Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Mardiyya ta kasance mai yawan zaginta hantararta da yawan faWa, a rayuwar yanzu ko Wan naka ya mallaki hankalin kansa sai da addu'a da kawar da kai, bare yar yarinyar da ta samu mai rarrashinta da nuna mata soyayya hakan na iya haifar da son nisantar mahaifiyarta da ta haifeta, karamin abu ne hakan)

Da mamaki ta kalli Ummu, da yanayin shashanci ta ce "ke ko har kin canza uwa ne haka zaki ringa kuka a hannuna?"

Ummu kam wajen ta bari ta koma saman kujera ta zauna tana mai bin Wudiliya da kallo wace ke zaune tana bin kowa da kallo itama

Wani murmushin ta yi ta kuma maida dubanta wajen yaran
Da idannuwanta take gallawa duk wanda sukai ido hudu harara, sai dai a yanayin yanda ta lura sun rigaya sun hade kan nasu na iya shege wato kar wanda ya gaishe da Mardiyya?

Sallamar Dayyabu ne ta saka su duban wajen

Shine ya fara shigowa cike da yalwatacciyar fara'a a fuskarsa
Bayansa wata yar budurwa ce kyakyawa fara tas , ta saka abaya baka har kasa ta yane kanta da mayafinta

Du sai yaran suka shiga murnar zuwansu
Zahrau ta mike tana yafa dan kwalinta cike da nuna kulawa suke yiwa budurwar yayan nasu barka da zuwa

Kasa ta zauna kanta kasa tana murmushi tana dan murza yan yatsunta, shi kuwa yana zaune kusa da Ummu yana mata magana kasa-kasa, haka kuma kannansa duk sun zagaye shi ban da Zahrau da ta shiga hidimtawa bakuwar cike da fara'a

Hannun Bilkisu ya dan doke ya ce" Mairama ki barni da tsegumi wai ba yayarku bace ku je mana ku tambayeta"

Jin abinda ya fada ya sakata dan dago dubanta tun bayan gaishe su da ta yi
Dan murmushi ne a fuskarta kafin ta mika hannu a hankali ta furta "Ku zo"

Sai da suka kara kallon iyayen nasu kafin duk su yi wajenta
Ai kuwa ta ringa cafe hannayensu suna gaisawa duk da ba sakin jiki suka yiwa juna ba amma fuskarsu da mawadacin farin ciki

Baki ta tabe kasa-kasa ta ja tsaki sai kokowa take da Nusaiba dake son zuwa wajen Ummu

Ammi ta kai dubanta wajenta ta ce "Mardiyya, barta ta je wajenta mana, mamanta ce fa, mahaifiyar Najeeba ce"

Da sauri ta dago ta kai dubanta wajen Ummu,
Sam Ummu bata kallonta, hasalima dariya take yiwa maganar DAYYABU na irin rigimar da suka sha kafin budurwar tasa ta yarda ta zo gaishe da su

A hankali ta furta "Na ji dadin jin haka, hakan na tabbatar min da tarbiyyarta, har ma na ji ina zumudin kasancewarta matar yarona"
Tana maganar tana kai hannunta gefen fuskarsa ta dan shafa a hankali sunna dariya a tare

Wani irin abu ne ya tokare kirjinta kokowa take da abinda zuciyarta ke tambayarta, dannewa take dan kar ya fito fili tana kara kallon su UMMU da DAYYABU ga kuma AMMI dake ta sakin murmushi da alama ta manta abinda ya kawo su gidan ko meye. Zuciyarta ce ta ci gaba da fadin 'What? Meye wannan? Wani irin abu ne wannan? Ko dai yar uwarsu ce? Meye tsakaninsu mai karfin da take zaune rashe rashe a gidan Ammi haka? Goye da Nusaiba ga kuma yaran sai wani hira suke uwa wace ta haife su da cikinta?'
Daga dogon corridor din dake hadawa da bangaren SULTAN iso ya ringa shigowa cikin maganar mutun kamar biyu

Da sauri Ammi ta kai dubanta, hakama Zahrau da du wani wandake wajen

Ita ce ta sanyo kai, cikin shigar da ta tafi da ita wato alkyabarta ce sai dai kamshin turaran ba wanda ta je da shi bane, kamshin turaran SHAHEED ne ya fara dukan hancin duk wani wanda ke wajen

Da sauri yayunta suka yo kanta, domin ja ta yi ta tsaya tana mai jin kunyar kallon su ido cikin ido
Wani irin farin ciki ne ya lulube zuciyar Ammi a lokacin da ta fahimci komai
Ummu ta sadfa kanta tana murmushin cin nasara

DAYYABU ne ya mike shima cike da farin ciki ya yi wajensu

A hankali suka kamota suka nufo ciki da ita
Budurwarsa da kallo take bin su, tabbas yau ta kara yarda da irin soyayar dake tsakaninsu, cike da mangari take dubansu, a ranta kuwa ji take inama ace sune haka? Ita bama yan uba bane aman ba wani kulawa da junna da suke da yan uwanta
A ranta take jin zata dauri niyyar kusantar yan uwanta koda kuwa ba zasu kulata ba har su samu fahimtar juna

Kanta a sade yake baki daya yau kunyarsu take ji, ji take duk sun gane abinda ya sameta hakan ya sa ta kasa hada ido da su sai kara sada kanta take

DAYYABU ya ce "Ke wai menene?"

Jakadiya da babar baiwar bangaren SULTAN ne kawunnansu sade JAKADIYA ta furta" Allah ya ja da rai , Allah ya taimake ki , Sarki na gaishe ki, yana mika sakon gaisuwa da godiya, yana neman afuwar jinkirin zuwan GIMBIYA"

Ammi ta kara yin murmushi kafin ta gyada masu kai suka mike suka fice

Mikewa UMMU ta yi ta karasa ta kama hannun Budurwar DAYYABU

Cike da kulawa ta mikar da ita tsaye ta kara matsota kusa da Ammi sannan ta dan dago habarta a hankali ta ce "Allah ya albarkaci rayuwarki yarinyata"

Kanta kasa tana kara sadawa domin ya sanar mata mamansa ce, cike da jin kunya da kaunar Ummu take kara sada kanta

Dubanta ta maida wajen su DAYYABU , a hankali ta furta "Ku tashi mu shiga ciki"
Duk mikewa suka aniyar yi suna kama hannun Najeeba ta mike kafin su nufi cikin

Wudiliya ta kalli MARDIYYA da ta yi mutuwar tsaye ta gyada kai cike da mamaki

Mardiyya ta karaso ta zauna tana kallon Ammi ta ce "Ammi baki ce komai ba, ko ya sake ni ne bani da labari ya auro wata?

Ammi ta kalleta, bata gane ta mata shiru ne dan ga bakuwar fuska? Sannan bata so maganar ta yi nisa irin haka a gaban yaran?
A hankali ta furta mata "Mardiyya, kar ki damu zan kiraye shi yau, idan ya so zai zo koda kuwa da ni ta kama zuwan zamu zo"

Yar dake kuka ta dire mata ta mike ta fara kama hanya
Da sauri Wudiliya ta mike ta bi bayanta

Sunna fita Mardiyya ta ja ta tsaya ta keta wani ashar tana fadin "ldan na yarda ya banzatar min da aure shegiya nake" (shi ya banzatar maki ko ke?)

Wudiliya ta ce "Yau na ga bariki gannin idona, kina zaune za'a yi maki sakiyar da ba ruwa? To ko danginsu ce ita wannan matar dake goye da Nusaiba? Ke anya baki yi sake ba za'a maki sakiyar da ba ruwa? Anya ba wasa kike da lamarin MUTALAB ba?"

Mardiyya ta kalleta, da kallo irin na son karin bayani
Wudiliya ta ce "dubi yanda y'ayansa suka nuna basu san da wata halitta wai ke a wajen ba, kuma suna kiran wancen da sunan Mama, dubi fa yanda babban dansa ke hira da ita kamar wace ta nakudo shi? Anya ba wasa kika tsaya yi ta fi ki iya bariki ba har ta fi ki fada a wajensa?"

"Ke kika san dalilin rabuwarsu? Kin ga kar ki wani raba min hankali, ina ce kin rakoni ne dan ki tayani sakawa ta masa magana? Nima ba zan yarda ba, wannan tsohuwar da na tabbata ta haife ni na rantse a yanda na san MUTALAB na tabbata ba zata dauke hankalinsa a kaina, inaga yar uwar tasu ce kuma kin ga bama zan bi ki ba zan koma na nuna hankalina ya ki kwonciya saboda jikin Nusaiba, zan jira shi ya zo ya fada min matsayina a wajensa a yanzun ehe, maganar y'ayansa basu gaisheni ba kuwa ban damu ba, dama me kike jira da fitsararri tambaWaWWi yan iska?" Mardiyya ta ida sa zuciyarta cike da wani tsoro da jin wata fargabar gannin Ummu, kwarai irin yanda ta ga yaran sun sake da Ummu ya daketa, irin yanda Ummun ta wani nuna ita din isasshiya ce a gidan ya daketa, ta jigata, accnt dinta ya yi kasa sosai, motarta tana bata wahala, ta je gidansu ya ce zai waiwayeta ya manta da ita, ko auren Najeeba sai a redio ta ji da kuma yanar gizo, ana ta yi mata barka wai ita matar ubanta, kwarai a yanda ta san MUTALAB da kwakwar mace ya bata mamaki, aman zai zo ba inda zata motsa wallahi kafarsa kafarta da tsiya tsiya! (Ko? Tsiya tsiya fa? Namijin? Ko kannin kemenka ne ka bishi a laluma domin yana dauke da igiyar da idan ya tsula maki ita sai kin rasa gane hanyar gidanku ko wacece ke!)

Kasa ce mata komai ta yi tana binta da kallon wawuya, idan ba wawanci ba ko Mutalab mahaukaci ne ai ita bata ga ubanda zai cireta daga gidansa a haka ba, bale mutumen a tsaye? Da alama Mardiyya sai ta sha bulaliyar duniya zata yi hankali

Du irin yanda suke so ta fada masu abinda ke damunta kallonsu kawai take, sai da ta ja iska a hankali ta kalli UMMU
Idannuwanta cike da kwallah, muryarta a raunane ta ce" me ya sa kika tafiyarki a lokacin da muke cikin rayuwar bukatar ki? Me ya dawo da ke a yanzu?"

DAYAyBU ya furta "NAJEEBA, meye haka?"

Najeeba ta dube shi ta ce "Yaya? Kai baka ssn sanin dalilinta na tafiya ne ko ka san dalilin nata ka ki fada min? Tsananin son kudinta ne ya hanata zama tare da mu ko kuwa bata dauki aurenta da mahinmanci bane? A yanzu da take son tirsasani zama da auren da bana so a matsayinta na wacce ta tafi ta tsinke nata auren tana tunanin zan mata biyayya ne?"

Da mamaki ya zaro ido, muryarsa kausashe ya ce "kina hauka ne? Mahaifiyar taki kike yiwa irin maganar nan, titaiyeta zaki yi kan abinda ba dolene sai ta fada maki ba ko fada zaki yi mata kan rayuwarta a matsayinta na mahaifiyar ki?"

Dan murmushi ta yi tana janye hannunta daga cikin na Ummulkhair, da yar yatsarta ta nuna Ummukulsum a sanyaye ta ce "abu nawa rashin uwa a kusa da ke ya tauye maki?"

Juyawa ta yi wajen Ummulkhair ta ce "har gobe cikinmu wa ke kukan da ace mamansa na nan?"

Zahrau ta nuna ta ce "yaya kika ji dadin zuwanta kusa da ke a yanzu?"

Ta koma wajen DAYYABU ta ce "da ace da daya wace ta rungume mu da yanzu ka haifi y'aya biyu ko uku, amma kasancewar kaine uwarmu a kulun tunaninka idan ka yi aure kar ka kawo wace zata daga maka hankali a kanmu"

Daga idannuwanta ta yi zata kuma yin magama suka sauka a kan ABIH, tsaye yake yana kallonta, duk basu san da zuwansa ba wanda tun da Mardiyya ta shaida masa zata je a message ya azamar ajiye abinda yake dan ya tarda ita kar ta je a yi rigima domin ya san wacece Mardiyya haka kuma ya san wacece NANA MARIAMA idan aka kawo mata raini

DAYYABU ya budi bakinsa a sanyaye ya ce "kennan har yanzu baki daina jin haushin auren nan naki ba?"

UMMU ta buda idannuwanta da suka cicika da kwallah
Karasawa ta yi ta zauna kusa da su sosai
Idannuwanta a kan Najeeba wace ta sada kanta tun da ta ga ABIH a tsaye

A hankali ta lumshe idannuwanta ta kuma budewa a kanta
A sanyaye ta furta "Ban taba aikin da na yi nadama irin tafiyar da na yi na barku a lokacin dakuke da bukatata ba, bayan sanin da na yi cewar y'a mace na samun tarbiyya ne daga mace yar uwarta, na san wa nake aure a lokacin, na saka kafa na shure y'ayan dake kallona su kirayeni *MAMA*, ya kara doke yaron dake zama ya dora kansa saman cinyata ya ce da ni *UMMU*, na tafi dan kawai fushin zuciyata bayan na kawo rantsuwa na gifta mai girman gaske da zafin kishin da ya rufe min ido wanda ya saka ni dana sani, na juya na tafi bayan na kunce goyonki a bayana ke da na haifa da cikina, ban ko waiwayoki ba na tafiyata da passport dina da visata na yi jiran jirgin da ya zo ya dauki passinger ciki harda ni ina hura hanci rai bace da kudadena da katina na banki na tafi na bar kasar haihuwata"
Sasautawa ta yi sakamakon hawayen da ya fara zubo mata daga gurbin idannuwanta
A hankali ta ci gaba da fadin "sai dai kashh, da na sani, da na kawar da kaina, na hadiye wulakanci da neman fitina da tashin dukiya da irin yanda kudi ke dukan kansa ke saka shi aiwatarwa a gareni na rungumi yan dagwai dagwai dina na rayu da farin ciki, domin kuwa daga bakin lokacin da na sauka, na fara kokarin ciyar da kaina, tufatar da kaina, neman abinda zan yi dan inganta rayuwata duk da tarin takardunna, da dukiyar da na tafi da ita ta gadona da iyayena suka bara min, sai rayuwata ta zamo wata sabuwar rayuwa mai cike da duhu duk inda na ga yaro ko yarinya sai na saki murmushi sai kuma hawaye ya biyo baya
Idan na zo kwontar da hakarkarina wani sa'in idan nonona ya soke ni sai ki fado min a raina
Nakan zabura ni kadai a dakin hotel dina ina jin kamar muryarki kina fadin *"MAMA, ZAN YI FITSARI"*
Na rayu cike da burin zama wata abu, da son goge ku a rayuwata na manta da ku na sake wani auren na haifi wasun
Sai dai me? Ashe na yiwa kaina mugun illah ta hanyar shakuwa da ku,
Makwoncinmu daya
A tsakiyarku nake kwanciya inai maku tatsuniya kunna hayewa jikina kuna kokoyi,
Idan kukai fada nakan ji hankalina ya tashi, zan saka ku shirya ta hanyar nuna maku ilar abin
Na saka shakuwa mai tsanani a tsakanina da ku, da yayanku har ya kasance na zabi kulawa da yara a matsayin karatuna"
Sosai take hawaye hakan ya saka ta saka hannayenta ta toshe bakinta dan kuka take son yi sosai

Dayyabu kansa da yake mai saurin hawaye ne idannuwansa sun cika da kwalla, hakama sauran du hawayen suke zubarwa ciki kuwa Harda Najeeba dake hango duk abubuwan da take fada a zahiri kamar a lokacin komai ke faruwa da rayuwarsu

Mikewa ta yi da sauri ta juya da nufin tafiya, domin ita dai da bakinta ba zata iya furta masu dalilin fushinta ba

Karron da ta ci da shi ne ya sakata kokarin zubewa
Sai dai bai bata damar hakan ba ta hanyar tareta sosai da hannunsa kafin ya maidota dakin da kyau kusa da yaran ya aniya zaunar da ita yana kallonta a sanyaye ya ce...
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



46


A sanyaye ABIH ya ce" ina zaki je bayan ina jiran wannan ranar shekara da shekaru dan na baiwa Najeeba amsar tambayarta wace du sauran yan uwanta ina iya basu amsa kai tsaye na dalilin da iyayensu suka bar gidana aman ita na kasa bata amsar?"

A tsorace take kallonsa, bakinta na rawa ta ce" amsar? Wace amsar kake tunanin zaka iya fada masu?"

Abih ya dan yi mata murmushi mai ciwo a hankali ya furta" haba *SIRRINA*, baki san sun san wani *Sirrin* rayuwata mai tsanani kuma suka hakura suka ci gaba da mutuntani ba? Yaya kike so ki ci gaba da fuskantar irin wannan shariya da abubuwan da y'arki kwalin kwal ke maki a kan namijin da ya kuntata maki? Kina da bukatar samun girmamawa, soyaya, kallon daraja daga wajenta, tabas kina samu daga wajen yan uwanta aman ita din ke kika haifeta fa? Dan Allah ya isa haka, ki barni na fada"

Har bakinta rawa yake ta furta" aa, ba ruwanka da abinda ke damuna, ni ban rokeka fadin wannan abin ba, ina fadawa Allah idan lokacin ta dubeni ya yi zata dubeni dan kanta"

Murmushi ya yi yana dubgure kanta ya karasa da sauri ya zauna gaban y'ayam nasa ya ce" ba ga irinta ba, ci gaba zata yi da boyewar, tana kakare laifina, ita dai a haka take so ta kare?"

Najeeba, na auri mata goma sha bakwai a rayuwata
Cikinsu ba wace ban haihu da ita ba, kuma ba wace ta ga girman y'arta take fecewa
Na birne mace uku a gidana wa'inda suka rasu a hannuna, sauran goma sha ukun nan du rabuwa muka yi, banda mardiya ta sha hudu
Najeeba, kamar yanda kuka sani, wasun dalilin na tarda su sunna dukanku ne, wasun rana tsaka zaku tubure da rigimar bakwa son su, wasun zasu nunan ba zasu iya rike y'aya birjik haka kawai bane, wasun zalamarsu ta saka, wasun kuwa sun aikata abinda ya hana min yafe masu ne ya saka ni rabuwa da su aman banda *NANA MARIAMA*

Sai da ya kalli UMMU dake kallonsa da mamakin wai da gaske bayanin zai yi ya yi murmushi ya ce" aminiyar BILKISSU ce, wato Ammi dinku, ita ta yi mata gorancen aurenta, sun kasance masu raba ayya daya, sunna rike sirrin junnansu duda BILKISSU ta bata shekara UKU a haife wanda hakan ya saka idan ta yi niyar tsokanarta ko idan tana cikin yannayi na tashin hankali takan kirayeta AUNTY domin takan ce da ita "Bani da kowa sai Allah sai ke"

Min sasanta kanmu da NANA MARIAMA a lokacin da nake amsa sunnan Yaro da kudi, ina jin wani irin tashen kudi dake daukana yana yawo da ni yana dadani da kasa

Na tara y'ayan sai dai ba wai takamaiman su din ne a gabana ba, ina dai da wani irin kaunarsu a zuciyata wada ke sakawa idan aka yi katari na dan zauna na ji damuwarsu to fa ko wace iri ce zan dage na magance masu banda zama da su da kukawa da tarbiyarsu da kuma gane irin ilar sakin iyayensu da shigowar bakin fuska a matsayin sababin iyayensu ke janyo min
Sai da na auri NANA MARIAMA na fara gane meye ma'anar zuri'a,
Tanadinta zuri'arta, burinta zuri'arta, farin cikinta zuri'arta, abokannanta zuri'arta a lokacin ta shigo ta tarda mahaifiyar Ummukulsum da tsohon cikin Ummukulsum

Zamansu bai yi nisa ba na sawake mata a lokacin da ta haifi yar jaririyarta sakamakon gannin itama ta haihu yanzun zata fara ware nata daban sauran daban wanda na kamata da hakan sau uku karshe dai na sawake mata na ci gaba da koyon rayuwa a wajen NANA Mariama

Fadace fadace, rashin zaman lafia, rigingimu na tsakanin miji da mata kan hada mu, sai dai wani ikon Allah daga lokacin da zan tabo ku zata zube a kasa gwuiwoyinta a kasa tana kuka ta ce" ka yiwa Allah ka yiwa Annabi muhamadu salalahu alaihi wa salam ka barni na huta, ka barmin yara su huta, kai baka gannin yarintarsu, soyayarsu, karfin zuciyarsu? Kar ka hargitsa min tarbiyarsu ko ka birkita min zaman lafiyarsu, yaren nan sune farin cikina, kai ka san ba dukiyarka ko kyanka ya saka nake hakurin zama da kai ba sai dan yaren nan"
Abinku da wanda shedan ya rigaya ya buga min ganga sai na sheke da daria sai na kalleta a kaikaice na ce" ku ji shishigi malan, yara ina ruwanki da su? Su tashi a tashama mana na san tarbiya ta Allah ce ba ta wani ba, dan haka idan kin gaji da zama da ni ki kama gabanki!"

Zata kawar da kanta, ra mike ta tatara ku ta yi vangarenku da ku, ta hanna yan aiki zuwa inda kuke da cikinta a jikinta ta yi ta kulawa da ku, har sai na kasa jurewa dan kaina na dawo na lalabata domin du abuna nakan kasa nutsuwa idan muka yi fadan da ta min fushi har ta kaurace min, zaku ga na dawo ina lalabata mu shirya"

Dan murmushi ya yi ya ce" har zuwa lokacinda yar uwarta wace ta kasance yar mahaifinta ce ta bayanna,
Wannan itace rayuwar da na yi mafi muni a cikin rayuwar da giyar kudi ta kaini ta baro ni"

Kallonsu ya yi da kyau ya ce" a lokacin bata fi wata hudu da cikin Najeeba a jikinta ba, murna farin ciki haka take bugawa mutane tana fada masu ashe tana da yar uwa? Kuma itama yar uwar nata da danginta bangaren mahaifiyarta, wato dai ta samu dangi

Sosai ake shige da fice ana tayata murna, harta da dangin na yar uwar tata sun zo sun taya murna, inda yar uwar tata ta tare a gidanmu suke zaune kalau

A hankali yau da gobe, kadara da haduwa da wata irina wace ta sako duniya a gaba muka shiga fandarew, munna watsewa, munna aikata alfasha a boye a cikin gidanta na aure cikin du dakin da hakan ta kama"

Subahannalah, Ummu ta fada da karfi ta ce" wai wa ya tambayeka?"

Hararanta ya yi ya ce" ko dai bakin ciki kike na huta da nauyin dake kaina ne?"

Ci gaba ya yi da fadin" tun bata sani ba, har Allah ya sanar da ita,
Ta ci kuka, ta yi dana sanni harma ta so bara min gidan sai dai a lokacin da DAYABU ya riki kafarta yana ihun UMMU UMMU, sai kawai ta fashe da kuka ta rungume shi ta bara mana wajen wato gamu ga duniyar"

Kunya ta hanna min zama sai na bara masu gidan na tsayin sati, ashe aikin gama ya gama har ta dauki ciki na tsayin wata uku, UMMU kuwa na dauke da nata wata bakwai

Dole na waiwayo iyalaina, dole na waiwayo matata da y'ayana,
Sai dai kash bayanuwar cikin ya kara hadasa mata tashin hankali

Na takaice maku, ni da kaina sannu a hankali na ringa haifar da dalilan da suka ringa kara nisanta ni da matata ta rufin asiri wace du abubuwan nan da nake mata ko kanwata daya kwal wace ta ragen a duniya kuma aminiyarta bata sanarwa ba, sai dai ta rufe daki ta ci kuka ta fito a yi abinda za'a yi

Akoy ranar da ta tasheni tsakiyar dare ta ce da ni" MUTALAB, na aureka ne domin Allah, ina zaune da kai dan Allah ya saka min kaunar y'ayanka, Mutalab a da ina tunanin ina iya hadiye komai dan yarenka, aman a yanzu na gane harta NAJEEBA dake da shekara uku ina iya bara maka na tafiata idan har baka bar rayuwar nan da kake ba, idan har baka takawa zuwan uwar yarinyar nan da take takenta birki ba zan wanke kafa na je na daki mamanta na daketa na yi kason haka, MUTALAB idan ka kai zuciyata makura zan halaka ka na halaka kaina, dan walahi walahi irin yanda nake maka magiyar ka aureta idan sonta kake ka nuna min yaya zaka kuma iya auro bara gurbi a cikin gidanka to fa ka kiyayi du wata mu'amala da ita, idan ba haka ba MUTALAB zan halakamu baki daya mu shiga uku, na roke ka ka sawake min na yi tafiata"

Sai kawai na fi ta hawa dokin zuciya, na rufe na ringa shiga ina fita ina fadin" Mariama, kin jima baki halakani ba, ki gwada idan kina yiwa Allah ki gani! Ni zaki nunawa zuciya? Kin san ni gaba da baya ko waye, kuma idan takamarki kina da kudi kin san na dame ki na shanye, ki zubar min da y'ayan mana, sai na auro wata ta zo ta kularmin ai kin san ba ke na fara aure ba, kai ni banma yarda da rashin aurena har yanzu ba, na tabata kin asirceni ne malama"

To fa ranta ya bace, muka ringa sakawa muna fidawa wannan karron har gaban sarki da kuma BILKISSU,
Ko a nan kin fadin dalilin fadanmu ta yi, Sarki na mata nasiha sai da aka tambayi musababi ba kunya na fadi dalilin kai tsaye wanda ban taba jin kunyar abinda nake aikatawar ba sai da ya ringa yi min nasiha yana tino min rayuwa da mutuwa, a lokacin na furta walahi walahi walahi sau daya tak ne, yarinyar ce ta cika neman fitina har take nuna kamar wani dinkewa muka yi da ita,

Sai da aka shirya mu da *SIRRINA* kafin muka dawo gida

Shekara
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment