Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

za'a bani dama ba? Bana tunanin zan iya bari ki ci gaba da zuwa wajen nan, zan sama maki aikin ofice ki kasance a kilace Najeeba, idan wata ya mutu ki dafe manya manya dan na san takardunki, Nadia ta fada min irin takardun da kike dasu

Murmushi ta yi tana kallonsa ta ce" waye ya ce maka aikin office ke birge ni? Ka ga aikin nan, shi na tashi da shi a cikin abubuwan da nake son yi a rayuwana shi yasa ka ga na ware nan
Da kake maganar aikin office, kidaya min zan iya samun nawa a wata?

Huzaifa da gagawa ya ce" zaki iya samun jaka dari hudu, ke har akoy na dari biyar din da zan iya zuwa na samu abokin mahaifina ya sama maki gurbi a wajensu domin idan ya ji matata ce zai samo mana da guduma

Murmushi ta masa ta ce" a ranakun da ban yi kwaliya ba, nakan tashi da jaka dari da arba'in, ko dari da hamsin, idan ba'a samu isasun mutane ba nakan tashi da jaka saba'in ko tamanin

Idan na samu yan kwaliya, amare nakan yi masu kwaliya a jaka hamsin, kawayen amarya kiwa jaka ashirin masu zuwa wajen biki jaka goma
Akoy ranakun da nake tashi daga shago da zunzurufun kudade kusan jaka dari hudu ko sama domin idan aka ce maka juma'a ce, asabar da lahadi wajen nan cika yake da mata da yan mata, amaren ne da uwayen gida,

Wayarta ta janyo iPhone tana kallonsa ta ce" irga min, ka dauka a jaka dari dari kulun zan iya tashi da nawa a wata?

Nadia ta ce" million uku

Najeeba ta yi murmushi ta ce" ba ruwa nake biya ba, ba ni ke biyan wuta ba sai idan na yi ra'ayi, Abih ke biyan duka
Idan kayana sukai kasa Anmy ke min oder ta cika min shago

Idannuwanta ta kara kura masa ta ce" shine zan je office na yi me karkashin ikon wani?
Murmushi ya ringa yi , a ransa kuwa ya yarda cewar ashe dai kasamcewarta babar yarinyar ba iya iya kwaliya da kyaun tsari ta tsaya ba, aljihunta nauyi ne da shi, rikakiyar boyayiyar mai kudi ce , to aman yaya aka yi ta zama lashe money? Shi fa ko gara ce ita wace take iya karar da dukiyarsa ya ji ya gani yana sonta

Rage muryarsa ya yi ya ce" ina son ki NAJEEBA

Sai da ta ji wani dan ras, tabas zuwansa kai tsaye da kalamansa na sakata kallonsa da duba na daban

Cire dubanta ta yi daga fuskarsa hakan ya saka ya kara matsota sosai yana kallonta ya ce" ina son na aureki Najeeba, dan Allah ki yarje min mana?

Kuma duban fuskarsa ta yi, tabas Huzaifa namiji ne mai kyau bakar fata ne shi mai tsafta,
Yana da fara'a sosai gashi mai tsayi daidai misali, yana da kakauran jiki sannan yana da dan tumbi na jin dadin rayuwa

Murmushi ta yi tana cire idannuwanta daga kansa,
Wayarta ne ta dauki kuka da wakar su akon wace yake fadin For ever i love for ever........ da yake ta kuma ajiye wayar a saman kujera ya saka du suka kai dubansu

*LIKITAN ZUCIYATA* , shine ke haskowa a saman sunnan mai kiran

Bata damu ba ta mika hannu ta dauko sannan ta daga

Salama ya yi mata kafin ya furta" ina cike da begen ranar da zan ganki, shin kina Niger kuwa?

Sai da ta dan saci kallon Nadia ta ga kamar zata dauketa da mari sannan ta dan yi murmushi tana satar kallonsa sai ta ga fuskarsa ta dan cenza daga yannayin fara'a zuwa sad

A hankali ta ce da shi" zan taboka Likitana

Shima murmushi ya yi ya kashe yana fatan ta tabo shin

Idan kana da time, ranar Wednesday ka zo fada

Farin ciki ne kuma ya mamaye zuciyarsa harma ya kasa boyewa da yatsunsa ya irga cewar....nan da kwana uku ko?

Kanta ta daga hakan ya sa ya mike, chek din da ya rubuto makudan kudi ya ajiye kusa da wayarta sannan ya juya yana murmushi ya masu salama

Da sauri Nadia ta dauki Chek din tana dubawa sai da ta yi dan ihu kafin ta ce" ke, wai kin san nawa ne?

Najeebama tana ta daria tana kallon chek din ta ce" da alama dan uwanki banar harka ne

Nadia ta ce" Najeeba ina fada maki ko waye shi kennan baki yarda ba? Babar harka ne,

Najeeba ta ce" na san waye shi, abinda ya sa na bashi matsayin babar harka nawa suke da kudi aman basa iya cirewa su yi kyauta da su? Sai ki ga sun tatare budurwa ita ba ga wani ba sai su kadai aman dan iskanci kudin zuwa saloon sunna bakin cikin bata? Gaskiya irin mazan nan basu da Mutunci!

Nadia ta ninke ta soke mata ita cikin jakarta tana fadin" bana tunanin zai kasance irin mazan nan, domin ni kaina dominki kwana biyun nan hajia ce bale ke

Ita dai Najeeba litafin da ake rubuta wa'inda suka nemi mak'up ta dauka tana ta dubawa dan gannin wanda zasu samu

Sai d yama ta yi sosai wajen ya kuma fara saukan mutane masu fitar dare

Ita dai zuwa lokacin sai ta kilace kanta sunna hira da yar uwarta wace ke magana kasa kasa bata jin dadin jikinta domin a jiya dai sarki sai da ya karbi sadakinsa

NAJEEBA ta zaro ido tana ganni uwar sarkar da ya baiwa Zahrau da makulin mota da hoton motar da kyautar wasu kuyangin amana kafin ta ce" Zahra wai kyautar meye wannan?

Zahrau ta yi murmushi kawai ta ce" zaki san ko ta meye, ba yanzu ba

Itama murmushin ta yi tana kallon uban badon da ta markada ta zabga masa madara da karanfani fiye da adadin da aka bukata ta kafa kai ta shanye
Zahrau da suke vido call ta zaro ido ta ce" Najeeba, ba zaki daina shan kayayakin gayran jikin nan ba ko? Gashi wa'inda kike dura min sai da na raina kaina , Najeeba sai da na ringa maki Allah ya isa

Najeeba ta yi murmushi tana gyara kayan gefe guda sannan ta rufe frij dinta ta koma ta zauna ta ce" aunty, ko gobe na ji abu naturel wanda zai sharen fage ya gyaran jiki zan yi na sha abina dan a gaskiya ba zama zan yi sai an tashi yi min aure a shiryani ba

Zahrau ta girgiza kai ta ce" anya ba babar mai jaraba bace ke kuwa? To yanzu idan kika auri mijin da hakan bai dame shi ba?

Najeeba ta yi murmushi ta ce" aunty ai shikenan, kin manta ban saba ba bale hakan ya wahalar da ni? In sha Allahu ko wani kalar miji na samu shi zai horani ta yada yake so na zame masa

Zahrau ta yi murmushi ta ce" wa kika tsayar? Dayabu ya fada min komai, dazu mai martaba ya turon sakon na tura number Ummu yarima na tambaya zai kirata , ke da Ummulkhair ku na sako gaba yanzun

Najeeba ta koma ta zauna tana sauke ajiyar zuciya, a hankali ta ce" ni kaina ban sani ba, abinda nake son yi zan tsaida kwara biyi, a cikinsu sai na kaiwa Allah kukana kan ya zaba min daidai da ni

Zahrau ta gyada kanta daga ringeshen da take, tana mai adu'ar Allah ya basu mazaje na gari, kwari ta yi mamakin irin yanda Najeeba ta yarda zata fitar da miji haka cikin sauki, sannan a yanzu ta kara jin nutsuwa ta shigeta jin cewar Najeebar da kanta ta kara jadada mata har Najeeba ce zata fitar da miji? Lale ta yarda kanwar tata ta fara zama mutun mai nutsuwa

Sun sha hira kafin suke katsewa ta barta cike da tunanin abinda ta fada cewar su janyo yar uwarsu jikinsu
To ita ta ina zata fara wannan lamari bayan Abih bai san cewa sun san da maganar ba? Yarinyar kanta menene halayenta shin tana da ra'ayin kasancewa da su a matsayin yan uwanta?

Bayan salar magariba ta shirya cikin wando da rigarta na spot ta saka takalmanta tun a nan kafin ta dora hijab dinta dogo har kasa ruwan ja mai duhu

Salama ta yiwa yaren shagonta ta harhada kudadenta cas sannan ta fito daga ciki

Bude mata daya ya yi da gudu sannan dayan ya zagaya ya shiga wajen direba ita kuwa ta shiga baya ta zauna daya ya zauna gidan gaba suka dauki hanya

A hankali ta masu bayanin inda zasu fara zuwa

Sunna zuwa ta ciro jaka goma ta mikawa na zaunen ta umarce shi da ya yo nama leda biyu a saka tukunya a dayar mai zafin gaske

Fita ya yi ya siyo naman ya dawo yana kokarin ajiye mata

Mai dauke da tukunyar ta ware ta mika masu dayar ledar, dan murmushi ta yi ta ce" na san baku ci komai ba ko? Ku ci abinci mana kuma ina dalili wai wannan kamewar? Kun ga dai ni kanwarku ce ba ruwana ba abinda zan maku ku ci abincinku mu je stade bangaren basket ball a cen zan buga ball yau
Kasancewar ta yi bayanin sport dinta harma Anmy ta amince sai dai ta fada mta cewar lokacin da aka yanke mata kar ta saki ta wuce shi a waje ya saka basu yi gardama ba, sannan alkhairin da ta masu ya saka suka ji dadi dan walahi yinwa suke ji an basu kudin abinci fa kawai ba damar su motsa ne yau suka fara aikin nan dole haka suka wuni da yinwarsu

Sunna karasawa ta cire hijab dinta daga cikin motar take hangen wajen

Terrain din bashi da dati ko daya, shi terrain din ne bai cika samun mutane a ciki da dare ba, da yama aka fi basket a samansa idan dare ya yi sai ya zamana yan gayun yan kata da samarinsu ke zuwa su yi zancensu a nan
Daidaiya zaka ganni a saman wajen sun zo buga basket

Shi daya kwal ta gani da wata irin ball a hannunsa
Irin yanda yake juyawa ya daka tsale ya jefa ball din cikin raga ya sakata shagala da kallonsa

*Freind* ta furta a hankali
Ashe kana basket? Ta kuma tambayar kanta

Sai ta ringa jin wasan na kara shiga ranta irin yanda yake bugawar sai kace wani jordan

A hankali take karasa takawa har ta isa

Bata yi masa magana ba sai gudun da ta fara shi kuwa tun da ta tinkaro amintacensa ke sheda masa ga wata na matsowa idan kar a barta ta karaso a tare ta,

Yana fahimtar itane ya furta" barta

Gudu ta ringa yi cikin nutsuwa da earpiece a kunnenta tana sauraron kidanta mai tashi a cikin sanyo ba kwaramniya

Sai da ta hada zufa jinna sannan ta shiga cirewa ta ajiye saman abin zama

A hankali ta ringa karasawa inda yake buga ball din shima ya hada zufar kamar me aman ya kasa bari dan ba yanzu yake bari ba sai ya gama bugawar yake zuwa wajen hutunsa ya dan huta kafin ya tafiarsa

Yi ya yi kamar a lokacin ya ganta ya juyo yana dan doka ball din tana dawowa hannunsa yana kallonta

Shamatarta ya yi ya cilo mata, da sauro ta cafe ball din itama ta shiga dan dokawa tana tunakararsa

Fahimtar da ya yi cewar tana son ta tsineshi ne ta je ta saka ya saka shi kokarin karewa yana tarewa ita kuwa tana neman hanyar bu tun karfinta

Sai da ya bari ta sha wahaka sannan cikin sauki ya karbe ball din ya juya ya yi wani tsalen da ya sakata zaro ido cike da mamakinsa daga inda yake ya cila ball din ta shige zuruf wato 3 point

Abin ya kayatar da ita, hakan ya saka ta shiga tafawa tana yar dariya cike da mamakinsa

Ai kuwa nan wasa ya bale suka ringa yi sunna kasawa da gudu sunna kilkila dariyar da su kansu basu san ta yi nisa har haka ba su dai dariyarsu suke sha idan ya amshe ball din

Ball din na hannunta ya dagata sama da hannunsa daya yana mata daria kadan kadan

Irin yanda take daka tsale tana fadin ya tsaya dai ya ga ikon Allah sai ta kamo ya shagaltar da shi harma ya kasance idan ta daka tsalen kanta na dukan kirjinsa sannan da hannayenta ta saka ta daki kirjin nasa tana fadin" in ba tsoro ba baki korere mana

Idannuwansa ya lumshe ya kuma budewa ya sakar mata ball din

Warta ta yi da gudun tsiya ta nufi ragar
Sai da ta karasa ta wurga ball din
Ai kuwa ta shige ciki hakan ya sakata sakin dan ihu na murnar ta saka sannan ta juyo ta shiga kwaso shoki tana watsa masa

Daga inda yake bai motsa ba sai hannayensa da ya harde yana kallonta
Murmushi ne ya subuce masa a lokacin da take kwasar shokin nan kafin ya dan girgiza kansa ya cire kansa daga dubanta yana gannin yanda mutanen dake zaune sunna zamcensu suka dauki hankalinsu harma suke kyakyata dariyar lamarin da masu yi mata tafin ta saka daya kwal bayan tun dazu yake ta sakawa ta kasa sakawa

Kansa ya dan girgiza ya juya ya nufi wata lafiyayiyar kujerar da aka ajiye masa da ruwan gora da abin goge zufa fari kart sai kamshin fitinanen turaran nan nasa yake ya yi ya karasa ya zauna

Ba din ta dauko ta kara jefawa sannan ta kuma daukowa tana kallonta ta gane ba karamar ball bace irin wa'inda ake kawowa daga americar nan ne masu tsadar gaske da karko

Wajensa ta karaso tana jin mugun kishi dan kana gannin fuskarta zaka gane ta sha wahala sai shasheka take sosai

Goron ruwan da ya bude ya kafa kansa ya dan sha kadan take kallo
Gannin ya sha sai ta cire kanta a wajen tana gannin yanda yake dan goge zufar jikinsa har wajen wuyansa
Ball din hannunta ta nuna masa ta ce" ball din nan ta kanpani Kapto ce? Ko copy ce?

Shima kallo ya yi kafin ya yi dan murmushi, wai copy wato ba zai iya siyanta ba take son sani ko?

Sai ya dan daga kafadunsa ya ce" ita ce, yayana ya siyan min

Bakinta ta dan tabe tana son ajiye masa ya miko mata ruwan dake hannunsa yana dan lumshe idannuwansa ya shafa shafefen cikinsa wanda ke dauke da wani irin gida gida masu tauri irin na masu sport din nan yana fadin" yinwa nake ji, gashi daga nan zance zan je

Ruwan ta tsurawa ido, ta dan makale kafadarta ta ce" ka kafa bakinka fa, kuma sai kawai nima na kafa?

Da mamaki ya kalli ruwan ya kuma kallonta

Murmushi ya yi ya ce" da zan fito fa sai da na yi broch kuma kin ga ban ci komai ba, sannan bakina baya wari

Itama murmushin ta yi tana kara makale kafadarta ta ki amsa

Juyawa ta yi ta daga hannunta

Su dama ita suke jura sun ci sun yi hani'an

Ledar ya fito da ita ya karaso ya kawo mata sannan ya koma ya zauna sunna jiran ta gama su tafi dan su kansu an masu gargadin daga bakin inda lokacin zuwanta gida ya yi koda a sume ne su maidota gida

Yannayin mamaki ya nuna a lokacin da take miko masa naman ya ce" aman, kika ce min baki san sarkin garinnan ba kuma na ga dogari guda ya kawo maki abu ko dai ke din y'arsa ce?

Da sauro ta kale shi, sai kuma ta yatsina fuska ta ce" ni kuam zai haifa? Yaro ne fa! Bayan wannan ai ba lale na sanshi ba, ni ban taba ganninsa ba kuma ko na ganshi ban sanshi ba tunda baya cikin tsarin mutanen da nake son mu san junna
Dan Anmy dina ne!

Tun da take maganar ya tsura mata ido da mamakinta, kai, shine yaron? Innalilahi sai kawai ya ringa jin me zai hana ya wanka mata marin da zata fita hayacinta har ta buda wannan muryar tata mai kwari ta fasa ihun nan kamar an kasheta?
Yau shine wannan ficiciyar yarinyar ke ce masa yaro?

Amshi mana,

Ta fada tana kara mika masa naman

Shima kafadarsa ya makale kafin ya ce" nima bana ci, na san ko kin saka a bakinki?

Da mamaki ta wangale baki tana kallonsa,

Sai da ya dan hade fuska ya ce" aman me yasa kika raina sarkin garin nan bayan na ji irin yanda ake tsoronsa?

Kafadunta ta daga ta ce" nima raina ni ya yi ai

Ido ya kara zarowa yana jin har kamar kirjinsa ya fara zafi yana kallonta , tabas ya tabata dole ya shaketa ya kara summar da ita a karo na uku a wajen nan

Bai idasa jin lale dole ya hukuntata ba sai a lokacin da ta kara dan gyara tsayuwarta tana duba agogon dake cikin wandonta dan tafia zata yi ta ce">ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


29



Ta ce" ni banma ga dalilin da zan nuna na san shi ba, bai min ba, ko a layin mutanen da zan iya jin nauyinsu ba,
Sam mutumen bai min a cikin tsarin rayuwana ba

Mikewa ya yi tsaye hakan ya bayanar da irin tsayinsa,
SHAHEED ya kasance namiji daya kwal da babu irinsa
Yana da tsayi daidai misali,
Shaheed ba shankalale bane kuma ba rubdede bane
Jikinsa ya kasance jiki kamame mai tsafta
Kirjinsa yana da fadin gaske sannan cikinsa ba a shafe bane yake luwai kamar na mace aa, a shafe yake aman da wani gida gida irin na masu daga karfen nan
Ya kasance mai hannaye masu tsayi da kauri, damatsunnan hannayensa tamkar na dan dambe wanda baka gane hakan sai ya saka irin rigunnan nan na gudu
Irin yanda ya kware wajen sarafa doki haka ya kasance tamkar doki a kowani fani, sam bashi da wasa ko laso laso
Fuskarsa dauke take da gira mai yawa wace har ta kusan hadewa da yar uwarta baka sidik,
Idannuwansa kuwa manya ne ba fici fici ba masu dauke da gashin ido mai yawa baki sidik, sannan sunna dauke da kwali mai ruwan maroon mai duhu wanda yake kyalkyali ko a cikin duhu ne
Hancinsa yana da dan girma sannan yana da karan hanci mai tsayi
Lebunansa masu fadi ne kadan sannan pink color ne yas da su ga taushin tsiya
Yana da cikar gashi irin na larabawa domin ya dauko gashin Anmy ne wanda yake yawan aske shi sai dai duda haka ya ajiye kyakyawan sajen da ya je masa har wajen habarsa ta fitar da san gemun da yake dan ragewa yana gyara shi yana kara hawa fuskar yasa das da shi ga baki ga kyalkyali
Cinyoyinsa sunna da tsayi da wani irin tauri irin na wanda ya sabawa jikinsa da sport sannan kaurinsa masu kauri ne da tauri suma a rike suke a jikinsu
Yana da manyan tafin kafafuwa irin na manyan mutanen nan na da duda basu da tuwo sosai

Cike da kasaita ya ringa takowa ya yi taku uku ya kasance tsaye kikam a gabanta hakan ya saka ta zama wata yar firit da ita tamkar wace zai yi kujera da ita


Kirjinsa ta dan kurawa ido kafin ta dan matsa kusancinsu ta dago da kanta tana kallonsa da dan mamaki ta ce" kanshin turaran nan, a ina ka samo shi?

Idannuwansa ya lumshe ainun a kanta a kasan zuciyarsa yana furta lale na yarda baki da kunya ko daya yarinyar nan, muryarsa da ta dan fara kausasa ya buda ya ce" kin san shi ne?

Fuskar tasa ta dan kurawa ido kafin ta cire dubanta daga kansa ta mayar gefe tana mai sakin ajiyar zuciyar da bata san dalili ba sannan ta ringa dan girgiza kanta

Fitowar dogarin dake tare da ita baban ya saka shi cije lebensa na kasa yana son kara kawar da fuskarsa irin na dazu don kar a je ya gane shi a hankali ya furta" na yayana ne na dan fesa, turaran ne na birge ni

Dan murmushi ta yi, bata ce komai ba, karamar eayar dake aljihunsa ya ciro ya mika mata yana kallonta ya ce" tunda yau kin aminta da abotakata, saka min number ki

Wayar ta kai dubanta sama, wata irin waya ce yar karama mai sulbi sannan fara ce kal kamar hannu bai taba tabata ba bale a yi tunnanin ana ajiyeta a wani waje

Tabas mutumen nan yana da tsafta, yana kanshi uwa uba saukin kansa ya saka eh lale zata iya zumunci da shi

Kwarai ta ji dadin da ba soyaya ya nuna mata zai yi da ita ba, domin kuwa a tsarin rayuwarta farin mutun baya cikin tsarin namijin da zata iya soyaya da shi ko na second daya

Kuma kai dubanta ta yi kansa, mutumen na tare da wani irin kwarjini, girmansa ya bata mamaki irin yanda farinsa kuwa yake har ya zarce matan nan masu karin mai a kan nasu

Wayar ta amsa ta saka numberta wace idan an kirayeta ana samunta ko wani irin time kafin ta mika masa ta juya tana daga masa hannu

Daga inda yake tsaye ya bita da kallo inda dogarin ya koma da gudu ya bude mata wajen zama ta shiga ta zauna

Wani uban tsaki ya ja yana yin kwafa ya koma ya zauna da wayar a hannunsa wada ta saka numberta

Ni SHAHEED ni ne yaro? Sam halitata ce bata yi mata ba? Wani murmushi ya saki yana dan kara cije leben nasa na kasa cike da takaicin abinda ta fada
Haka kawai ya ji yana jin haushin kalamanta

Kansa ya dan kara girgizawa yana mikewa dan karasawa ya huta a ransa kuwa fadi yake" sannu sannu bata hanna zuwa yarinya, abinda na yi niya a kanki sai na cinma burina marar kunya!

Sun hade a falo sun yi hira kamar yanda suka saba, Anmy na tare da su tana jara hankalcewa da yannayinsu baki daya, sai Ummu da ta wuni da ita tana ta kokarin gannin ta fitarwa da yarinyar abin daga ranta , ba laifi ta dan kara sakuwa kan yawan shiru da kukan da ta dauka na kwana biyu

Da sasafe wajen karfe tara, Najeeba ce tsugune kusa da kafar Anmy bayan sun kara gaisawa cikin kara sada kanta ta ce" Anmy, dama saman maganar tsayar da mutumen da aka ce din nan ne, akoy mutane biyu da muke tare nake son a rokar min alfarmar su fara zuwa a cikinsu sai a ware guda in sha Allahu

Da sauri ta dubeta, da wani yannayi mai cike da rashin jin dadi, saurayi? Zance? Kennan tana da wanda take so ko me?

A hankali ta ce" Najeeba, kina da wanda kike so ne a cikinsu?

Najeeba ta kara sada kanta irin kana jin kunyar nan ba zaka iya yin magana ba, hakan ya kara sanyaya gwuiwowin Anmy
Muryarta kasa kasa ta ce" ki basu dama

Kara sada kanta ta yi ta yi godiya kafin ta mike daga ita sai rigar bacin dake jikinta wace ta kafe a jikinta , rigar bata da shara shara sai dai kasancewar ta velour sai ta lafe a jikinta ta yi mata dass ta fitar da tsarin halitarta

Da kallo Anmy ta bita har ta shige dakinsu dan zuwa ta shirya ta fita wajen aikinta kafin take sauke wata nanauyar ajiyar zuciya
Shin da wa zata iya yin irin maganar nan wanda zai bata kyakyawar shawarar da mutane ba zasu ga ta yi son rai ba? Da wa zata zanta wanda zai dubi lamarin da duba irin na fahimta ba zai bi bayan dayan biyu ba ya bata shawarar da ta dace?
Tabas ba zata iya tauye yarinyar kai tsaye haka ba,
Waye wanda zai bata hanyar da zata bi cikin ruwan sanyi ta samu cikar burinta? (ya mama ta ce ku shige daka tana da kyakyawar shawara Anmy=ØÞ)

A yau da ta tashi sai ta yi shiga cikin wando na jins irin wanda ke dame kafar nan daga cen kasa sannan ta saka riga ruwan pink color mai dogon hannu da botira daga gaba
Da ta zo bala botiran sai ta bar daya bata bale su dukansu ba sannan ta caje gashinta da kyau ta daure shi a tsakiyar kanta

Turare ta bulbulawa jikinta kafin ta dauko wata abaya baka sidik wace sam bata da siri domin tamkar sange haka take ita dai an
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment