dasu cikin gida, ta kawowa daddy ruwa da lemo da Abinci.
Duk abun nan, Jawwad besan su Jalila sun dawo ba, Jalila da kanta ta tafi part din Jawwad tana shiga palourn sa ta tarar da Jawwad a kwance akan kujera ya lumshe ido Jalal kuma yasa TV a gaba amma sam ba tv yake kallo ba tunani yakeyi.
Sallama Jalila tayi, sallamar tata ce ta dawo dashi daga dogon tunanin da yakeyi, be taba zaton kafin ya tafi zega Jalila ba, seda suka danyi seconds suna kallon kallo, dauke kanta tayi ta nufi gurin da Jawwad yake kwance,

"Yaya Jawwad" ta kira sunansa amma be amsaba, hannu takai ta dafa goshinsa yayi zafi sosai da sauri tace "Subhanallah" dan girgiza shi tayi,
A hankali ya bude ido yana kallonta murmushi yayi mata yace "Baby saukar yaushe haka ba Labari?"
Cikin kulawa tace "Yaya Jawwad baka da lafiya ne haka"?
Mikewa yayi zaune yace "kai amma nayi murna da dawowarki, munyi missing girkinki da kiriniyarki"
"Yaya Jawwad keep jokes aside ka rame sosai baka da lafiya, nakira layinka baka dagawa, Hanan ma ta kiraka amma bata shiga, yanzu daddyn Hanan ne ya kawoni, yana son ganinka"
Jawwad yace "Shikenan bari inje"
Jalal ya kalli Jawwad yace "dagaske baka da lafiya? Meyasa baka gayamin ba?"
Jawwad yace "meye Amfanin gaya maka banida lafiya? Kaika gayamin dalilin dayasa zaka bar kasar nan? se dazu daddy ya gayamin abunda yafaru, kuma matakin da kake shirin dauka shine ya dace? Gaba daya hankalina a tashe yake Jalal, ni bakasan a matsalar danake ba, gashi kaikuma da maganar dakazomin, gaba daya hope din iyayenka akaina yake, bakaga magiyar da daddy yakemin akan kar inbari ka tafi ba narasa yadda zanyi ba dole rashin lafiya ta kamani ba, gaba daya narasa meyake min dadi" gaba daya tausayin Jawwad yakama Jalila
Jawwad Ya mike ya fice a dakin ba tareda Jalal yace masa uffan ba, Jalila ma bayan Jawwad tabi.

Ba karamin tausayi Jawwad yabashi ba, shikansa yana tunanin yin rayuwa ba tareda Jawwad ba, amma yana daga cikin dalilansa na son barin kasar nan yanaso Jawwad yasamu kwanciyar hankali, ya karbi Aiki ya hutawa ransa dawainiyar daya dingayi masa tsawon shekaru a ganinsa wannan ce kawai hanyar dazewa Jawwad halaccin abunda yayi masa.

Jawwad yaje gurin daddy, sun dan dade suna magana da Jawwad sannan yayi musu sallama yatafi.
Tunda Jalila ta koma gidan Naja take habaici tana yada magana
"ko anki ko anso, koda dariya koda kuka seta Auri Jawwad, Jawwad ba mijin kafura bane"
Jalila tabawa banza ajiyarta, duk yadda Naja taso ta tsokani Jalila, Jalila taki kulata.
Bayan daddy ya tafi, bayan la'asar Jalila ta tafi dakin Jawwad domin tana son yin magana dashi matuka, dakin ta shiga da sallama amma bakowa a palourn, bedroom dinsa taje tana knocking sannan ta bude dakin, ta hango Jawwad yayi rigingine ya lumshe ido kaman me bacci, sallamar Jalila ce tasashi ya bude ido, mikewa yayi zaune a hankali tareda kakalo murmushi yace "Babyn Ummi, ya gajiyar hanya? Na zata by now kina can kina hutawa"
"ina batun hutawa Yayana ba lafiya, ya jikin naka?"
"lafiyata fa kalau"
"A'a ni ban yadda ba ina zuwa"
Jalila takoma cikin gida ta hadawa Jawwad tea ta kawo masa, ya karba ya shanye yace "Nagode Jalila"
"meye kuma na godiya? Yaya Jawwad magana nakeso muyi da kai"
Gyara zama yayi yabata dukkan Attention dinsa Jalila tace
"Yaya Jawwad meyasa ka amince da Auren Naja?"
Ajiyar zuciya yayi ya danyi shiru sannan yace "Jalila Maama ta takura na rasa yadda zanyi ne"
"Yaya Jawwad, tun tasowarmu bantaba son wani sama da kai ba, amma ganin Hanan tana sonka, kuma Maama bata son Alkarmu tare, banason tayi fushi da kai, bana son ta fadi wani mummunar kalma akanka dazeyi tasiri a rayuwarka, Yaya Jawwad ba dan nadena sonka nakoma gefe na zuba maka ido na barwa Hanan kai ba, ina ganin kona barka Hanan zata maye maka gurbina, Amma meyasa zaka yadda da Auren Naja, Na tabattar Abba besan komai game da Wacece Naja ba, ita kanta Maama akwai abubuwan da bata saniba game dasu Naja" Jalila takarasa maganar idonta taf Hawaye,
"Yaya Jawwad, Hanan zata shiga damuwa sosai, tana maka so bana wasaba shiyasa na yadda da soyayyar da Hanan take maka ne dan samun nutsuwa da daidaituwa tsakaninka da mahaifiyarka, amma meyasa zaka Amince da Auren Naja?"

"Jalila bijirewa Auren Naja ze kuma jawomin wata damuwar ne, Har Yanzu Maama takasa gane Yaya mairo ba kaunarta take ba, ta riga ta zigata idan nace banason Auren nan komai ze iya faruwa, Amma ni kaina bana son Auren nan Jalila, Jalila na hakura da kene kawai saboda nasan idan har na Aureki bazaki samu kwanciyar hankali da nutsuwa ta fannin dangin mahaifiyata ba, Jalila bayan tafiyarki Maama ta kirani akan maganar Auren tace Abba zemun zancen Auren muddin na bijire nace ke nakeso" sekuma yayi shiru yakasa cigaba
"Ina jinka bakomai karasa"
"Jalila Maama cewa tayi muddin na bijirewa maganar Auren Naja nannunawa Abba ke nakeso bata yafemin ba"
Zare ido sosai Jalila tayi, ta danyi shiru sannan ta girgiza kai
"Yaya Jawwad ka kwantar da hankalinka kayita Addu'a komai zezo da sauki Insha Allah, Allah ya ganar da Maama, Amma zaka iya Auren sister na ko Yaya?"
Shiru yayi bece komai ba
"Yaya Jawwad nida Hanan duk dayane, tana sonka sosai Zata kulamin da kai yadda yakamata, Insha Allah zanyi duk kokarin da zanyi amma bana son kacigaba da damuwa"
"To Babyn Abba na dena Insha Allah"
"Yawwa Yaya Jawwad dina, kamanta da wannan batun gaba daya, Mutum managarci kamarka be dace da mace irin Naja ba, kadena damuwa kar ciwo yakama ka"
Gyada mata kai yayi yana murmushi. Jalila ta mike ta fito daga dakin tanajin wasu Hawaye, harga Allah tana kaunar Yayan ta a zuciyarta babu macen dazata so tarasa managarcin mutum kamar Jawwad, harzata fita ta hango abu akan center table, dan haka ta dawo da baya ta tsya tana dubawa.

Jalal yana dakinsa yakuma tattar dukkan wani abu dayake bukata, ya hadesu guri daya sannan ya fito ya tafi cikin gidansu, dakin daddy ya tafi ya tarar dashi yana Aiki akan system dinsa.
Daddy na ganin Jalal ya ture system din yana murmushi
"Welcome my son"
"Thank you dad"
Jalal yasamu guri ya zauna sannan yace "Daddy naga bazan iya tafiya ba tareda nayi maka sallama ba, ina kaunarka fiye da tunani dukda kamin abunda bazan manta ba, amma bazan iya rabuwa da kai ta har Abada ba, daddy duk inda zan kasance a fadin duniya muna tare, Dubai zan tafi zamu dinga haduwa in kaje can, zan dinga zuwa Nigeria saboda wasu mutane, Amma Mummy taje ta riki Ilham a matsayin yar data haifa "

"My son nibana farinciki da wannan tafiyar taka, nafison ka kusada mahaifiyarka, Jalal idan katafi ba idon kowa akanka babu mece maka bari, bam san wace irin Rayuwar zakayi a can ba, Dan Allah Jalal
" Ya isa haka daddy karka rokeni dan Allah 🙏, Mummy bata sona bata kaunata, bata son farinciki na kanta kawai tasani, damuwarta ce kawai damuwa damuwar wani bata ta bace, daddy kasan yadda zuciyata takemin idan nasan cewa uwata na raye amma bana tareda soyayyar ta saboda wani dalili nata, kalli Rayuwar danakeyi saboda son zuciyarta, daddy Jawwad yayi yayi yaga nakoma mutumin kirki amma abu ya gagara, Amma wani dalili da ban taba tunani ba yana kokarin sani in rabu da shaye2, daddy idan har na cigaba da zama a kasar nan Mummy tanamin abunda takemin to bana tunanin bakin ciki ze bari in rabu da shaye2" Hawaye sosai Jalal yake kaman mace
Jalal yakamo hannun daddy ya rike a cikin nasa, Sannan yadanyi murmushi yace "Daddy na kasan wani abu? Inada Ajiya a Nigeria bazan iya barinta gaba daya ba, in kaga nabar Nigeria gaba daya to Ajiyata na dauka, kamin fatan Alkhairi daddy na"
Yana gama maganar ya sumbaci hannun daddy ya sakeshi ya juya ya fice, daddy yarasa abunda yake masa dadi, idan Jalal bayaji ta wani fannin baya ganin laifinsa saboda tabbas rayuwarsa cike take da kalubale daban2.

Jalila takoma daki sukayi waya da Hanan amma batace mata komai akan Batun Auren da za'ayiwa Jawwad ba, sannan tacigaba da kokarinki kwantarwa da Jawwad Hankali tareda bashi karfin gwiwa,
Jalila sam taki kula Naja, ta maida ita kamar wata mahaukaciya, tayi zage zagenta da habaici amma Daga Nana har Jalila sukaki kulata.

Ilham ta shirya takuma zuwa gidansu gurin ummanta, domin din yadda sukayi da malaminsu,

"Ilham malam ya tabattar min Jalal baya neman mata, Sannan aikin da'akayi masa har yanzu yana nan ajikinsa, amma akwai matsala"
Da sauri Ilham tace "matsalar menene kuma?"
"Malam yace aikin da'akayi masa ya rage tasiri akansa, saboda akwai wanda yake ta kokarin rusa komai"
Girgiza kai Ilham tayi tace
"Umma wallahi wannan yarinyar ce da na nunamiki a Asibiti, hatsabibiya ce ta gaske ni Jalal yaciwa mutunci agaban iyayensa yace ya tsaneni ya tsani me sona"
Zare ido Umman tayi "Yatsaneki ya tsani me sonki dan Iskanci, kan bala'i ai wallahi daga shi har khadija basu isaba senaga abunda ya turewa buzu nadi"
"to ai Umma ba wannan bama, akan case din nan na zargin yana neman mata, yace kasar nan ze bari wai inyaso Mummy ta rikeni ni ta haifa bashi ba"
"Yabar kasar nan saboda me? Ke Ilham akwai aikifa baki kirin agabanmu, idan yaron nan ya tafi be Aureki bafa? Ita khadija me tace?"
"me kuwa zata ce ranar kaman ze rufeta da duka"
"tsinanniya ni dama ya daketa ta mutu in yaso yakare rayuwarsa a prison"
"Ahha umma akan me? Ta mutu akaishi prison bamu mallaki dukiyar damuke Hari ba?"
"to ai Ilham tsawon zamanki a gidan nan ba wani kokari da kikeyi, ace duk wannan shekarun ko kallon kirki baya miki sema tsana"
"to Umma yazanyi? Ni tun farko sonayi inyi me gaba daya kowa ya huta, kuma kiris ya rage amma ina shegen taurin kaine da shi kamar dutse ne a kirjinsa ba zuciya ba"
Umma ta numfasa tace "Munyi maganar da maman Yaseera, tacemin akwai wani malaminta a can Nijar, munyi da ita zanje ta rakani shima mu jarraba irin nasa Aikin mugani"
"to Amma Umma tayaya? Kasar fa ze bari"
"Dan ubanki kije kiyi duk yadda zakiyi, ki lallabashi in ta kama hada kuka akan bakya so ya tafi, ni nama rasa dalilin dayasa ya tsaneki haka wallahi, keba muniba to kodai yasan abunda mukeyine?"
"Haba dai yaza'ayi yasani? Ni dai Umma dan Allah ki kai Sunan yarinyar nan kawai intakama a kasheta, dan wallahi yanzu ba zargi nake ba, na tabattar ita yakeso"
"tayaya kika sani?"
"Umma ninake ganin abunda nake gani, wallahi Umma idan kinga Jalal ya tabani to bisa kuskure ne, koda wasa baya bari ya tabani, bama ni kadaiba kinsan halinsa bayason mata su rabe shi, amma ganin idona naga ya rungumeta, itakuma makirar tsinanniya tayi luf a kirjinsa, Allah ka dai yasan abunda sukeyi wallahi na tsaneta kamar mutuwata, kuma bakiga yadda baban Jalal din yake mutunta ba, keba shi kadai ba har Mummy bakiga yadda take mata ba"
Jinjina kai Umma ta shiga yi sannan tace
"kyaleni da ita, zata gane kuskurenta, nasan yadda zan bullowa lamarin zata gane bata da wayo, kafin inje gurin malamin, zan gayamiki yadda zakiyi kowa se ya tsaneta"
Haka sukayi ta hirarsu su saka wannan su kwance wancan.

Jalila kullum dare setayi salla takaiwa Allah kukanta haka take raba dare, gata gwana gurin yawan tilawar Alqur'ani, shiyasa Jalila ta yadda da duk wani abu da take aikatawa a rayuwarta take Nasara tasan dogaro ga Allah, riko da ibada da nacewa Alqur'ani shine matakin dukkan wata Nasara a rayuwarta, duk abunda ta tinkara setaga bayansa, ta taba duk wanda takeso komai matsayinsa amma babu abunda ze faru da ita, ta yadda da dukkan abunda ta roki Allah intaga bata samu ba to lokaci ne beyiba, ta yadda wannan shine matakin Nasararta a rayuwa wadda Umminta da akewa kallon tubabbiyace ta dorata a wannan tafarkin.

Tunda Jalal yace zeyi tafiyar Nan Mummy hankalinta yakasa kwanciya, gashi tasan yadda Jalal yakejin haushin nan nata baze saurareta ba, Amma yazama dole Jalal ya Auri Ilham dan cikawa Saudat Alkawarin ta wannan ne kawai abunda zatayi ta wanke laifin ta a gurin Saudat.
Mummy tayiwa daddyn Jalal magana akan yayi wani abu ya hana Tilon danta tafiya ya yabarta amma amsar daya bata ta mata ciwo
"da lokacin danake miki maganar ki hakura da tafiya karatu kikula da tilon danki da kinji magana ta da koba duka ba ko yaya da Jalal yaji maganarki, ko kin manta watansa bakwai kika dena bashi Nono, a wata bakwanma se lokacin da kika gadama, niba abunda zan iya ki kyaleni"
Ba karamin ciwo maganar daddy tayi mata ba amma ba yadda ta iya.

Ilham ta shirya taje dakin Jalal don jarraba ganin ko ze saurareta amma kusan ya kwashe komai nasa dake dakin nan se abunda ba'a rasa ba, tasan yana gidansu Jawwad dan tunda abun nan ya faru yakoma can dan haka ta bishi can gidan.
Jalila ta kaiwa Jawwad Abinci amma baya nan, se Jalal a palour, bata kulashi ba ta shiga tana gyrawa Jawwad bedroom. Tagama ta fito palour yana zaune inda Tabarshi yana daddana waya, ta fito tazo ta zauna a teburin dake gabansa, tana fuskantar sa, dagowa yayi ya kalleta, kallon dayake mata dukta tsargu, basarwa tayi tace
"Abokin Yaya wai dagaske tafiya zakayi?" A ranshi yace lallai yarinyar nan sekace bata san sunansa ba, nikam nace ai kaima haka kake cemata kanwar Jawwad 🙄,
Sauke idonsa yayi sannan yace "Kafin kiyi tafiya ai nagaya miki ko?"
"Aini ban zaci dagaske kake ba" dagowa yayi yana kallon ta karo na biyu yace "na taba yimiki karyane? Ko Ba kya son in tafine?"
"to inma ka zauna mekake karamin inka tafi hutunane ai, dan ba karamin wahala nake sha saboda kai ba, da inka tafi na huta banga abunda kayiba balle inji haushin ka, amma ni Su Mummy nake dubawa da Yaya Jawwad"
Ilham ce ta shigo dakin da Sallama Amma abunda ta gani zata iya kiranshi da mummunan gani, Amma ta dake tunda sulhu take nema, gaba daya suka daga kai suna kallon Ilham, tattara nutsuwarta ta boye damuwar ta ta tako a hankali tazo gaban Jalal ta tsuguna tace "Yaya gurinka nazo"
Bece mata uffan ba itama Jalila bata tashi daga gabansa ba, Ilham tace "Yaya Jalal san girman Allah dukda kace baka sona, dan Allah karkayi tafiyar nan, bana son ka tafi, Mummy ta shiga damuwa sosai bata iya cin Abinci se kuka takeyi dan Allah kayi hakuri nikaina zan shiga damuwa sosai, Jalal so fa ba karyane ba ni ganin gilmawarka a cikin gidanma ya isheni farinciki amma bansan dalilin dayasa kake kina hakaba "
Wani kululun bakinciki ya tokarewa Jalal rai a fusace yace " dalla malama ki tashi kibani guri, ai bakinku daya Mummy karkinemi ki rainawa kanki hankali, bana sonki bana kaunarki kifita daga rayuwata tun kafin inyi miki Illa, babu wanda ya isa ya hanani tafiya ba kukan Jini ba ko Hawayen karfe zatayi ba ruwana, ta manta sanda nake mata magiya take tafiya tana barina, lokacin danake matukar bukatar ta, kinga dalla bacemin daga nan ko in ballaki" yakarasa yana zazzare ido gaba daya jikinsa bari yake

"wai dan Allah wace irin zuciya ce da kai, baka yafiya baka mantuwa, koma metayi maka ai ita takawowaka duniya, tana sonka shiyasa bata so ka tafi, Yaya Jawwad ya dena zaman gidan nan saboda bayason ya dinga tuna zakayi tafiyarka ka barshi, kalli yadda Ilham take kan gwiwoyinta tana kuka amma kai ko a jikinka meye hakane?"
Kafe Jalila yayi da idanuwansa da ita kanta wani lokacin suke bata tsoro, gashi yakara hade rai sosai.
Wani bakinciki yakara tokare kirjin Ilham kamar zuciyarta ta fito waje.

A hankali yafara motsa baki yace
"Wallahi idan har banyi tafiyar nan ba to bana raye, ba ruwana da halin da wani ze shiga saboda babu wanda ya damu da halin da nake ciki" yafada yana kallon kwayar idon Jalila
Kawai sukaga Jalila tana dariya, wadda ke matukar kara mata kyau tace
"to shikenan Ai seka tafi in gani" ta mike tsaye takuma kallon sa ta kwashe da dariya seka dawo, karka fasa tafiya naga ta inda zaka tafi ai, kekuma Ilham na dawo koki dawo da abunda kika dauka kokuma inzo da kaina"
Kawai ta juya ta fice ta barsu a zaune suna mamakin maganar ta.

Ina yinku ABDUL JALAL group irin sosai din nan fa 😍😍😍 inajin dadin Comments dinku, kuna Comments kana karamin kaimi typing duk bayan kwana biyu, kuna bari ina lalaci posting duk sati 😜😜😜

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹

_ABDUL JALAL (2020)_

_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)

PART 2
_PAGE 3️⃣5️⃣88

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]






_MY FIRST NOVEL _

Mikewa Jalal yayi ze fice yabar dakin Amma Ilham ta mike ta sha gabansa
"Haba Jalal yanzu bazakaji magiyar
danake maka ba, dan Allah Jalal kayi hakuri, karkayi tafiyar nan, zan shiga mugun yanayi dan Allah Jalal, wallahi ina sonka,

Please Login or Register in order to submit comment