Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kuma kikai shiru kema zaki bita, Nadia koda kuwa Allah ya yi wannan shi nr hanyar da zaki mutu kin fi so ki mutu ba tare da kin fadi abinnan ba? Bale da izinin Allah an kare, ba wanda zai kuma taba ki, ki buda idannuwanki ga mijinki, ga mahaifiyarsa, ga mahaifinki, ga yan uwansa da iyayensa , ki fadi koma menene"

Nadia ta dora kanta saman cinyar mahaifiyarta ta rintse idannuwanta, ta ce" Amintace ne, da kuma wannan mai rike katuwar bulala kusa da Sultan idan an zo shara'a, su ne suke zance, shi wancen ya ce shi dai baya cikin maganar kisa, abinda yake so kamar yanda aka hana masa jin dadin aure shima ya wayi gari Sultan baya iya jin dadin aure..........

Sai ta fashe da matsanancin kuka ta dora da fadin", shine Amintace ya ce" kamar yanda ya katse masa dukan farin ciki, ya dawo ya dauke shi a matsayin dogari ya ajiye komai nasa na farin ciki, to lalle shima sai ya kai ga ransa, kafin nan sai ya cikawa Gimbiya burinta na son raba shi da kowace mace ko ta halin kaka sannan ya kashe ya kashe Sultan"

Wata irin faduwar gaba NAJEEBA ta ji, har ta yi gagawar kallon SHAHEED dake tsugune kusa da Nadiar yana kallonta tamkar TV

Da sauri Zinaria ta sauko kasa hannayenta saman kanta ta ce" Na san a duniya idan akoy abinda na fi tsana shine mijina ya rabi wata macen, burina koma wacece ta bar min mijina koda kuwa mutuwa zata yi, aman ban taba gigin kashe kowa ba, ba ni nake kashe masa mata ba, ban taba zuwa dan kashewar ba, na san bakina na furta kalamai aman ban taba gigin kashewa ba, kuma haduwar da nake yi da shi ba wani abu bane sai taimakon da yake kawo min ba dare ba rana cewar na aikata ko na zubawa Sultan a abinci hakan zai saka ya tsani matan da ya aura, ni ban san maganar maciji ba, banma san cewar wai har ta kai shi ga haka, tabas ina da matsanancin kishi, ba zan iya raba mijina da kowace mace ba, aman ban taba aikata kisa ba....." ta karashe tana mai fashewa da matsanancin kuka

Kamar wace aka kunna ta kuma zabura ta dora da fadin " kuma a jiya a jiya kirana ya yi, bamu hadu ba yake ce min zai saka ni farin ciki yau, zai fara rabani da daya kafin dayar, ni ban san nufinsa zai kasheta ba "

Ammi kai kawai take girgizawa hawaye masu zafi suna zuba daga gurbin idannuwanta sunna sauka saman fuskarta, NAJEEBA kanta a zaune take ta zubawa mutanen nan uku ido, tun daga kan SULTAN, NADIA, uwa uba Zinaria
Haka kawai take jin abin sosai a ranta, harma irin tsayuwar da ya yi na yan mintunna ya kura mata ido ya bata tausayi

A hankali ya juya ya nufi dakansa wanda hakan ya saka du wani mutun dake wajen rakashi da ido, UMMU kanta hawayen take cike da mamakin wata amanar ta mutanen yanzu da sam basu da amana, shekara nawa kana tare da mutumen, du yawancin sirinsa da yardarsa ya yarda ya baka shikenan rana tsaka a kama irin wadinnan magangannun a kansa

Bai jima sosai ba ya bayana, cikin shigarsa ta sarakai sosai ya fito a yanda yake fitowa da

A yanzu sai ya zauna saman kujera ya dake
Ya dan jima a haka sannan ya dago da dubansa ya sauke kan NAJEEBA dake zaune jikinta doguwar rigar nan ce kawai ba wani lulubin da ya dace , dan haka a sanyaye ya furta " AMMI da UMMU, a lulube GIMBIYA NAJEEBA da NADIA "

AMMI na kallon yannayinsa cike da wani irin tausayinsa a zuciyarta ta janyo hannun NAJEEBA ta sakata a jikinta sannan ta lulubeta da alkyabar dake jikinta hakan ya sa sosai ta baza Alkyabar kasancewarta mai fadi da tsayi ga kauri sai ta wadace su ta baje da kyau ta rufe su su duka
Hakama UMMU ta aiwatar ta hanyar mayarwa da Nadia tata jikinta bayan ta kara lulubeta

Sandar dake hannunsa ta sarautarsa wace a yanzu a komawarsa ya daukota ce ya doka da karfi wanda hakan ya saka lokaci daya daga Zinaria, UMMU, AMMI, suka yi kasa da kawunnansu, Nadia da mahaifanta ne basu gama gane wasu sirinan maganar sarki ba hakan ya sa sai da suka kalli yanda su AMMI suka yi sannan suma suka sada nasu

Budewar da aka yi aka shigo da salama ne ya saka gaban AMMI yankewa ya fadi, muryar Amintace ne ta bayana rikeken Namiji maji karfi, tsayaye mai yannayin tsayayen namiji,

Sai da ya dan saci kallon mutanen wajen sannan ya yi irin gurfanar da yake dan kawo gaisuwa ga SULTAN SHAHEED

SHAHEED kallonsa kawai yake, sai da ya jima a haka sannan ya ce " Ka kula da bata mutu ba, gatanan ta mike da ranta AMINTACENA? "

irin yanda ya furta kalmar AMINTACENA din yana mai cije lebensa da karfi ya saka Ammi rintse idannuwanta cike da bacin rai da fargaba

Kara sada kansa ya yi, du da irin yanda gabansa ya kwonci kwonci ya fadi, sai ya yi kokarin anfani da kwarewarsa ta wajen yaudarar mutanen dake tare da shi da zuciya daya wa'inda basu gama fahimtar shi din ko wanene ba ya kara tausasa kalamansa domin sam bai taba tunanin Zinaria wawuyar da zata iya sakarwa lokaci daya bane harma ta fadi abinda ke faruwa dan haka ya dauki aniyar karyatar da Gimbiya a gaban sarki duda hakan baban laifin da ake iya gurfanar da shi ne, sai dai zai yi anfani da tarin yardar da Sarkin ya yi masa shima ya kwatanta kwatar yancinsa, dan haka ya ce " wace bata mutu ba ya uban gidana "

Shaheed ya kara lumshe idannuwansa cike da dacin zuciya ya dan saki murmushi yana kawar da kansa, ta yaya zai zauna su ci gaba da wulakanta junna? Dan haka dubansa ya kai wajen mahaifin Nadia ya ce" honorable, gashi a tafi da shi PeJi, ka sani wannan yaro horona ne, domin tun yana da yan dabarunsa na kasancewa police a da, na kara nitsar da shi na bashi horo kala daban daban na yau da kulun, sai kun yi taka tsantsan da shi, sai kun dora idannuwanku a kansa sosai, kar ku saka shi a daki mai kasa ko mai ruwa, ku kiyaye saka shi a daki mai duhu , ya kasance a kejin da hasken wata da rana ke iya haske shi, ya kasance koda mutun daya ne na ganninsa hakan zai hanna masa du wani yinkuri na gannin ya kubutar da kansa"

Dan sasautawa ya yi gannin irin yanda ya dago a gigice yana kallon SULTAN

SHAHEED ya maido dubansa cikin idannuwansa, ya kasance sun yi ido cikin ido da wani irin kakausan kallo da idannuwansa da suka dauki ja yake kallon na Amintacensa, da sauri ya sada nasa duban dan kuwa baba da babansa fa, sai dai baki daya jira yake ya karasa ya bashi damar yin magana aman sai ya ji ya dora da fadin " A bincika maganar Gimbiya NADIA, sannan a yi anfani da shaidar abokiyar aikatawar tasa, na baku damar ku shigo fada ku yi binciken da ya dace da su baki daya, du wanda ya taka doka ta taka shi koda kuwa *Gimbiya Zulaihat* ce ! Ya karashe yana mai doka sandar nan a kasa a kausashe ya furta " *Idan har ka yi gigin tashin da kake kokarin yi a wajen nan zan tashi mu gwada karfi da kai wulakantace mai wasa da Amanar Allah! Domin ina mai tabatar maka ba zan barka ka huta ba har sai ka samu naka hukunci daidai da laifinka, sai ka girbi abinda son zuciyarka ya kaika aikatawa!*

Sakwat ya yi ya mayar da kafar tasa, ba zai yarda du haukansa Sultan shaheed ya ajiye alkyabarsa dominsa ba, shi kam ba yau ba ya ringa tunanin karfin Sultan Shaheed kamar mai iskokan dake doka mutun da kasa, irin mutanen dake kawo masa tsagerancin da wani sa'in dole sai shi zai iya tankwasa su bake wa'inda suka shigo da takamar asirinsu dake tatare da su hakan ke sakawa su gagari dogarai, daga ya fuskanci hakan yake gagawar yiwa tufkar hanci tun kafin a gane gazawar dogaransa da ba gazawa ce sukai ba, lale lale shi din ne ya san abinda ya taka shi yasa du wani kwaro mai jin kansa na hayaki yake yin lakwas a gaban Maza, dan kuwa makashin maza maza ka kashe shi ba shaka!

Sojoji ne su hudu suka shigo, babansu ne da yara uku,

Suma dukawar suka yi suka kawo gaisuwar sannan mahaifin Nadia ya kora masu bayani, da irin tsaron da ya kamace su da komai, sannan suka sakawa Amintace ankwa wanda ke ta fitar da huci yana son kallon Zinaria dake kuka ya kasa har suka fita da shi

Sai da ya kuma rintse idannuwansa ya bude a sanyaye yana kallin iya mutanen da suka rage domin mahaifin Nadia an tafi da shi, sai mahaifiyarta , ya kai dubansa wajen AMMI ya furta" A kilaceta bangaren bayi "
.yana gama fada ya mike inda baki daya Zinari ta idasa kara zubewa tana son kama kafafuwansa dan ta bashi hakuri, aman ina ya ki bata damar hakan domin na farko da ta rike irin yanda ya wancakalar da ita ne ya sakata idasa fashewa da kuka tana fadin ita bata yi kisa ba, bata yi zina ba za'a kilaceta a bangaren Bayi? Ita ba baiwa ba jinnnin sarkin Agadez, matar Suktan shaheed wace ta bashi d'a, itane yau za'a kai bangaren bayi? Dan ta yi kishi shikenan sai a wulakantata?

Da zafi zafi AMMI ta ce" wato har yanzu baki ga ilar tarbiyarki da mashawarantarki da son zuciyarki ba har kike furta kalaman nan? Wato har yanzu baki gane alfarmar kin amsa kiran sunnan matarsa ya saka ba'a saka maki ankwa an fita da ke a gaban talakawanki ba? Wato har yanzu baki gane kina cikin matsala mai girman gaske dan kuwa ke kanki baki san irin abinda yake bakin ko na menene ba har sai sun gama bincikensu a kanki sun gano irin girman laifinki shin ya cencenta a barki a hora ki a sirri ko kuwa dole a fitar da sirrin ba? Ke baki gane cewar alfarmar mahaifinki kika ci ba?, Baki gane cewar a yau, a yanzu ke din nan ba kowa bace sai sakaryar macen da ta kasa yin hakatacen kishi ta tafka kuskure wa rayuwarta ta wulakanta kanta ba? Baki ji daga bakin wanda kika yi mugun abun dan ki malake shi naki ke kadai din kin cenza sunna daga ZINARIA zuwa Zulaihat ba?, kaicon ki ZULAIHAT, kaicon ki, ke kau kin shiga uku, ki rasa wanda zaki ci amana sai mijinki?, kishi ai ba hauka bane ZULAIHAT! Ke yau koda an samo gaskiyar lamarin cewa babu hannunki a maganar kisan nan kina tunanin SHAHEED zai sauko da wuri wuri ya dube ki ne? Zaki samu irin darajar da ya baki a da ta kasancewarki matar da ya fara aura, wace ya fara haihuwa da ita ne? Zaki yi asara ta yardar da mijinki ya baki, zaki yi asara ta irin gannin girmanki da kimarki da yake, zaki gani a aikace ke din ba wanda kika fi, zaki fahimci halayanka sune limamin dake jan ragamar rayuwar da zaka iya fuskanta da mutane tun a nan gidan duniya! Kin san kina son sa kika yarda aka aura maki SULTAN? Inace y'ayan zamani akoy gungiyar dake kare hakin ku, koda kuwa mahaifinki ne sai su hanna shi yi maki auren dole, ita mahaifiyar take da ta kasance babar banza ta isa ta hanna kanta zama da kishiyar ne? Yaya bata iya hanna komai da nata rayuwar gidan mijin ke kike gannin ta isar maki? Dan ta haife ki shikenan komai halayanta sai aka ce ki yi mata biyaya? Ke din sakarai ce da baki san abinda ya dace da rayuwarki bayan haihuwa guda da bari uku da yanzu y'ayanki hudu a gidan nan, da a gabansu zaki amshi hukuncin cin amana wa abihnsu? Yaya zaku yi auren gidan sarauta ku yi tunanin zaku kasance ku kadai jal?, ke a zamanin nan ko talakan da bashi da ko sisi ya samu damar jera mata hudu jera sun zai abinsa koda kuwa bashi da abinda zai ciyar da su ne, bale wanda Allah ya horewa? ke da kina da hankali, ko da kina tare da magaya masu nazari da sun nusar da ke cewar idan akoy mai dama a wajen mijinku ke ce, ke kika fi kowa sanninsa kafin wata, ke ce mai dauke da lakanin da zaki iya zuwa kai tsaye gare shi kafin wata, ke din nan da kin koya masa yanda a duniya koda ya so wata fiye da ke to fa tsananin girmanki, darajarki, kauna ta zaman tare zai hanna masa wulakanta ki, an fada maki matar farko abin wasa ce a zuciyar mijinta? Idan kin ga namiji yana abun kirkin da a da ba haka yake ba sai bayan aurensa tabata harda gudunmuwar matarsa, idan aka ce lalacewa halayansa suka yi tabata wace ta ja hakan ita ne, menene burinki? *MULKI, ARZIKI, KI KADAICE SHI IYA KE* dan kar KAWAYE SU ZAGE KI, ko a gazawarki? Sai gashi ina mai cike da tsoron kar a je kin rasa komai.......AMMI ta karashe tana mai share hawayenta sosai

Dubanta ta mayar wajen mahaifiyar Nadia da Nadiar kanta dake zaune kawunnansu a kasa ta ce " Ku yi hakuri, a yanzu ba zai iya bayar da hakuri ba, ku tashi a raka ku bangarenta ta huta "

Da sauri Nadia ta ringa girgiza kanta, a tsorace ta ce" AMMI, dan Allah aa, akoy maciji a cen "

AMMI ta dam sauke ajiyar zuciya ta ce " to ku tashi ku je bangarena, nima gani nan zuwa "

Ai kuwa mikewar suka yi ita ta yima mamanta jagora hanyar bangaren AMMI suka bi suka shige

Dubanta ta kai wajen UMMU a sanyaye ta ce" idan yaya ya dawo zamu yi shawara da shi kan maganar wannan ware waren turakar, bana jin zan iya kuma barin hakan ta faru"

Ita dai kai ta gyada kawai, domin baki daya jikinta ba karfi, harma mamakin irin karfin zuciyar AMMI din take, duda takan share hawaye lokaci zuwa lokaci aman sai kokarin gannin ta daidaita komai take

Wayarta ta ajiye, tana kara taba jikin NAJEEBA

Cen sai ga tsohuwar JAKADIYAR dake kula da kebantacen wajen da ake kebe ahalain gidan da wani abin ya ritsa da su

Sosai ZINARIA ta fashe da wani irin kuka tamkar zata side a lokacin da suka kamata suka mikar da ita

A kausashe Jakadiyar ta furta" Hatara dai Zulaihat, sasauta muryarki a falon mai damagaram kike "

Ai kuwa ta yi kitttt tana ji tana ganni suka fice da ita duda an bi ta sirri da ita aman ina ta tabata wannan magana har ta gama yada fada, ita kam ina zata saka ranta? Ina zata tsoma ranta? A irin yanda take da wulakanci, yanda ta dauki masu yi mata hidima da sauransu tamkar wasu bayinta, sam ba maganar mutuntawa sai tarin wulakanci da tozarci, dan ta tofa maka yawu ta kireka dan talakawa bawanta ba wani abu bane, dan ta saka a yi maka bulaka ba wani abu bane, tana jin dadi idan tana wulakanci, takan ji kwonciyar hankali da nutsuwa a zuciyarta idan tana wulakanci, a ganninta wannan shi ne bambancinta da sauran, wannan shi ne bambancinta da talaka, sai gashi yau zata je kebantacen wuri, wajen da ba rasa ci, sha , sutura zaka yi ba, bambancin shine bata da wata alfarma a wajen sarki, bata da damar ganawa da shi, bata da damar dora doka ko taka wani, tana da yan hidima sai dai bata da damar wulakanta su domin inci ne da su, suma sunna wajem da suke fada a ji ne, zata je duniyar mahidimta ne, wajen da suke nasu sarauta ne, y'aya da jikoki ne, bata da damar sakawa ko hannawa sai abinda hali ya bada ne, hakan ya matukar razanata, ya hanna mata sukuni har aka karasa da ita fadi take a bata wata

Basu hanna mata ba, suka bata wayar , nan da nan ta yi kiran mahaifiyarta ta shaida mata wannan labari da ya kusan saka maman nata jin zuciyarta zata tsaya
Itama hankali tashe ta nemi gannin sarki a kusancin magaribar nan wanda a yau bangaren Zahrau yake, sai dai amsar da aka bata cewar ba zata samu ganninsa ba ya sakata yin zaman yan bori, a nan kasa inda kuyanginta suka rikice harda yar kazaginta wace ta fece da gudu bangaren Yarima dan kai masa labarin halin da mahaifiyarsa ke ciki


Wannan kennan


Sai da AMMI ta ja numfashi ya fi a irga sannan ta kara shafa kan NAJEEBA a hankali ta ce" tashi Najeebana "

Da taimakonta da na UMMU ta mike tsaye

Ammi ta kama hannunta da niyar tafia da ita bangarenta , duda ba haka take so a kasan zuciyarta ba sai dai gannin kamar NAJEEBAR nada bukatar taimako sai ta kasa barinta a nan din

A hankali UMMU ta ce" AMMI, me zai hanna ita a barta a nan? Mai yiwuwa ta taimaka masa da wani abin?"

Sai da ajiyar zuciya ta kwacewa Ammi, aman sai ta kada furta komai ta ja ta tsaya tana kallon yannayin NAJEEBAR

Gannin kanta a kasa tana ta wasa da yar yatsarta sai AMMI ta lumshe idannuwanta ta juya a hankali ta yi gagawar kama hanyar tafia, kwarai tana son ya samu kadaicewa da mace koda kuwa ba abinda zai shiga tsakaninsa da ita, koda kuwa ba zai yi maganar abinda ke damunsa ba, koda kuwa ba zai kulata ba, tana son wani ya kasance a kusa da shi, shima fa mutun ne, mai rauni, mai tare da damuwa, mai son idan yana cikin damuwa ya samu mai taya shi, mai bashi shawara, mai nutsar da zuciyarsa

UMMU ta kama hannun nata da take wasa da shi, a sanyaye ta ce" ki shiga ruwa masu zafi ki jima a ciki sosai, sannan ki sha ibuprofen"

NAJEEBA ta dan gyada kanta tana hadiyar yawu masu zafi a makogwaronta cike da yannayin damuwa

UMMU ta dago habarta a sanyaye ta ce" my BEEBA? "
Najeeba ta kaleta jin wani sunna da ta fada

Ummu ta yi dan murmushi ta ce" SHAHEED ne yake ce maki MY BEEBA, a lokacin da ake kawo ki wuni wajen AMMI din ki "

Da mamaki a fuskarta, muryarta a sanyaye ta ce" Dama yana min magana ina karama? "

Murmushi UMMU ta yi ta ce" yana son yara kananu, burinsa AMMI ta haifa masa kani shima, ganninki a wajenta sai ya samu abin nishadi idan ya baro fada da wajen horo da hawa doki, yakan yada zango a bangaren da aka zuba maki kayan wasa da masu kula da ke, sukan bara maku wajen shi kuwa ya ringa saka ki tatata kamar yanda kike tafiarki a hankali sai ya ce *ZO NAN MY BEEBA* , tun baki iya sunnansa ba, irin yanda yake zuwa da ke wajen mai martaba shi kuwa yana kama sunnansa ne kai tsaye har kika iya da maganar yara sai ki ce " JAHITT, wai SHAHEED "

Wani murmushi ne ya dan subuce mata , sai kuma ta kalli UMMU ta ce" to me ya da daga baya ya tsane ni? Me ya sa daga baya na kasance babar makiyiyarsa? Kaf cikin yan uwana na dawo ni ya fi tsana? "

Ummu ta lumshe idannuwanta, a hankali ta ce" ni kaina ina son sani, ko zaki yi kokari ki samo mana amsar nan?"



.............hi............
[3/31, 11:36 PM] BAK'A CE: >ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



57




Kanta kawai ta sada bata iya baiwa mahaifiyarta amsa ba, a haka UMMU ta saki hannunta ta bi bayan AMMI

Ta jima nan tsaye tana saka tana kwoncewa,
Tana ta nazari ne a kan rayuwarta ita kanta, kafin ta daga kafarta da kyar ta shiga takawa ta nufi dakin da a ranar ta ga ya fito da Nadia daga ciki

A hankali ta idasa saka kafafuwanta tana bin dakin da kallo, ba sanyi domin Ac a kashe, sai dai da kamshin sansanyan turatan wuta

A haniali ta taka ta nufi bayi du kuwa da irin yanda take jin jikinta ba karfi kwata kwata

Ruwa ta tara masu zafi ta rintse idannuwanta a hankali ta fara saka kafafuwanta sannan ta rintse ido ta zauna wanda hakan sai da tmya sakata kama abin nan ta rike da karfin gaske

Idannuwanta rintse suke kakam, abubuwan rayuwa take ta tunawa, yau gata a gidan da ba saki sai ka aikata kisa ko zina, biyu daga cikin abubuwan da rana bata fitowa ta fada bata nemi da Allah ya tsareta daga mumunar kadarar da zata kaita aikatasu ba
Yau gata a matsayin matar aure, matar farin mutun,
Sai dai abinda ya ki barin kwakwaluwarta shine irin yanda yake son ya jata da dan wasa duda ba wai wani sakewa ya yi ba aman yannayin da yake nuna na kamar zai tsokaneta na bata matukar mamaki

Kafarta ta riga dan wanawa a cikin ruwan tana kara hauda shi jikinta a hankali ya ringa salabcewa har zafinsa ya ragu sosai

Wannan karron sai ta hada na sabulu mai kunfa sosai mai sansanyan kanshin da ya sakata lumshe idannuwanta,

Ta jima a cikin ruwan nan har sai da ta ji kiraye kirayen sallah sannan ta dauro alwallah ta fito daga bayin da tawul din da ta gani

Tsaye ta yi a dakin daga ita sai tawul, tunaninta kayan da zata saka

A hankali ta fara leko kanta dan so take ta je wajen wayar cen dake ajiye ta yi kira bangarwn AMMI a kawo mata kayanta, sai dai tana lekowar sai ta hangi akwatinta wace take malakinta

Da dan sauri ta fito ta kama tana janta har ta shige dakin sannan ta datse tana sauke ajiyar zuciya

Bata buda akwatin ba sai da ta je wajen turarukan dake ajiye

Ido ta buda sosai gannin turaran nan, sai kuma ta turo baki tana dan gunguni ta dauki guda ta buda ta shiga yiwa jikinta barinsa sosai har kai tana ta kara juyawa da daria a fili ta ce" Na rama cicije min nan da ka yi malan ehe"

Sai da ta gama barnar da gangan dinta sannan ta koma wajen akwatin ta shiga bubudawa
Wata doguwar riga mai hade da hijab dinta har kasa ta ciro wace ta tabata an saka mata ita ne dan sallar

Pant da bras ta ciro sababi ta ajiye
Sai da ta fesa masu tyraran nan son ranta sannan ta saka ta zira rigar ta shiga neman abin sallah
Sai dai sama ko kasa babu, tana nan tana ta zagaye kamar da wasa ta tsinkayonkiran salar isha'i, hakan ya sakata zaro idannuwanta da sauri ta fito ko kashe fitilar da ta kunna bata yi ba tana son yin saurin sosai aman har yanzu ba wai ta saku yanda ya dace bane, ta dai rage jin azabar da take ji dazun aman kuma har yanzun wajen na sukanta

Ba tare da tunanin komai ba ta tura dakin nasa da salama kasa kasa ta shiga

Tsayuwa ta yi tana kallon dakin, ba kowa ciki aman da kanshin turarrn wuta da ya garwaye da turaran daki da kuma na jikinsa da ya fesa sai abin ya bada kamshin ya hade ya cika ko'ina na fakin
Ga sansanyan sanyi dake dakin na AC din da bai kashe ba

Dan tabe bakinta ta yi ta nufi kebantacen wajen da ake sallah a dakin

Wajen a kawace yake, ga alkur'anai mai girma a saman wani dan sif fari kal a jefe da litatafan musulunci da carbunna dai masha Allah

Sallah ta kabarta a
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment