Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

😍😍😍😍

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.
..🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹

_ABDUL JALAL (2020)_

_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)

PART 2
_PAGE 3️⃣1️⃣84

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]






_MY FIRST NOVEL _

Kallonsa Jalila take kaman wata sokuwa, ya daga kai yaga su Jawwad da Abba suna tahowa, yakuma durkusowa yace mata "Allah ya kaiku lafiya"
Hanan tana kallon abunda yake faruwa harsuka karaso inda motar take, Abba yayi musu nasiha tareda fatan suje lafiya, Abdallah ya shiga ya kunna mota, yafito da ita daga cikin gidan, Nana tace "Jalila dan Allah inkin tafi karki dade, zanyi missing dinki sosai"
"Bazan dadeba Nana, nima zanyi missing dinki" suka rungume juna sannan Jalila ta karbi jakarta a hannun Nana.
Hanan tazo bayan Jawwad ta wajen kunnensa tace "I love you Haidar, i wish to see you soon" ta juya ta shiga mota, murmushi kawai Jawwad yayi, Jalila ta bude mota ta shiga amma hankalin ta yana kan Maganganun Jalal.
Jalal yazaga sukayi musabiha da Abdallah yace "Allah ya saukeku lafiya, ya kiyaye hanya"
Suka amsa da Ameen banda Jalila da taketa zancen zuci. Abdallah ya kunna mota yafara ja a hankali Jalila tanata waigawa tana kallon Jalal harsuka bar layin, Hanan ta daki cinyarta tace "To ai seki dena kallon nasa haka"
dan hade rai Jalila tai tace "kamarya indena kallonsa? Wakenan?"
"Jalal mana, aishi kike kallo tukuna ma meya gaya miki ne naga jikinki yayi sanyi?"
"Bansaniba, niba shinake kallo ba"
Hanan tai dariya tace "Queen ba dai taurin kai ba, bakyason gazgata zuciyarki, ga abu a zahiri amma kinata wani basarwa"
"Ke dan Allah ki kyaleni Hanan"
Hanan tace "Na kyaleki"
Abdallah yana jinsu yai murmushi yace "Hanan kokece sirikar tamu ne? Keda Jalal kuke boyewa"
"Tab Allah ya kiyaye, bawani sirika, wadda ze Aura tana gidansu cousin dinsa ce Ilham"
Hanan tace "karya kikeyi, kefa kikace bazaki bari ya Auri Ilham ba"
"to dan ban bari ya auri Ilham ba kuma ni seya Aureni?.
Abunnasu na nema yakoma fada dan haka Abdallah ya shiga yimusu hira aka manta da wannan zancen, Jalila ta rarraba hankalinta me Jalal ya ajiye mata a cikin Al'qur'ani tsawon wannan lokacin bata taba ganiba? Sannan mezesa yace ze bar kasar nan haka taita zancen zuci, Hanan ta fuskanci Jalila nacikin damuwa, Amma taurin kai ya hanata yadda.
Nana taji babu dadi sosai da Jalila ta tafi jinta take kaman marainiya, Naja taje ta samu Maama ta gayamata abunda yafaru, Maama taimata alkawarin tasan matakin dazata dauka, zata kawo dukkan karshen wannan yaran, zatayi wa Abbansu Jawwad magana.
Jalila se kusan takwas na dare suka isa garin bauchi, wani irin katon estate ne, dake dauke da gidaje dayawa a ciki, kuma kusan duk irinsu daya, tundaga farkon estate din suke cin karo da sojoji, da sunzo wucewa Abdallah yake daga musu Hannu, wani gida suka nufa, duk gidajen da Jalila ta gani a estate din wannan gidan yafi shi girma, shima akwai sojoji abakin gate din, bude musu akai Abdallah yashiga sunata daga masa hannu, Abdallah ya tsaya suna gaisawa, suna masa sannu da hanya, daya sojan cikin gurbatacciyar hausar sa yacewa Hanan "Madam ba magana? Ko gajiyar ce?"
Hannaan tace "kai ba'a magana nagaji kam" dubawa yayi yaga Jalila a motar, kafin yayi magana Abdallah yaja motar zuwa makekiyar harabar dake cikin gidan, Abun yabawa Jalila mamaki bayan sojojin dake bakin gate akwai wasu a cikin gidan, Hanan tafara fita sannan Jalila dukda magariba tayi, amma ko ina hasken fitulu ne, Jalila ta bude motar ta sakko, ga mamakin ta gaba daya idan mutanen dake harabar gurin yadawo kansu, harta dan fara tsarguwa, Abdallah ya bude motar yana janyo kayansu.
Abdallah ina kasamo wannan kuma? Ko dama Hanan tanada sister ne? Suka dinga jerowa Abdallah tambayoyi, Hanan ta kalli wani soja tace Phillips ga kaya nan shigo dasu upstairs taja hannun Jalila suka shige cikin gidan. Gidan shiru se kamshin turare da Abinci dake tashi, gidan shiruu wani tangamemen palour suka shiga, tundaga palourn Hanan take kiran "Anty fiddo, kina inane?" wata matashiyar mace ce wadda bazatafi shekaru Ashirin da biyar ba ta fito tana cewa "Hanan wane irin kirane haka, Salla nakeyi ai yau kinzo kowa se san kin iso wannan ba.... Bata karasa maganar ba tayi shiru, ganin Hanan tareda Jalila, matar tace
"Hanan menake gani haka, ina kika samo wannan me matukar kama dake?"
Jalila tai murmushi tace "ina wuni Anty"
Hanan tace "daga zuwanmu kin isheni da tambaya, ina mutan gidanne?"
"suntafi shirye shiryen biki, anjima maybe kiga sun shigo" ta kalli Jalila tace "Sannu da zuwa baiwar Allah, shigo"
Hanan tace "aiba gurinki tazo ba, innancy tana dakinta ne?"
"Hanan ko kara babu, tana daki tana salla" Hanan taja hannun Jalila zuwa wata kofa, dakine me dauke da katuwar katifa da tv da bandaki da komai a ciki, gefe wata dattijuwace sanye da hijjabinta tana salla, daga imda Jalila take tana iya ganin dattijuwar fara ce tas daganinta kasan tana hutawa amma Jalila gani take kaman ta taba ganinta amma ta manta a inane.
Hanan tace "Shugabaa Inna salla ake tayi ne? Jalila ga toilet nasan zakiyi Alwala bari in dawo" Jalila tace to, koda Jalila ta shiga cikin toilet din shima ya hadu, kaman ba na tsohuwa ba, Jalila tai alwala ta fito harta tada salla tsohuwar bata idar ba.
Koda Hanan ta fito se tambayoyi suke mata ina suka samo Jalila, Hanan tace "Anty fiddo kimfiye tambaya wallahi"
Abdallah yace "kusan shekarunsu takwas kenan a tare, yarinyar da daddy yake gaya muku ce yayi ya mekama da Hanan, itace yace zekawow Inna taganta"
Wadda suke cewa Anty fiddo tace "Masha Allah, sekace wadda taimana maganin Hanan ce, kai amma Abdallah bantaba ganin wanda ba yan uwa ba masu kama kaman Hanan da wannan yarinyar ba, bari in kaimata Abinci masha Allah ashe itace 'yar daddy"
Jalila ta idar da salallolinta a lokacin tsohuwar ta kammala nata lazimin, kurii ta zurawa Jalila ido, Jalila ta idar tazo kusada tsohuwar ta zauna tace "inna barka da yamma" kasa amsawa tayi sedai kallon Jalila da takeyi, Anty fiddo ce tashigo tareda su Abdallah, Inna ta daga kai ta kalli Hanan ta kalli Jalila tace "Haba nifa imce, nasan Hanan bata da wannan nutsuwar, amma ko idona neke ganin ba daidai ba, kamar duk Hanan dince?" tsohuwar kana jin yadda take magana kasan bafulatana ce, hausarta bata fita sosai
Anty fiddo tace "daidai idonki ke gani, kinga me kama da Hanan ko? Ita daddy yake cewa ze kawo miki ki ganta ai"
Inna tariko Hannun Jalila tace "mairo ashe dama kina raye zankuma ganinki, baki ganeniba, hafsatunki cefa? Allah sarki mairo ina kika shiga tsawon lokaci bamganki ba" sosai tsohuwar ta rike Jalila tana kuka, saroro Jalila tayi tana kallon Inna, Hanan tace "kekam Inna wai har yanzu bazaki dena wannan abun ba dan Allah?"
Abdallah yace "Inna idan mairon takice haka zakiganta bata tsufa kamarki ba, wannan fa yarinya ce sosai, bakuwarmuce kamar da takeyi da Hanan dinki yasa Daddy yace ze kawo miki ita ya nemi alfarmar mahaifinta alfarmar mahaifinta ankawomiki ita amma kina kuka"
Goge hawayenta tayi tace "yi hakuri yarinyata, daga zuwanki zanmiki shirme, zauna kusada ni"
Anty fiddo tacewa "Inna bari muje taci Abinci se adawo miki da ita" inna tace "ita ya sunanta ne? Ko itama Hanan din ce" Abdallah yace "sunanta Jalila"
"Kai wannan sunan da wahalar fada, na dauka itama Hanan dince ko mairo" Anty fiddo tace "Jalila taho muje" Jalila ta mike suka fito,
Anty fiddo tace "Kiyi hakuri haka takeyi wani lokacin haka takewa Hanan ma, wani lokacin setayi ta kuka wai Hanan tana abu kaman kanwatta, kumafa mu bamu san kanwartata ba, bawanda yasan inda take wata kilama ta mutu, amma har yanzu inta tuna setaita kuka"
Jalila tace "Allah sarki, kinsan babu abunda yafi dan uwa dadi duk tsufansa duk yarintarsa"
"Hakane kam"
Sun karrama Jalila sosai sukayi dinner sannan Hanan takai Jalila masauki, Jalila tace "Hanan bari inwa Inna seda safe ko?"
Hanan tace "inkikaje bazatayi bacci ba kuka zata cigaba, ki kyaleta seda safe"
"to shikenan, amma Hanan meyasa duk gidan nan naku sojojine, koduk saboda babanane?"
"Aiba daddy ne kadai soja a estate din nan ba, sannan duk wanda kika gani a estate din duk family dinmune, kaso uku bisa biyu na mazan dake estate din naan sojoji ne shiyasa kikaga sojoji ko ina, yanzu gobe in Allah ya kaimu zan kaiki kigansu akwai yan mata kamanmu, amma basu san munzoba, da yanzu an cika part din nan, Inna itace tushen family din nan, duk yarantane da jikoki da yaran jikokinta, sekuma kanin mijinta shima ya rasu amma akwai yaransa shima da jikoki a cikin estate din nan, mijin inna ya rasu shekaru bakwai baya, amma bata tunanin sa kaman kanwar nan tata tanabamu labarin kanwar ta, babban dantane kawai ya san kanwartata, shima bashida wayo sosai lokacin amma haka wataran take birkicewa ta wuni kuka"
Jalila tai ajiyar zuciya tace "Allah sarki, tunda kika ga haka ba karamin shakuwa ne tsakanin ta da kanwar tata ba" sukayi ta hira sannan suka kwanta bacci, amma Jalila tana tunanin meyasa bata dakko Al'qur'anin nan ta taho dashi ba, tana son sanin me Jalal ya ajiye a ciki, ita tsawon lokacin da qur'ani yayi tareda ita bata tab ganin komai a ciki ba, to me Jalal yake nufi.

Nana duk gidan yamata ba dadi, se yanzu takejin akwai shakuwa sosai tsakanin ta da Jalila, Naja kam haushin kowa takeji musamman Nana, Nana tarasa mema zatayi taji dadi, ta dakko waya ta kira Jalila suka sha hira, bayan sungama waya da Jalila, wajen karfe shadaya Nana ta fara kwalemar dakinsu kaman yadda Jalila takanyi wani lokacin, ta hargitsa komai tana gyarawa, Ilham ce ta shigo dakin babu ko sallama Nana ta daga kai ta kalli Ilham tace "Ilham anya ba batan hanya kikayi ba yaukece a gidanmu haka, yaushe rabonki da gidan nan"
Ilham ta tabe baki tace "ba dole indena zuwa gidan nan ba na fuskaci anamin zagon kasa, dama mummy ce ta aikoni, tace ace tanason ganin Jawwad, naga bayanan, kuma bakowa a palour, kuma naji ance wannan yarinyar bata nan shiyasa nazo nan dakin, badan hakaba bazan shigoba"
Nana tace "nifa bangane mekike nufiba Ilham, wani irin zagon kasa akemiki hakane a gidan nan"?
"Haba Nana karki rainamin hankali mana, kema haushinki nakeji kun hada kai za'akwacemin Jalal"
"wai dawa kike ne haka kimin bayani dalla2, dawana hada kai za'a kwace miki Jalal din?"
"wannan tsinanniyar 'yar uwar taki mana, Kun hade kai zata kwace min miji"
"Wai kina nufin Jalila ce takeson Jalal kokuma yaya"
A fusace Ilham tace
"Nana nifa wannan maganganun nan naki batamin rai suke karayi, ta yaya zakidinga rainamin hankali ne Nana, kina nufin bakisan kulla2 datakeyi na kokarin rabani da Jalal ba, son Jalal takeyi kuma nida ita tace seta rabamu akanme zan kaunaceta"
Naja ce ta shigo dakin ta kalli Ilham tace "to yanzu tsakanin nidake watake rainawa hankali, waini narasa wannan shedaniyar yarinya ya take? Ba'agane gabanta ba'a gane bayanta, kekince tanason yayanki, ni daza'ayiwa baiko da Jawwad yace ita yakeso, katsam sega wata jarabbabbiyar tazo wai itama shi take so, nibana gane kan wannan yarinyar sekace dan wake Allah kadai yasan gabanta"
Nana tace "Allah me iko, Allah gatan bawa, kowa ya kwaso tarkacen tsiyarsa seta jibge akan marainiyar Allah, yanzu ke Ilham keda Jalila tace miki tanason JALAL iya sanina ko shiri basayi dashi, tayay zakizo da wannan maganar kuma yanzu?"
"Nana ke kanki yanzu haushin ki nakje kina rainamin hankali, ninaga abunda baki ganiba, sonshi takeyi kuma wallahi bata isaba"
Naja tace "Ai daga ita har Nanan bakinsu daya, kedai kiyi iyayinki ki kwaci Saurayinki dan wallahi bata isa ta auri Jawwad ba daga ita har wannan kodaddiyar yarinyar, banda zalama ki hada maza kice kina so duk jarabarta ai daya zata Aura"
Ilham tace "Aikuwa ba dai Jalal ba sedai ta Auri Jawwad dan bata isaba"
Nana zuba musu ido tayi, dan tarasa mema zatayi kotace
Naja tace "Ayi mu gani ai tafi dacewa da wanann dan shaye2, ba Jawwad ba kema banda jaraba mezakiyi da mashayi, ki kyalesu taje ta aureshi suta haukan tare"
"ke gyara kalamanki ni dan shaye2 nakeso, kika fadi bakar magana akan Jalal zanmiki ba dadi wallahi"
Abu yanemi yakoma fada tsakanin Naja da Ilham, Har Ilham ta juya zata fita, ta dawo ta nufi gaban drower da Nana ta fito da komai amma banda wani Dan karamin redbox, gaban drower taje tasa hannu ta dakko Al'quranin ta kalli Nana tace "Nana ya akayi wannan Al'quranin yazo gidan nan?"
Nana tace "Na Jalila ne lafiya?"
"Wallahi Nana ke makaryaciya ce, to wannan Al'quranin Jalal ne, kakrsa ce ta fanso masa a saudiyya, yanzu gashi a gurin ta, nace miki suna soyayya amma kin karyatani"
Nana tace "kinga Ilham wannan Al'quranin fa tun wani zuwa datayi akabata shi daga gidanku, kekika kawo kayan amma kina wani zance daban"
Ilham tace "to tunda kince nina kawoshi, to yanzu zan dauka, bekamata Abunda yake na Jalal yaje hannunta ba, kinsan son dayakewa Al'quranin nan kuwa?"
"Ilham karmu yi haka dake, ki bani inta dawo sekuyi da ita"
"Inta dawo kice meshi tazo ta dauka, inta matsu ta biyoni ta karba"

Bayan Jalila tagama waya da Nana, sunyi waya da Jawwad yagaya mata yakira Abdallah yace masa sun sauka lafiya sukayi waya, ta kira Abba ma ta gasheshi, Hanan taja Jalila suka koma gurin Inna,
Suna zuwa takuma rungume Jalila ta shiga yimata hira da labarai irin nasu na tsofaffi, Inna tanada abun dariya sun dade auna hira, zuwa jimawa 'yan mata da samarin gidan suka ding shigowa duk wanda yaga Jalila seyayi mamakin kamaninsu da Hanan kaman yan biyu, Hanan ta dinga zagawa da Jalila cikin estate din nan, suna da karamci kaman dama can sunsan Jalila tasamu kyakyawar karba, kwanan Jalila uku a garin daddyn su Hanan ya iso shida Mummynta, yaji dadin ganin irin karbar da'akayi wa Jalila, wannan karon sam Mummy bata nunawa Jalila tsana ba sema mamakin girman da Jalila tayi take.
Inna tacewa daddy "dan Allah dan nan kacewa baban yarinyar nan yabarmin ita, wallahi kamar mairona haka take, musamman intana dariya ko tafiya"
Daddy yace "haba inna, yazasu barmiki diyarsu, yanzunma sunyi kokari dasuka bari tazo nan" haka yaita lallaba Inna ta hakura.
Dukda kulawar dasuke bawa Jalila hankalin ta yana kan Jalal tanason sanin hali dayake ciki, amma bata san wazata tambaya ba.
Yau daddare Har sunyi shirin kwanciya Hanan tace "Jalila kina fama da damuwa a ranki, kuma nasan akan Jalal ne meyasa kika damu dashi haka, in ance kina sonsa kice karyane?"
"niba damu dashi ba, ni bantaba jin son Jalal a raina ba, ina tausayinsane kawai"
"karya kikeyi Jalila, kina son Jalal"
"Hanan keba wadda zan boyewa wani abubace ba, bantaba jin son Jalal ba"
"Naji bakyason Jalal, amma mekikeji akansa?"
"Ina tausayinsa ne kawai, dakuma kasancewarsa da Abu mafi soyiwa a gurina wato Jawwad, ina tausayinsa ne da son ganin yazama mutumin kirki saboda Jawwad Hanan koke kikaji labarin rayuwar Jalal zaki tausaya masa"
Nana Jalila tagayawa Hanan komai na labarin Jalal, har kokarin da tayi na ganin an kama oga KB da Jeje, dakuma abunda Jalal yagaya mata lokacin dazata taho
Hanan jikinta yayi sanyi matuka sannan takara jinjinawa Jalila da wannan namijin kokari datayi da sa kanta a hatsari a boye ba tareda kowa yasani ba
Hanan tace "gaskiya Jalal ya cancanci a tausaya masa, Amma kina ganin kowane ze iyayiwa Jalal abunda kikayi masa, Amma tsaya kinason sanin me Jalal ya ajiye miki a Alqur'ani"
"tunda muka taho nakeson Sani"
"yakamata musani, kira Nana a waya kiji in Alqur'anin yana nan ta duba mana"
"Ai in banda ke seshi Jalal ba wanda yasan me nayi"
"eh ai bazata gane ba"
Jalila ta amince ta kira Nana, seda suka gama hira da Nana, kafin Jalila ta tambaya Nana tace "Baby Ilham fa taga Alqur'anin ki wannan Jan, yau inayimana gyaran daki tazo, tace wai na Jalal ne, kakarsa ce tabashi ya akayi yazo gurinki tace inkin dawo kisameta ki karba"
A fusace Jalila tace "What!!!?

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹 🌹

_ABDUL JALAL (2020)_

_Story and written by_
AISHA HUMAIRA (daddy's girl)

PART 2
_PAGE 3️⃣2️⃣85

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]






_MY FIRST NOVEL _

Jalila tace "Yasalam, Nana kiname Ilham zata shigo har cikin gidan nan ta daukarmin abu natane? Meya kai hannunta kayanmu harta daukarmin abu"

"Jalila Al'qurani fa ba Novel bane ko littafin hausa da zan kamata da kokawa in karba, gyaran daki nakemana tashigo ta ganshi ta dauka"

"Nana kingama dani dakika bari ta tafi dashi, amma tunda tace idan na dawo na je karba ki gayamata ta saurari dawowarta wa, tasan karona da ita ba dadi, zanzo in karba idan bata bayar dan Allah ba zata bayar dan dole, karma kikuma tada maganar tabaki zan dawo in karba, banda Jahilace me zatayi da Al'qurani metasani aciki? Inma tasani bashida amfani a gurinta ai"

"To nidai Allah yabaki hakuri, ni bayan haka wasu maganganu tazomin dasu dasam ban gane inda ta dosa ba?"

"Kamar yaya?" Jalila ta fada a kagauce

"Nikam Baby meye hadinki da Jalal ne?"

"Wane irin tambaya ne wannan Nana?"

"Jalila inkinga rashin mutuncin da Ilham ta dingayi a dakinmu sekinsha mamaki, tana gayamin wai na hada kaidake zaki kwace mata Jalal, wai taga abunda ban ganiba, Kina son Jalal ne, Naja tazo suka hadu sukayi tayi, ni abun yabani mamaki iya sanina ko shiri bakwayi dashi amma maganganunta sun ban mamaki "

Jalila tayi ajiyar zuciya tace
"Nana kyale ta aikinyi ne bata dashi, kinsan tun asalina yarinyar nan batayi min ba, shiyasa take neman masifa, nime zanyi da wani Jalal, ai Jalal se ita makakkiya itama din ba Auren ta zeyiba, ki manta da ita zan dawo ai daidai nake da ita ai"

Nana tace "Hmm Jalila kenan, inaji kaman kina boyemin wani abune, amma inba rami meyakawo rami? Shikenan dai sekin dawo din, ki gaida min Hanan dan Allah 🙏"
Nana ta kashe wayarta, Jalila ta kalli Hanan a salube,
"me Nana take nufi?" dan daga mata gira Hanan tayi tace
"Queen kenan, naga kin damu da abunda Ilham tayi, amma keda bakyasonsa meyasa kike son abunda yafito daga hannunsa haka har kikejin babu dadi?"

"Hanan bansan mezan gaya miki ki yadda dani ba wallahi, Hanan Al'qurani abune me girma, sannan inason sanin meye Jalal ya ajiye tsawon lokaci ni banganiba, sannan muddin ina raye Wallahi sena nunawa Ilham iyakar ta"

"to meye na wannan tada jijiyoyin wuya haka easy queen i know you can do it, amma meye next plan dinki akan Jalal, kina ganin tafiyarsa Dubai akwai Alkhairi kuwa?"

"To yatafi uwar Dubai mana, daga nan yatafi bangon duniya idan yanaso? Ke nagama abunda zan iya akansa kowa tasa ta fishsheshi, dama yace ina takuramasa kinga se yaje yayi abunda ya gadama, nima takaina nake, yatafi bayan duniyama yaje ya bude gidan giya in yanaso" takarasa fadin haka tana kokarin kwanciya
Hanan tace "karya kike tawajena, nasan halinki kaf Jalila yanzu kina jin wani abu ze sameshi zaki kuma tashin hankalinki, kya gama zagaye zagayenki ne"
Banza Jalila tai mata ta ja bargo ta shige, Hanan tai murmushi itama ta kwanta.

Jawwad yaje kiran da Mummy take masa, amma ya lurada wani kallon banza da Ilham take masa bebi takanta ba ya durkusa ya gaida Mummy dake zaune a palour,
Har kasa ya durkusa suka gaisa, Mummy tace "yawwa Jawwad dama nace kazone saboda Jalal, inason ganinsa amma nasan nidashi bazezo kiran danake masa ba, dan Allah Jawwad ka dinga yimasa fada, sati me zuwa daddynsa zezo akwai maganar danake so muyi nida shi da babansa, dan Allah idan daddynsa ya dawo zanmaka magana inaso ka kawomin shi "
Jawwad yace
"insha Allah Mummy zan masa magana, acigaba da hakuri ana masa Addu'a Insha Allah komai ze wuce, Alhamdilillah yanzu yafara rage wasu abubuwan"

"Hakane Allah yasa hakan nima ina masa addu'a"
Yatashi yai sallama yafita, Ilham tayi tsaki tace "Nifa Mummy gani nake wannaan Jawwad din ke kara ziga Jalal yake wani rashin mutuncin yake kara kina"
"Kinga nidai ba wannan ba, kokarina kawai inga abunda na shirya ya tabatta akan auren nan naku, idan kika matsa kika nuna bakyason Jawwad kinsan baze taba aurenkiba ko? Dan haka kishiga hankalinki"
Ilham ta zumbura baki ta tashi tabar palourn.

Zaman bauchi ya karbi Jalila, tayi kalau da ita, kusan koda yaushe tana tareda Anty fiddo kokuma gurin inna, susha hira taci dariya, gashi cousins din Hanan suma 'yan shaftane mazansu da matansu, haka ake zuwa a cika babban palourn gidan aita wasa da dariya, samarin gidan da yawansu suna suna son Jalila amma fafur Hanan tace, ai Jalila tanada miji. akwai wani cousin din Hanan yusuf akayi bikinsa, komai da Jalila akeyi, kaikace 'yar gidance dama can sunsanta, sunajin tsoron yusuf sosai saboda baya wasa ma sosai, anan gurin babban abokin ango ya like yace shi nan duniya Jalila yakeso, Yusuf yaji dadin hakan, dan haka yace "Aitunda daddy yace da Hanan da Jalila duk' ya'yan sane, shima da Jalila da Hanan duk kannensa ne, ya yaba da halin Jalila dantafi Hanan nutsuwa"
Bayan biki yusuf yasamu daddyn Hanan, yagaya masa Abokinsa Ahmad yana rikon 'yar baba
Daddy yai murmushi yace "indai' yar baba ce inta amince sannan kun cika ka'idojinmu ai semu duba inkun cancanta abaku semu baku"
Yusuf yace "daddy kenan indai ana sanmu ai zamucika dukkan sharudanka" daga nan sukayi ta hira daddy agaban Mummy akayi tace "Amma danayi murna, dan Ahmad mutumin kirki ne zataji dadin zama dashi, amma ina tunanin yadda zata zauna da matar Ahmad, kasan 'yar taka bata da hakuri' ya'yannak ban san wadda tafi wata hakuri ba"
Daddy yace "Ai indai tana sonshi lafiya kalau zasu zauna, inmuka koma zanyiwa Abbanta maganar, indai basuyiwa wani Alkawari ba, Zanbawa Ahmad"
Yusuf yaita godiya kaman shi za'a bawa.

Daga Jalila har Hanan basu san me akeyiba Yauma, an taru a palour ana hira da daddare Daddy yake cewa abashi list din sunayen wanda

Please Login or Register in order to submit comment