Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kasheka da hannuna na huta

Da sauri ya yi wata irin dira ya tari gaban mai martaba kafin yake saka hannunsa ya tare wukar nan da hannu daya ya janyeta daga hannunsa ya riketa taf a hannun nasa

Ihun kukan da ta saka tana dora hannayenta duka biyu a saman kanta ne ya ankarar da fitowarta hakama mahaifiyarsa gaba daya jikinta ya dauki wani irin bari itama ta dora hannayenta saman kanta tana jin abinda ke shirin riskarta duka a zuwa bakaken halitar nan! A yau ta ga balakin da ko mutuwar ubanta bai girgiza mata kwakwaluwa irinsa ba
Tashin hankali ya risketa na mamaki kafin ta gama fahimtar wani ko baci ya ki daukanta ga wani ya sameta yau itace tsaye a gaban tarin abin kunyar nan
Sai kawai ta dafe kirjinta ta silale kasa

Muryarsa a dake ya furta" idan har magana ta daukaka ta fita tsakar gida ba abinda zan iya yi maku baki daya! Ku sanni sirrin masu mulki, da manyan malamai ya fi tarwatsa al'umah, ya fi lalata tarbiya! Ku sani idan har waje ta dauka haka ya faru da yariman garin agadez to kuwa matasan garin agadez zasu dauka su mayar da hakan abin yi! Ana iya tankwasa rigima idan bata yi yawa ba!

Yana gama fada karasawa ya yi ya sungumeta ya fito da ita

Dakin Zahrau ya nufa da ita kafin ya kuma fitowa ya sungumi NAJEEBA itama ya nufi dakin da ita sannan ya yiwa sauran alamun su biyo shi

Saman bed du ya jera su kafin ya yi tsaye ya kura masu ido
Ta ina zai fara? Me zai ce? Tabas sun shiga rudani mai girman gaske, shi kansa ji yake kamar zuciyarsa zata samu matsala a irin lamari

An dauki kamar mintunna ashirin sai ga bugawar kofar, du a zaune suke sunna ta kuka su biyun, Ummu ta dawo hayacinta aman bata iya komai waje daya kawai take kallo sai hawayen dake bin gefen kumatunta
Shi kuwa yana tsaye ya kura ma waje daya ido

Karasawa ya yi ya bude kofar

Likita ce ta shigo Sarki kuwa na tsaye daga baki baki bai shiga ba domin ya san ko a yanzu basu saka kaya ba, irin yanda yake zufa sai abin ya baka tausayi ya koma ya jingina da kofar yana kallon yanda iyalansa suka rikice

NAJEEBA dake sume ta fara baiwa taimakon gagawa
Ai kuwa ta farka a rikice tana ta waige waige, sai ta kwala ihu mai karfin gaske ta fashe da matsanancin kukan da ya saka yan uwanta suma fashewa da wani irin kuka mai cin zuciya da zafin gaske sunna ririke junna

Karasowa ya yi ya saka hannunsa ya bambare hannun Zahrau daga jikin Najeeba kafin ya kuma saka hannunsa ya k'ara cicib'arta.

Bai zame ko ina da ita ba sai cikin bayi direct ya idasa wajen bath da ita.

Zaunar da ita yayi sai ihun take tana kuka kamar ranta zai fita ga gazar gazar din gashin idannuwan nan nata sai kara far suke.

Bata tsamaci jin ruwa ba sai saukarsa ta ji a kanta hakan ya saka gashin kanta gaba dayansa ya yi lingib a bayanta da wani karfi ta so zabura ta tashi sai dai ya saka hannunsa ya maida ita cikin ruwa ya zaunar da ita sannan ya riketa tam a ciki.

Tun tana gunjin kukan har ya zama ta ringa rage sautinsa tana yi sannu sannu har ya dawo na zuci ne take yi sai hucin da take furzarwa.

A hankali ta langab'e a saman damtsen hannunsa shima ruwan ya jik'a masa jalabiyar jikinsa
cikin wata shak'ak'iyar murya dake cen ciki ta furta" Ya halakamu, ya wulak'antamu, ya goga mana penti, me mukai masa? Ya ketawa yar uwata hadi."

Gani yake ta d'aukaka firgicinta, gani yake ta zurfafa firgicinta bayan ba haka ya dace ta nuna ba duba da ita din aikinta kennan, harkar maza ya zame mata abinda ta fi k'warewa a kai, akan me zata ringa irin wannan abu? Sai yake tunanin tana pretending ne, sai yake gannin kamar so take ta raina masa hankali
Jin rawaninsa na son jik'ewa ya saka ya ringa janye jikinsa a nata
Idannuwansa ya sauke a kanta da niyyar yi mata magana sai dai da kansa ya kawar da kansa da wani irin sauri yana mai rintse idannuwansa domin ruwan nan da ya jik'a mata jiki da shi baki daya ya lafe mata da rigar nan mai santsi a jikinta a yanzu ne hallitar k'irjinta ta wani irin bayanuwar da ta saka shi ji gaba d'aya jikinsa ya d'auki rawa.

*(mai damagaram yana ruwa, kusa da kada inji breaker>Ø#Ý)*

Mik'ewa yayi da sauri ya juya ya fita a bayin.

Yana fitowa ya tarar da su sun saka suturun da suka rufe masu suturarsu, sannan sunna zazaune gefen kanta likitar kuwa ta bata maganin da zata sha dan rage rad'ad'in dake damunta na bak'on lamarin daya ziyarceta bayanshi bata samu wani mugun raunin da zai saka a kaita asibiti ko a mata d'inki ba, tana shiga ruwan zafi komai zai dawo normal sai dai abinda aka yaye din da ba za'a iya maido shi ba.

Tawul ya d'auko ya mik'awa Ummu ya nuna mata bayi hakan ya ganar da ita abinda yake nufi.

Wasu kayan ta d'aukar mata ta nufi bayin da su.

Kamata tayi ta fitar da ita daga cikin ruwan dan har lokacin tana ta zubar da hawaye wani irin ciwo take ji a zuciyarta domin a rayuwarta idan akoy abinda ke tayar mata da hankali, ya sakata a firgici to fa irin abinnan ne.

Kayan ta saka jikinta a mace suka fito tare.

K'arasawa tayi ita ma ta zauna ta d'ora kanta gefen wuyan Ummu
Muryarta a sanyaye ta ce" Ummu, kiyi magana mana, dan Allah ki ce wani abu mana."

Suma hawayen suka ringa sharewa shi kuwa yana kallonsu.

Sun d'auki kamar minti goma a haka kafin a hankali ta bud'a bakinta, hawaye ne wasu ke korar wasu cikin disashiyar muryarta ta furta" Dama me kuke jira da rayuwata? Kun manta wacece mahaifiyata? Yanzu haka idan kuka je tudun jamus layi na biyu babbar k'ofa mai ruwan blue gidanta ne, zaune take tana amsar kud'in wannan."

"Ki yi min shiru!" Ya bud'a bakinsa tun d'azun ya fad'a da wata murya ta tsawa wace ta saka du suka rintse idannuwansu suka sada kawunansu

Muryarsa ya kuma bud'awa yana cijewa yace" ku tashi baki d'ayanku mu fita!"

Da sauri Najeeba ta d'ago tana kallonsa, sai dai ba damar yin magana domin har ya juya ya fara fita.

Zahrau kam bata da katab'us, baki d'aya duniyar ce ta yi mata zafi ta rasa wani tunani zata yi da irin wannan lamari, aman tsawatarwar daya yiwa ummu ta sakata jin dama dama domin idan har haka zata ringa fad'i idan bakinta ya bud'e tana iya idasa halaka masu tunani su yi ta kuka.

Kamata suka yi ta mik'e da k'yar tana rintse idannuwanta kafin ta sauko.

Kamata suka yi a hankali tana tafiya suka fito domin basu san inda zai kaisu ba, su kuwa basu isa su k'i fitowar ba.

Irin yanda suka ga duk mutane ne a zazaune kama daga Sarkin Agadez, na damagaram, Gimbiyoyin, yarima da matarsa sai du suka ji hankalinsu ya k'ara tashi.

A hankali suka k'arasa da niyyar zaunar da ita a kasa, sarkin garin Agadez dake kallonsu ne kamar zai fashe da kuka shi kam ko rawanin babu a kansa yau an yi abinda ya cujewa buzu nad'i ya nuna masu doguwar kujerar dake ajiye."

Nufar wajen suka yi suka zaunar da ita kafin su zauna kusa da ita sosai a jikinta.

Najeeba irin kallon da take bin yarima da mahaifiyarsa da shi irin kallon nan ne wanda zaka ji kamar ka kashe mutun.

Yayi d'agowar kansa ya fi a k'irga sai zai bud'i baki sai ya kasa hakan ya saka Gimbiya saurin zamowa kasa ta had'e hannayenta tana kallonsa muryarta na rawa ta furta" dan girman Allah a rufa mana asiri, kar ku manta yarima shine mai jiran gado, sirrinsa ya fita tamkar sirrin baki d'aya gidan nan ne zai fita, Allah ya huci zuciyarka a rufawa yarima asiri a gafarta masa."

Tayi gaggawar juyar da kanta wajen SHAHEED ta d'an k'ara rarafawa hannayenta a had'e ta ci gaba da fadin" Ku rufa mana asiri, wannan sirri namu ne baki d'aya, dan girman Allah ku rufa mana asiri."

Du wani motsin kowa yana hakimce ne yana bi da kallo, bai furta ko A ba.

Kansa dake kasa ya dago, irin kukan da yake sai ya baiwa mutun tausayi.

Da sauro ya rarrafa ya nufi wajenta hakan ya sa sarki sakar masa tsawar da ta saka bai idasa idasawa har inda take ba aman ya ja daga d'an nesa.

Hannayensa ya had'e ya kara duk'awa sosai yana ta kuka kamar zai mutu yace" Dan girman Allah ki yafe min wannan lamari da na aikata maki, na rantse maki da Allah ni ba mazinaci bane
na je d'akin iyalina ne ta fito ta bar min d'akin sai na biyo bayanta a tunanina inda kike tsaye itace a tsaye domin idannuwana sun rufe, satina biyu kennan tana guje min a shinfid'ata, zaki ga na rufe maki ido da bakinki ba dan komai ba sai dan sannin tana iya k'wala min ihu ta tara min jama'a ni kuwa na yi alk'awarin a daren sai ta bani hakk'ina, ban san cewa ba da ita nake mu'amala ba sai da na kai ga shiga wajen da ba nawa ba, wallahi wallahi ni ba mazinaci bane, sannan ba mai afkawa mutane bane, na kasance ina koyi da halayen nagartatun mutane dan na kasance nagartace,
ban tab'a aikata zina ba ko a lokacin da bani da aure, dan girman Allah ki yafe min wannan b'arna da na aikatawa rayuwarki sannan na aikatawa rayuwata, ki maka ni kotu a yanke min hukunci daidai da laifina ko ki kaini kotun musulunci a yanke min hukuncin jifa domin ba zan iya rintsa ido da hak'inki irin haka a kaina ba."

Mahaifiyarsa ce ta fashe da kuka mai tsanani.

Da sauri ya juya ya k'arasa kusa da SHAHEED ya duk'a ya kama k'afafuwansa yana gunsheken kuka ya shiga fadin" Dan Allah yaya ka saka baki ta yafe min, ka saka baki ta gafarta min kar abin nan ya tab'a d'iyan d'iyana, ka ga wannan dake zaune zata iya maimaita abinda ya faru tsakanina da ita kafin ta baro d'akina, hakan yasa na biyota da sauri ban san inda ta lab'e min ba na fito da gudu ina nemanta sannan itama wando ne a jikinta da rigar baci na rufe bakinta da hanuna da idanuwanta dan kar ta min ihu ko ta fad'a min abinda zai fitar min da son zuwa gareta a raina hakan ya sa na afka mata, ba zan iya fahimtar ba da matata nake ciki ba, hankalina ya gama tafia burina na samu nutsuwa."

Gannin ya k'ura masa firgitatun idanuwan nan nasa masu matuk'ar abin tsoro ya saka shi sakinsa ya juya wajen mahaifinsa ya karasa ya kama k'afarsa.

Kafin ya fara magana ya hamb'are shi da k'afar tasa hakan yasa ya fad'i gefe aman bai gaza ba ya kuma tashi ya kara ruk'unk'ume k'afar tasa yana wani irin kuka murya a cakule ya furta"BABA."

Sarki ya saka k'afarsa yana kiciniyar kuma hamb'are shi aman ya gaza dan baki d'aya jikinsa yayi sanyi lamarin ya shige shi a lokacin da bai shiryawa hakan ba.

Muryarsa ya bud'a a birkice ya furta" Inna lillahi wa'ina ilaihi raj'une."

Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une! Sai kawai muryarsa ta shiga rawa sai kuka ya k'wace masa, hakan ya saka SHAHEED saurin rintse idanuwansa ya sadda kansa.

Muryarsa na rawa ya shiga furta" Lalle kana wasa da adininka, kana wasa da ibadunka, idan kuwa ba haka ba kaima k'addararka mai tsauri ce domin kamar yanda ka fad'a saina hukuntaka! Wani irin rayuwar aure kake da macen dake gudunka har cutuwa ta shiga tsakaninku haka mai tsanani mugun raini ya shiga tsakaninku har ya kaika ga neman afka mata da tsiya ya kasance ka fad'a kan wace ba ita ba?"

Dubansa ya kai kan matar tasa dake kukan ita ma cike da dana sani ya furta" Anyi haka? Mijinki ya zo maki kin fito da suturar da tayi kamanceceniya da ta baiwar Allahn nan? Idan waje ya ga kin nufa ina kika lab'e masa ya fito waje nemanki? Kina ganni ya aikata haka baki katse masa hanzari ba ko baki gani ba?"

Fashewa tayi da kuka tana k'ara sada kanta muryarta na rawa ta ce" Allah ya huci zuciyarka a yi mana afuwa, a gafarta mana, a ji k'anmu, tabbas hakan ya faru daidai da abinda ya fad'a, kuma a lokacin da na zo fita lab'ewa na yi dan ina jin haushinsa ya hana min wasu kud'ad'e, dan ina so yana fita na koma na d'auka domin mun jima muna gaba tsakaninmu sakamakon mahaifiyarsa ta nunan cewa kar na yarda ya yi yan mata ko ya yi tarayya da 'ya'yan turawa a waje shi kuwa yayi budurwa shine ni kuwa nake nuna masa fushina ta hanyar hana masa abinda yake buk'atar."

Sai kuma ta k'ara sadda kanta tana kukan da na sani da tarin nadama.

Kansa yake girgizawa ya ma rasa me zai ce? A hankali ya furta" Ga irinta nan, ga irinta nan, kin yiwa sarakuwarki muguwar hud'ubar ita ma kar a mata kishiya ga inda abin ya kaiki, lalle ke ba uwa ta gari bace, ke ba mata ta gari bace sannan ke ba shugaba ta gari bace, tabbas kema hukunci zai hau kanki domin ba zan iya ci gaba da zama da ke a matsayin matata ta aure ba."

Baki d'ayansu a zabure suke kallonsa sai a lokacin SHAHEED yayi gyaran murya yana kallonsa ya furta" Allah ya huci zuciyarka, Allah ya ja da zamaninka tuba muke."

Baki d'aya suka ringa maimaitawa banda su NAJEEBA.

Kansa ya k'ara sadawa ya shiga fadin" Tabbas wannan lamari idan ma da ganganci a ciki to fa zanen k'addara ce, abin ne ya zo a harhad'e, shi ga abinda ya fitar da shi daga d'akinsa ita ma ga irin lokacin da ta kai tare da yan uwanta suna shashanci maimakun su kasance a cikin bautar ubangiji!"

Sasautawa yayi ya kuma d'auka da cewa" Tir da matar dake gudun shinfid'ar mijinta, tabas kina cikin tsinuwar ubangiji sannan kina da naki kason a cikin wannan lamari."

Dubansa ya maida wajen yarima ya kausasa muryarsa ya furta" Tir da namijin da ba zai iya rige arzizimun wandonsa a lokacind a fitinarsa ke harbinsa ba!"

Sai kuma ya maida dubansa wajen Gimbiya ya sasauta muryarsa ya furta" Kaico ga uwar da zata ringa shinfid'a hanyoyin b'araka a cikin ahalinta, domin kuwa wannan uwa ta d'auko hanyar tarwatsa iyalanta da al'uma mai yawa, dan kuwa mu dukanmu muna samun tarbiya ne daga iyayenmu, daga bakin lokacin da aka samu gurb'attaciyar tarbiya lamarin b'atanci zai yawaita a cikin al'umah."

Sassauta muryarsa yayi yana kallon sarki ya furta" Rud'ani, tashin hankali ya hana min kallonsu a cikin idannuwa, sai dai ya zama dole zamu hau wata shari'ar a yau a wajen nan dan danne wata b'arakar, amar yanda na fad'a cewar a duniya baki d'aya babu mumunan sirrin da fitarsa ke haifar da mugayen sakamako irin sirin masu mulki da kuma manyan malamai da masu iko,
akan d'auki hakan da fuska biyu, masu d'aukarsa da mummunar fuska ta hanyar kwaikwaya sukan yi yawa a cikin duniya baki d'aya, k'alilan ne ke yi masa kyakyawan fahimta har su gane b'atancinsa."

Kuma kausasa muryarsa yayi ya furta" Ba'a kyauta ba, an tafka abinda Allah ya haramta, sannan an shiga hakin baiwar Allahn da bata ji ba bata gani ba." Shiru ya kuma yi kafin ya dubi wajensu.

Muryarsa ya sanyaya sosai kafin ya furta" UMMUKULSUM, shin zaki iya jurewa, ki jajirce, ki d'auki hak'uri ki yafewa bawan Allahn nan duba da irin abubuwan da suka gabata da shaidar wace abin ya faru a sanadiyarta ? Zaki iya yafe masa har cikin zuciyarki? Ki tuna Allah na yafewa bayinsa masu yafiya ya Ummu."

Kanta dake kife a jikin kafad'ar Najeeba tun daya kama k'afarta yana gunsheken kukan nan ta ji wani irin tausayinsa ya tsirga mata haka kawai sannan wani irin tsigar jikinta ta ringa tashi, bata k'arasa jin tausayinsa ba sai da ta ji kalaman mahaifinsa da kukan mahaifinsa da shi kansa.

Gimbiya ce ta k'ara duk'awa tana kallonta muryarta na rawa ta furta" Ki rufa masa asiri, ki rufawa kanki Ummukulsum, kar ki manta kema mace ce, fitar sirin nan tamkar fitar da sirrinki ne, ki rufe shi dan girman Allah."

Cire dubanta ta yi daga kanta, muryarta na rawa ta furta" Na yafe masa."

Sai kuma ta fashe da kukan da ya saka Najeeba wace jikinta ya d'ume da zafi kanta na sarawa ita ma fashewa da kukan tana k'ara rungumeta, Zahrau kuwa ta zama wata mutun mutumi sai juya kai take baki d'aya ta rasa me take ji.

Hamdallah yayi kafin ya maida dubansa wajen sarki a sanyaye sarki ya ringa sakin ajiyar zuciya, muryarsa a sanyaye ya furta" ina neman alfarma, ina neman alfarmar a bar min ita a nan gidan, ta yi istibra'i a d'aura masu aure, domin na rantse shi zai gyara abinda ya lalata."

Daga Gimbiya har matarsa a tsorace suka kalli sarkin da ya watsar da su yana cike da jin haushinsu, sam tamkar basa wajen tun da ya masu tambaya yayi watsi dasu.

Da baya ta kai zaune tana mai d'ora hannayenta saman kanta a b'oye, kishiyarta kuwa bayan tarin tausayin yarima domin yaron yana da mutunci sosai, sai kuma tarin al'ajabin abinda ke shirin faruwa, auren yarima da matarsa aure aka yi na zobe, yar k'awar gimbiya ta k'ud da k'ud wace ak'idarsu d'aya cewar ba za'a yi masu kishiya bace ya aura, hakan yasa Gimbiyar ke taya ta yak'in maganar kishiya sai gashi a yau abu biyu ya faru da su baki d'aya, wato wanzuwar *KISHIYA* a tsarin da basu ajiyeta ba.

Kansa ya kuma sadawa yarima ya k'ara duk'awa shima yana rok'an hakan.

Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya furta" zamu juya gida a jirgin safe in sha Allahu, zan yi kira na sanar da abinda ake ciki."

A haka dole aka tashi, sarki na zaune saida kowa ya tashi sannan ya bi bayan Zahrau dake son shiga d'akin jikinta a mace.

Hannunta ya kamo ya maidota baya
A hankali ya sakata cikin jikinsa ya rungumeta yana buga bayanta kad'an kad'an kafin ya jata suka koma saman kujerar
Sai a lokacin ta samu kuka ya kubce mata cike da tsoro take nuna masa ba zata iya zama ba yan uwanta a wannan gidan da ya gama tsoratata ba.

Sosai yayi anfani da hikima ya ringa rarashinta har ta dawo nutsuwarta ta ringa sauke ajiyar zuciya da kansa ya mata alk'awarin zai nemi alfarmar malan ya bashi y'aya biyu k'annenta su tare da ita su tayata zama kafin a kawo mata Ummu.

Da wannan ya samu ta kwontar da hankalinta kafin ya rakata har d'akin suka ci gaba da gabatar da sallah baki d'ayansu suna godewa Allah da irin wannan ranar.

....................................

Zabura ya yi tsaye sai kuma ya yanke jiki ya fad'i zaune saman kafet d'in hannayensa aje saman kansa muryarsa na rawa ya furta" innalilahi wa'inna ilaihi raj.une, hasbunnalahu wani'imal wakim
aya ta tabbata a kaina ni MUTALAB gashi, abinda na aikata ya kamo ni da wuri haka a kan yarinyata."

Sai ya fashe da kuka yana kallon yanda D'AYABU ya tsurawa sarki ido kamar wanda ya suma a zaune.

Da sauri Anmy dake kukan itama ta kaleshi a firgice jin zai tona asirin da suke lullub'ewa kansu da k'afarsu, zai tonawa kansa asiri a cikin irin rud'anin nan da suke ciki zai k'ara masu wani.

Duban da Ummu ke masa ne ya saka shi k'ara sada kansa yana hawaye
Ummulkhair ta kalli Najeeba wace ita ma ita take kallo kafin Najeeba ta bud'a bakinta a hankalì tana kallon Ummulkhair tana dan yatsine fuskarta tace" eyah, eyah, yau kin yarda da ayar tambayar da na d'ora a kan maganar da Abih kan fad'a wani sa'in?"

Maida dubanta tayi wajen Abih a sanyaye ta furta" *ABIH, WACE AYA CE TA TABBATA A KANKA?*

komawa sarki yayi ya jinginar da bayansa jikin kujera yana lumshe idannuwansa, ta faru kuma ta k'are, rikicin cikin gidansu zai k'ara kunnuwa a yanzu, ya tabbata wani tashin hankalin ne zai k'ara kunno kansa hakan ya saka ya idasa had'e fuskarsa da dukan wani abu wai shi annuri ya lumshe idanuwansa a lokacin da Anmy a firgice ta kallesu tace "...






Happy juma'at>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



27


A firgice, a rikice, a tsawace Anmy ta ce" yaya muna cikin wannan tashin hankalin zaki yi mana wata tambaya kina mai kokarin tirke mun tamkar kece uwarmu mu kuwa y'ayanki?

Baki daya yan matan sai abin ya basu mamaki, yannayin Anmy din ya saka jikinsu ya yi sanyi harma du suka zuba mata ido da wani irin duba na mamaki

Anmy ta kawar da kanta tana jan hancinta tana kara rintse idannuwanta da sukai mata luhu luhu ranta hade ta ce" ku tashi ku je dakin ku

Jiki sanyaye du suka mimike, Najeeba ta kara waigowa ta kalli mahaifinta ta ga kansa a kasa sannan hannayensa sai rawa suke, ta kai dubanta wajen yayansu ta ga shima kan nasa a sade shi kuwa kuka ne yake a hankali ta saci kallon mai martaba ta ga ya yi wata kwonciya a jikin kujerar ya daga kansa sama idannuwansa lumshe rawanin dake kansa ya kara fadi sakamakon yannayin kwonciyar nasa, shigar alkyaba ne a jikinsa mai ruwan duhu wace ke da igiya wajen wuyanta, fari kal din hannunsa daya ne a waje yana rike da sandar girmansa dake ajiye a kusa da kafarsa, sai dayan dake dafe da gefen zuciyarsa

Da sauri ta cire dubanta a kansa ta juya da wani irin sauri ta bi bayan yan uwanta

Sunna shiga da sauri Ummulkhair ta zube a kasa tana mai dora hannunta saman kanta tana dubansu a rikice ta ce" shin kun fahimci abinda na fahimta? Kun gane cewar akoy wani gagarumin sirin dake damun mahaifinmu wanda da alama mahaifinmu ya shafa wanda nake kyautata zaton idan har ya fito fili mun kade?

Najeeba ta jefar da iPhone dinta saman kujerar dake ajiye ta cire alkyabar jikinta ta jefar ta zauna a kusa da Ummukulsum ta shiga cakuda gashin kanta

Dagowa ta yi da wani irin yannayi ta ce" aya ta kasance a kansa da wuri? Bai fadi haka ba sai da ya ji cewar wannan tsautsayi ya afku da Ummu? Me ke faruwa da mahaifinmu? Wace aya ce wannan ta kasance a kan ubanmu?

Ummukulsum dake share hawaye itama ta budi bakinta a hankali ta ce" sai jake jin tsoron abinda zuciyata ke fada min, sai nake jin tsoron abinda nake tunani

Ummulkhair ta ce" me kike tunani ummu?

Ummu itama ta dora hannunta a kanta ta ce" sai zuciyata ke ce min bayan mahaifiyata mai amsar kudin zina ce mahaifinama ya taba fadawa wata

Da sauri Najeeba ta matso kusanta tana daga hannunta da ihu ihu ta ce" ke ke, yi min shiru, walahi zan tsinka maki mari idan kika fadi cewar Abih ya taba yiwa wata fyade

Ummulkhair ta shiga yarfe hannayenta tana fashewa da kuka ta ce" Najeeba ai ba haka ta fada ba, abinda kike tunani ne kika fada kuma nima abinda nake tunanin kennan innalilahi wa'ina ilaihi raj'une me ke faruwa da mu?

Itama Najeebar baki daya kafafuwanta ne suka gaza daukanta

Tana kokarin zubewa kasa Dayabu ya shigo
Da wani irin sauri ya karaso ya tareta a jikinsa suka kai kasan tare
Da rarafe sauran suka karasa wajensa suka rungume shi sunna kuka baki dayansu

Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une, yake maimaitawa hankalinsa a tashe ya shiga fadin" tabas kadara, mumunar kadara ta faru da kanwata, sai nake jin ba wanda ya kaini jin ciwo duda irin yanda aka fada min lamarin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment