Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

abinsu

Gannin yana son daga hannunta niyarsa ya wanke mata hamata ya sakata dan zaro ido tana kallonsa
Ai kau bata ankara ba ta ji ya fara mata cakulkuli

Dan ihu ta saki ta fashe da daria da gudu gudu ta shiga kokowar kwacewa
Shima dariar tata ta tafi da shi har ya shiga yin daria kasa kasa yana kara rikota jikinsa yana jin tana ihun sai ta rama tana masa cakulkulin shima hakan sai ya zama ta matso sabulun ruwan ta shiga wanke shi tana mumurza ko'ina hankali kwonce tana son sai ta taba wajen da zai saka shi daria kama daga lafafen cikinsa mai gida gida, da keyarsa, ta duka ta taba tafin kafarsa, ta mike ta kama hannunsa ita sai ta yiwa hamatarsa aman ta kasa daga hannun sai kawai ya shagala yake rakata da ido yana jin nishadin lokacin
Kunnayensa ne suka jiyo masa salamar dake nuni da an gama sallar

Ido ya zaro da wani irin sauri ya kamota gabansa ya nuna mata yannayi na ta yi alwallah dan har an gama sallah

Itama alwalar ta maida hankali ta yi ta bi bayansa da tawul din da ta janyo a shanye a bayin

Tana fitowa ta tsinkayo maganarsa yana fadim" haka kawai yarinya ki wani saka mu kokowa a bayi bayan ba kyau magana a bayi, kuma ki wani saka na rasa jam'i kai yarinyar nan bakya jin magana"

Baki ta bude da mamaki tana karasawa inda yake miko mata doguwar rigarta ta sallah da har ya fice ya dauko mata

Da sauri ta warwareta ta shiga sakawa sannan ta saki tawul din kasa
Ita kanta ta manta da komai bale shi dake kallonta hakan ya sa a rashin tunawa ta duka ta zare jikaken wandon dake jikinta ta ciro shi baki daya

Ido ya zaro gannin katon wandon da ya mata daidai, itama sai a lokacin ta ga abinda ta aikatan, ai da sauri ta matse shi a hannunta tana tura baki ta juya zata koma bayin

Hannunsa ya mika ya kamota yana mai kara bin jikinta da kallon kasa kasa, hankali ya ce" Let's pray "

Kai ta dan gyada masa, suka nufo kilatacen wajen sallah

Lalle ta yabawa limancinsa, ta yabawa irin tsarin sallarsa harma ta ji a ranta zata kara dukawa ya kara koyar da ita adininta domin kuwa ita ko a ina ta hadu da wanda ta san ya fi ta ilimi a kan wani abin bata jin kunya ko girman kan duka masa ya koya mata bare adinin musulunci mai dauke da abubuwa masu girman gaske wa'inda wasun har ka koma ga Allah ba zaka taba saninsu ba

Mikar da ita ya yi a hankali ya sakata gabansa shi kuwa a bayanta , bayanta mane da kirjinsa ya shiga takawa da ita suka nufi falon gidan

Ita dai inda ya yi da ita take bi, sai ganninsu ta yi sun yi dakin cin abinci

Kayatacen tankamemen table din diner ya nufa da ita mai dauke da wasu irin kuloli masu ado da zeba
Kana gannin kulolin nan ka san na manya ne, ga fruit wanke tass a cikin wani bowel mai shara shara domin ana iya gane ko meye a ciki kuma a rufe da wani marfi
Sai zug zug din da ta yi imanin jus ne a ciki

Idannuwanta ta lumshe sakamakon jin hucinsa wajen wuyanta wanda ya zame hular doguwar rigar tuni , sai take jin jikinsa da dan gumi, aman ta kasa tambaya

A hankali ya ce" ni yinwa nake ji "

Dan murmushi ta yi wanda bata shirya ba domin irin yanda ya yi maganar sai da ta ji kunya walahi

Kanta ta dan dago ta dube shi, sai kuma ta cire dan ita a yanzun irin duban nan nasa da sam baya barinta da shi ke rikitata, gashi dai maganar sanyi ke fitowa daga bakinsa zuwa gareta, ama kuma idannuwansa na jifanta da kallon tsanar dake ladaftar da ita!

Wajen cin abincin suka karasa

Kafin ta zauna ta dauki plat daidai cin sa
Aman sai ta ga ya cenza mata da wani baba

Yana kallon yanda take zuba abincin yana koya, domin dai sultan ko dafa ruwan zafi bai iya ba, inama ya samu damar dafe dafe shi da ya tashi cikin horon koyon abubuwa da dama ciki harda kasuwanci wanda bai fara harkokin mahaifinsa ba sai da ya kama masters a marketing dinsa sannan ya karbi komai yake tafiar da shi daidai da gwargwadon iyawarsa domin kuwa harta da takardar business communication sai da ya hada saboda tsaro

Tana gama zuzuba komai ya mike ya dauki farantin ya yi gaba

Bayansa ta bi da kallo, gane cewar ba a nan yake so su ci abincin ba ya sakata dan bubuda jus jus din
Na aya ta dauka da abin zubawa ta bi bayansa

Cikin nutsuwa ta karasa wajen da yake zaune yana jiranta ta ajiye sannan ta zauna itama
Bismillah ya yi mata ya fara saka hannunsa ya fara ci , kafin ta fara ci itama

Ta yi dagowa ya kai biyar tana kama shi da irin kalon nan, hakan ya sa ta yatsina fuskarta bayan ta hadiye abincin ta kura masa ido
A sanyaye ta ce" Me ya sa kake jifana da kallon tsana tun shekarun baya? "

Da mamaki yake kallonta, kallon tsana kuma? Wani irin kallon tsana ne yake jifanta da shi?

Gannin tana son cire hannunta ta tashi sai ya riko hannun nata
Idonta ta dora saman hannunsa dake rike da hannunta
A hankali ya fitar da hannun nata sannan ya matsota sosai
Hannun nan nata dake rike a nasa ya shiga sidewa daya bayan daya yatsotsin wanda hakan ya sakata shagala da kallonsa
Sai da ya gama sannan ya maida nasa hannun, wanda dama ga vokali ta dauko aman sai ya saka hannu ya diba a hankali ya nufi bakinta da shi
Dan langwabewa ta yi tana sauke ajiyar zuciya ta ki ta bude bakin nata

Yana mai dubanta a sanyaye ya ce" Ki ci kin ji, ki yi hakuri ki ci ko zan iya ci "












.............sai da na gama ya goge=Ø-Þ=Ø-Þ=Ø-Þ=Ø-Þ=Ø-Þ=Ø-Þ
[3/31, 11:36 PM] BAK'A CE: >ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



63





Wannan karron sai d akirjinta ya doka, harma ta ringa jin tamkar zata fashe da kuka da tashin hankali, a hankali ta kuma kurawa fuskarsa ido tana kallonsa ta kasa karbar abincin, shima dai kallon nata yake harma yana jin bashi da wani abu mai dadin kallo irinta a duniya sai dariar mahaidiyarsa

"Kin san kin ada kyau kuwa JEEBA?" Ya fada kasan makoshinsa yana mai shafa gefen fuskarta, bai bari ta dawo daga sumar da ta yi ba ya dora da fadin "Ina so idan Allah ya sa inafa rabon haihuwa a duniya y'ayana su ringa yin kamaninki da fatar jikin ki, da shahwabarki, ama banda fadan ki"

A hankali ta furta" Na shiga uku, meye hakan kuma?"
A kasan zuciyarta ta yi maganar, ama a fili ta bayana cikin sanyi da rarabewa,
Bakin nata da ya yi furucin ya kurawa ido, da ba dan baya son matse mata waje ta hanyar nuna mata zanlar zalamarsa a kanta ba, da ya kara kusanci a tsakaninsu a wannan zaman ta hanyar mayar da su abu guda a irin wannan lokacin

Buga kofar da ake a karro na ba adadi ne ya saka shi kai dubansa, haka itama

Hannunsa ya mika ya dauki remote tare da tablet dinsa ya kunna ya shiga kallon mutanen dake tsaye a cen wajen dogarai

Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya ajiye wayar ya dauki jus din nan ya zubawa kansa ya sha sosai

Kallonta yake kasa kasa kafin ya furta "zan je na dawo, ki ci abinci kin ji?"

Kanta kawai ta iya gyada masa tana mai binsa da kallo har ya shige cikin baban dakinsa

Ya dauki lokaci kamar minti ashirin sannan ya fito
Gaba daya sai ta ji wani irin yam yam yam a jikinta a lokacin da kamilin sarkin, mai wukar yankan ya bayanar mata a Sultan SHAHEED
Ajiyar zuciya ce ta kwace mata tana kallonsa sai ta ga wajenta ya nufo hakan ya sa ta ji zuciyarta na rawa

Yana karasowa da gaya sai ya ja ya tsaya kamar yanda yake yiwa Zinaria ta kwashi kirari ko ta dukar da dubanta har sai ya fice

Da farko kan nata ta dukar kasa kamar yanda idan aka kawora shara'a ko ta yi rakiya
Sai dai kamar yanda ya yi tunani ko minti daya bata yi a hankan ba ta shiga dago dubanta a hankali har ta sauke saman fuskarsa

Murmushi ya saki ya rage tsayinsa ya mikar da ita tsaye

Hannunsa ya saka ya janye abin wajen bakinsa sannan ya kusanto fuskarsa da tata
A hankali ya shiga kissing din lebunnanta har sai da ta bashi amsa son ransa sannan ya cikata ya sakata a jikinsa yana sauke ajiyar zuciya
Muryarsa ciki ciki ya ce" Yaya aka yi bakya jin tsoron hada ido da ni? "

Itama sai ta ki bashi amsarsa, domin ai ita ta fara tambayarsa ya mata banza ko, sai da ya gaji dan kansa sannan ya cikata

Har ya fara tafia ya ji ta ce" baka koshi ba kuma zaka fita? "

Dakatawa ya yi ya juyo gareta, sai da ya mata kallon tsaf ya ce" ki tanadar min wani abincin, domin zan fita da matsananciyar yinwar ki, fatana kar na ringa magana ina ambatar sunnanki a lafuzana......." ya karashe yana mai kashe mata ido daya sannan ya juya yana mayar da rawanin wajen bakinsa ya fice

Ta kai minti biyar a tsayen nan tana kallon kofar da mamaki
A bayane ta ce" kan Uba," sai kuma ta juyo tana sakin murmushi

Sai da ta dan jujuya ta kwaso shokiiiii ta juya wajen kofar nan ta sauke masa ita a fili ta furta" gayen zai halaka ni ".........

Sunna fita daga nan waje suka samu mahaifin Nadia ya gabatar masa da dukan sakamakon binciken da aka yi, hakama lauyan da ya dauka da kuma police din da ya shiga cikin mutanen gidan sarautar ya yi basaja
Sosai ya gamsu da bayanansu, sannan aka tafi da dukan wa'inda suke da hannu a ciki tun daga kan wanda ya ga lokacin da ake kama macijin ya ji labarin macijin ne ya yi kisan an bai fada ba, da wanda macijinsa ne, da sauransu

Sai da aka gama hargitsa gidan sannan aka saka kowa kuble dan za'a fitar da Zinaria

Da kansa ya saka aka fitar da ita aka kawota gabansa

Gaba dayanta ta zube kasa har jikinta na rawa ta fashe masa da kuka tana neman afuwarsa, cewar ba zata kuma yarda ta hada kai da wani dan a cuce shi ba
Ta dora da fadin" Haba ya mijina, ka gafarta min laifukana a gare ka, na san da ban kyauta ba, ama ba zan taba hada kai da shi dan na ci amanar aurenka dake kaina ba, ban taba cin amanar aurenka dake kaina ba "

Ransa bace matuka , ya kalleta, muryarsa kausashe ya ce" Da kin san darajar kanki, da kin kilace min kanki, sai dai kashhhh........, shiru ya yi na dan lokacin kafin ya furta" idah ta hau kanki, na tura takatdarki wajen sarki"

Yana gama fada ya juya ya shiga takawa, yana jin lokacin da ta kwala wani ihu duda muryarta a shake take ta zube kasa sumamiya, haka suka konkimeta suka sakata a mota, a hanya ne suka yi kokarin gannin ta farfado kafin tale gane komai sun sakata a motar hayar da akai mata shata zata dauki hanyar damagaran zuwa Agadez, hanyar da bata taba bi ba a mota tun da Allah ya haliceta, sai gata yau an sakata da ranar gari zata shiga garin agadez a motar haya, ita kam ko a haka aka barta ta gane rayuwa bale idan ta tuna mahaifinta na jiranta da takardar saki? Ita kam ta kawo abinda ba wanda ya taba kawowa gidansu, aman ta tabata mahaifiyarta zata tare mata (uhum, baki san itama an turata gidan ba=ØÞ)

Daga nan bangaren su Nadia ya nufa domin ya yi niyar yau ba zai fita ba

Yana zuwa suka gaisa da iyayenta, sannan ya mata yaya jiki da tambayar ko akoy abinda suke da bukata?, sun bashi gamsashiyar amsa sannan ya fice ya koma falonsa

A nan ya tile, a nan ya kuma bajewa, a nan ya ringa shigar yarinya ta inda bata zato bata tsamani, a nan ya ringa kara yiwa kansa ilah da soyayar yarinyar Ammi, a wajen nan ya ringa baje kolinsa , suka ringa samun kusanci da shakuwar da bai yi da wani mahaluki ba.......

Bayan kwana biyu da daurin auren su UMMU yaya DAYABU ya dawo daga tafiar da ya yi garin Niamey bisa aikinsa
Farin ciki ba irin wanda bai nunawa Ummu ba, sannan ya shigi abin da karfi karfi dan kuwa kiri kiri ya nuna ba zata zauna a wancen gidan ba, dan haka aka shiga gyare gyaren rantsatsen gidan Abih dake anguwar jeune cadre
Tsananin farin cikin da Abih ya shiga ba'a cewa komai, hakan ya sa shima ya shiga gabatar da bincike a kan yarinyar da DAYABUN ke nema, dan kuwa ya shiryawa bikin DAYABU, a duniya DAYABU ya kasance jigon rayuwarsa da ta y'ayansa, kowa dai rigimarsa shi yake zubawa, kowa shi yake kaima, shi kuwa ya dauka ya rungume ya nemi mafita , sam baya wasa da ahalin MUTALAB dan haka shima ya fara dukan lamarinsa da dukan katfinsa, dan kuwa zai masa biki na dan gata.

A cikin sati gudan nan idan fitar SHAHEED ta yi yawa bai fi sau hudu ba, NAJEEBA kam tana ji tana ganni zuwa bangaren AMMI ya gagareta domin Shaheed ya wani irin kasawa ya tsare dukan motsinta a kan idannuwansa, ya zamana idan ka ga an neme shi to abu ne mai girman gaske wanda dole sai ya fita, ko harkar kasauwancinsa da yake yawan operat a dakinsa ya ajiye ya basu dama, ya kasance Najeeba ta gama salamawa zuciyarta da gagarumin abin dake dawainiya da tunaninta
A yanzu kwata kwata ta daina yi masa maganar wani, koda ya yi dan ya nemi fitina takan yi murmushi kawai ta yi masa shiru
Ta yi maganar fita saloon ya fi a kirga, da ta ishe shi ya nuna mata saloon dinta su Aida na aiki , da mutane ba masu wani uban yawa ba domin sai da aka buga bage, idan kana son aiki a wajen zaka ciri tikite ne ka yi jiran rana da lokacin da aka baka,

Ta ji dadin hakan kwarai, harma ta tambaye shi yaushe zata koma bakin aikinta? Sai ya nuna mata zata koma idan ya ji hankalinsa ya kwonta da hakan

A yanzu Najeeba na dawainiya da wani irin kishi a cen kasan zuciyarta, a yanzu take jin haushin du wata mace mai sunnan tasa ko wace suka taba maganar da ta zarce ta yan uwantaka ko ta aikinsa
Ita kanta tana mamakin kanta , basu furtawa junna kalmar so ba, ama sunna wani irin kafa kafa da junna fiye da tunanin mai tunani

Yau suka cika sati guda, kuma a yau ne zata bar aiki Nadia ta kama, haka kawai ta tashi da bacin rai sosai

A cikin ruwan wanka take kwonce ta lumshe idannuwanta, ba komai ke mata yawo a kwakwaluwarta sai irin lamarin da ya wakana tsakaninta da mijinta a daren jiya
Ta kasa cire wannan lamarin a cikin zuciyarta,
A yanzun tsakaninta da shi abu daya ne kwal ya kasa furta mata, wanda zata iya rantsewa zuciyarta na bukatar jin hakan daga bakinsa

Zuciyarta dake tashi ne ya sakata juyar da kanta ta tofar da yawu ta kora da ruwa sannan ta idasa wankanta ta fito tana mai jin wani irin baci

Tana fitowa da gagawa ta karasa wajen kayanta da aka turo mata da su ta shiga kimtsa kanta dan bata son ya tardota har ta yi wanka ta tabata zai nuna bacin ransa ne

Tana gama dora alkyabarta ta karasa gaban madubi da gashin idon da aka sako mata wanda ta sa su Ummu suka sako mata komai ta gyara ta shiga dorawa
Fuskarta ta gyara kadan sannan ta saka jan baki kalar kasa kasa a dukan lebunnanta

Turarensa ta dauka ta shiga fesawa, a haka ya shigo da waya a kunnensa yana amsawa

Bayanta ya kurawa ido, alkyabarta, a hankali ta juyo ya zamanto sunna facing din junna

Murmushi ta sakar masa , wanda shi kuwa fuskarsa ta nuna yannayi na ya shiga halin damuwa a yanzu yanzun

A hankali ta taka har inda yake tsaye , tana zuwa ta shige jikinsa, tana jin muryarsa a sanyaye ya furta" zan tabo ka daga baya "

Bai tsaya ya ji amsa ba ya kashe yana mai sakin wayar nan ya saka hannayensa bibiyu ya rungumeta a jikinsa yanna jin yanda zuciyarsa ke dokawa

A hankali ya ce" Har gagawa kike ki bar ni? Shine har kika yi wankan ki bayan kin saba cuta min bayana? "

Dan murmushi ta yi na karfin hali a ranta tana ayanna ai gara kai idan ba daya da daya, ni fa? A fili kuwa sai ta furta" ango fa kake mijin Nadia, na tabata zata yi maka fiye da hakan "

Bai ce komai ba sai dan murmushi kawai da ya yi ya karasa saman kujera da ita suka zauna yanda suka saba dare dare tana saman cinyarsa

Cikinta yake shafawa, ahi kadai yana adu'ar Allah ya sa kwalonsa ya gama shiga rijiya, yana da burina rayuwarsa, shi ne ya buda ido ya ga cikinta ya tasa, ko zata daina rigima daga ranar?

Sunna nan zaune sai shiririta tafiarta yake, da kyar ta samu ta kubce masa

Ta yi mamakin yan rakiyarta matuka, yayunta ne su biyu da jakadiya da bayi mutanen dai masha Allah

Haka suka sakota tsakiya anai mata wani irin kirarin da ya sakata jin wani irin girma na hawa kanta, a haka har suka karasa bangaren AMMI

AMMI, Yaya Dayabu, Abih, da kannenta ne cike a wajen ana ta hira ana daria
Sai ta ji wata irin kunyar hada ido da su ta kama ta, bata taba jin haka irin na yau ba, ga bacin da take faman ji, ga tunanin barinsa da ya saukar mata da kasala

Basu dai samu yanda suke so da kanwar kuma yarsu ba, dan kuwa sama sama ta tsaya kafin ta shige dakinsu tana sauri

Tana shiga ta tarar da UMMU na ware jigidar nan da Zahrau ta ajiye sauran a saman sif

Da sauri UMMU ta sha murr gannin Najeeba ce, ta idasa fitarwa ta saka a jakarta tana kallon Najeebar dake kallon jakar tara

Daria kawai Najeeba ta yi ta haye bed din a hankali ta yi matashin kai da cinyarta tana mika

Ummu ta yi murmushi ta shiga shafa lalausan kanta, haka kawai ta yi ra'ayin yi mata kitso dan haka sai ta gyara mata kwonciyarta ta dauko kayan kitson ta haye gadon ta gyarata yanda zata ji dadin tsara mata kitson ta shiga yanyara mata shi kannana sosai

Ummulkhair kuwa ta dama masu lale na hausa , Ummukulsum ta je ta kawp skoth ta zauna tana yankawa sunna hirar su har baci ya dauke Najeeba......

YAYA DAYABU kuwa kayan UMMU ya ringa jida yana kaiwa motarsa har ya gama komai ya kulle motar ya dawo dan yana son ganawa da SULTAN yau yau din nan kafin ya kai kayan UMMU a kimtsa mata su dan an gama gyara an zuba kaya an gama jera komai mai dakin kawai ta yi saura, Mardiya kuwa tana wancen gidan na Abih
__________________________

Washe gari ta tashi da rashin kuzari, haka ta yi wanka ta kimtsa kanta suka ci gaba da ayukansu da yan uwanta

Wajen karfe goma suka yi waya da Zahrau da dukan yan uwansu hakan ya sa wayar ta dauki dan lokaci kafin su katse

Garin dan wake suke gyarawa zasu jwfa dan wakensu shelar shigiwar Sultan ta karade wajen

Ai kamar ana wuwurga su suka ringa tserewa kowa na shigewa ciki, hakan ya baiwa NAKEEBA daria har ta dara abinta ta ci gaba da hada garin da kanwa da miyar kuka ko foku

A lokacin da ya shigo sai da ya gama da iyayensa sannan ya karasa wajen da yake hangenta ta dage tana kwaba garin hankali kwonce da muciya

Zama ya yi yana kallonta, a ransa fadi yake hankalinta kwonce, yanzu haka ko tinawa da ni bata yi ba, dama fama take ta dawo ta zuba sangartarta

Gaishe shi ta yi tana dubansa, a lokacin shi kuwa sai ya zame ya zauna saman ledar da suka shinfida dan kar su bata wajen

Daga UMMU har AMMI ido suka zaro daga inda suke zaune da matsanancin mamakin gannin ya zauna a nan ba kan kujera ba, ba cike da takama ba

A hankali ya ce" Na ji, ko ki kiraye ni ko? "

A ranta ta furta'ina ni ina kiranka kana tare da matar so raina ya baci ', a fili kiwa baki ta dan tabe bata ce komai ba

Zamansa ya gyara da niyar yi mata tambayar da ya zo da ita, Allah yana ganni yana matukar mamakin lamarinta, haka kuma bai taba sakawa ransa wai tambayar na iya kawo matsala ba, dan haka hankalo kwonce ya ce" BEEBAH "

Dan dakatawa ta yi da motsawar tana kallonsa, jin ya yi mata irin kiran dake kasheta dan haka ta kura masa idannuwanta masu hadasa masa kasala

Sai da ya ja numfashi sannan ya dora da fadin" Me zai hanna ki baiwa kawarki abinda kike sha kike kasancewa haka? Na san mata fa bakwa rabo da dan taimakawa kanku"

Idannuwanta ta dan wara dan neman karin bayani, hakan ya sa ya dan kara matsawa kusa da ita a hankali ya ce" idan wani abu ne na sha kike sha , ki taimaka mata itama ta ringa sha, irin na saukar da ni'imar nan "

Ya salam, wani irin faduwar gaba mai hade da bacin rai ne ya ziyarceta, idannuwanta ta saka cikin nasa tana kallonsa kafin ta cire muciyar tana nuni bangarensa ranta a bace aman kuma muryarta ba sama sama ba ta ce" Ai ba sai ka min haka ba zaka nuna min ka sadu da matarka ba Shaheed, koda baka fada ba na san matar so dole ka kula ta, waima yaya kake tunanin zan saka damuwa a raina dan ka kwatanta min ka kadaice da matarka bayan kiri kiri ka nunawa duniya ji din ba kowa bace ta hanyar karbar hadin da akai maka a fili aman a zuci ka hadani da aminiyata? Sai me dan baka so na? Allahn da ya sa nima ban rasa mai sona ba, kafin kai nima ina da mai so na, kuma nima ina son abuna dan haka kana iya...............................................................................................DIF maganarta ta dauke sakamakon wani azababen marin da ya sauka a gefen kumatunta da kunnenta kadan ya yi sanadiyar dauke jinta harma ganninta ya fara nuna mata biyu biyu uku uku

Zabura AMMI ta yi tsaye ta furta" Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une, SHAHEED lafia?"
Tana fada ne tana yiwowa wajen da wani irin sauri

NAJEEBA kam daga tsayen da take ta durkushe kasa saman gwuiwoyinta , dan kwalin dake kanta ya fadi, kitson da akai mata ya bayana kansa sai yar sarkar dake wuyanta mai heart ta shiga dan yawo kadan kadan a wuyan nata, still hannunta na jikin kincinta

AMMI na karasowa da sauri ta duka ta kamata tana maimaita " meye haka? Me ta yi maka daga zuwa sai mari? Me ke faruwa? Me aka yi? "
Du a rikice take fadin hakan , shi kuwa yana tsaye kikam idannuwansa sun kada sun masa wani irin ja, gaba daya jikinsa ya dauki rawa tamkar yana filin yaki, hannayensa kuwa ya jimke ya saki, nan da nan jikinsa ya yi ja irin na bacin rai, idannuwansa suka kara kadawa
Kuma dagowar da AMMI ta yi ta ga yannayinsa a haka ya saka gabanta faduwa

Da sauri ta kama NAJEEBA ta mikar da ita , bata kuma ce masa komai ba sai jan NAJEEBAR da ta yi da sauro ta turata cikin kicin ta janyo kofar ta rufe

A tsayen nan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment