Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

du wani gashi dake fuskar ya kwonta luf luf

Hannayenta ta hade tana kallonsa ta ce" ban san kamaninsa ba, wace kalar fuska ne da shi? Tsoho ne ko yaro ne karami? Wani irin mutun ne? Dan karami ne ko yana da girma?, yaya kai ka san bana son farin mutun, burina kulun shine na auri mutun mai lokacin kansa, wanda yake da lokacina kowani time, wanda zamu yi wasa da daria da shi, wanda zai mayar da cikin gidanmu filin nishadinmu, filin kwonciyar hankalinmu, filin samun nutsuwarmu, yaya...ta kuma fada a sanyaye ta ce" ina da burin mijina ya zamo abokin wasana, idan na yi niyar ganninsa koda a tsakiyar dare ne bani da wani shingi tsakanina da shi, babu wani abu da zai hana min ganninsa.

Yaya, ka san bana son mai mata, ina ji a cen kasan zuciyata cewar idan har na auri mai mace ba zamu zauna lafia ba domin ina da madaukakin kishi a kan abinda yake nawa
Idannuwanta ta kuma lumshewa ta kara sanyaya muryarta ta ce" ya tsane ni, ban san me na masa mai girma har haka da ya tsane ni ba, yakan min kallon da ba zai yiwa kashinsa ba, ya jefe ni da mumunar kalmar dake nuna yana zargina, shin yaya dama ana aure da zargi?

Hannayensa ya saka ya janyota jikinsa, ya kasance kanta saman kirjinsa hannunsa kuwa saman gashin kanta
Ummukulsum na rike da hannunta ta kara matsowa sosai kusa da ita suka sakata tsakiya
A sanyaye ya ce" ba kulun bawa ke tsara rayuwarsa kuma ya ganta yanda ya tsarata ba,
Shin kin san lokacin mutuwarki? Ko da za'a halice ki an maki shawara ne? A hankali yake dan shafa gashin kanta dan ya samu ta rage kukan da take yi,
Ta sasauta kukan ba dan komai ba sai dan ta ji ya furta mata cewa" NAJEEBA, dan wannan ne kike kuka? Ba zan iya gannin kanwata na kuka haka ba dan haka an fasa maki auren hadi da mutumen dake jiran hanyar halaka ki ba!

Sai kawai ta ji ya ci gaba da fadin" Njaeeba, ba kai tsaye muka tunkari abin nan ba, haba Najeeba meye a tatare da dan uwan naki wanda har kike irin wannan dan an ce za'a aura maki shi?
Najeeba shine kike hada soyayar wani dan duniyan da yake maki ta karya da girman darajar auren nan?
Ina yanzu kika gama fada min abinda shi saurayin naki ya saka ki yi, take dokarmu, ya ingizaki kika yi satar hanya kika tarda shi, sannan harma ya so ya wulakanta ki? Najeeba shin bakya mamakin irin yanda Allah ya ringa kare ki har zuwa wannan rana? Zaki butulce masa ne? Ina so ki kwontar da hankalinki kin ji an kanwana?

Ya karashe yana dan taping din bayanta

Kanta ta dago tana girgiza kanta a hankali ta ce" ka kasa ganewa yaya, ni fa ba wai butulci zan yi ko wani abin ba, ni kawai sonsa ne bana yi shi yasa na ce ba zan aure shi ba, sam bai min ba, sam bana son sa, baki daya ya saba halin irin mutumen da nake so

Hannunsa ya saka a gefen damtsenta ya riketa da kyau kafin ya ce" Najeeba Mutalab, bismillah!

Yana gama fada ya mike ya saketa ya daga muryarsa a zafafe ya ce" ke wace irin mai taurin kai ce? Ko kunya bakya ji? Yau ke zaki nuna bakya iya auren dan Anmy na cikinta? Koda yana dauke da cutar da zata iya halaka ki, koda yana dauke da cutar hauka ina ga ido rufe zaki amsa tayin aurensa balema ba daya? Ke Najeeba kin san alfarmar da Allah ya saukar a kanki kuwa? SULTAN SHAHEED kike tambayar yaro karami ne ko tsoho ne shi ya sa za'a hada aurenki da shi?

Murmushin takaici ya yi yana gyada kansa, ya ci gaba da fadin" Ke gani kike roka ya yi? Najeeba da ace kadarar da ta samu yayarki a kanki ta fada kice da du mun mace da damuwa zuwa yanzu? Gatanan gabanki zaune, tana cikin jin ciwon abinda ya sameta aman ta dane ta shanye take cudanya da kowa dan ta san Allah ya dora mata ba wani ba kuma shi zai bata mafita

Najeeba?????
Sai ya rasa me zai kara furtawa daga cikin bakinsa
A hankali ya kai zaune ya sada kansa kasa
Ya tabata wannan lamari ne kadai zai yi ta saurareshi
Kansa na kasa ya rintse idannuwansa ya yi forcing din kansa hawaye ya shiga bin kumatunsa

Dago fuskarsa ya yi da muryar kuka ya ce" na zata na isa da ke, na zata idan na haka rami na nuna maki na ce fada zaki fada ne ba tare da kin tsaya tunanin komai ba,
Sai gashi Najeeba, saboda maganar aure, maganar aurenma mai daraja kike tunanin zan cutar da ke ni DAYABU? Najeeba Anmy da Abih kike tunanin zasu cutar da ke?

Baki daya jikinta ne ya kara daukan rawa
Da sauri ta diro ta nufo shi aman sai ya mike yana mai dakatar da ita da hannunsa
Yannayinsa a hargitse ya ce" Najeeba, ba komai ki yi hakuri na yi katsalandan a rayuwarki ashe ban isa da rayuwar taki ba

Hannayenta ta kara dorawa a saman kanta ta karasa da gudu tana neman fada masa

Kuka take bilhaki tana furta" da wane kake so na ji yaya? Da wane kake so na ji? Nima kai din kaine zan fadawa tashin hankalina, walahi ina cikin tashin hankalin da ban san iyakarsa ba, yaya zuciyata zafi take , ban taba zaton haka a rayuwata ba

Idannuwansa ya lumshe jin ta fara sasauta muryarta a kan tasa
Da hannu ya yiwa Ummu nuni kan ta gyara shinfidarta

Da hanzari ta gyara wajen kwoncinta sannan Dayabu ya nufi bed din da Najeeba

A hankali ya shinfidar da ita sannan ya kamo kafafuwanta ya dora sama
Safar dake jikin kafafuwanta ya cire mata sannan ya karasa kusa da kanta a hankali yana shafa gashin kanta ya ce" *FA'INAMA AL USRI YUSRA*,
na fi so ki fadawa Allah , ki ringa fadin" ALLAH, idan alkhairi ne ka tabatar min da shi cikin kwonciyar hankali da kosashiyar lafia
Idan kuwa ba alkhairi bane, ka saka a fasa koda ana gobe daurin auren ne

Idannuwanta ta lumshe a kasan zuciyarta tana furta wani alkhairi? A ina yake? , tana jin Ummulkhair ta fito daga bayi ta ci kukanta ta koshi ta wanke fuskarta ta aro jarumta ta kara nufo wajen kanwar tata
a hankali ta kwonta gefenta ta rike hannunta na dama,

Ummukulsumma ta dawo gefenta na hagu ta hau ta kwonta itama ta rike hannunta na hagu a cikin nata
Tamkar wasu kannanun yara sai da ya masu adu'ar tsari , ya kara tsayawa a wajensu har ya ga ta daina kukan baki bude sai hawaye dake bin gefen kumatunta, sosai abin ke damunsa aman zai jure dan idan bai nuna mata ba wani abu dan tana kuka ba tabas zata rikita su
Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya fita ya ja kofar yana kara sauke ajiyar zuciya tare da goge hawayensa

Cikin nutsuwa ya yiwa su Anmy bayanin cewa a ci gaba da shirye shirye!

Nan take Anmy ta dauki wayarta ta koma gefe ta yi kiran mutanen da ita suke jura, mutanen da ta yiwa wannan lokacin tanadi, wa'inda zasu saka Najeeba daka har sai lokacin ya yi su fito, mutanen dake kula da gimbiyar saudiya, tun da aka fadi maganar ta kakabe dukiyarta ta shiga shirye shirye, ta dauko su ta sauke su a wani tankamemen gidan SULTAN, jiran yau suke dama su taho


Tun da suka zube kawunnansu ke kasa jikinsu ke bari basu iya dagowa ba haka kuma bakinsu bai daina furta kalmomin ban hakuri da neman afuwar saken da suka yi har ta bace masu

Amintacensa ne ke fada tamkar zai kai masu bugu tare da nuni cewar zai cenza su ya maida su filin horon dogarai domin a irin abinda suka nuna ba za'a iya bugun kirji da su ba a filin daga ba!

Sai da ya kara lashe lebensa na kasa da yake jin a yau ya cika bushe masa kafin ya buda bakinsa a hankali ya ce" a ina kuka hadu da ita? Tana cikin wani yannayi? A ina ta cenza suturar da ta fita da ita?

Baban ne ya kara sada kansa ya nemi afuwa sosai kafin ya kora bayanin abinda suka sanni da inda suka ganta da kukan da take

Komawa ya yi ya jinginar da bayansa jikin kujerar da yake zaune ya mayar da idannuwansa ya lumshe
Da yan yatsunsa ya yi masu nuni cewar su tafi

Da sauri suka kara dukawa kamar zasu kwonta sunna ta neman afuwa kafin su fito daga falon

Kara zubewa Amintace ya yi kansa kasa ya shiga neman afuwar Sultan , domin du horon dogarai na gidan nan a hannunsa yake haka kuma idan suka aikata laifi yana da baban kaso a ciki

Idannuwansa da suka kara yi masa nauyi ya buda da kyar yana kallonsa

Sai da ya furzar da huci mai zafi kafin ya ce" daga yau, bata da wani mai tsaronta sai kai, du inda zata saka kafarta ka saka, du abinda zata ci ka fara tabawa, du wanda zai mu'amalanceta ka hana

Da mamaki kansa a kasa yake amsawa, ya cika da matsanancin mamakin jin cewar shi, shine zai tsare wannan yarinyar? shi rantsatsen mai baiwa Sarki tsaro ne, ko Gimbiya bai taba baiwa tsaro ba baban yaronsa ke bata tsaro aman yau shine aka wakilta da maganar baiwa wannan yarinyar tsaro?

Kara tasowa ya yi daga jikin kujerar yana kara dunkule hannunsa ya kara kakausa muryarsa ya ce" *hukunci zai hau wuyanka ne daga bakin lokacin da ta zile maka ka nemeta ka rasa, shu'uma ce, zata iya shiga duban mutane ka lalubeta ka rasa, hakan zai wanzar da tashin hankali a rayuwarka!*

Yana gama fada ya mike tsaye ya shiga takawa shi kuwa amintacensa kansa a sade a kasa yana fadin" Allah ya huci zuciyar mai damagaram, Allah ya huci zuciyar zaki, namu sarkin sarakaine na gida da dawa, Allah ya kara maka lafia da nisan kwana

Dakatawa ya yi, bai juyo ba daga inda yake ya furta" ka saka a binciki wacece *NADIA MOCTAR a UNIVERSITY*

Daga haka ya shige ciki yana jin wani irin al'amari mai girman gaske dake damunsa
Ta ina zai bi ya horata?
Ya je ya zubar da kansa ya shiga jikinta dan ya samu kusancin da zai kamata tsamo tsamo da laifin da take aikatawa sai gashi a lokacin da ta aminta ta bashi numberta harma suka fara sakarwa junna fuska ta hanyar yin yar doguwar hira da junna shine za'a katse? Shi ne zai auri yarinyar nan, nan da kwana goma?

Kansa ya daga ya kai wajen agogo,
Idannuwansa ya lumshe a lokacin da ya ga har karfe goma sha biyu ta gifta a ransa ya furta *aa ba kwana goma bane, kwana tara ne*

Lebensa ya kara cijewa na kasa yana mai ajiye rawaninsa

Hannunsa mai cike da yannayin karfi ya daga yana yamutsa summar kansa da ta taru wace yake so ya shiga ya aske kayansa da kansa

Idannuwansa ya kuma budewa a kasan zuciyarsa yake furta" da ace kin kilace kanki, da ke din babar harka ce da ba dai yaro ba sai dai baban yaro
Sai gashi kin banzatar da kanki,

Idannuwansa da suka dauki kalar ja dan bacin rai ya kara budawa yana furta"
Zaki zama matana ne, sai dai rayuwarki zata zama cikin kunci
Abinda kika saba da shi, kina ji kina ganni zai gagare ki, sai ya zame maki fiye da zinari domin zaki nema ruwa a jalo ki rasa shi, zan saka maki matakan tsaron da ko dan jaririn namiji ba zaki gani ba bale ki hadiyi yawunki a kansa
Zan kasance maki fitinar da baki taba tunanin zata shigo ratuwarki ba! (Ma ji ma gani)

Sai da ya shige sannan ya dago kansa

Ransa bace ya mike ya fita daga falon yana cike da matsanancin bacin rai
Du darajarsa? Du girmansa za'ace yanzu an nada shi kula da yarinya karama irin wannan?
To wai, meye girman darajarta da za'a nada shi, shi ya bata kula?
Meye tsakaninta da shi?
Sai kuma maganar Nadia Moctar, ta ina zai fara bincikenta? Nadiar nawa ce a cikin University?
Dole zai dauki wayarsa ya yi aikin, tunani yake me hadinsa da wata Nadia?
Wani murmushi ya yi yana girgiza kansa, wani auren zaka sake? Halitarka ba ta mace daya bace,
Kansa ya girgiza yana kara wani murmushin a kasan zuciyarsa ya furta

*Ga fili, ga mai doki*


Idannuwanta bude suke har goshin asuba
Ta kasa yarda cewa itane haka ke shirin faruwa da ita
Ta kasa tsayar da takamaimai abinda zata yi da rayuwarta
elle n'arrive pas a y croire (ta kasa yarda), cewar ita Najeeba, itane haka ke shirin faruwa da ita
Lokaci daya ta ringa da ta sannin rayuwa
Ashe du irin tara samarin nata zata kare a auren dole ne bata sani ba?
Sai kuma ta ji zuciyarta ta raunata, a hankali zuciyarta ta ringa kara rufeta da fada kamar haka" dole Allah ya kama ki Najeeba, ke ce zalinci wancen, yiwa wannan karya, cin kudin wancen, mazan da kika saka hawaye yawa ne da su ashe ke banza bami san cewa haka zaki kare ba? Ta tabata idan har ya yarda ya amshi aurenta ba dan wani bane sai kawai dan ya idasa nufinsa na son kasheta
Wani irin shakarsa take ji a kasan zuciyarta, zata iya rantsewa rabonta da ta shiga harkar matarsa ko shi din kansa tun da ta ganni ido da ido yana rike wuyan maciji harma ya saka yar yatsarsa a wajen bakinsa ya ringa fitar da wani ruwa mai duhun gaske
Tana kallonsa yana kallonta ya yi mata wanka da ruwa masu sanyin gaske bayan ya san tana fama da cutar athsma
A haka, bata yi masa komai ba ina da ta yi masan?

Sai goshin asuba barci mai wani irin nauyi ya kwasheta wanda sam bashi da dadi sai mafarkai mararsa dadi sosai a cikinsa

Da duhu duhu mata shida suka shigo har dakin da yan matan Anmy suke, wa'inda suke saman salaya sun gama sallah aman sun raba adu'a sunna yi dan Allah ya tankwasa yar uwarsu

Saman bed din Anmy ta kai dubanta bayan ta amsa gaisuwarsu
A hankali ta furta" bata yi baci ba jiya?

Ummulkhair ta gyada kanta kafin ta sada kanta

Matan nan fararen larabawa ne, kusan su duka farare ne tas tas sai wani irin shu'umin kamshi suke ga fatarsu kamar ka kali kanka a ciki

Anmy ta kai dubanta kansu a sanyaye ta ce" ban san ta inda zamu fara ba, bana iya yi mata tsawa ko na rufeta da fada, abinda na sani idan ta farka ta ganni zata so tayar da rigima, gashi dole a yau za'a sakata dakin dumin cen da gyara ku kanku ba zaku kuma fitowa ba bale ita sai ana gobe daurin auren, ban san ta yaya zata amince da abubuwan nan ba, ga wajen aikinta, ga ..................
Hannunta da datijuwar ciki ta rike ya saka Anmy sauke numfashi a maganarta tana ta lumshe idannuwanta domin sam bata so ta ga Najeebar a cikin wani yannayi na rashin jin dadi

Cikin harshen larabci ta ce" kin san cewar wannan ranar mun ci alwashinta, muna jiranta ko? Kin fi kowa sannin mun shiryawa wannan ranar ko? Kukanta, ko ihunta, ko summarta ba zai hanna mu wanketa ciki da bai ba, domin kuwa shinfidar da zata taka mai daraja ce! Dole zata koyi rayuwa da yanda zata tafiar da sarkin mu! Mace na iya shanye wuyar nakuda, hawayen da zata zubar sune samun sasauci a zuciyarta! Maganar so kuwa
Murmushi ta yi ta kai dubanta wajen Najeeba dake kwonce ta rungume fillow a jikinta gashinta ya warwatsu ko'ina, rigar aida ce a jikinta har yanzu sai shaf din pant da kafafuwanta masu tsananin hasken tafin kafa da wani shap a jikinsu ta maido dubanta kan Anmy ta kara sakin murmushi a hankali ta ce" lokaci zai nuna mana idan har ta isa ta kaucewa zuciyar *GURNANIN ZAKI*



..................salam alll........>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



35


Ajiyar zuciya Anmy ta kuma saukewa ta koma gefe tana kallon su

Karasawa babar cikinsu ta yi ta saka hannunta a hankali ta yi bismillah
Sauran du dukar da kawunnansu suka yi har sai da ta saka hannayen nata cike da kula ta talabo Najeeba

Idannuwanta ta buda a hankali kafin ta ware su da sauri tana kallon matar

A dan zabure ta so mikewa tana fitar da idannuwanta waje sannan muryarta da ta disashe dan kukan da ta sha ta ce" lafia? Menene? Wacece ke?

Bata daina kokarin tayar da ita zaune ba kafin ta mika hannunta a miko mata alkyaba wata iri ta veloor kalar baki sidik
Tana daga zaunen sai zaro ido take matar nan ta rufa mata shi a jikinta ta dora mata shi a saman kanta

A hankali cike da nutsuwa cikin harshen larabci ta ce" a kowani hali shugaba ta farka daga baci ta kiyayi saurin buda bakinta ta yi magana ba tare da ta shiga bayi ha ta wanke bakinta, domin baban abinda zata aikata na bada hanyar da Uban gidanta zai ji zuciyarsa ta hautsine da tashin zuciya shine ya ji warin bakinta, shi kuwa baci idan aka tashi daga shi koda na minti talatin ne baki kan daukan wari marar dadi, irin warin nan na saka ciki ya rikice ko mutun ya yi gagawar kawar da kansa daga wajenka

NAJEEBA ta kara zaro idannuwanta tana gannin wasu biyu sun zo sun hadu sun mikar da ita tsaye, cikin nutsuwa wace du ta fi su yarinta ta matso, sannan kana ganninta ka ga kakarfar mace

Hannun Najeeba ta damka ta kamata ta cicibata suka kama suka dorata a bayanta

Baki hangame Najeeba ke binsu da kallo ta ga an goyeta a baya luf ta aniya neman dirowa da ihu ihu ta ce" Anmy, Anmy meye wannan? Su waye wannan?

Anmy ta matso da sauri tana son kamo hannunta tana fadin" Najeeba, ba wani abu bane zamu koma wancen bangaren ne kin ji? Ki nutsu kar su nutsar da ke

Wannan kalma ta kar su nutsar da ita ya sakata yin wani irin sakalau tana bin kowa da kallo du a firgice

Kara rufa wani zani mai kamshin gaske suka yi a saman kanta hakan ya saka ta daina gannin komai sai tafiar da ake yi da ita
Kwata kwata aka fita daga bangaren Anmy aka yi bangaren da aka tanada domin gyrare gyaren

Dakuna hudu ne a wajen, baban dakin nan suka shige da ita
Mafarin barowar Najeeba daga cikin yan uwanta, mafarin shigarta sabuwar rayuwa mai cike da abubuwan ban mamaki,
A wannan ranar tana ji tana ganni sai da aka tubeta zindir kafin a saka mata wata yar yololuwar riga baka kirin wace aka fara yi mata darzar fatar jikinta da ita
Dakin wani irin dumi ne yake dauke da shi wanda da farko ta ringa zufa sosai sai daga baya zufar ta shanye a jikinta a lokacin da suka yi mata wata irin darzar da ta kusan fitar da ita daga hayacinta

Sosai suka bi lungu lungu na jikinta suka darji fatar Najeeba da wasu irin abubuwa dake dame masu fitar da kanshi abin nan basu barshi iya fatar jikinta ba har fatar kanta sai da suka darza

Da ruwa mai dumin gaske mai hade da ruwan turaren nan mai mugun tsada wato sandal FLEUR aka darwaye jikinta tas
Sabon broch da maclean aka bata ta wanke bakinta sai kakare kirjinta take da kuma kasanta tana biye da su da wani kallon mamaki irin yanda du yanda take neman botsarewa sai su tarota idan ta so nuna karfi sai a barta da wannan matashiyar ta maida ita zaune

Alwallah ta dauro suka fito
Rigar sallar da aka ware aka miko mata ta kabarta sallah cikin nutsuwa ta gabatar
Ta jima kanta a kasa tana hawaye, tama rasa me zata ce? Ta ina zata fara, abinda ta fi fada shine Allah kar ka bari su min auren nan dan kasheni zai yi

Tana dagowa ta yi tahiya kanta sade ta ja carbinta ta gama

Sai da ta gama sannan aka mikar da ita

Rigar tata suka kama mata ta cire hakan ya saka ta tsare su da kallo ranta a yannayin bace ta ce" wai zir zan yi ta zama ne ko me?

Datijuwar nan ce ta girgiza kanta tana kallonta cikin ido ta ce" idan mace zata yi magana, ya kasance ta ragewa idannuwanta tsauri da yawa, irin ta sada su kadan ita bata rufe su ba ita bata bude su sosai ba
Idan maganar fada ce zata yi ya kasance ta sada idannuwan sosai idan ta faro a sanyaye sai ta bude su baki dayansu, bafa daga murya zata yi ba, aa, idannuwan nata ne zasu nuna yannayin da take son isar da sakonta

Hannunta ta saka ta ja Najeeba ta zaunar da ita bakin bed mai dauke da zani mai duhu
Wasu oil ne dake hannunta ta raba zamanta ta shiga tsaga gashin kanta a hankali tana dan shashafa mata shi ta ce" idan kuwa zata yi tambaya ne, ya kasance da kwayar idannuwanta zata dasa question mark din, wato ta yi yawo da su ta dasa su ta hanyar kai kwayar idannuwan nata kasa

Manyan kitso ne ta fara yi mata irin da ake kira zane kwaya hudu ne ta yi niyar yi mata dan haka ta ringa yin kitson a hankali tana lalumata tana tufke har karshen gashinta

A sanyaye ta ce" bale ke din daga yanzu kin zama uwar talakawa, nauyi mai girma ne ya hau kanki wanda yake a wuyan mijinki, zai kasance ke ce mai tarbarsa a du halin da ya shigo maki

Shugaba kan daukan abubuwa, yana shanye duka a waje, yana shanye du wani tashin hankalin talakawansa,
Daga bakin da ya shigo wajenki, sai ki ga ya gaza, a gabanki ne zai iya fitar da bacin ran da ya shaka, a gabanki ne zai iya fitar da tarin yannayi na tausayi, tsoro, ko firgicin da yake hange a tatare da talakawansa wanda hakan zai taba shi sosai, harma ya nuna maki hakin da zuciyarsa take ciki
Ke kuwa *Kece mai shanye damuwarsa*, zaki mayar da shi a gabanki tamkar yaron dake da kiwya kike son ke kuwa sai ya saba da ke, hakan kuwa zai faro daga yannayin idannuwanki

Zaki kasance idannuwanki dauke da haske da kwali, zaki kasance mai sada dubanki a gaban kowa bale a gabansa, zaki kasance mai lumshe idannuwanki a gabansa

Dan saurarawa ta yi tana tsaga na karshe ta ce" sai movement din hannayenki da jikin ki baki daya
Zaki kiyaye irin motsinki a gabansa, ba daga ya nuna maki bacin rai ba zaki tarbi magana da" wa ya isa? Aka yi haka? Ina ba'a isa ba?

Ta hanyar maganarki zaki daukaka muryarki har ki ji maganarki ta girmi tasa,
Daga bakin lokacin da muryarki ta girmi tasa zaki ga ya yi lakwas yana jin zuciyarsa na kara ruruwa yana son kara daukan abin da zafi

Ke din nan, ke ya dace ki sanyaya muryarki ki sada kanki da dubanki
Muryarki ta kara sanyi, ki nuna kin fi shi shiga damuwar da ya shigo maki da ita, a hankali ki nuna masa kowani tsanani yana tare da sauki kafin ki nuna masa cewar idan har yana fadarki, farin ciki mai dorewa shine abinda zai wanzu a tatare da shi

Dago kanta ta yi ta kalli matar, sosai take jin abubuwan da take fada tana kuma anfani da su, idan ta nuna a wanda zata aikatawa ne sai ta yi murmushi karara ta dan girgiza kanta
Za dai ta anfanarwa HUZAIFA, domin ta tabata Allah zai amshi adu'o'inta

Kanta ta mayar ta sada matar ta karasa kitse mata gashin kanta tas sannan ta bi shi da wani man mai dadin kamshi

Mikar da ita ta yi da rigar nan ta jikinta sannan ta kwontar da ita saman bed din
Ji take gajiya sosai
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment