Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a duba in jininsu zeyi a samata"
Da sauri Maama tace "Wane Jawwad din? Jawwad yana Abuja ya samu Aiki ai, nikam Yaya mairo ga wannan" tasa hannu a Aljihu ta dakko kudi tabata sannan tace "ga wannan ku sai magani, zan koma gida magariba tayi, se na dawo dubiya, Amma yakamata kunemo wanda yake da alhakin cikin nan, yazo ya dauki nauyin ta, se anjimanku"
Maama ta juya ta fito daga ward din, tana ta tunani tareda mamaki, da kyar Maama ta kai kanta gida, saboda tunani da Mamaki, da tuno marin da tayiwa Jawwad saboda Naja se taji gaba daya jikinta yayi sanyi.

Haka ta koma gida jiki a sanyaye, tunda ta koma take tunani, Nana ta lura da Yadda Maama jikinta yake a sanyaye dan haka taje ta sameta a daki take tambayar ta "Maama wai me yake damunki ne? Tukuna ma ina kikaje?"
Dan shiruu Maama tayi, sannan tace "Nana naso inyi ganganci da rayuwar dana"
"gangancin menene?"

Nan ta kwashe komai ta gayawa Nana, Nana tayi murmushi tace

"Allah sarki Rayuwa, Maama kinga wannan abun to izina ne a gareki, Allah yasa kar alhakin marainiyar Allah ya kamaku, kunsaka Jalila kuka ta zubda hawaye ba a dadi, ku zageta ku mata cin mutunci, ku mata gori amma se gashi su sunyi Abun kunyar da 'yar arnan ba tayi ba, Maama lokaci yayi da yakamata ki gane su waye ke kaunar ki, Yaya mairo' yar uwakki ce amma abun hannun ki takeso, ki duba irin biyayya da Jalila tayi miki tsawon lokaci, duk fitsararta da kuke fada, ke dai bata taba yimiki ba, se dai Yaya mairo, Maama a ci zarafin iyayen mutum dacin abun ya wuce yadda kike tunani, kun cutar da ita gaskiya, fatan Allah ya yafe muku, yanzu seki gane, Ummi da take ba musulma ba da farko, tayiwa 'yarta tarbiyar da wanda aka haifa a musulinci bata yiwa' yatta ba, Allah yasa hakan ya zama izina a gareku"
Maama kasa cewa komai tayi, se jujjuya maganganun Nana da takeyi, tabbas Maganganun Nana gaskiya ne,
Nana tace "Maama bari inje daki inada Assignment da zanyi"
Gyada mata kai kawai Maama tayi, Nana kuma ta fice, koda taje dakinsu Jalila tana kwance idonta a rufe, kaman me bacci, amma ba baccin take ba, tunanin abubuwa da dama ne ke zagayawa a cikin kwakwalwarta.

Daddy yakasa samun sukunibda abunda ya faru, gaba daya hankalin sa yaki daidaituwa, yarasa maganar wa zebi, ta Jalila kokuma ta Wannan yarinyar, Amma yakasa bawa kansa amsar wani tabacci Jalila take da shi akan Jalal, Mummy ta lura da yadda daddy ya dami kansa dan haka tace

"Ni dai a ganina wannan yarinyar da gaske take, ba'a shedar mutum, shiyasa nake son mu aurar da Jalal, shekarunsa ya kai ya ajiye iyali, ita kuma wannan yarinyar da tazo da wannan maganar, indai da gaske take, a lallabata abata kudi tayi hakuri"

"bana tunanin Jalal ze aikata haka, kuma tunda Jalila ta bada sheda akan Jalal, abun dubawa ne, amma yazama dole in bincika, lamarin yaron nan na ma rasa yazanyi, Allah ya shiryamana zuri'a"
Dadd yasa hannu ya dau wayarsa ya kira Jalal a waya, seda ta kusa katsewa sannan Jalal ya daga, koda ya daga ma beyi magana ba, shiru ya gudana na wani dan lokaci sannan daddy yace "Jalal kana jina?"
"Ina jinka daddy"
"ya kake ya aikin kuma?"
"lafiya kalau Alhamdilillah daddy, kana Nigeria kenan?"
"Eh ina nan, nakira ka ne, ina so muyi magana"
"ina jinka"
"Wace ce Hannah?"
Gaba daya Jalal ya manta da wata Hannah a rayuwarsa, Amma ya maze yace "Ban Santa ba"
"Jalal ban sanka da karya ba, wannan yarinyar itace kwanaki tazo min da waccan maganar, wannan karon tazo min da maganar wai tana dauke da ciki kuma nakane, Amma Jalila ta karyata ta, sannan tacemin Yarinyar tana da matukar hatsari ga rayuwarka, kamin bayani "
Ba abunda ya farantawa Jalal rai sama da jin batun Jalila ta kare shi, duk da furucin da tayi na bashi ba ita, daddy yace" Jalal ya naji kayi shiru? "
"to me zance maka daddy? Duk hukuncin daka ga dauka akaina dai2 ne, inma ka yadda gaske ne ko karya, dan Allah ni ku kyaleni hankali na ya kwanta, ina jin dadin zamana a inda nake karku daga min hankali"
"Amma Jalal meye hadinka da yarinyar nan har take bibiyar ka? Tana ikrarin zata kai kararka"
"Daddy in dai har bana nan, a bayan idona yarinyar data tsaneni zata bada shedar kirki akaina me kake so ince maka, kana so inta rantsuwa ne seka yadda dani? Kasan ba haka nake ba, Idan bata kai karata ba ni zan dau mataki akanta"

"Amma meye hatsarin yarinyar ga Rayuwar ka? Kamar yadda Jalila ta fada?"
"ka tambaye ta mana, tunda a bakinta kaji"
"Jalal yaushe zaka dawo?"
"ba yanzu ba, se nan gaba, nifa zamana anan yafi min zaman gidan nan, da za'adinga takura min"
"to shikenan tunda haka kace"
Haka sukayi sallama ya kashe wayar.

Mummy tace "wai nifa nakasa gane wannan maganar, ita Jalila wacece dinsa da za ta fadi abu ka yadda, ya akayi tasan abunda mu bamu sani ba akan danmu, haka akeyi?"
Murmushi daddy yayi ya dan kashe mata ido yace "haba deejat to meye a ciki? Kin samu me kulamiki da son, you have to thank her, har gida tazo dan kare shi"
Kara kunna Mummy yayi, dan haka ta tashi fuuu ta bar masa dakin.

Ilham tayi safa da marwa yafi sau Ashirin a dakinta, tana son ta tabbatar da Hannah dagaske take koda wasa, yanzu abun ya kuma kwabe mata, da ta manta da batun Hannah, amma yanzu yakin ya kuma zame mata biyu, ga Jalila ga Hannah, da tana tunanin tayi maganin Jalila, tunda tayi mata makirci a gurin Mummy, "Amma Jalila nan naci ne da ita bata da zuciya, shegiya se nayi maganin ta, sena kuma kunna mata wata wutar, to amma in dagaske Jalal yayiwa Hannah ciki fa? Da sauri tace" kai karyane, da Jalila yayiwa Hannah ciki da yanzu wani zancen ake ba wannan ba, karya takeyi"
Ilham ta fito daga dakinta har tana tuntube ta tafi daki Mummy, tana zuwa ta tarar Mummy ta cika tayi fam, fuskarta sam babu walwala, Ilham taje ta zauna a kusa da Mummy tace
"Mummy lafiya kuwa?"
"ke rabu dani, ni zancen wannan yarinyar mana, gaba daya daga Jalal din har ubansa naga hankalin su ya karkata kan wannan yarinyar Jalila, ga itama wannan wadda tazo din da wannan maganar cikin"
"mhmm wallahi Mummy in bakiyi wasa ba yarinyar nan se ta hana Jalal din ma shigowa gurinki, ta ne Santa shi dake, meye nata na sawa anema masa aiki a nesa? Kuma ga daddy yafara biyewa maganganun ta, wallahi Mummy da sannu zata janye miki shi gaba daya"
Mummy ta numfasa tace "ni Ilham gaba daya kaina ya kwance akan lamarin Yaron nan, narasa yadda zanyi"
"to Mummy kiyiwa daddy maganar, ayi mana Auren mana, saboda ayi maganin abun, tunda har ya fara bin mata"
"
A fusace Mummy tace" Ke dan Allah ki rabu dani, kina gani ba irin kokarin da banyi ba, Amma abu ya ga gara, ni ki kyaleni nace ki bani lokaci, sena fara shawo kan matsalar, ni na miki alkawarin Auren nan, ki karamin lokaci in gama da wannan matsalar mana"
Ilham ba tace komai ba ta mike ta bar dakin, tana fita tayi kwafa tace "Wallahi zaki gane kuskuren ki Mummy, zanyi maganinki, sena Auri Jalal din na mallake shi, ke da shi sedai kallo"



Amin Afuwa nayi busy sosai,
Gashi nan ba editing

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

*ABDUL JALAL*

_Story, writing and edited _

By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(π•Žπ”Ό 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 π”Ήπ•Œπ•‹ π•Žπ”Ό'ℝ𝔼 π”Έπ•ƒπ•Žπ”Έπ•π•Š, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 π•†π•Œβ„ π”Ήπ”Όπ•Šπ•‹ 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ π•†π•Œβ„ β„π”Όπ”Έπ”»π”Όβ„π•ŠπŸ’ͺ)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️

PART 2
_PAGE 4️⃣4️⃣97

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724



_MY FIRST NOVEL _

Shiru Jalila tayi ta kalli kayan daya ajiye mata sannan tabi bayansa da kallo har ya fice daga gate, din shiru tayi ta tafi tunani, Ahmad yace
"my queen, meya farune?"
Da sauri ta dawo hayyacinta tace "bakomai fa"
"Amma waye wanan?" ya tambayeta yana me kureta da ido, ta dan sauke numfashi tace "Yaya na ne"
"Yayanki queen, ba Jawwad ne kawai Yayanki ba?"
"Abokin Yaya Jawwad ne, dan haka Yayana ne kawai"
"Amma babu wani abu a tsakanin ku kuwa?"
"Meyasa kake min wannan tambayar? Ko baka yadda dani bane?"
"Ahh haba waneni ince ban yadda da gimbiyata ba, ina so ne in tabattar da abunda ke tsakaninku, dan da idonsa yana shaye2"
Ba karamin haushi maganar Ahmad ta bata ba, kenan shima yanayi, in ba yanayi ba, ba abunda idon Jalal yayi dayake nuna yana shaye2, dan haka tace
"baya shan komai, kawai bashi da son magana ne, baya kula mutane"
Kyaleta Ahmad yayi yaga alamar bata son zancen suka cigaba da hira, Jawwad ne ya fito ze wuce su Jalila ya tsaya suka kuma gaisawa da Ahmad dayake dazu sun gaisa, Jawwad yace "to sirikina zan iya ce maka se anjima, ni zan tafi kai Jalal airport ne"
Da sauri Jalila tace "Ina zashi?"
Jawwad yayi murmushi yace "Aiki mana, an tura shi Lagos, se lokacin biki inaga ze dawo, bari inje karyai ta jirana, kin san baya son jira, se anjimanku" Sukayi sallama da Ahmad ya fita.
Ahmad ya maida idonsa kan Jalila yace "Gimbiya naso a haďa bikin nan hada namu, na kagu in mallakeki"
Murmushi kawai tayi amma hankalinta baya kansa, tanata zancen zuci ne, dayaga haka yace "queen naga kaman Akwai abunda yake damunki, bari in tafi semunyi waya"
Ta mike ta rakashi har bakin gate sannan ta dawo ta zauna akan kujerun tana nazari
"At least yakamata ace sunyi sallama da Jalal, tayi masa nasiha, Amma bata tunanin zata iya kuma rabarsa ba saboda mahaifiyarsa.

Jawwad ya ga sam fuskar Jalal a daure take, babu alamar walwala ko fara'a, Jawwad yai masa magana yafi a kirga, amma ko daya be bashi amsa ba, dan haka ya kyleshi suka cigaba da tafiya a haka kaman kurame.

Gajiya Jalila tayi da zaman tunanin ta mike ta tafi cikin gida, Nana tana zaune a palour suna waya da Mahmud,
"Nana waike dan Allah ba kya gajiya da wannan wayar ne? Kuyita surutu tun ana fadar gaskiya se an koma fadan karya"
Nana taki kula ta seda ta gama wayarta sannnan tace
"waike Baby an gaya miki kowa irin kine me tsarin tsiya, ke yadda ba kya son yawan waya kowa ma hakane, ai a rana inji muryar Mahmud sau hamsin bazan gajiba, musamman mu da muke distance relationship, ai Ahmad din nan ma ban wani yadda kina sonsa ba"
"Inasonshi sosai, amma hakan bashi ke nufin a dinga uzzuramin da surutu ba"
"Hajiya Jalila, kyaji da shi dai"
Hanan ca ta kira Jalila a waya, ta daga tasa a kunnenta
"hello Baby, 'yar uwata rabin jikina ashe Family dinmu daya Baby? Narasa inda zan sa kaina dan farinciki, dazu Abba yake gayamin kuma wai an kawo kudin Aurena da Haidar, Baby na rasa me zanyi dan farinciki"
Murmushi Jalila tayi tace "na riga ki ji ai, kiyi Azumi ki godewa Allah"
"queen na rasa inda zan saka raina dan farinciki, daddy yace zasuzo karbar kudin Nana, narasa yadda zanyi dan murna"
"haka Al'amarin ubangiji yake Hanan, yana juya komai yadda ya so"
"Hakane Queen, amma naji haushi da baza'a hada da nakiba, ni ina Jalal ne ma?"
"yaje interview din nan ai, an turashi lagos zeyi wata uku"
"Allah sarki bawan Allah, wallahi Jalila bana kaunar Aurenki da Abokin Yaya Yusuf din nan, in duniya da gaskiya Jalal ya kamata ki Aura"
Wani dogon tsaki Jalila tayi ta kashe wayarta, dan bata son Hanan ta bata mata rai.
Jalila ta mike har zata bar palourn taga Maama tazo ta wuce kitchen, gaba daya Jalila bata jin dadin yadda kowa ya fita harkar Maama, dukda abubuwan da Maaman tayi mata, Akwai lokutan da ta kyautata mata, dan haka taga be dace ta mata hukunci da laifin da take mata ba, dan haka tabita kitchen din, Maama na kokarin kunna gas Jalila tayi maza taje ta karbi lighter tace "Maama kawo in kunna miki, me zaki dafa?"
"barmin Abina zanyi"
"A'a Maama, tunda ba abunda nake ki barshi in dora miki"
Jalila ta karbi lighter ta kunna gas, dan jimm Maama tayi tana Kallon Jalila, yadda Jalilan ke Acting kaman Maama bata taba yi mata wani abu na bacin rai ba.

Jawwad suka isa airport yayiwa Jalal Sallama amma ya amsa masa a ciki, sam baya walwala, yasan halin Jalal baya son takura, tunda be niyyar gaya masa meke damunsa ba, ya ja Akwatinsa yayi gaba yabar Jawwad.
Haka Jawwad ya taho yanata tunanin me akayiwa Jalal yake wannan bacin ran haka?

Bayan Jalila ta gana yiwa Maama girki, ta koma daki, ta dauki Alqur'anin nan tana ta jujjuyawa, Kamshin turaren Jalal yakeyi, hakama dan teddyn ta, tasa hannu ta ta dinga duba Alqur'anin nan page by page, amma sam bata ga komai a ciki ba, kodai Jalal dama yana son raina mata hankali ne kawai?
Shiru tayi ta tuna yadda taga yana yinsa bayan ya gansu tareda Ahmad, Fuskar nan tasa a daure babu alamun sassauci, tayi shiru ta cigaba da zancen zuci, ;yanzu ze tafi lagos bashi da kowa a can, babu me kula dashi, Allah kadai yasan meze aikata,
"kinfi so in cigaba da shaye2 na ko? Ke Garkuwa ce a gareni" ire iren wannan maganganun nasa da Maganganun Antynsa da take gaya mata tabata amanar Jalal ne yasa take tunanin Anya hukuncin data yanke yayi dai2 kuwa?
To Amma nikuma mutuncina fa? " gaba daya ta rasa me yakamata tayi? Yanzu tana gaya Hanan, tasan Hanan zata canza mata magana tafara kawo wani abu daban, dan haka tabar Abun a ranta ta cigaba da Yiwa Jalal Addu'a.

'yan kwanakin nan sam Abba ya dena shiga harkar Maama, har gara Jawwad ma yana zuwa gaisheta, Nana kuwa seda Jalila tasata a gaba ta nuna mata be dace ba abunda take yiwa Maama, wannan abunda yafaru tsakanin ta da Abba ne da kuma' yan uwan ta, sannan ta samu Nana ma take shiga sabgar Maaman, Abba ya gayawa Maama ranar Lahadi zasuyi baki, za'a kawo kudin Auren Nana, abakin su Nana taji batun haduwa da 'yan uwan Abba a Bauchi, ba tayi mamaki sosai ba jin ance su Hanan' yan uwansu Abba ne ba, sakamakon matukar kamannin dake tsakanin Jalila da Hanan, sedai taji haushin rashin sanar da ita da Abba beba.

Tun ranar Juma'a suke shirye2 domin bakin daza'ayi, Jalila ce jagorar girke2 da shirin yadda za'a karbi baki.
Gefe guda Jawwad yana ta shirye2 Ranar litinin shima ze tafi gurin nasa Aikin, ba karamin kulawa Hanan take bashi ba, da soyayya da kuma shagwabarta, yanayin yadda take nuna yarinta a wasu bangaren ba karamin birge shi yake ba.

Kamar yadda aka saka ranar lahadi daddyn Hanan yazo Kano aka karbi kudin Auren Nana, itama lokaci dayane dana Jawwad dakuma Abdallah Yayan Hanan, ranar har mutan bauchi seda sukazo garin kano karbar kudin, da kuma kara taya juna murnar haduwar su a matsayin 'yan uwa. Jalila taji dadi da akazo hadda Hanan da Mummynta, Maama seda ta sha jinin jikinta ta raina kanta ganin manyan mutanen da sukazo gidan, Abun Arziki ya hadu dana Arziki, dangin Su Jawwad dana Su Jalal, Ranar anci ansha, kai ka dauka bikin Aure akeyi rana ce me matukar tarihi da wannan Ahali bazasu manta ba. Jalila sam bata samu kebewa da Hanan ba, saboda Hanan na manne da Jawwad, sam bata jin kunyar kowa take nuna masa soyayya.
Mummyn Hanan se mita take tace "Ni gaskiya naso a hada abun nan hada na Jalila, in aurar da 'ya' ya uku, amma in shirya da kyau, amma bakomai anata se nafi shiri ko Jalila?"
Ita dai Jalila sedai tayi murmushi ta sunkuyar da kai.
Duk yadda Maama take jin kanta take kuma jin haushin Auren Hanan da Jawwad boyewa tayi, Saboda sam bata da makusa, 'yar dangi ce, kuma' yar uwar dan tace, tana da kyau dai2 gwargwado kuma tana da Ilimi, yanayin kyau da gayun mahaifiyar Hanan ya isa ya nuna maka 'yar ta ma hakan take. Koda ta hasko Naja seta ga abun se A hankali, kuma tun abun nan da sukayi mata ta tabattar da Ko Auren akayi Naja zata iya wulakanta ta.
Da ire iren wannan tunanin yasa ta ajiye duk wani bacin rai aka shiga hada2. Tareda tsara yadda suke ganin bikin ze kasance, Ba laifi Mummyn Hanan ta saki jiki Maama, Sunyi hira sosai kaman sun saba, sannan suka tattauna akan yadda harkar bikin yaran nasu ze kasance. Se la'asar Suka tafi, mutanen Bauchi suka tafi, Su Hanan ma a ranar suka juya kaduna saboda Su Hanan suna jarrabawa, su kuwa danginsu Mahmud, suna kawowa Mahmud kudin Aure sukaci Abinci suka juya Borno.

Wasa2 sosai tunanin Jalila ya hana Jalal sukuni, da yafara aiki in ya tuna da ita gaba daya se yaji duniyar tayi masa zafi, yarasa inda zesa kansa, meyasa Mummy tayi masa haka? Idan yaji abun ya dameshi se ya tafi club yaje ya cika cikinsabda giya, dukda wasu lokutan yana bawa aikin da yaje yi mahimmanci, Sam Jalal bashi da sakewa da mutane, dan haka be saba da kowa ba, sedai yana girmama shugabanninsa na gurin aiki, girmamasun da yake besa sunga alamar ze bari su taka shi ba, inda yake burgesu yana maida hankali akan aikinsa sosai.
Duk lokacin da yaje Club mata da suke damun sa ne ga kuma shigar tsirara da suke yasa shi dakatar da kansa ga zuwa Club, idan yaji ba yadda zeyi se yayi shaye2 se yayi abunsa a dakinsa na hotel da yake ciki.
Amma duk da haka yarasa dalilin da yasa mata ke binsa, sedai in baze fito ba.

Hannah ce zaune akan kujera tana kwalliya, Sa'ada na kwance akan gado tana danna waya, dan dakatawa da kwalliyar Hannah tayi ta dan kurawa madubi ido, sekuma can ta daki kan mirror tace "Impossible baze yuwu ba wallahi"
Sa'adah ta waigo ta Kalle ta tace "lafiya kuwa?"
"Akwai matsala Sa'ada" Hannah ta bata amsa
"matsalar me fa?"
"Sa'ada ki kalleni ki kara, kimin kallon tsaf tun daga sama har kasa, ki kalli yadda nake gara kan maza, in taka wanda naso in wanke wanda naso, amma a hakan har rububina wasu suke, in sauke Ajina in cewa Jalal idan ya Aureni zan dena bariki, Amma ya watsa min kasa a ido"
Wani dogon tsaki Sa'ada tayi tareda fadin "Nina dauka ma wani mutumin kirkin ne, A she akan wannan mashayin ne, ni ba wannaan ya dameni ba a yanzu"
Hannah tace "Mutumin kirki ne mana, ki kalleshi kallon tsaf Sa'ada Namiji ne irin wanda duk wata mace zatayi burin Aure, shaye2 ne kawai matsalar sa, da farko da nakewa su Jeje aiki, nna zata zan samo kansa ta sauki ya yadda dani, Amma duk wata dabara da kisisina ta matan bariki nayi amma yaki amincewa dani"
"to kibi wani mana, ko shine kawai namiji?"
"bazaki gane ba Sa'ada, bakiga irin kirar da Allah yayi masa bane, kuma da kike ganinsa a haka, dukiya ce dashi kaman abun banza"
"Ya akayi kika sani, nasan dai babansa yana da kudi, amma shikam ko aikinyi ba shida shi" Sa'ada tayi maganar tana yatsina fuska
"Hmm to wallahi har ki mutu in ba wani ikon Allah ba, kaf danginku daku da abunda kuka mallaka, bazaku kaishi dukiya ba, yana da kudi da mahaifinsa yasa ake juya masa, Jeje yaso ganin bayan dukiyar nan shida mai gidansa amma abun be yuwu ba suka kare a prison"
Sa'ada ta tashi zaune tace "to ke yanzu meye abunyi, ni ban taba sani ba, kin san ya taba kusa tonamin Asiri ina zuwa club agaban babarmu"
Dariya Hannah tayi tace "Abune mawuyaci ya tona miki Asiri, bar ganinsa a haka, yasan abunda yakeyi, naje har gidansu na dana masa tarko, amma ga dukkan alamu ya tsallake shi, wannan karon zan masa tarkon da zan rike shi a wuya, be isa ya kuma subuce min ba"
"Yakamata kam, Amma ni nan tunanin yadda zan huce abunda abokinsa Jawwad yayiwa Naja nake, kiri2 yafasa Auren ta, yarinyar nan duk ta shiga damuwa"
"Allah sarki, to wai ya'akayi aka fasa Auren? Waye yaje yai mata gulma a gurin baban nasa?"
"ya za'ayi in sani, Amma da nafi kyautata zaton wannan munafukar kanwar tasa ce"
"Wace kanwar tasa ya'akayi tasan abunda Naja take? Ko dai itama tana ta bawa?"
"Ke bari, wata yarinyace yadda kika san boka haka take, ni dai ban san tana wani biye biye ba, Amma kina zaune in taso seta nemo waye ubanki koda ke baki sani ba, wai ita Jalila makirace ta bala'i, idan tace bata san abu seta ga bayansa, tasa Jawwad ya fasa auren Naja se kawarta"
Jin an ambaci Jalila yasa Hannah zare ido tace
"Kan bala'i ai nasan wannan yarinyar, tabdijan ni zan gaya miki makira ce, ke wallahi keda kike bariki tafi ki iya rashin mutunci, ke zata iya yuwu wa ita tasa aka hana, bari in gayamiki yarinyar nan tafiki bala'i, dan koni tasa min ido akan Jalal, ita take rusa min komai "
Cikin mamaki Sa'ada ta kalli Hannah tace" wai kin santa ne? "
" Nikuwa na santa, kuma nasan illar ta, munyi Arranging da Jeje mun gama komai, zamu sace Jalal ranar birthday din sa, idonta na kanmu, muka bugar da shi da giya ta shammace mu tasa aka dauke shi daga gurin, ke ina jin kishin cewa ita tasa aka kama Oga KB"
Zaro ido Sa'ada tayi cike da mamaki tace "Ke haba dai? Shikuwa oga KB yana me,duk iya kuri da gadarar rashin mutuncin nasa, yarinya ce fa karama"
Hannah tace "hmm ke dai bari, mace kenan, kaidin wata yafi wata, irinsu kuma sa'a ce dasu a rayuwa, kibi a sannu kawai"
"Tabdijan amma babu kama, dan bakiga cin mutuncin da muke mata ba mu da babarmu, kin san uwarta tsohuwar arniya ce, bakiga cin mutuncin da muke mata ba"
Hannah tace "Yawwa kuma ga cin mutuncin da tayi muku nan, kuma ta gama daku ba"
"Sosai makuwa ta gama damu"
"shiyasa wannan karon shirina ita da Jalal ne, dan bana ta wannan Ilham din dan wannan ba mace bace, wannan tafi hatsari, baze tsallake wannan tarkon ba a yanzu, na duba mashayar da yake zuwa ba adadi amma ance ya dena zuwa, duk da haka zan nemoshi"

Yauma duk da tarin farinciki da Jalila ta tsinci kanta a ciki yau, amma bacci ya kauracewa idanuwanta, jikinta na bata Jalal yakoma shan giya, da kyar ta samu bacci ya dauke ta, amma mafarkin Jalal a cikin wani yanayi na shaye2, yasata farkawa,

Please Login or Register in order to submit comment