Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ku zagine mu je tare =ØÞ=ØÞ=ØÞ=ØÞ=ØÞ
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



7





A hankali NAJEEBA ke shafa lallausan gashin yayar nata da dan kwalinta ya fadi sakamakon kukan da take shekawa

Du a firgice suke, aman sun rasa wace irin tambaya zasu yi mata

Hannunsa ya saka ya janyeta daga jikin NAJEEBA ya jata saman kujera ya zaunar da ita sannan ya shiga sintiri

Baki dayansu suka koma suka zazauna

Yar budurwar cikinsu mai shekaru goma sha biyu ta ce" shikenan yanzu anko din shada da lesh da komai din da akai mana an fasa auren?

Hararanta Bilkissu ta yi hakan ya sa ta yi shiru ta rafka tagumi cike da zulumin an fasa aure shikenan ba zasu yi sabga a gidansu ba

Hannayensa da yake hadewa yana kara budewa ya kuma hadewa ya ce" wani irin ya fasa aurenki? Wani abu kikai masa?

Tana kukan dai ta ce" aa, dazu ne da ya zo yake tambayana wai me ya kaimu gidan sarki ne? Sai nace masa ziyara
Shine ya ce min" Zahrau karya kike, ashe abinda momy ke fada min gaskiya ne? Ku dangin jaraba ne baku da aiki sai masifa da fada? A gaskiya zahrau ba zan iya auren macen da ta kai karar ubanta aka bashi laya ba, kuma a gaban mutane kanwarki ta mari matar ubanku maimakun ku horata sai kuka tare mata fada, to gaskiya wace kika shakar nan aminiyar momy ce kud da kud, da ita aka kawo kayanki ita ta je tana kuka ta zayanewa momy komai ashe ku dai dangin jaraba ne?

Ummulkhair ta zabura ta mike ta rike kugunta ta ce" mu ne dangin jarabar?

DAYABU ya harareta hakan ya sa ta koma ta zauna tana gunguni

ZAHRAU cikin sanyinta ta ce" nima nace da shi ya yi hakuri, abinda ya kai mu gidan sarki sirrin cikin gidanmu ne, kuma fadan nan da aka yi suna da yawa fa suka rufawa NAJEEBA ita kadai, ta yaya yake so na kyale ina kallo a dakar min kanwata?

Shine shine.....sai ta fashe da kuka tana kara dora kanta a kirjin NAJEEBA wace du ta manta ciwonta jikinta sai rawa yake dan walahi a duniya sun rayu da rayuwar jin ciwon dan uwansu a cikin jinnin jikinsu
Ana fadin maganar dan ubanci a duniya, su basu san da wannan kalmar ba
Sunna fada tsakaninsu fa, aman idan kana son ka ga hadin kai da tsantsar soyaya wani abu ya samu dayansu

DAYABU da hankalinsa ya kara kololuwar tashi ya ce" shi ne me?

Dagowa ta yi tana kallonsa ta ce" shine ya kara kiranmu da jarababu harma yake ikirarin ko Abanna zai bashi hakuri ba zai hakura ya iya zabawa y'ayansa uwa irina ba dan sam ban samu tarbiya ba bare na tarbiyantar da yaransa

Nima raina ya baci shi ne shi ne.....

Kara tsareta ya yi da ido ya ce" shine me ZAHRA?

Ta sada kanta kasa ta ce" shine nima nace masa mu ai du da sauki, shi da yake shege wanda uwarsa ta haifa ba aure bayansama ta haifi uku kannensa baki daya su ba'a zage su ba sai mune zai saka gaba yana ta zagi

Idannuwansa baki daya ya rurubo lokaci daya ya tafa hannayensa ya ce" MAHAMADU rasululahi salalahu alaihi wa salam

Da wani karfi karfi UMMULKHAIR ta ce" kin min daidai, ai walahi da kika kai karshe baki fada min ke kuwa me kika ce masa a kan irin zaginmu da ya saka ki a gaba yana yi ba da sai na dauke ki da mari walahi, dama sam bai min ba mutun ne sai shegen taurin hannu idan zai maki kyauta sai kaf danginsa sun sani

Namijin dake buga gem kuma yana kallonsu a wayar yayansu wato Najeeb ya ce" lalala, ba yaya ya hana karami yace zai daki baba ba?

Yayansu kam dake salalami dubanta ya yi ransa bace ya ce" sau nawa zan maku magana kan koda ranku ya baci ku ringa tauna magana kafin ku fadeta? Yaya zaki masa gori Zahra dan ya zage ki? Ke baki da bakin rama zagin da ya maki koma wani kala ne aman banda irin wannan gori? Shin shi ya saka mahaifiyarsa haihuwarsa haka ko me? Ko ke kina tunanin an maki albishiri din zaki gama da duniya lafiya ba tare da wata jarabawar da zaki ringa jin kunyar kanki ta same ki ba? Ina gannin kece mai hankalin cikinsu aman sai ki bani mamaki har haka? Na tabata da Najeeba ce da ake gannin ta fi ku rashin hakuri ba zata yi haka ba sai dai ta cire masa bakinsa dan gobe kar ya kuma

Sanyi ya yi gannin du sun zuba masa ido shi kuwa yana fada sama sama

Yatsarsa ya dago ya shiga nuna su daya bayan daya ya ce" ku yi kokarin gannin kun rufe naku sirrin,
Ku sanni, bana so, bana son ku kasance masu izgili da kuma son daga fitina a duniya
Domin kunada baban tabo
Kuna tare da baban tabon da mai tabon kansa bai san na san yanada tabon ba
Bana son abinda zai taba min nasabarku
Bana son a fara da haka a kanku cewa ana fasa aurenku
Bana so abin ya yi nisa

Wata iska mai zafi ya furzar yana kallonta ya ce " to in ba rashin hankali irin na dan fari a wajen uwa ba me ya kaiki buda baki ki yi wannan shirmen?

Ita dai kukanta ne ya tsaya a lokacin da yake bayannin suma sunnada sirri, tabo! Wannan kalmar sau uku kennan tana jinta daga bakinsa idan ta tsare shi sai ya nuna sam shi ba wani abu yake nufi ba yana nufin dai ita mace ce ya dace ta kasance mai taka tsantsan

Baki Najeeba ta tabe tana hade mata gashinta
Ta riga ta shaka, ta shaka iya wuya hakan ya sa ta kasa kida tofa ufan ne sai irin yanda take ayanna yanda zata yi da shi

Ummukulsum ta ja tsaki ta ce" shine kike kuka? Kike kuka dan namiji yace ya fasa aurenki? Da me kuke jira ku a duniyarmu? Koda mun yi auren za'a sako mu ba tare da an waiwayemu ba, idan mun fito da ciki za'a irga mana ranakun haihuwarmu muna haihuwa za'a dauke dan a kaishi nesa da mu
Me kuke jira? Me kuke tunani a rayuwarmu? Yanda ya yiwa y'ayan wasu, yanda ya ringa wulakanta y'ayan mutane yana saki a kan dalilinsa na son zuciya dole sai muma an ringa sako mu ana laya masa zawarawa,
Dole sai mun cika masa gidan nan mun tsufa tare mun mutu tare......
Wani gigitacen marin da ya sauka a kan fuskarta wanda ya tsorata yan uwanta ya saka su zabura sunna kallon wanda ya yi marin a firgice ya sakata dantse harshenta har jinni ya fito na walaha

Kafin su yi wani abu ya warci igiyar cajin dake ajiye ya shiga laftar du wanda hannunsa ya kai...kun san balarabe idan ya tashi dukan yaro yakan yi masa duka kamar zai kashe shi

Mahaifinsu baya duka a banza, aman du randa hannunsa ya daga sai ya daka

Da wani irin tsinanen gudu DAYABU ya warci kananun biyu ya fada dakin NAJEEBA wace ta rigayi kowa guduwa

Yana shigowa suka dantse kofar wanda hakan ya saka uban nasu dukan kofar ransa bace yana jijigawa

Ransa a matukar bace ya ce" bude min, marar kunyar banza marar kunyar wofi, bude min ki fada min maganar banza a gabana
Ummu ni ne zaki yiwa fatan na maku aure a sako ku? Kennan ni jarabawar sake saken mata ba zata iya samuna ba ko? Zahrau shine kika zagar masa uwa kika ce masa shege?
DAYABU shine ka saka su gaba sunna munanan kalamai a kaina ba zaka tataka su ba?

Khairy shine kina ji ta zagar maki uba baki mareta ba?

Najeeba me ya hada ki fada da dan gidan docter Basheer?

Hannunsa ya saka ya kara dukan kofar NAJEEBA wace ita ta fi kusa da shi kafin ya zame ya zauna a jikin kofar yana sauke ajiyar zuciya

Dawowarsa kennan ya tarar da wanda ke neman auren Zahra da mahaifiyarsa da kawayanta biyu a kofa sunna jiransa mai gadi ya hanna su shigowa sai kunfar baki suke wai sai ta fada masu a inda ta ga ta yi shegu

Dama tun a hanya inda ya tsaya siyan fruits ya tsinci maganar fadan NAJEEBA harma ta summa
Daga cen ya nufi asibiti aka shaida masa yayanta ya daukota an sake su

Shine ya shigi ya tarar da Ummu na fadin irin wadinnan magangannun wai koda sun yi aure za'a sako su ne da ciki ko daga sun haihu a sake su

Idannuwansa ya lumshe ya yi shiru yana tunanin rayuwa
A jiya ya so kwarai ya saki Mardiya, sai dai gannin yanzu y'ayan nasa kansu sun fara fada masa magana a kan auri sakinsa ya saka shi kyaleta domin ba'a taba masa y'aya a wanye lafia

Idannuwansa ya kuma lumshewa yana tunanin inda zai bi ya yiwa tufkar hanci, ya zama wajibi ya katse hanzarinta, ya zama wajibi ya yiwa tufkar nan hanci idan kuwa ba haka ba lale watarana y'ayan nasa zasu yi abinda zasu zubar da hawayen jinni, zasu ja sirrin da yake binnewa ya fito fili
Zasu saka baki daya su tatara su bar kasar a lokacin da suka zama abin kyamata sannan abin gori a cikin kasar nan

A hankali ya ce" ku fito

Du sun ji shi, aman ba wanda ya yi yinkurin fitowa

Ajiyar zuciya ya kuma saukewa ya ce" ku fito, ba zan daki kowa ba

Zahrau ta fashe da kuka ta ce" ABIH, dan Allah ka yi hakuri

Muryarsa ya dan daga ya ce" magana nake so mu yi ku fito na fada maku ba zan daki kowa ba

Shiru suka kuma yi, wanda hakan ya saka shi sada kansa yana jin zuciyarsa ba dadi

Sam baya jin dadi a kasan zuciyarsa

Karar bude kofar da yake jingine ya saka shi sauri dagowa harma ya mike tsaye ya juyo yana son gannin wanda ya iya fitowa

A hankali ta fito tana matsowa kusa da shi hankalinta a kan fuskarsa

Shima idannuwansa ya sauke a nata fuskar
Lokaci daya ya ji wata kauna irin ta da da uba na mamaye zuciyarsa

A hankali ta daga kanta tana kallon fuskar nasa, idannuwanta da ta gama sannin sunna da effet a kan mahaifin nata koda ya tashi duka sunna saka shi dakawata

ta kara masu girma sosai sannan ta yi masu kwal kwal
Nan da nan kwallah ta cika su, bakinta take son budawa aman ta kasa

A hankali ta shiga kokarin riko hannayensa muryarta na rawa tana son fitar da lafazi ta kasa, sannan hannayen nasama ta kasa rikowa dan sai take gannin sun mata nisa sosai

Idannuwansa ya rintse sakamakon jin wani irin tausayinta ya gama halaka bacin ran nasa
Tsantsar kaunar y'ayansa yana matukar yin tasiri a rayuwarsa
Ko dan sun kasance mata da yawa wa'inda ya dauki son duniya ya dora masu?

A hankali ya kama habarta ya dan dago yana kallon kwayar idannuwanta

Muryarsa ya sanyaya ya ce" kuka zaki yi?

Jin ya sauko hawayenta suka samu damar zubowa tana kallonsa sai a lokacin kuma bakinta ya bude cikin sanyin murya sosai ta ce" kar ka dake mu Abih, ka ga an summar da ni bayan bani da laifi, ka ga ya zazageta dan kawai an fada masa abubuwa
Abih ina zamu shiga mu ji sanyi ne?

Da sauri ya kama hannayenta ya karasa kusan dakinta sosai

Muryarsa ya dan daga ya ce" ku zo gare ni, ku zo kun ji?

Jin irin yanda muryarsa ta sanyaya ya saka du suke budewa sunna fitowa

Du kusa da shi sosai suka zo suka zazauna wasun su har sunna dora hannunsu saman jikinsa

Murmushi ya yi yana kallon ZAHRA ya ce" Zahra, daga yau kar ki kuma zagin mutun da nasabarsa, ko dukiya, koma menene kin ji?
Na gwamace ace da ni gaki cen kun daku da mutun na je na raba da ki yi irin wannan abin, kin san me ya sa?

Kanta ta girgiza tana kallonsa, hakama sauran

Hannayenta ya riko ya ce" abinda ya sa shi mutun ba'a gama halitarsa, baya fasa gannin jarabawar rayuwa har sai ranar da aka saka shi cikin kabarinsa

Eh lale yin fari ne kadara, na biyu ganganci na uku kuwa da gangan
Aman koda y'aya goma ta haifa na hane ki yi mata gorin hakan domin ko ke kin tsufa zaki bar baya kin ji?

Kanta ta ringa gyadawa
Ya maida dubansa wajen Ummu ya yi murmushi ya ce" haba Umana, idan inada mumunan hali ai bana tunanin zaki kulaceni haka, na fi tunanin zaki min adu'a sannan ki yi fatan kar Allah ya jarabeni da ku, wato ya dora hakan a kanku dan na rantse maki ban san wani hali zan shiga ba, ki ringa kyakyawan fata kin ji?

Kanta ta ringa gyadawa itama tana share hawayen fuskarta

Hannun NAJJEBA dake cikin nasa ya kara rikewa yana kallonta, murmushi ya yi ya ce" ni ko dai kece jinnin abuna ba ni ba? Yaya aka yi da wahala safia ta yi dare ya yi baki yi fada ba? Allah ya shirye ki

Kanta ta kifa saman cinyarsa
Ya kai dubansa wajen DAYABU dake tsaye da NAJEEB a hannunsa wanda ya ki yarda ya sauka daga hannun nasa tun da ya tsorata kar aban nasu ya dake shi

Murmushi ya masa mai tsayawa a rai kafin yana kallonsa ya ce" wa ya ce maku baku da wajen da zaku je ku ji sanyi?

Kunada wajen da zaku je ku ji sanyi sosaima
Ina raye, a doron kasa ai zan kasance maku katifar da zaku zo ku kwonta

Tunda shi ya fasa aurenta, dama yana neman hanyar silibe mata ne, da izinin Allah, Allah zai fitar maki da miji na gari

Murmushi DAYABU ya yi gannin du sun dodora kansu jikin Aban nasu

Dan haka ya karasa da najeeb a hannunsa ya ringa dauko ledojin dake dauke da burger din yana kawowa yana ajiyewa

Nan fa suka baje abincin, inda mahaifinsu ya fita ya je ya dauko yar karamar wace ta kai shekara uku a haife wajen uwarta ya dawo da ita bangaren y'ayan nasa inda uwar ta ringa cika tana batsewa ya zaunar da ita tsakiyarsu suka hadu sunna cin abincin sunna hira sunna wasa da daria tamkar ba sune suka shiga hali na matsananciyar damuwa yanzun ba

......................................


Da wani irin karfi ya diro daga saman bed din da yake kwonce a mike idannuwansa lumshe ya kai dubansa kan yaronsa da mamansa ta shigo da shi tana kuka tamkar ranta zai fita ta ajiye masa shi saman bed din hannayenta saman kanta sai jujuya kai take

Irin yanda zuciyarsa ta buga gannin yanda yaron ya mimike sannan jijiyoyin kansa sun yi rado rado sun yi tsanwa sharr idannuwansa na kallon sama sam baya motsi ba allamun motsi a tatare da shi

Hannunsa ya kai wanda ke wata irin rawa a hankali ya juyo yaron

Zinariya ta kara fashewa da kuka hankali tashe ta ce" ya mutu ko? Ya mutu?


Shaheed ya kalleta da sauri haka kuma zuciyarsa ta kara bugawa da karfi ya kara riko yaron ya ce"......
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



8




Da wani irin karfi ya juyo shi yana kuma kallon fuskarsa

Idannuwansa ya lumshe cike da tausayin kansa da kansa kafin ya rage tsayinsa ya shiga dodora hannayensa dan tabatar da abinda yake ganni a gabansa

Tsintsiyar hannunsa ya kama ya saurara da zuciyarsa dan kara tabatarwa kansa

Jikinsa a mace ya juyo wajenta inda ta yi tsaye tana jiran jin amsa

Wani ihu ta so saki, sai dai ta sake shi a cikin zuciyarta sakamakon rufe mata baki da ya yi da hannunsa na dama sanann ya talabeta da hannunsa na hagu

A hankali ya jata ya nufi falo baba da ita inda ta saki jikinta tamkar sumamiya tana gunjin kuka

Sunna fitowa falon a kujera ya zaunar da ita still bai saki bakinta ba

Yana dubanta har sai da ya rage tsayinsa ya kasance sun daidaita da junna a hankali ya ce" ihu zaki yi masa?

Gunjin kukan da take har jijiyoyin wuyanta da kanta sun fito rado rado ya saka shi janyota ya bata kyakyawar runguma
Hakan ya sakata kara sakin kukanta tana mai tambayarsa" shikenan ya tafi ya bar ni?

Idannuwansa ya lumshe yana shafa bayanta, baki daya ta yi jajajir ta rikice

Ta kuma fashewa da kuka ta ce" sai da na hana shi yin wankan nan na dare, ina shafa mai ya shige bayi har yanai min gwalo ya shiga kasan shower ya sakarwa kansa ruwa a kansa
Sai da ya ga raina zai baci ya fito ya bude min
Sai dai tuni jikinsa na rawa hancinsa na zubar da jinni

Fashewa ta kuma yi da kuka tana rike hannunsa da ya tsurawa fuskarta ido yana sauraronta ta ce" shikennan sai ya fara karkarwa sosai da sosai har hakoransa na hadewa waje guda sunna bada sauti hakan ya tsoratani na yi gagawar rufa shi da bargo na je dakinsa na shiga binciko magungunnansa tare da wasu kayan darin dan na saka masa

Ta rushe da kuka tana nunawa ta ce" ina dawowa da na daga shi na ganshi a haka, baya min murmushin, baya cewa" ki yi hakuri Anna
Baya barin jikin shine nace ko summar ce ya kuma yi?

Idannuwansa ya rintse yana jin wani irin yanda yake jin kansa ba karfi ba dabara
A yau ya samu kansa cikin wani tashin hankali mai gigitawa a tarihin rayuwarsa
A mutanen dake makale a cen cikin zuciyarsa yau ya shafe mutun na biyu kennan, bayan shafe idannuwan mahaifinsa da ya yi da kannanun shekarunsa

Hasbunnalahu wani.imal wakim
Sosai ya barta a kirjinsa ta samu kukan ita wanda hakan ya saka ta dan ji saukin zuciyarta

Sai da ta ci kukan har ya so zarce misali kafin ya dago habarta yana kallon fuskarta

A hankali ya kai bakinsa daudai nata, idannuwansa ya rintse kafin ya damki lebunnanta ya shiga tsotsa yana jin zuciyarsa ta yi masa nauyi
Bashi da kalaman da zai nuna mata ta yi shiru
Baya so gawa kwonce ta ringa irin wannan kukan

Sai da ya san ya kashe bakin kukan sannan ya dubeta ido cikin ido cikin yannayin tausasawa domin ita uwa ce, ba wanda zai kaita jin ciwon rabuwa da yaron nan shi ya tabata da hakan, shi yasa yake jin bashi da kalmar da zai iya rarashinta sai dai ya tunatar da ita cewa itama yau ko gobe, ko watarana sunnanta gawa, wannan kira na mahalici ba wanda ya isa a manta da shi ko a yafe masa, an halice mu ba tare da mun roka ba, zamu mutu ba tare da mun shirya ba
Tabas shi daya suka malaka a duniya sai bari biyu da ta yi bayansa, aman kuma wanda ya halice shi ya fita son sa
Dan haka cikin tausasa kalamai da iya yinsa dan gannin shi ya jure ya bata kwarin gwuiwa ya ce" ki daina kuka haka zinaria
Ki yi masa adu'a irin ta bakin uwa na tabata mala'ikun rahama zasu yi rige rigen zuwa amsarsa
Ki yafe masa har cikin zuciyarki tun daga daukan cikinsa, naludarsa, shayar da shi da kika yi, da hakurin tarbiyantar da shi, ki yi kokari daga yanzu idan kin buda bakinki dan ki yi salatin annabi ne sai ko ki yi ta yi masa shinfidar kabari har a kai shi
Wannan ita ce kaunar da zaki iya nuna masa a matsayinki na uwa
Wannan itace babar kaunar da zaki nuna masa zinaria
Kar ki manta *dukan mai rai mamaci ne*
(Allah jikanka babyna=ØÞ=ØOÜ)

Gani take du da ya samu bakin yi mata magangannun nan dan ba shi bane ita
Gani take sam bai san irin zafin ciwon da take ji a kasan zuciyarta ba
Yaya zai hanata kuka da daga murya?
Yaya zai hanata ihu da birgima?
Yaya yake so yarensa na shiru ya kasance a kanta a irin wannan bakar rana a gareta?
Bai san zafin da take iya ji ba, bata tunanin zai iya sanin karfin zafin da zuciyarta ke mata ba dan ba zai haihu ba kasancewarsa namiji
Wannan lamaru kuwa shi zai sa har ya mutu ba zai ji jrin yanda baki daya zuciyarta ke tsartuwar jinni ba


Zaunar da ita ya kuma yi sannan ya juya cikin irin tafiar nan tasa ta kasaitacen bujimin sarki
Sam bai iya sauri ba , wannan shine saurin nasa domin har yana kokarin kauce sawunsa na kafar gaba

Dakin ya koma,
A hankali ya karasa wajen bed dinsa

Cike da jin lamarin a kasan zuciyarsa ya langwabe kansa yana kallon gawar yaron
Ko jiya har kusan karfe goma yana zaune gefensa, abinda ya fi tsaya masa a rai irin yanda yaron ya nace sai ya ga fuskarsa sai ya cire masa rawaninsa a wajen karatu

Bai barshi ba har sai da ya ga ya fara gyadi gyadi ya dauko shi ya taho da shi nan bangarensa ya shaidawa mahaifiyarsa ta zo ta dauke shi yana jin baci
A lokacin ne kuma ya dauke rawaninsa wanda hakan ya saka yaron yin murmushi yana shafa gefwn fuskar mahaifin nasa sai kuma baci ya dauke shi
Ashe farkawa ya yi har mai afkuwa ta afku da shi?

Cikin nutsuwa ya shiga shirya shi
Yana yi masa wanka ne hawaye ya shiga zarya a saman fuskarsa
Shikenan mutun din kennan, shikenan an kare kana kwonce sai yanda aka juyaka
A hankali ya ringa llaba shi dan raunin fitar rai
A hankali ya gama tsaftace shi ya kimtsa shi

Ruwa ya watsa a jikinsa ya saka farar jalabiya irin ta saudiya sannan ya fito

Hannunsa ya mika ya dauke shi a hannayensa ya rungume shi ya karasa saman bes dinsa da shi ya dora shi

Alkur'ani ya dauko ya zauna ya buda ya shiga karanta masa murya a bude a bayanne

Irin yanda yake karatun zaka gane zuciyarsa a cikin wani yannayi mai rauni da tashin hankali take

Cikin nutsuwa ya samu ya yiwa yaronsa dukan abinda ya dace kowace gawa mai sa'a ta samu, ya samu adu'o'i kamar me

Kiran sallar fari akai a baban masalacin gidan sarki wanda yake cikin gidan

Shiru bai fito ba, a na biyu ne har hankalin liman ya fara tashi sai gashi ya fito

Sallah aka gabatar, ana gamawa ya fadawa liman cewa idan an jima a samu a leko rakiyar yarima, Allah ya yi masa rasuwa

Da mugun mamaki liman ke kallonsa irin yanda ya sanar da rasuwar cike da nutsuwa wada a irin ahekarinsa da yawa zaka same su da rashin nutsuwa har haka
Tabas ya yarda abin sarauta ya gama ratsa sarkin nasu sai fatan Allah ya tsare

Nan da nan ya sanar, wanda rasuwar ta matukar fifita mutane harma aka yi ta kokarin son ganninsa dan gabatar masa da gaisuwa sai dai ya shige da sauri ta kofar da yake shigowa


Direct bangaren mahaifiyarsa ya je

A hankali ya cire takalmansa ya karasa shiga ciki

Tana lazumi zaune saman salayarta, sanye da wata bakar riga mai hade da hijab har kasa rigar kuma budadiya ce sosai wace take sallah ne da ita

Yana karasawa gabanta ya je ya zauna wanda hakan ya sakata saurin dago kanta tana dubansa

Rawanin kansa ya shiga warwarewa a hankali da sauri ta maida dubanta sosai a kansa

Yana gama warwarewa ya kamo tafin hannunta ya dora a gefen fuskar nasa sannan ya lumshe idannuwansa

Da sauri ta kai karshe tana kallonsa , zuciyarta kuwa ta shiga tsintsinkewa

Muryarta na nuna tashin hankali ta ce" me, me ke damunka?
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment