Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ta kwonta sannan ta janyo hannunsa tana sauraron kulawarsa
Ta kasance a kulun sai dai ta yi kwonce abinta shi kuwa ya bada kokarin komai

Hannunsa ya kai jikinta a hankali, sai dai ya ji laushin riga a hannunta
Rigar ya amsa ya ajiye gefe kafin ya shiga kokarin gannin sun samu nutsuwa baki dayansu

Ta fi so su yi ta romance, ta fi ganewa hakan ,
Tana samun hakan, mai sakata samun nutsuwa kuwa sai dai sam gogan nata shi baya samun nutsuwa a iya hakan

Sai da ta kankame jikinta cike da tsoro jin zai kai gareta

Hakan ya saka shi sasauta mata rikon da ya yi mata a hankali ya ce" ki saki jikin ki dan samun gamsuwa cikin salama

Ajiyar zuciya take ta saukewa tana son sakin jikin nata sai dai ta rigaya ta saka tsoronsa da tsoron abin a kasan zuciyarta hakan ke bata wahala matuka

Ta gurzu sosai dan sai da ta biya kwanakin nan kafin ya saurara mata

Bai koma saman bed din da dauda ba sai ya nufi bayi

Sai da ya tsaftace kansa sosai sannan ya fito ya dawo ya tarar ta cenza zannin gadon kamar yanda ya gindaya mata

Sai da ta gama ta dauke wancen zannin ta nade shi sosai ta mike bayan ta mayar da kayanta jikinta

Rigar dake ajiye ta karasa ta dora hannunta zata dauka
Sai dai bata kai ga dauka ba ya saka hannunsa ya rike rigar hakan ya sa ta sakar masa ta kara sada kanta tana dan murmushi ta ce " ka huta lafiya sarkina, Allah ya hutar da gajiyarka uban y'ayana

Cike da kasaita ya sakar mata murmushi yana kallonta ta juya ta fice

Me yasa bata iya zama a bangarensa komai dare bata iya kwonciya saman gadonsa sai dai ta je falo ta kwonta?

Kafadunsa ya daga yana baiwa kansa amsa cewa bata da ra'ayin hakan ne

Rigar d aya lura ta yi ta sinsinnawa da nishadi sai dai daga baya fuskarta ta cenza ya kai wajen hancinsa yana mai sinsinawa

Da sauri ya maida baya baya kusan ciki inda idan ya saka zata kawo masa daidai cikinsa ya shinshina

Da sauro ya cire daga hancinsa yana mai dafe gaban goshinsa
Kanshin turaranta ne wannan
Wani irin turare take anfani da shi mai kamshi mai tsayawa a jikin mutun haka?

Bakinsa ya tabe yana ayanna" idan har kere na yawo.....zabo na yawo na tabata wata rana zasu hade........................


Tun da sasafe suke kinkimtsawa

Sai da suka gama kimtsawa suka hadu a saman tafkeken table din wajen du suka zazauna

Cike da farin ciki ta shiga zuzuba masu abinci da kanta tana yi tana dubansu
Inama ace su dawama da ita haka? Gashi yau har zasu koma gidajensu inama ace mahaifinsu ya iya bata koda matan ne ya rike mazan?

Abincinsu suka ci cikin nutsuwa kafin ta dauko ambulope din nan ta budeta

Abubuwan ciki ta zubo wanda hakan ya saka su baki daya zazaro idannuwansu ciki kuwa harda GIMBIYA

Da sauro ta dauki farar takardar dake ajiye ta buda, a fili ta karanta" *ina rokon alfarmar daga yanzu du wata dawainiyar gimbiyata ta dawo hannuna, idan nace kowace ina nufin kowace ciki kuwa harda kudin kari da kati.....fatan zaki rike wannan catin na banki sannan ki faranta min ta hanyar anfani da shi a kowani lokaci daga ni mai ke in sha Allah*

Wani ihu ihu yan matan suka kwasa sunna dariya, NAJEEBA dake firfito ido ta daga hannayenta duka biyu tana sarawa ZAHRAU ta ce" *AN BASHI DAMA, AN YARDA*

Zahrau kam kanta ta sada da mamakin kalaman ciki, dama zai iya neman wata dama a wajenta maimakun ya bata umarni?

Ashe sarakai na neman dama maimakun su bada umarni ko dai shine mai saukin kai?
Irin kallon da ya ringa yi mata jiya ta tuna hakan ya sakata saurin kara sada kanta tana murmushi kafin ta sauke dubanta saman makudan kudadan da suka zubo wai na karinta ne da kuma katin da yar agogon azurfa kamar dai soyayar yara masu ji da kansu

Kanennta ta bi da kallo tana gannin yanda suke shoki
Sannan ta sauke dubanta saman Anmy

Ganni ta yi Anmy harda su tagumi tana kallon NAJEEBA wace ke murmushi tana kada kai tana hangota ta zama aunty

Anmy ta dubi kananun ta ce" ku tashi ku je falo

Bayan sun bar wajen Anmy ta dubeta cikin nutsuwa ta ce" bana so ki amince masa dan dukiya daughter
Na fi so ki ji kin amince masa duda kin ga ba yaro karami bane da zai zauna yana soyaya irin naku na yara, sannan ba zaman jiranki zai yi ba duba da irin darajarsa
Aman ko da wasa ba zan yi maki auren dole ba kin ji?

Kanta ta ringa gyadawa a hankali sannan anmy ta dubi su NAJEEBA

Murmushi ta yi masu ta ce" kar ku manta, ku ringa kiyaye darajarku ku rike mutuncinku kun ji?

Su duka suka amsa mata da nutsuwa kafin du su tashi su tafi bayan sun gama yin salama da ita

.............................................

Kansa a sade yake gaban mahaifiyarsa
Kunyarta ne ya ji ta lulube masa zuciya sai wani irin takaicin zinaria da haushinta da mamakin ashe har yanzu bata da hankali? Yarinta ce ko raini ne ya shiga tsakaninsa da ita?


Cikin tausasawa Anmy ta kara tambayarsa kamar haka" *SHAHEED, SHIN ZAKA IYA FADA MIN KAMSHIN TURARAN WA MATARKA TA JI A JIKINKA KAFIN ZARGI YA SHIGA TSAKANINKA DA ITA DA NI KAINA MAHAIFIYARKA KO BA ZAKA IYA BANI AMSA BA?*

Me zai ce mata? Ce mata zai yi ga mai turaran ta tambaye shi me ya kai turaranta jikinsa? Ko fada mata zai yi ga abinda ya kawo turaran nata jikinsa ta titsiye shi kan a kan me?
Aman yana tunanin ya yi girman da zai iya tara mata hudu shine zinaria ta masa gangancin kawo irin maganar nan kunnen mahaifiyarsa? Ta kuwa san irin yanda yake kiyaye lamarin mamansa shine ita zata masa wannan shirmen?

Anmy ta shiga girgiza kanta a hankali sannan ta ce"
[1/20, 7:40 PM] Ummu Suhan=Ø
Þ: >ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



14



Bude matan da aka yi ya sakata saka kafarta da bismillah ta shiga shagon

Sai dai bata kai ga idasa shiga ba ta ji wata murya sama sama ana tafa hannu aka ce" oyah, gata fa ta shigo, karuwar yar dake zuwa nan ta amshe kudadenku kuma ta raba ku da mazajenku

Da sauri ta dube ta
Duba irin na tsanaki nan ta tabatarwa kanta cewa wannan itane matar Ambasador din

Ko karya na yi maki? Idan karya na yi maki ai sai ki musa ko kunya bakya ji yarinya karama da ke kin mayar da kanki karuwa kina bibiyar mazajenmu

Yarinyar dake hannunta ta kara rikewa dan kar ta fadi tana kallon matar

Zata iya rantsewa idan auren kauye ne matar nan tana iya nakudota ta haifota ba tare da an talafa mata ba
Gata ta wani zama wata kantamemiyar mace ba wani waje dake rabe ko'ina a hade yake
Gaske, shi ya sa mijinta ke haukacewa ko wani dan karamin tabara nata

Fuskarta ta dan yatsine ta juya a hankali ta nufi ciki

Mayafinta ta warto tana fadin" ke dan ubanki ki tsaya min a nan dan ko uban wa nake magana da shi bai isa shigewa ba sai na gama! Zuwa na yi ki fada min karuwancin naki a kan mijina zai tsaya ne ko me?

Da sauri Najeeba ta karasa saka kanwarta ciki ta zaunar da ita ta mika mata wayarta wace bata da wani code ta fito tana janyo kofar cikin

Mai aikinta babar ce ke ta raraba ido hannayenta saman kanta , fadi take" Hajia dama abinda ya kawo ki kennan? Ki yiwa girman Allah ki yi tafiarki kar ki rikita mana wajen aikinmu dan mu aiki muka fito

Wata bagwariya da ake dinkawa atash kuwa ta yi saurin fadin" jesus, wannan yalinya da gaske ne?

NAJEEBA ta dubeta, ta kuma kallon mutanen cikin shagon

Kafadunta ta daga ta karasa da karfi ta warce mayafinta dake hannun matar ta ce" eh haka ne, ni karuwarsa ne, nice nan mai haukata maki miji ya je gida yana ihun kiran sunnan NAJEEBA NAJEEBA NAJEEBA a tare da ke!


Dan ubanki karya kike, ke nan har mace ce? Ina wajen da zai rike har ya haukata shi? Ta fada a zabure

Najeeba ta yi far da idannuwanta ta ce" meye kuwa ba zai rike ya kasa zaburar da shi ba tunda har yake iya banbance sama da kasa, teba da mazaunai? Ke ko jiya a wajena ya raba dare mijinki!

Tabas a jiyan kuwa ya raba daren domin shi dama mutun ne mai yawan yawace yawace ga cika dare a waje, ga uwa uba a jiyan ya nemi Najeebar kamar me dan ya jima wajen shagonta bai sameta

Najeeba ta dora da fadin" kin ga kuwa idan har baka iya kiwo ba, baka iya daure akuyarka ba dole ta fita waje ta ci! Hakan na nufin ba'a karuwa daya shima mijin naki namijin karuwi ne

Abin da ake busar da gashi na kusa da ita ta kinkima wanda ke jikin abin jonawa a jone ta shanmaci NAJEEBA ta tafka mata shi daga gefenta wanda hakan ya sakata yin tangal tangal ta je ta daki garun dake kusa da ita

Ta saurin balaki ta sabule takalman kafarta ta rike guda a hannunta da yake mai dan tsini ne kadan

Da gudu ta karasa ta shigi matarnan da wani irin masifa tana doka mata du inda hannunta ya kai

Kawayenta da suka rakota basu shiga fadan ba sai rabawa da suke, wanda hakan ya fi yiwa Najeeba ciwo gannin mace kusan hudu ta ririketa

Su dukansu kallonsu take , sai a lokacin ta gama fahimtar tare suke mace kusan shida dan hudun sun riketa sunna bata hakuri biyun kuwa sun rike Hajiar sunna tausarta sunna fadin ya isa hakannan ta bari haka

NAJEEBA ta ringa kokowar kwacewa aman du sun saka mundula mundulan hannayensu sun ririketa hakan ya sakata sakin wani irin kukan takaici
A rayuwarta ta tsani tana fada a riketa, ta fi so a barta idan akai mata jina jina zara rabu dan kanta, ta fi so a barta ta ji jiki ko wanda suke yi ya ji jiki da haka raini zai rabu tsakaninsu

Tana ihun kukan take fadin" ku sake ni! Ku sake ni! Idan baku sake ni ba na rantse da wanda raina yake hannunsa kuma kun jazawa kanku fitinar da ba zaku iya dauka ba
Dan walahil azim ko mazajenku kushewa ne a tsufa, ko a masalaci suke kwana tsabar musulunci ya ratsa su, ko mata maza ne sai na birkita lisafinsu, sai na rikita maku gidajen aurenku, sai na fitine ku ba dare ba rana! Walahi sai na koyawa mazajenku cika dare, sai n koya masu bibiyar mata! Sai Na gwada maku bariki iyawa ce!

Dayarsu ta saketa da sauri cike da tsoron kalamanta
Wada ke kusanta ta ce" ke ki riketa mata idan muka saketa zata koma wajen hajia ne kin ga fa ta fasa mata goshinta sai jinni yake

Kanta ta girgiza da sauri ta ce" to ku saketa hakanan mana zaku kama riketa mu tafi, kunna fa jin abinda take fada kuma ni na san wacece ita dan haka ba ruwana

Wa'inda ke tare da hajiar ma sun tsorata da hakan, dan haka suka ringa turata waje sunna fadin kawai ta kai kara gidan sarki a mata tsakani da ita da mijinta kar ta rabata da mijinta haka kawai da y'ayansu

Da wannan shawarar suka samu suka tura hajiar waje

Sai da ta fita sauran suka saketa

Da wani irin masifa ta ringa wawurarsu tana jufansu hakan ya sa du suka fice a guje

Dukewa ta yi wajen tana kukan takaicin bata yiwa hajiar yanda ta so yi mata ba,

Da gudu yarinyarta ta duka tana fadin" aunty, dan Allah ki yi hakuri, walahi talahi ban san abinda ya kawosu wajen nan kennan ba, ki yafe mini ki daina kukan nan

Dago dubanta ta yi tana kallonta

Idannuwanta ta lumshe wasu hawayen suka zubo a hankali ta ce" kin ga wadincen? Baki dayansu sai na saka su a uku! Yanda suka tozartani bayan bani da laifi ko? Sai na tozartasu daidai da laifinsu!

Mikewa ta yi tana goge fuskarta da tissu tana gannin yanda ake ta bata hakuri

Murmushi ta yi tana kallon mutanen dake zazaune ana ta masu aiki aman an dakata sanadiyar fadan ta ce" saloon dina a bude yake daga safe har zuwa dare
Zakunna zuwa nan ne muna amshe kudadenku muna gyara maku abinda ya dace mu gyara! Inaga kun san cewa mace sai da gyara ko?

Ta kara lumshe idannuwanta ta ce" irin haka ke kara min gwuiwar fitowa daga gidanmu
Idan bana samun masu jirana dan su fada min cewa lale ni din wata kwaro ce mai bada wuta a duniya da ba inda zan je sai na boye a daka

Murmushi ta yi tana kara fadin" tawa sallon daukakar kennan kwacewa du wace ta yiwa mijinta rikon sakainar kashi da wace bata tashi tsakiyar dare tana adu'ar Allah kar ya hada mijinta d aalshe money idan dai ba matar aurensa bace

Wata yar daria ta yi tana dage gira ta furta" du Alhajin da ya saki bakin aljihu zan kwasa ne!


Ihu ihu saloon din ya kwasa ita kuwa ta juya ta shige ciki ranta du a bace tana jin haushin irin yanda bata wanwanke fuskar banzar matar nan ba

Zama ta yi kusa da kanwarta ta janyota ta shiga tsefe mata kanta da dabara dan kar yarinyar ta yi kuka, tana tsefe mata tana mata cakulkuli nan ta samu ta ji sanyi a ranta sakamakon wasan da ta ringa yi da kanwarta

Aiyukansu suka ci gaba da yi, duda a darare suke aman sun san da zata yi fushi da su nan take zata yi shi ne
Itama cikin nutsuwa ta gama gyara kan kanwarta ta yarfa mata kannanun kitso ta saka mata tsakiya sukai kyau sosai a kanta ta shinfideta sannan ta saka a kawo mata abinci

Kanta ta fita suka wanke mata tas ta shiga wajen busar da gashi
Bayan ta gama ta zauna babar yarinyarta ta shiga yi mata wani irin kitso manya manya kwara hudu kawai, wanda ake yinsa kamar zane ya tafi baki daya baya
Da yawan lokuta an fi yinsa da atash, Kasancewar tana da gashi sosai sai ake mata da gashinta hakan ya saka kitson ya yi tsayi ya yi tudu sannan ya yi wani irin kyau mai tsarin gaske tamkar ka kwace ka dora saman kanka

Tana gama yi mata ta je ta zauna ta shiga gyara kwontacen gashin dake gaban goshinta tana nanade shi tana gyara shi da gel, a haka har gefe da gefen fuskarta ta gyara shi sosai
Gashin ido ta fitar da wani sabon kala wanda ya fi zama natural, ga tsadar gaske da yake da shi

Zama ta yi cikin nutsuwa ta saka abinta tana kallon yanda yake a idannuwanta

Wata budurwa mai ji da kanta ce ke kallonta tun dazun, ita kanta ta lura da kallon sai ta share dan ba magana ta mata ba gashi kana ganninta zaka gane irin yan matan nan ne masu jiji da kansun nan

Sai da ta gama ta dauki jan baki a cikin kayan mak up din ta shafa kalar lebenta ta juyo

Wauh budurwar ta fada a lokacin da bata shirya ba tana kallon Najeeba
Murmushi ta sakar mata ta mike ta mika mata hannu

Itama hannun ta bata suka gaisa kafin ta dan sakar mata murmushi

Budurwar ta ce" kina da kyau sosai, na yaba

Wani dan murmushin NAJEEBA ta yi mata tana kallon kafarta
Irin sarkar da ta gani da kuma zobe a yatsarta ya shaida mata ko wacece ita
Dan rabata ta yi kusa da kunnenta kasa kasa ta ce" sorry, na haramta bin mata

Budurwar kadai ta ji sai ita da ta fada , tana fada ta shige ciki ta daura alwallah ta gabatar da salar la'asar sannan ta ci gaba da zama da carbinta irin na hannun nan tana dan dannawa a hankali a hankali

Sai da dare ya yi ta dauki kanwarta, ta gama hada kan kudaden da aka samu a ranar ta hada da takardar gidan wuta da ruwa da aka kawo masu ta salami sauran baki daya sannan ta rufe ta yi adu'o'i ta totofa sannan ta tayar da motarta ta nufi gida

A kofar dakin mamanta ta sauketa tana mata byby, yarinyar ta ringa nokewa ba zata je ba dan ba karamin dadi ta ci a wajen Najeebar ba ga wasan da suka yi ta yi na goyo a dakin ga ta bata wayarta ta yi ta dannawa

Daukan yarinyar ta yi ta nufi bamgarensu da ita dan sam ta ki ta shiga wajen mamanta

Sunna shiga ta yi turus sakamakon gannin yayunta du sunna tsaitsaye da alama ita akae jira

Yayanta ne da fada fada ya ce" daga gidan ubanwa kike Najeeba?

Da mamaki take kallonsa ta ce" yaya, daga saloon nake mana ina zan je ni kuwa yau?

Ummulkhair ta ja tsaki ta ce" a saloon din naki ne kuka yi fada yau? Gashi har an kai kararki gidan sarki ga samaci an kawo wai ke kam me ke yawo a cikin kwakwaluwarki na masifa ne? Me ya hada ki fada da matar ambasador?

Gaban goshinta ta dafe a lokacin da Bilkissu ke fadin" aunty, me yasa kika tafi da Nusaiba kin ga mamanta ta yi ta zage zage da fada tana fadin zaki lalata mata yarinya har a gaban abih

NAJEEBA ta ringa gyada kanta a hankali ta ce" inaga sai na sha magannin baki yaya, ka ji fa kowa ni na masa laifi yau harda kai? Yaya to ka san me ta min ne?

Koma me ta maki sai ki duba yannayin da Anmy ke ciki, gashi shara'ar karfe hudu za'ai maku da wahala ace sarki baya nan! So kike a kara zuwa a fada mata cewa gaki cen yauma wata ta kawo kararki? Ke bakya tsoron kur'anin da ake saka maki ya lalata ki ne? Ina dalili wai ke kamar yar agunla?

Bani y'ata! Bani y'ata
Kuma daga yau kar ki kuma daukan min y'ata ja fada maki, haka kawai kin fi karfin uban da ya haife ki ki koyawa y'ata irin fitintinun ki?
Tana fada tana warce Nusaiba dake hannun Najeeba

Najeeba ta sakar mata yar, tana kallonta

Zahrau ta ce" subahannalah, ke kuwa meye hadinki da shiga tsakaninmu da yar uwarmu? Kin taba gannin mun sakota a cikin matsalarmu da ke? Dan Allah ki daina zagar mana yar uwarmu, yau koda Najeeba yanda kike fadi ne ai bai dace ki ringa zaginta haka ba
Kema fa macen kika haifa, kuma kema mace ce, bale kanwata ba yar iska bace walahi, ki fita a harkar shiga tsakaninmu da Nusaiba, Najeeba ba zata taba cutar da Nusaiba ba, na san ko baki daya mun mutu koda dako ne Najeeba zata yi ta rike kanwarta dan Allah ki shafa mana lafia hakannan mana kema?

Sai da ta harareta sama da kasa ta yi daria irin ta wulakancin nan ta ce" wai kililin kasau macijin kumba
Wace ake kawo sadakinta ana fardewa ne zata nemi ta bani shawara? Munanan halayanki sun hana maki samun mijin aure kina wani kumbiya kumbiya ke ga ta kirkinsu ko? To bari ki ji, a tafin hannuna kuke baki dayanku kuma ma rantse maku baku isa ku raba ni da gidan nan ba
Ko a irin yanda na fi sauran iyayenku jimawa da mutumen nan kun san ya mace a so na
Matar ubanku nake dan haka dole a kira ni mama

Ummukulsum ta budi baki zata yi magana da sauri Dayabu ya dubeta duba irin na ido cikin ido

Muryarsa har rawa take ya ce" Mardiya me yasa kike mana haka ne? Yaya kike tunanin cin riba idan har kika shiga tsakaninmu da yar uwarmu? Kin tabata zaki kai girmanta zaki iya tarota zaki iya rayuwa da ita ke daya kin iya mata?

Tana zaro idannuwanta irin masifa na cinta ta ce" eh, ba abinda ya shafeku da y'ata ba domin baki dayanku kun kasance jinnin masifa karku koyawa y'ata

Daria ya yi yana girgiza kai ya ce" haka ne, aman masifar inaga itama jinnin nata ne idan kika yi la'akari da ubanmu ne daya baki daya
MARDIYA, ba dai NUSAIBA ba? Nusaiba dai ce ko? Ki rubuta ki ajiye daga yau daga kaina har zuwa wannan yar karamar dake kusana
Yana nuna yar kanwarsu wace bata fi shekara shida ba
Ya daki kirjinsa ya ce" Ni DAYABU MUTALAB idan har na isa da kannena daga bakin zahra har zuwa ummi na kankare mana wannan yarinyar daga cikinmu, yarki ko? Ki rubuta ki ajiye bamu isa mu tatse jinninta daga jikinmu ba aman mun isa mu kankareta daga cikinmu! Ko a titi, ko a cikin gida ba mu ba ita!

Gaba daya yaren mutuwar tsaye suka yi sunna kallon irin yanda ran yayansu ya gama baci,
Yana gama fada ya juya ya yi ciki ransa a matukar bace ya je ya gyara shinfidar kananu du ya kora su daki

Manyan kansu silalewa kowace ta yi, zuciyarta da mugun rauni, me ya sa ta yi wannan aika aikar ne? Me ya sa sai da ta kai mutun mai hakuri da kare yan uwansa bango har ya aiwata haka yau? Ya fi su saukin hali da kawar da kai ko dan ya kasance mamiji? Aman a yau ta kaishi bango har haka ta faru

Sun yi baci hankalinsu ba a kwonce ba
Da sasafe ta rigayi kowa barin gidan ta zarce saloon

Yau da kanta ta ringa yin aikace aikacen ta jirga zaman kujerun ta kakabe atach din dake tare ta wanwanke abubuwan wanke kafa ne, ta goge du wajen da ya yi dati

Sai da ta yi aiki jina sannan ta zauna tana maida numfashi

Da wuri wuri aka ringa cika wajen
Nan ta shiga aikinta tana yi tana duba time

Ba abinda ta ci sai da karfe uku ta yi ta bara masu ta shiga ciki

Wanka ta yi mai tsari ta gyara jikinta tsaf ta fito sanye da wata abaya mai ruwan ja mai duhu da bakin hannu
Dan kwalin abayar ta rataya a wuyanta ta fita ta shiga motarta

Bata zame ko'ina ba sai fada
Tana tsayawa ta saka gilas dinta fari dan siriri ta fito a motar

Cirko cirko ta gansu su biyar a tsaye

Ido ta zaro ta karasa wajensu a hankali ta ce" me ya kawo ku nan ku kuwa?

Yaya DAYABU ya harareta ya ce" baki da kowa ne da zamu barki ki zo ke daya?

Fuskarta ta sanyaya ta ce" eyah, na ga du na bata maku rai ne

Zahrau ta kamo hannunta ta ce" mu je lokaci ya yi Najeeba, komai bata mana da zaki yi ba zamu barki ke daya gaban mutane dubu ba

Wani sanyi da kaunarsu ce ta ji a ranta, nan suka rankaya da su ummu suka shiga bayan sun cicire takalmansu

Tun da suka zauna yake yi mata mayatacen kallo

Matarsa ta shiga bayanin a yi mata tsakani da mijinta ba ita ba shi

Da sauri ya ce" aa, Allah ya taimaki waziri ni kam ba da yawuna ba, yarinyar nan ni na je na ce ina son ta, idanma laifin ne ni na yi mata dan haka bana cikin maganar a rabani da ita dan aurenta nake son yi!

Gaba daya wajen ya yi tsit, sai Najeeba da ta kara sada kanta dan kunyar da take ji na irin kallonta du da ake

Daga inda yake tsaye ta wajen tagar dakinsa yake hango komai
Irin yanda ya fahimta yauma itace aka kawo kara

Juyawa ya yi ya karasa wajen wayarsa karama ya danna kira, idan yana son jin abinda ake fada yake hakan sai a ajiye yana jin komai

Zama ya yi ya yi zamansa na sarki ya bude litafi a hannunsa na hadisi yana dubawa still yana sauraron abinda ake fada

Kansa kawai yake girgizawa a lokacin da ya ji ambasador na neman yin sakiyar da ba ruwa ta hanyar sakin matarsa har yana daga muryarsa cewa idan har ta yarda aka sakawa Najeeba wannan layar to ta tabata a bakin aurenta

Karshe
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment