Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

dai sai itane ta dawo bayar da hakuri cewa a bari kar a saka
Abinda ya fi bashi takaici da haushi shine yarinyar ko A bata furta ba mutanen wajen ne ke ta hayaniyarsu tun dazu, ita ga isashiya

Karshe dai kashewa ya yi a lokacin da ya ji shara'ar ta koma neman sasanci tsakanin matar ambasador da kuma Najeeba, inda aka shiga sasanta su da gindaya masu sharudan kar wace ta kuma tarban wata da neman fada, shi kuwa aka yi masa kwakwaran kashedin ya zama namiji ya tsawatarwa iyalinsa sannan idan auren Najeeba zai yi ya maida hankali ya aureta ba ya ringa neman fitina da girmansa ba

Sai kusan magariba aka sake su

Ranta kwata kwata a bace yake a yau din nan dan haka ta zarce wajen da ake siyar da shawarma

Siya ta yi isashiya sannan ta karasa wajen hutun da takan je lokuta da dama


Wajen bai cika mutane ba, idan ka ga mutane a wajen tabata irin manyan yan gayun nan ne

Salaya ta shinfida ta gabatar da sallarta a wajen da hijab dinta dake cikin mota
Haka ta yi ta isha ta shafa fatiya

Mikewa ta yi ta adana komai ta dauko shawarmar ta zauna saman daya daga cikin kujerun wajen a lokacin duhu ya shigo sosai ta shiga harba yan kafafuwanta tana bude takardar shawarmar

A hankali ta rike a hannunta tana fadin" Aikin banza! Aikin banza aikin wofi! Shirme shirme shirme kawai! Ta karashe tana murguda bakinta

A hankali ya furta" ke da wa?

Da sauri ta dago dubanta, sai dai bata idasa dagowa sosai ba gabanta ya fadi haka kawai ba tare da ta san dalili ba

Wannan mutumen ne na ranar, wanda ya taimaketa ya fitar da ita
Yauma wani irin turarensa ne ya fara yi mata salama kafin ta sauke dubanta saman jajayen lebunansa
Irin yanda tsarin haliyar jikinsa take kuwa shi ya fi komai bata tsoro
Haka kawai ta ji jikinta na yi mata wani yam yam yam dan irin yanda take gannin idannuwansa da girma ga kwali sai ta ji tsoron kar dai aje aljani ne?
Bata idasa tunanin da take ba ya karasa saman kujerar dake daf da tata ya zauna yana jan dan karamin tsaki a cikin zuciyarsa yana mai dannar kansa cewa ka yi hakuri, ta hanyar nan ne kawai zaka iya cinma burinka! Ka yi hakuri.
a fili kuwa sai ya furta" kema an kona maki zuciyar ne? Ya Allah ban san menya sa mata suke haka ba!

Gaba daya sai ta ji kanta a takure, abincine fa zata ci ya wani sakota gaba, to wai wayema shi? Ina ruwansa da ita ne? Ita dake boyon cin abinci idan ba da yan uwanta bane sai anmy sai abih
Haka kawai wani garjehen kato ya wani shiga yi mata bayanin da bata tambayeshi ba? Yanzu haka da budurwarsa ya yi fada, shirme! Shirme! Aikin banza kawai!

Da yannayin tsiwa ta dube shi ta ce"....
......



Commetn comment na sis

Ina jin dadin comment dinku, karo min zai karan karfin gwuiwa hajiyoyina=Ø Þ=Ø Þ
[1/23, 6:57 PM] Ummu Suhan=Ø
Þ: >ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



15




Da yannayin tsiwar nan ta ce" ka sanni ne?

Kwarai hakan ya bashi mamaki, ya matukar bashi mamaki, shi? Shine yau mace macenma wace ya fi rainawa take furta masa magana haka kai tsaye?

Saurin kawar da hakan ya yi yana kirmiro murmushin da bai yi ba baki daya wunin yau ya miko mata hannu irin su gaisa din nan yana fadin" je suis desoler ( i'm sorry), ban gabatar maki da kaina ba, FARID ELHAJ BASHIR by name, ni dan Abuja ne ina shigowa garin nan ne dan kawowa yayana ziyara Elhaj Muctar Garba mai gold, ni matukin jirgi ne sannan dan kasuwa ne

Du wannan jawaban da ya yi Najeeba ta yi sakalau da abincinta a hannunta tana kallonsa
Tambayar da take yiwa kanta shine, to ita ina ruwanta ko tambayarsa ta yi ne?

A hankali ta bi hannun nasa da ya miko mata yana nufin su gaisa ko me?
Wani sakaran murmushi ta dan sakar masa ta maida hankalinta kan ledarta ta dan duka ta dauke sannan ta mike tsam ta koma kujerar dake nesa da shi ta barshi nan sakaye da hannu baki da hanci bude cike da mamakinta

Wai bata ganninsa sa kyau ne?
Duba da irin shigar da ya yi tau ya yi shiga ne irin ta yaran atajiran nan, ya saka riga da wando na wani mahaukacin yadi wanda koda baka san yadi ba idan ka gansa a idannuwanka zaka gane ba fa na wasan yara bane
Ya dora yar hula a kansa wace ta kara kashe kyansa ta fitar da dogon hancinsa zuwar sannan ta kara masa kima
Rigar ba wata mai budadan hannu bace, dinkin ya kama hannayensa sosai har kana iya gane hannayen nan nasa bafa na wasa bane
Sai ya ringa dan kara kallon kansa a kaikaice kafin ya yi gagawar karyata abinda yake tunani ta hanyar fadawa kansa kalamai kamar haka" ranta ne a bace, shi yasa ta ki baka hannu, idan ba wannan ba yarinyar dake jira a tayata ta karba a guje?

Tuna hakan da ya yi ya saka shi kara baiwa kansa hakuri ya mike cimak ya koma kusa da ita, wannan karon face dinta ya zauna yana dubanta ya ce" i'm sorry plz
Na bata maki rai ne? Nima ina cikin damuwa ne shi yasa kika ga ina yi maki magana haka sannan kamar na taba ganninki

Sai kuma ya dan zaro ido ya ce" oh yes, ke ce, ranar nan na fitar daga stade kun je ke da saurayinki nah?

Tsatsareshi ta yi da ido ga abincinta ta cira ta fara taunawa hakan ya saka ta kasa ci gaba da taunawa sai kawai take kallonsa
Ko maye ne? Abinda ta tambayi kanta
Idan ba raini ba shi a nan bai gane ni ba sai yanzu?
Ta kuma tambayar kanta

Sai da ta juyar da kanta ta labe fuskarta ta karasa taune abin bakinta sannan ta juyo tana dubansa ta ce" aman bawan Allah fisabililahi me na yi maka ne? Ka dai san tunda na baro gidanmu na zo nan kadaicewa nake da bukata kuma shikenan sai ka shiga zayano mon magangannun da ya shafeka? To waima an rubuta a goshina cewa ga NAJEEBA maganin damuwarka ne? Plz ka girma ka je ka iya da matsalar budurwarka haka kawai ka wani matsa min , to ni ba ni ka ganni a inda kake tunanin ka ganni ba


Tana gama fada ta mike ta bara masa ledar a nan ta yi gaba da sauri ta karasa wajen motarta tana jan tsaki ta fada ta rufe ta tayar ta warceta da gudu gudu ra bar wajen

Zuwa wannan lokacin har sai da ya talabi habarsa dan mamaki
Wato ita bata tsoro ga tashen iskanci ko? Bata tsoron ko shi wani mugu ne ya fafalawa fuskar nan tata mari ta zo ta saka abin idannuwan nan dake mayar da ita tamkar wata aljannah ta tata masa rashin mutunci ta tafi

Kansa ya girgiza ya kai dubansa wajen ledar

Dauka ya yi ya buda ya ciro abinda ke ciki

Jujuya abin ya ringa yi kafin a fili ya furta" da na halal din ko da na haram din aka siye ku?

Mayarwa ya yi ya ajiye a nan ya mike yana tafe kamar mai jin tsoron taka kasar ya bi ta cikin duhun da ya ratso ya shigo wajen yana mai ayanna" sanu sanu dai bata hanna zuwa, zaki yi bayanni ne daga bakin lokacin da na kama ki da laifinki, na rantse maki sai na fitar da ke waje zan hukunta ki a wajen da ba wada zan iya kallo na daga maki kafa marar mutunci kawai!

.......................................


Hotunnan y'an matan da aka turo masa ne yake bi ta compte professional dinsa

A gajiye yake tilis, ga kallon hotunnan da yake yana son a yau a yau din nan sai ya fitar da yarinyar da za'a kawo masa a matsayin mace ta biyu gidansa
Yana son kara auren nan ba yau ba sai gashi da banzarsa ta buda masa hanyar yi

Ya yi hayaniya mai yawan gaske hakan ya hadasa masa da gajiya mai yawa sai kawai ya dawo juyawa a saman bed din yana sauke ajiyar zuciya

Shi kam a kan hitunnan wasu yan mata uku ya tsaya
Ba dan komai sai dan irin shigarsu ta kamala sannan iyayensu mutanen kirki ne
Biyu y'ayan hausawa ne sak, dayan ce bafilatana

Turawa wanda ya turo masa ya yi, kafin ya mayar da kansa har ya turo masa da message kamar haka" *Su duka ukun uban gidana?*

Tambayar ya kurawa ido, su duka ukun? Sai ya ji wani abu na ce masa me zai hana ka dauke su su ukun? Idan ka yi hakan ka gama cikewa sai ka koma gefe ka karbi salon kowace

Bai bashi amsa da gagawa ba, shi kuwa ya yi ta jiran amsar karshe shima ya bar wayar a kunne ya kasa kashewa dan gudun ya sauka a je ya turo amsar

bayan ya gama salar asubah ya dawo bangarensa ya kwonta yana duba agogon dakinsa ya lumshe idannuwansa

Irin yanda zinariya ke ta tsatsareshi da ido aman ta kasa tambayarsa abinda ta masa ke bashi mamaki
Me ke damun kwakwaluwar yarinyar?
Shin sarautar ce ko sakarci ne?
Yakan cika da mamakin wasu abubuwan nata
Tabas shi mutun ne mai son sauki a rayuwarsa bai san dalilin da ya saka mutane da yawa ke tunanin ya cika son zafi ciki kuwa harda abokiyar rayuwarsa wace ya dace ta fi kowa sanninsa da fadin halayansa

Yana so ace matarsa ta san cewa shi mutun ne mai son shakuwa da mace
Yana son ya gabatar da rayuwar aure irin yanda ma'aiki ya koyar
Yana so koda bai cika komai daidai hakan ba ya kwatanta
Ya so ace shi din mutun ne marar nauyi a kansa, da ya rantse abinda zai hana shi zuwa ga matarsa lalle baba abu ne
Sun yi auren biyaya ga iyayensu da zinariya, ya sameta a matsayin cikakiyar budurwa, sai dai a kulun abinda yake nema ido rufe ya rasa shine kasancewarta irin matar da yake so
Yana so idan ya fita ya bayar da umarni idan yana daka a umarceshi cikin kissar da shi kansa ba zai gane umartarsa aka yi ba
Yana so tsakaninsa da matarsa idan da ido ta yi bayani ya fasara abinda take nufi koda a cikin duban mutane ne
Yana so tsakaninsa da matarsa ace idan akoy wani abu mai sunna kirari to fa ta yi shi ne a lokacin da idan ta yi shi zai kara kaimin faranta mata ya farantawa kansa ya lula da su a cikin duniya mai dadin gaske
Sai kawai aka samu matsala tasa matar takan kwashi kirari ne kamar wata jakadiyarsa a duk lokacin da suka hadu
Shin sai ya koya mata ne ko sai ya karo auren ta ga yanda wata zata wakanar sannan itama ta dauki hannu?

Murmushi ya yi yana adu'a dan samun hutu, ya gaji walahi yawan maganar nan ta jiya ba karamin gajiyar da shi ta yi ba hakan ya sa ya takaita maganarsa daga jiyan zuwa yau a wajen gaishe da mahaifiyarsa ta hanyar sirrinsa ne kawai ya budi baki ya yi wata maganar

Bai waiwayi wayarsa ba sai da garin Allah ya waye sosai har kusan karfe goma sha biyu

Yana gama daura agogonsa ya janyo wayar nasa
Direct cikin message dinsu ya shiga ya rubuta" halayanta su zamo nata ne ita daya, ta kasance mai halayan dawissu
Ina son wace ta san kanta
Ina son wace ta rufe kanta
A yanzu ka ware daya a cikinsu ka tabatar komai ya gama a yau dan ina so nan da kwana hudu a gama komai ba zan ja ba, ba zan yi wani gangami ba dan ba aurena ne na fari ba!


Yana gama turawa ya zauna bakin bed dinsa yana jin wani haushi haushi
Ya tabata bai isa ba, komai yanda zai kiyaye tara mutane sai sun taru an masa yawan magana da tsarewa
Shi kuwa alkawari ya yiwa kansa sati ya baiwa kansa sai ya ajiye wata macen a saman bed dinsa wace zai raya sunnar ma'aiki da ita,
Wace zata cike zargin zinariya, ta faranta ran Anmynsa ta hanyar bin umarninta,

Ajiyar zuciya ya sauke duba da bata lokacinsa ne yake sannan ya mike ya koma dakin da yake hangen abubuwan dake wakana a masarautar

Kansa kan daukan caji fiye da tunanin mai karatu
Matsalolin cikin gidan marauta a gaban idannuwansa suke, da yawa sun fi karfin titsiye su tashi daya dole ta sannu yake binsu ya ruguje su, da yawa rainin hankali ne yakan yi kamar bai ji ba bai gani ba
Shi dai a matsayinsa na sarki mafi yaro a wannan karni yana iya yinsa dan gannin yana kare wasu abubuwan

Shi mutun ne mai son motsa jikinsa kamar me, motsa jiki a wajen da ba wanda zai zo kallonsa ko ya san shi waye hakan ya saka yake fita da mutun kwaya daya tak su je wani tafkeken filin LAKD ya bale a guje ya yi ta gudu son ransa
Idan ya yi ya gama ya yi pompe mai yawan gaske sannan su je wajen da yake shan dadar iskar garin ya zauna ya saje da kowa ya sha iska ba tare da ya yi aboki ko budurwa ba
Ya saba fitarsa ba yau ba, idan bai yi fitar sirrin nan ba tabata wani abu mai karfi ne ya hanna masa yin hakan......

Wannan kennan
............................................

Kallon sarkokin Abih yake daya bayan daya wa'inda Dayabu ya saka aka yi masa tun daga kansa har zuwa kannensa

Irgawa ya yi ya kuma irgawa ya kalli DAYABUn, to ko ya manta su goma sha takwas ne?
Sai abin ya so bashi dariya da ya ambaci hakan a zuciyarsa
Me zai hanna shi mantawa kai kuwa? Ya kuma tambayar kansa

Abih ya kuma daya sarkar ya kalle shi ya ce" to kaima sakawar zaka yi?

Murmushi ya yiwa abih ya ce" hum Abih rigimar y'arka ce wai yo sai na saka mana kamar wani dan daudu ko wani dan duniya

Daria Abihn nasa ya yo yana bin yan siraran sarkokin zinarin da kallo
Tabas yana godewa Allah da samun baban d'a mai hankali da nutsuwa wanda yake iya yinsa dan gannin yana gyara irin barnar da shi ke aikatawa

Koma meye dalilinsa na sakin mata bashi da kyau domin saki Allah ya halata shi aman shi kansa baya son sa
Shin y'ayansa sunna jin haushinsa ko? Irin yanda yake korara matansa haka kawai
Akoya matarsa da ya saka wace zai iya rantsewa bai kamata da laifin komai ba, ya saketa ne dan ya wayi gari da maganar cewa a kan me ita zai barta bayan ya rabu da iyayen sauran? Sai mahaifiyar NAJEEBA wace ta maka shi a kotu sai ya saketa

Murmushi ya kuma yi yana kallonsa ya ce" yayansu ka manta ku goma sha takwas ne y'ayana na cikina?

DAYABU ya dago ya kurawa fuskar Abih ido, a hankali ya ce" aa mu goma sha tara ne Abih

Gabanta Abih ne ya yi wata irin yankewa ya fadi wanda hakan ya saka shi saurin zabura yana kallonsa

Su goma sha tara ne?

Ku goma sha tara ne? Ya maimaita masa da sauri ya dora da fadin" a ina ka samo ta cikon sha taran?

Fuskarsa dai ya kuma kurewa da ido yanai masa kallon nan da ake fadin kai ka san na san da hakan
Sai ya yi gagawar basarwa yana murmushi ya ce" Abih, na manta ne, wani sa'in fa garin magana har cewa na yi mu goma sha uku ne sai da zahrau ta yi ta min daria

Wata biyayiyar ajiyar zuciiya uban ya sauke sai dai sak ya kasa sakin jikinsa su ci gaba da hirar kamar yanda suke a dazu

Sarkokin ya kuma rikewa yana fadin" ina ta NUSAIBA?

duban mahaifinsa ya yi ido cikin ido a karo na biyu ya buda bakinsa ya ce" ban yi da ita ba

Uban ya tsare shi shima da ido, kamar yaya bai yi da ita ba? Amsar ba wata a boye take ba a bayanne take cewar bai yi da ita ba
A kan me bai yi da itan ba? Mantawa ya yi ko yi ne bai yi da ita ba? Aa ai ba cewa ya yi ya manta ba, cewa ya yi sak bai yi da ita ba

Sai ya ji wani shaku da tsoron son jin abinda ya saka yaron nasa na farko a rayuwa yin wani abin kyautatawa wa kannensa banda daya a ciki
Hakan ya saka shi fadin" gaba kuke da mahaifiyarta har yanzu wanda ya shafeta ko wani abu mahaifiyarta ta yi maka ne?

DAYABU ya sauke ajiyar zuciya yana murmushi ya ce" Abih, ka san bamu taba zuwa muka kawo maka karar matarka ba
Da yawa wasu matan ka sake su ne dan kawai idannuwanka sun kama wani abinda bai dace ba a kanmu

Ban san girman laifukansu ya dame nata ya shanye ne? Ban san ita din lale gaskiyarta ne itace rayuwarka ba? Abinda na sani shine na gaji da sakin mata da kake, kuma bana so ka kuma sakin mace dan a yanzu na lura lalefa kanena sun taso har sun fara gabatar da mazajen aure wanda nake fatan idan sun shiga sai dai a fitar da gawarsu fita na har abada
Abih abin zai yi matukar wahala sai dai ikon Allah kawai zai kubutar da su
Shine nake so ka yi kokari ka yi zamanka da matarka , in sha Allah idan dai mune damuwar ba zamu kuma zama damuwa ba aman fa Abih muma a kiyaye namu rayuwar dan kai ka san cewa ba zan iya lamuncewa mutun shiga hakin yaran da nake yiwa kallon marayu
Basu rayu da baban jigo na rayuwa ba wato uwa
Hakan ya saka nake yi masu uzuri a rayuwar yau da kulun, hakan ya sa nake kara jin tausayinsu

Abih kam ba amsarsa ya samu ba, sai dai gannin yaron nasa ya daure shi da jijiyoyin jikinsa sai kawai ya yi masa shiru bai kuma tofa komai ba aman ya kuduri niyar tambayar ita natar tasa dan ya tabata bafa zasu fada masa komai ba tunda har yayansu ya hana............................

Sarkokin ya mike da su ya nufi cikin dakansa

DAYABU na zaune yana kallon ikon Allah, Abihnsa zai fito ya bashi sarkokin ko ba zai fito ba? Har ya kusan cin rabin awa karshe ya mike yana murmushi ya girgiza kai ya yi gaba dama ya yi hakan ne dan ya isar da sakon cewa ya cire y'arsa a cikinsu!



Ihu ta saka bayan ta kashe kiran da suka gama da Anmy

Da wata irin daria ta ce" jama'ar gidanku wannan karron ina gayya, ina gayya ne da kaina kuma sai na buga wasa a kofar gidan sarki

Ummulkhair ta dago daga yankan akaifunta tana yiwa kanwar nata kallon anya Najeeba baki haukace ba kuwa?

Najeeba ta ce" ke ke aunty, wallahi du jarabar da za'a yi sai na kirawo ANNABO MAWAKI ya kada min waka da orchestre na shiga na cashe domin kuwa *DUNKUM* zai kara aure inji Anky, kuma auren nan da kwana biyu ne taxe maza maza mu je wajen mai dinki ta tura sakwanninmu mu zabi kalar da muke so

Zahrau ta fito da waya tana daria itama ta ce" haka fa sannan Anmynki ta ce kar ki yarda ki dauki dinkin da bai mata ba dan ba sakashi zaki yi ba!

NAJEEBA ta waiwaya tana kallonta ta ce" wai kin san aurensa mai yake nufi? Hehehe, yana nufin za'a kawo wata yar rainin hankalin ta biyu wace zata ci min uwar wace ta raina halitar Allahn ta farko ta dane min kan banza ta daki bakin mai bakin shegun nan, zamu ga karyar zagi da takama za'a yiwa zinariya kishiya da gold>Ø#Ý>Ø#Ý>Ø#Ý>Ø#Ý






Hum a dai a slow najee
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



16





Hakan ne ta kasance abu na manya nan da nan abubuwa suka kankama cikin dan kankannin lokaci a wajen mutanen da suka iya aiki da lokacinsu

Nan da nan mutanen da anmy ta ringa fadawa suka fara halara cikin masarauta

Su Najeebama sun tare a gidan ne tun ana gobe daurin aure hakan ya sa gidan ya ringa yiwa Anmy dadi ga uwa uba irin yanda Najeebar ke ta yi masu kitso da kunshi cikin nutsuwa a daka

Idonsa cikin nata ya ce" in sha Allah gobe za'a dauran aure ZINARIA

Irin yanda maganar ta daketa ta sakata baki daya yin luuuuu zata kifa hakan ya saka shi yin taku biyu ya damki damtsen hannunta ya tareta a jikinsa ya yiwa bayanta mazauni a kirjinsa

A hankali ya kuma fadin" ki daina yi min garage da yaron cikin nan, dan shine abinda zaki yi mafi ganganci a rayuwarki wato barar min da shi da gangan

Tabas ta gama yarda cewa kwananta ne ya kare a wannan rana a irin wannan lokaci a tare da sarkinta

Kukan da take rikewa ne ya samu damar kufce mata da karfin gaske har tana cicije lebunnanta

Me ya sa? Me na yi? Me na gaza? Kyauna ya rage ne ko hasken fatana da ya saka aka min lakabi da zinaria ya disashe ne ya mai garina? Ta fada tana rike hannayensa baki daya ta kuma fadin" kar ka yi auren nan, idan ka yi na koma baya, idan ka yi ko a cikin kawayena na daina tinkahon kaf cikinmu nice bani da kishiya, idan ka yi min haka ko a masarautar AZ za'a kafa tarihin lamarin domin mahaifiyata ta jima kafin a yi mata kishiya kuma daga ota ta rantse ba kari! Kar ka min haka dan kishiya mafisa ce, balaki ce,
Shin y'ar gidan wani sarki zaka aura? Wani sarki ne ya baka y'a? Wata gimbiya ce ta yi gigin hada aurenka da y'arta bayan ta san wada ke cikin gidanka?

Ikon Allah shine abinda ya tsaya ganni a tare da Zinariya
A yau sai yake gannin ta fi sako reputation dinta a kan gaba fiye da ainahin kishinsa da ya dace ace ta furta kalaman tana son sa tana kiahinsa tana kishin hada shinfida da shi

Da karfi ya juyota sunna facinha din junna inda ta sada kanta kasa jikinta na bari tana mai ci gaba da kukan nan

Ya so kwarai da gaske ya rarasheta koda kuwa itane silar karin auren nasa a yanzu
Aman irin kalamanta sai suka nuna masa ita tana tunanin wani abu na ta isa ya jinkirta masa karin aure? Ashe har takamar mahaifiyarta kennan cewa wancenma da ta shigo da kyar ne kuma daga ita ba kari?

Murmushi ya sakar mata daga cikin rawaninsa wanda rabonta da gannin fuskarsa kiri kiri tun randa ta shigo ya yi mata gargadi da idannuwansa

A hankali ya furta" sai ki ce da du wanda ya yi maki tambayar yanda aka yi aka maki kishiya cewa *komai ai mai shudewa ne, ko ya bace bat ko a cenje shi*


Yana gama fada ya juya yana tafe cike da kasaitarsa da mulki ya shige cen ciki domin dama a falonsa baba ne suka yi maganar

Wani ihun kukan ta saki tana ta rike kanta mai sanye da hular alkyaba

Da sauri ta juya dan komawa bangarenta, ya zama wajibi ta yi kiran mahaifiyarta ta sama mata mafita
Baban abin takaicin auren gobe? Me ta masa? Shine abinda ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment