Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a hanyar shiga babban parlour, yace

"Yawwa Alhamdilillah, naji dadin ganinki a yanzu, zomuje kimin wani dan aiki"

Jalila tace
"to Yaya" yana tafe tana binsa a baya, ya shiga inda ake ta hada2 dafa Abinci, ya dakko wani kwando da manyan warmers akai da plates, da spoons da serving spoons, yabawa Jalila ta karba ta rike, shikuma ya dakko cartons na ruwa da lemuka, yace
"muje Bakinmu nasa akayiwa girki, dare yayi Abinci ya kare
" Jalila ba tace komai ba ya shiga gaba ta biyo bayansa, wani part din suka nufa, ita bata taba sanin da gurin bama, saboda parts din da suke bangare daya na estate din ma dayawa, tundaga waje harabar part din ake iya juyo hayaniya na tashi da dariya na 'yan maza, Yusuf ya shige gaba yasa hannu ya bude kofar ya shiga, ya juyo ya ce mata
"Shigo Jalila"
ba musu ta bishi da kayna a hannunta, kallo daya tayi musu ta sauke kanta, mazane sun kai su bakwai a cikin palourn, inma basu fiba, dan haka duk taji ta takura, kanta a sunkuye ta dan risina ta gaishesu, suka amsa mata gaba daya, dayan yace "A'a wannan kaman Hanan"
Taji muryar Abdallah yace
"Ba Hanan bace, sister dinta ce, Amaryar Ahmad to be"
Ahmad yace
"Tun dazu nake magiya ki fito in ganki kika ki, cikin sa'a sega Yusuf ya kawomin ke, amma dan mugunta ya hadaki da wannan kayan nauyin, memakon shi ya dakko"
Sunkuyar da kai Jalila tayi tana sauke kwandon hannunta, Yusuf yace
"Au ban maka abun Arziki bako? Nida yakamata ka godemin"
Ahmad yace
"nina isa in fadi haka, ince bakayi min abun Arziki ba, Kamin abun Arziki sirikina, wallahi Yusuf ji nake kaman a daura namu auren nida Jalila" ya dan kalli Jalila yace

My Queen yakamata muyiwa Daddy magana, yadda kikayi shar dake haka kamata yayi kawai muma ayi namu"
Jalila ta sunkuyar da kai cike da jin matsananciyar kunya.
Daya daga cikin Matasan yace
"dan banza uban zumudi, dole kayi zaman jiran shekara guda, kacigaba da lallabawa da Ameera, kokuma kayi biyu babu"

Gaba daya kunya suke bawa Jalila, tayi kokarin mikewa domin tabar dakin, ta mike kenan kawai idonta ya sauka ana Jalal da tunda ta shigo bata kula da shi ba, farar Jallabiya ce a jikinsa fara kal, sumar kansa ta sha gyara se sheki take, watanni hudu kenan bata ganshi ba, amma ya kara kiba, gaba daya ya tattara hankalinsa akan danna waya da yakeyi amma gaba daya idonsa akan Jalila yake, yana mata wani irin kallo da takasa gane na menene? Tuhumace, kokuwa meyake nufi?

Muryar Abdallah taji yace
"Queen kin san kuwa ranar dinner, Siyama zasuzo ayi dinner anan, ranar daurin aure in angama da nan, zamuje kaduna a can gidansu za'a daura namu"
Cikin sakin fuska ta juyo tace "Dagaske Yaya Abdallah, zanga Siyama? Rabon da in ganta tun ranar dana bar kaduna"

Ahmad yace "tasan Amaryar taka ne?"

Abdallah yace

"tabdijan Aminiyarta ce ta kuruciya, wadda take Jawa duka, kai Jalila ai an girma an dena neman magana, Siyama tana bani labarin wahalar da ta sha saboda ke, gaskiya badan badan ba sena rama mata"
Jalila ta dan zumbura baki sannan tace "Seku rama din ai"

Ahmad yace "Ka rama me? Munci bulus ko queen?" ta dan jinjina kai tana murmushi.
Koda aka bude warmers din nan, jallof couscous ne, ya sha nama da kayan vegetables, ta dan kalli Jalal ta kalli Abincin tasan Jalal baya cin Couscous kome zeci oho?
Kai bazakace Jalal yayi existing a dakin nan ba, duk hayaniyar nan da'ake yi, kala bece ba, shida kujerun gurin kusan daya, dan ko uffan baya cewa, ko abun dariya sukayi fuskar nan tasa murtuk take babu alamar wasa.

Kallon da yake wa Jalila gaba daya yasa ta tsargu har taso ta diricice, dan haka tace "seda safenku"
Ahmad yayi farat yace
"tsaya in rakaki zamuyi magana"
Yusuf yace
"Sena gayawa Amira, wannan rawar kan da kake yi"
"Karka fasa gaya matan"
Jalila ta nufi hanyar fita, dan gani take kaman Jalal ze iya tashi ya dizgata agaban mutane, tana kokarin wucewa tayi tuntube da kafar Jalal kasancewar ya mike kafafunsa kuma takusa da kafafunsa zata wuce, ga shi a rude take dan haka ta kusa faduwa, Allah ya temaketa bata fadi ba tace "Subhanallah" shikam Jalal ko a jikinsa dan ko kallon inda take beyiba, Ahmad yace
"Haba ya haka? Kana kokarin nakasa min mata, ka baje kafafunka akan hanya, at least yakamata ka bata hakuri"
Wani irin kallon baka isaba Jalal yayi masa ya maida kansa kan wayarsa ya cigaba da abunda yakeyi, ba tare da ya furta koda harafi daya ba Jalila tace

"No karka damu, base yabani hakuri ba, wannan ai besan yayi laifi yabada hakuri ba, da na fadi kafar zan take inga ta tsiya"

Kallon da Jalal yayiwa Ahmad ba karamin batawa Yusuf rai yayi ba, dan da'a waje ne wani civilian din yayi musu haka, seya gane shayi ruwane, shibe ma san daga Ina wannan mugun dan jiji da kan yake ba.
Abdallah yace
"Yusuf kabi a hankali, wannan da kake yabata hakuri, in yaso se ya hana abaka Auren nan, sirikin kane ka bishi a sannu, yayan Mahmud ne daze Auri kanwarku Nana, kuma babban Aminin Jawwad"
Yusuf yace
"wannan din"?
"Kwarai Shidin"
Jalila dai ta fice waje, Ahmad ya biyo bayan ta,
"Jalila wai me wannan mutumin yake takama da shine da yakewa mutane kallon basu isa ba??"
Jalila tace
"ba kallon mutane basu isa bane, haka yake, haka halayarsa take, ka lura ko Mahmud da yake kaninsa baya kulashi sosai, Yaya Jawwad da Abdallah kawai yake shiga shirginsu"

"Amma meye hadinki dashi da ze dinga kallonki haka?"
"Ba wani kallona da yake, kaika ga hakan, bani da Abunda Jalal ze tsaya kallo, A lissafin Rayuwarsa baya shiga shirgin mata, koda 'yan uwansa ne, muna gaisawane kawai saboda Aminin Yaya Jawwad ne"

"Kai queen, duk taurin kai da dagiyar namiji, baze iya dauke kai akanki ba, Amma me ya kai Jawwad abota da wannan bahagon mutumin". "Amintarsu hadin Allah ce"
"to shikenan, abar maganar ya gajiya,? naga kunshi ki yayi kyau, kamar in saceki in gudu"
Murmushi tayi tace
"Tabdijan kaida Daddy kuwa, inka gudar masa da 'ya"
Haka suka cigaba da hira, ya rakata har kofar part din Anty fido, sannan ya koma.
Tana shiga part din tabi ta babban parlour, bakowa a ciki ta nufi makwancinsu, tana shiga Hanan ta kalleta tace "daga ina haka?"
"Naje cikin gida ne, Yaya Yusuf yasakani aiki" Hanan bata kuma cewa komai ba, Maimakon su kwanta suka zauna sukayi ta hira, seda suka raba dare sannan kowacce ta nemi guri ta kwanta.

Washegari yakama ranar daza'a fara biki, ranar ne za'ayi kamu, iya mata da yamma, ko Angwaye bazasu gurin ba, iya mata ne a gurin kamun, , a wani katafaren dakin taro,
karfe biyar na Yamma, Amare suka iso dakin taron sanye da shiga irin ta fulani, Suka fito a ainihin usulinsu na fulani, 'yan matan ma, duk kayan fulani suka sa, se manyan iyaye da suka saka Atamfar anko na kamu, karshen haduwa kam sunyita ba' a magana, Sunyi kyau, Amara kirjin biki ma wato Jalila tayi kyau, ammata simple make up, gashi anmata ado da gashin kanta, sosai kayan suka karbeta, Anyi raye raye, anci an sha, an lika kudi, anyi hotuna da 'yan uwa da abokan Arziki, anyiwa Amare kamu, ba' a tashi daga gurin ba se karfe goma na dare, motoci sukazo suka kwashesu zuwa gida. A motar Ahmad Jalila ta koma gida, Jalila banda motar Jalal bata taba hawa motar wani ba se Ahmad, suna tafe yana yaba irin kyawun da tayi. Da suka koma gida ma a idon Jalal suka dawo, Jalila tayi kyau se hirarsu suke ita da Ahmad.



Tunda suka koma, Jalila bata tsaya tabi takan kowa ba, ta tafi part dinsu, Mummyn Hanan ce tazo ta samesu a dakin da suke zama, tace "Kuyi maza kuzo, Uwar mijin Nana tazo, kuzo muje ku gaisa"
(wato Salma uwargidan daddyn Hanan)
Jalila najin haka tace "nima bari in biku"
Ko kayan basu canza ba, suka bi bayan Mummy.
Koda suka shiga masaukin da'aka bawa Maman Mahmud kamshin turare ne ya gauraye dakin, tana zaune akan kujera, Jalal na zaune a kusa da ita, se wasu 'yan mata, da kuma Antyn Jalal tana salla, da alama hira sukeyi da Jalal, kamarta daya da dan nata Mahmud, haka kuma tana dan yanayi da Jalal din, suka shiga da Sallama, ta dago cikin fara' a ta amsa, Mummy Hanan tace "to Hajiya Salma ga yaran naki nan, sune Amaren"
Ta kallesu daya bayan daya, ta kalli Nana tace "ga sirikar tawa nan, ita nasan ta ai"
Sukayi murmushi suka durkusa suna gaisheta.
Jalal ya kalli Jalila tayi kyau sosai, Se murmushi takeyi, Hajiya Salma tace "Jalila baki sanni ba ko?"
Jalila ta Kalle ta ta jinjina mata kai, Hajiya Salma tace
"ni na sanki ai, kamar ki daya da mamanki, Amma kuma kusan duk kamaninku daya keda Amaren"
Jalal ya juya harshe sukayi magana da Hajiya Salma.
Nan ta shiga yi musu Nasiha akan Aure, da mahinmancin biyayyar Aure. Tana cikin yi musu ne Maama ta shigo, ta kawowa Hajiya Salma Abinci, nan suka hadu aka cigaba da yiwa Amare nasiha, Jalila kam ta kame tana sunkuyar da kai sekace itace Amarya. Jalal ma yana kusada Hajiya Salma ake musu wannan fadan, ko a jikinsa, be kula Jalila ba haka itama bata kulashi ba, tsakanin ta da shi se kallo.
Jin da Jalila tayi Hajiya Salma tana bayani da manyan bakake, Mummy Hanan ba ruwanta suka dinga yiwa amare fada, da koyar dasu zaman takewar Aure, ba shiri Jalila ta mike zata fice, Maama tace "Ina zaki kuma?"
"Amm... Zanje inci Abinci yunwa nakeji"
Sosai Jalila ta bawa Hajiya Salma dariya,
Tace
"dawo ki zauna, ina da magana dake dama" shiko gogan har akayi aka gama ba inda yaje yana zaune, daga karshe ma Abincin da aka kawowa Hajiya Salma ya zuba yafara cin Abunsa.
Yadda Jalal yake wa Hajiya Salma kamar irin dan Autan nan nata, kuma ga dukkan alamu tanaji dashi.
Seda aka gama yiwa su Nana fada, Aka sallamesu amma tace Jalila ta tsaya, suka tafi Maama ma komawa tayi, dan Akwai Ayyuka sosai a gidan, Maama na fita Jalal yabi bayanta, yace dan Allah yanaso a bashi tea.



Ya rage daga Jalal se Mummyn Hanan, Jalal da Hajiya Salma.
Hajiya Salma tace "Jalila me dana yayi miki ne?"
Jalila ta kalleta da alamar bata gane ba.
Hajiya Salma tace
"ABDUL JALAL mana babban dana kuma ďan Auta, kince bake ba shi, me yayi miki ne? Ba laifinsa bane, nasani laifin Mummyn sa ne, Amma kiyi Hakuri, Daughter Jalal yana jin maganar ki fiye da yadda kike tunani, Jalila Taimakon Rayuwar Jalal kike, Jihadi kikeyi, Allah ne kadai ze biyaki, karki duba abunda mutane zasu fada, kedai kiyi dan Allah, duk yadda muke da Jalal bana masa fada, idan nayi masa fada se yafara gaba dani ko wayarsa na kira baze daga ba, Amma da yake Allah ba yadda baya lamarin sa, kinga dake da Jawwad, musamman ke yanajin maganar ki, ban san me kikayi masa haka yake jin maganar ki ba" tai maganar cikin zolaya, sannaan tace
"Naji dadin ganin cigaban da aka samu a rayuwarsa ta bangarenki, ko danginsa babu wata wadda yake sakewa da ita kamar ke, yana jin maganar ki dukda shirin naku na Tom and Jerry ne"

Jalila ta sunkuyar da kai, Mummyn Hanan tace
"gaskiya nima yadda na lura da shi, baya son. Mutane sam, mussaman ranar da suka je mana can Kaduna, Amma dukda haka a nutse yake". Hajiya Salma tace
"Wallahi sister badan kaddarar Rayuwa da ta faru da shi ba, yarona mutumin kirki ne, ki tambayi Jawwad kiji, Wallahi banga abunda bazan iya mallakawa Jawwad ba saboda dawainiyar da yayi dashi ba"
Mummy tace
"ke kika haife shine?"
Hajiya Salma tai murmushi tace
"Dan ex-husband dina ne?"
Zare ido Mummy tayi "Haba dai, duk abun nan bake kika haifeshi ba?" sukayiwa Jalila nasiha sannan, Hajiya Salma ta sallami Jalila, sannan suka cigaba da hira ita da Mummyn Hanan.


Tunda Hajiya Salma tazo, duk abunda take bukata sedai ta kira Jalila, duk inda zatayi kuma seta kira Jalila, kamar dama can sun san juna, Mafi yawan tattaunawarsu akan yanayi na Rayuwar Jalal ne, Sosai Hajiya Salma taji kaunar Jalila a ranta, Jalila tanada biyayya, da girmama mutane, ga kuma namijin kokarin da take akan yaransu Jalal.




Washegari yakama ranar daza'ayi dinner, tun safe ake shiga ana fita a gidan nan, gida yacika da mutane,
Shabiyun Rana Siyama ta iso itads 'yan uwanta, Labari na ishe Jalila Siyama ta karaso aids gudu ta nufi cikin gidan tana zuwa suka Rungume juna, Maama tace
"Jalila kiyi a hankali, karki ji mata ciwo mana"
Jalila tace "Siyama ta, dama zan kuma ganinki?"
Siyama tace "gani kuwa kin ganni" Jalila ta janye Siyama, Zuwa bangaren Anty fiddo, Hanan Ma na ganin Siyama ta rungumeta itama tace "Na dauka tun ranar kamu zakizo, Amma shine baku zoba se yau"
Siyama tace "Ai muma munyi kamu da party a can ne, saboda wanda bazasu samu damar zuwa nan ba"
Suka gabatar da Siyama ga Nana, dan basu san Juna a zahiri ba, Amma sukanyi waya saboda Jalila,
"Nana tace, Sannu da zuwa Siyama, ya hanya?"
"lafiya kalau Nana, ya taro?"
"Alhamdilillah"
Suka zauna suka dinga hira, suka shantake a gurin, suka dinga hira suna tuna kuruciya da shiritar da sukayi, Nan Jalila ta dinga basu labarin Artabun fadanta da Jalal, har lokacin daya taba yi mata duren hayakin taba. Sunsha dariya, Nana sam bata san rashin jituwarsu ta kai haka ba, Amma bata gaya musu fadi tashin da ta dinga da kokarin ganin ya shiryu ba, har labarin su Hannah da Jeje bata gaya musu ba. Suka shantake suna ta dariya.


Anty Fiddo ta shigo ta samesu a zaune suna hirarsu suna ciye2, kaman karsu rabu, Anty fiddo tace
"waikuna nan a zaune, kamata yayi ku hanzarta ku fara shiri, ku tafi gurin kwalliyar nan, kar a bata lokaci" seda ta kai aya ta lura da Nana, taana ganin Siyama
"Tace Amryarmu, gaskiya Abdallah ya iya zabe, Jalila ke Alkhairi sanadiyar kawancenki da Hanan, mun gano 'yan uwanmu, kuma sanadiyar ki Abdallah yayi mata shima, Allah ya kaimu Aurenki da Ahmad"
Hanan tayi farat tace
"ba Ameen ba"
Anty fiddo tace
"Saboda me?"
"nifa bana son Auren ta da wannan Yaya Ahmad din wallahi, matarsa bata da mutunci, wannan Ameeran tab, ni wallahi bana son Auren su"
"ina ruwana da rashin mutuncin matarsa, dai dai da ita nake, ai dani ze zauna ba dake ba"
Siyama tace
"Nikam Jalila ina Jalal, ina son in ganshi"
Tsaki Jalila tayi tace "ina nasan inda wani Jalal yake"
Hanan tace "Karya takeyi, yana nan Haidar ya gayamin, suna tare"
Nana tace "Too Siyama kema kin san Jalal, ai dole ki ganshi, nasan watakila anjima yaje gurin dinner zaki ganshi"
Anty fiddo tace "kunga abar surutun nan haka, ku tashi ku fara shiri"
Haka su fara shirye2, karfe hudu suka tafi gurin kwalliya.



Karfe tara na dare Jalila tana tareda Amare an musu kwalliya me daukar hankali, kayansu iri daya, sea green din material, da takalmi da purse, Jalila kuma tasaka blue-black na material kaman yadda shine yazama ankon dinner, Tasaka bakin takalmi da jaka, jikinta babu mayafi, Su Jalila ne 'yan shigo da Amare, masu shigo da amare kowacce gefenta da namiji da, Amare da Angwaye, Jalila Ahmad ne a gefenta, suka shigo da Angwaye, ana musu hotuna tareda likin kudi, suka kai su har kan high table, nan aka tsaya aka fara hotuna, Ba zato ba tsammani Jalila taga Jalal, sanye da shaddarsa coffee colour, me tsadar gaske, ta sha aiki da bakar hula da takalmi sau ciki, tsinstiyar hannunsa dauke da wani dankareren Agogo, fuskarsa ba yabo ba fallasa, ya durkusa gefen Jawwad yana masa magana a Kunne, nan aka shiga hotuna 'yan uwa da abokan Arziki, Jalila anyi hotuna da ita ba Adadi, nan Hanan ta nunawa Siyama Jalal,
Siyama tace "Yadda Jalila ke masa rashin mutunci bazakace haka yake ba, hadadde dashi" sukayi dariya
ba karamin kyau Jalila tayi a idon Jalal ba, Amma ganinta ba mayafi yasa duk yaji ransa ya baci.
Nan aka fara gudanar da taro kaman yadda aka tsara, dukkan bangarorin sunyi bajinta gurin lika dukiya kaman ba'a san dadinta ba, Hajiya Salma ba'a barta a baya ba gurin yin wannaan hidimar, tunda ta hau kan stage Jalal ya fito ya dinga lika mata kudi, kamar be san ciwonsu ba. Aka dinga mata kirari, ko Mahmud da ta haifa bata masa likin da tayiwa Jalal ba, ta koma gefe, takira Jalila tasa me hoto ya dinga daukarsu hoto itada Jalila da Jalal.
Hakama Sunsha hotuna Jalila da Maama, Jalila tayiwa Maama likin kudi sosai ta dinga rungumeta suna hoto a wayar Jalila, kamar ba Maaman da take gallaza mata ba.
Lallai halayar Jalila daban take, sam bata riko.



Aka jima M. C ya kira Amare da Angwaye kan stage, suna dan takawa, yasaka wakar da Jalila ke matukar so, dan haka stage din nan ba kowa se Amare da Angwaye, Jalila ta fito, tafara Rawa itada Su Hanan Jalila Rawa take me cikeda daukar Hankali, ba wani girgiza jikinta take ba, Amma ta dau hankalin mutane, Ahmad ya fito ya dinga mata barin kudi, ana musu hotuna.
Jalal ya kai karshe a bacin rai, Ga jikinta ba mayafi, ga dinkin yayi fitting dinta, gata tubarakallahu tana da diri me daukar hankali bawata rawa take ba, juyi kawai take Amma Jalal ya kule musamman yadda Ahmad ke mata barin kudi, yana mata wani irin kallo, wayar Jalila ce tafara ringing dan haka ta sakko daga kan stage din ta fita daga hall din domin amsa wayar, tana fita Jalal yabi bayan ta.



Tofa Fans Oga Jalal ya dau Zafi, A tunanin ku mezeyiwa Jalila?
Nayi muku dogon typing dan haka ina bukatar Comments
ABDUL JALAL NOVEL FANS GROUP 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹 🌹
My Love for you is endless, daku da masu bina pvt da masu karanta littafin duk ina godiya Allah yabar kauna, ina sonku kaman yadda kuke nunamin kauna

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
πŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈπŸ–ŠοΈ

What's app only 07063065680.
Follow me onWatpad @Ayshercool7724
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹

*ABDUL JALAL*

_Story, writing and edited _

By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(π•Žπ”Ό 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 π”Ήπ•Œπ•‹ π•Žπ”Ό'ℝ𝔼 π”Έπ•ƒπ•Žπ”Έπ•π•Š, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 π•†π•Œβ„ π”Ήπ”Όπ•Šπ•‹ 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ π•†π•Œβ„ β„π”Όπ”Έπ”»π”Όβ„π•ŠπŸ’ͺ)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️

PART 2
_PAGE 4️⃣8️⃣101

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724



_MY FIRST NOVEL _


Daddyn Jalal ne a tsaye da yana rataye da 'yar karamar Jaka, da alamu zeyi tafiya ne, Mummy na kan three seater ta kalmashe kafa tana danna remote. Daddy yace

"wai dagaske deeja bazaki bikin nan ba?"
Ya tsina fuska tayi tace

"Nifa bana son yin doguwar tafiya inba a jirgi ba kasani, kuma me zanje inyi musu, banda jaraba ayi biki a inda suke sun kwasa sun tafi wata uwa bauchi biki, ko meye amfanin hakan oho?"

Daddy ya samu guri ya zauna yace
"deeja, in duniya da gaskiya be kamata kiyi haka ba, duk gudunmuwar da Jawwad ya bawa Rayuwar danki, ga tsawon lokacin da kika dauka kuna makotaka, ga harkar kasuwanci da kikeyi da mahifiyar yaron nan, sannan koba komai kema Mahmud danki ne, shima kodan shi bazaki ba? "

"daddy a dawo lafiya, ka musu Allah ya sanya Alkhairi in sun dawo na musu Allah ya sanya Alkhairi, bani da lafiya bazan iya zuwa ba, ka tabattar sakona ya isa gurin Jawwad"

Ta juya ta cigaba da danna remote, haka ya mike ya fice daga palourn tabi bayansa da harara.
Ya fita ba dadewa sega Ilham ta fito daga dakinta, tazo ta samu guri kusa da Mummy ta zauna. Ji tayi Mummy tana tsaki ta dan kalleta tace
"Mummy lafiya kuwa?"

"barni da abun haushi, daddy ze batamin rai, wai se in bishi bauchi gurin bikin nan, ta yaya zanje gurin da Salma zata, ana Auren danta inje, ai na gama zubewa, ba dan ita ba da kodan Jawwad senaje bikin nan, Amma saboda Salma da wannan banzar yarinyar bazani gurin nan ba, Amma bayan biki har can Abujan zanje gidan Jawwad in masa Allah ya sanya Alkhairi, yanzuma na bawa Daddy sako ya bashi, Amma ai naga ke kawar Nana ce, meyasa baki bisu ba? "

Ya mutsa fuska Ilham tayi tace

"Tabdijan akan me zanje, Ai daga baya na gane da hadin bakin ta Wannan banzar take son janye hankalin Yaya Jalal daga kaina, dan haka ba abunda zanje in musu, suje can su karata"
Haka suka cigaba da hirarsu, Ilham na kara kushe Jalila a gurin Mummy.





Jalila Tana fitowa daga hall din ta samu jikin wata mota ta tsaya tana waya, Ahmad ya kirata, tasa wayar a kunnenta tace

"Hello my, ina jinka" ba"a iya jin me ake cewa amma tace "Shikenan in an nagama zan maka magana se mutafi tare" ta dan kumayin shiru tace "A'a idan na koma gida zanci Abinci, bazan iya cin Abinci yanzu ba, in aka tashi zan maka magana"

Ta kashe wayar, tana juyowa taji gabanta ya fadi, Jalal ne a tsaya a bayan ta, ya kura mata ido ko kyaftawa ba yayi
Dan tsayawa tayi itama tana kallonsa, tunda yazo ko sannu bata hadasu ba, ba karamin kyau manyan kaya sukeyi masa ba, gashi gaba daya ya cika gurin da kamshin turarensa, tayi kokarin bin ta gefensa ta wuce, ya kara tare mata hanya, dagowa tayi tana kallonsa ya hade rai kamar be san meye dariya ba yace
" Zoki wuce mu tafi"

Tai masa kallon ban gane nufinka ba tace "Kamar ya, mu tafi ina?"

"ban sani ba, ki wuce mu tafi nace" yayi maganar cikin fushi"

Zumbura baki tayi, tace
"Wallahi ba inda zani ba'a gama ba" yasan halinta da taurin kai, dan haka yasa hannu ya janyo ta har tana kokarin faduwa saboda takalmin ta me tsinine, ba shiri tabi shi be tsaya da ita ko'ina ba se gaban motarsa, ya bude motar yace
"Shiga"
ta kalleshi, cikin muryarta me sigar shagwaba tace
"meyasa zan shiga? Ina zaka kaini kowa yana can ana abun Arziki"
"Wallahi in baki shiga ba zan sakaki da kaina"
Zare ido tayi ta kalli idonsa, babu alamun wasa a abunda ya fada tabbas ze aikata, ba shiri ta shiga motar, ya za gaya ya shiga ya kunna motar, yafara tuki cikin nutsuwa ya bar harabar gurin, yafara tukin kenan aka kirashi a waya, ya daga wayar yasa a hands free, da'alama abunda ya shafi

Please Login or Register in order to submit comment