Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

a kan sunnan da wani tunani daban
Gannin zai cutu ta hanyar tinane tinanen nan sai kawai ya nemi kusanta kansa da Allah ta hanyar dora nafila, domin kuwa ba zai yarda yana ji yana gani kamar wani yaro karami ya tinga tino maganar yarinyar nan da bata jin magana mai fadan tsiya gabansa na faduwa haka kawai!


Morning people=ØÞ, ga breakfast=Ø Þ>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



52


Tun karfe bakwai su Najeeba suka gama kitson nan, kitson da akai masa wani irin kannanun tsinta har sai da Zahrau ta ce yanzu Najeeba haka kikai min kannanun kitson nan wa zai tsefe min?
Sai kawai Najeebar ta yi murmushi abinta ta janyo sabuwar wayarta IPhone da yaya DAYABU ya kawo mata a jiya ta kunna
Whatsup din da ta riga ta yi installed ta shiga, tarin numbobin mutanenta da take yiwa gyara wa'inda Habu dan daudu ya tuturo mata ta shiga saving kafin ta yi message daya mai dauke da gayatarsu gidan Mai Damagaram cewar saloon dinta ya koma nan, za'a ci gaba da aiki kamar yanda ake budewa a da, da sasafe sannan a cika dare kafin a rufe, daga kasa ta saka sunnanta da kowa zai iya ganewa kafin ta fita a whatsup din

Instagram ta shiga ta yi posting din hotunnan talar kalolin mak'up din da take yi masu ita da yan uwanta sannan ta dora da albishir din dawowarta
Hakama ta shiga Facebook da tsohon cmpte dinta shima ta yi posting din bayani wa mutanen da suke hira a ciki
A kwoncen nan hankali kwonce ta ringa aikinta ta hanyar posting din tarin hotunanta masu matukar kyau da tsari,
A haka take samun tarin tambayoyin mutane masu son sannin wai da gaske tana gidan sarki? Wai da gaske Mai damagaram ne ya aureta?,
Sai tarin masu turo mata invitation din son ta zamo kawarsu a Facebook
Cikin sabon posting dinta harda numberta na whatsup wanda ta jadada ga mai son kwaliya da gyaran jiki yana iya tuntubarta a number ta tura
A haka ne wasu daga cikin tsofafin samarinta suka ringa bata nishadi ta hanyar turo mata habaici, zata karanta ne ta yi daria kafin ta yi block din mutun ta je ta maka numbersa a black liste
Number Aida ta dannawa kira

Kamar wace ke jira ta daga tana salama

NAJEEBA ta ce" Aida, goben in sha Allah ku fito da wuri fa, yanzu su aunty Zahra sun je su ga yanda aka yi wajen, ni ban je ba in sja Allahu sai goben, ina so ku fito da wuri ku yi dukan gyare gyaren da ya dace kafin na fito domin na tabata wajen nan namu sai ya cika ko dan masu son gannin kwakwaf"

Da sauri Aida ta amsa cike da ladabi kafin su kashe, itama ta shiga kiran ma'aikatansu tana shaida masu sakon mai gidansu inda suka cika da farin cikin tashin aikinsu kai da fata ga mai gidansu a gefe gasu a fada, sukan hasaso yanda abin zai kasance ne, sun tabata ci gaba ne

Isashen Baci ta samu a lokacin da yan uwanta suka yada zango a saloon dinta
Sosai wajen ya mugun tsaruwa ya birge su, haka suke yiwa wajen vidio cike da mamakin irin tsarin ginnin da akai a dan kankannin lokaci aka shake shi da kaya cikin tsari

Kaya dai gasunnan, an zuba sai fatan samun ribarsu

Da farin ciki suka yada zango dan yiwa Ummukulsum gyara tsakaninsu har sai da kusan yama sannan suka firfito sukaiwa masu tsaron kofar salama domin kuwa wannan karron bama dogarai AMMI ta saka a kifar shagon NAJEEBA ba, haka kawai tsoron dora dogaran take dan haka ta tura takarda wajen commissioner yan sanda aka turo mata mutun biyu ginanu ta ware masu mota daya da dukan abibda zasu bukata hakan ya sa su kansu farin cikin wannan aiki domin kuwa ci gaba ne suka samu mai girma

Vidion kawai take ta kallo tana karawa, sai wani zumudin zuwa ta gani ya shiga zuciyarta, wata irin kaunar iyayenta ta kara shiga cikin zuciyarta hakan ya sa cike da farin ciki ta duka har kasa ta shiga koro masu adu'o'in gamawa da duniya lafia da dukiya mai albarka

Da farin ciki Ammi ta mikar da ita ta ce" Najeeba, bafa mu mukai abin nan ba, wannan din da kike ganni daga mijinki ne domin da na kai masa maganar ne ya samu mai zane ya zana yannayin ginnin ya zuba ma'aikata sannan ya zuba kudin kayan da za'a zuba a cikin"

Sai ta ji abin wani bako a wajenta, aman kuma farin cikin da take ciki ya hanna mata jin abin sosai din nan sai kawai suka ci gaba da farin cikinsu, ita kanta UMMU ta sha mamakin wajen, lalle an dankara dukiya ba laifi sai adu'a da fatan a mora

Zama sukai sunna hirarsu domin yama ne

Hanyayoyin dake jere su uku ne aka shiga kokarin bude daya da kys hakan ya sa suka dan dakata dan gannin ko waye sai dai ba dukansu ba,

A hankali ta fara leko kanta kafin ta sanyo kafarta muryarta kasa kasa ta yi salama tana karema mutanen fallon kallo
Dukan Alamau sun nunna a tsorace take da shugiwa wajen hakan ya sa take ta rabe rabe har idannuwanta suka sauka kan NAJEEBA da ta dago dubanta daga kan wayarta tana amsawa mutane maganarsu ta sauke a kanta

Da sauri Nadia ta sada kanta haka kuma da dan sauri ta karasa wajen su UMMU ta duka har kasa harta da muryarta na dan rawa ta shiga gaishe su ta hanyar fadin" barka da safia mama"

Ummu ce ta saki murmushi ta mika hannunta ta kama na Nadia , da kulawa ta ce" ki karaso daga nan Gimbiya, barka da yamaci"

Baki daya ta kasa samyn nutsuwa ko sakewa, du tsoro ne bayane karara a fuskarta, yau tun da safe take shan gumurzu da kanta kan shin zata zo ne ko kar ta zo? Gashi dai ba yan rakiya , ita daya zata zo, a yanzun da maman Najeeba ta kama hannunta sai ta jara jin tsoro, itafa tsoronsu take gaskiya

Dosanuwa ta yi kanta kasa ta shiga gaisar da su daya bayan daya

Ga mamakinta sai suka ringa amsata da kulawa, har tambayarta UMMU ke yi yaya bakunta fatan komai lafia bata da wata matsala

Ajiyar zuciya ta sauke ta jin sanyi sanyi a ranta, dan kuwa sai da auntynta ta rakota har kofar ta turota kafin ta iya shigowa domin zuwanta uku har sai da ta sha stop diarhee tsabar rikicewar da ta yi dan kawai ta saka tsoro da tunanin idan ta yarda ta zo zasu hadu su yi mata jina

Baki dayansu sun amsata, hakan ya sa a hankali ta dago dubanta dan satar kallon NAJEEBA

Sai da gabanta ya kuma tsinkewa ya fadi, da sauri ta sada kanta kasa ta rike hannunta da dayan hannun nata tana fatan Allah ya fitar da ita lafia,
Gata dai zaune itace farar mace kaf a wajen nan aman baki daya da ta sauke dubanta kan Najeeba sai ta ji ta muzanta, munnin kanta ta ringa ganni a bayane, irin yanda NAJEEBA ta kara zama ne ya bata mamaki, a gaskiya ta kara zama wata irin babar yarinya, gashi dai ba kwaliya ko dis a fuskarta, sannan suturar jikinta doguwar sakakiyar riga ce irin ta shan iska, kanta kuwa a kunce yake ba kitso sai tasubala da ta soka a ciki da alama tana shirin gyara kan ne, tarin gashin nan nata sai ya yi uwa tukunya a saman kan nata hakan ya sa gaban goshin ya kuma yin luflufluf
Abinda ya kara kayar mata da gaba ido hudun da suka yi, irin kallon da Najeeba ke binta da shi ba zata iya fasara ko me ke cikin zuciyarta gane da ita ba, kamar mai yi mata kallon ta bata mamaki, ko macuciya, ko zata hadu da ita, hakan ya sa ta ringa jin fitsari na mintsinar mata mara

A hankali ta kara rage tsayinta bayan ta dan mike ta yi masu salama

Da mukawa Ammi ta yiwa su Ummu magana cewar su yi mata rakiya

Ai kuwa da ido NAJEEBA ta bi su har suka bacewa ganninta suka shige lungun da zai sadata da bangarenta

Bakinta ta tabe a hankali ta mike tana mai jan tasubalarta daga kanta tana kwonce daurin da ta yiwa gashinta ta nufi cikin dakinsu

Du da kallo suka bita, sannan a bayane AMMI ta saki murmushin da ita kadai ta san ko na meye, Zahrau kuwa ta mike ta bi bayanta dan tana son ta kama mata su gama hada abinda zata tafi da shi gidanta
.................................. ..........

Bayan salar isha, GIMBIYAR garin Agadez ce zaune da waya kage a kunnenta tana sauraron kalaman kamilin mijinta, a sanyaye yake maganar sai dai abinda ke neman kasheta shine irin kashedin da ya yi da irin alwashin da ya ci a kanta, bata gama farfadowa ba ya dora da fadin" ban san yaushe zaki yi hankali ba, abinda na sani shi ne ni ba tsohon banza bane, na zuba maki ido na zata zaki yi tunani? Sai na ga kin kara bani mamaki a karo na ba adadi a lokacin da kika tare a gidan sirikinki da sunnan kina jinya, shin ina iyayensa? Ina yan uwansa? Ko ba su shi kansa bai isa ya kula da matarsa ba? Ki sani na san me ke damunku ku duka, daga ke har Zinaria idan baku farka ba zan saka maku hukunci mai tsananin da zai firgita du wani mai kaunarku, idan a gobe baki biyo jirgin da zai fito daga garin Niamey ya yo damagaram daga nan ya yo Agadez ba komai na iya faruwa da mulkinki, idan nace maki komai ina nufin komai!"

Kitt ya kashe kiran da ya sakata zabura har hannayenta na rawa tana kallon screen din tanfatsetsiyar wayarta
Ta kasa yarda cewar shi ne, yau ita ce mai martaba ya yiwa magana a haka? Ita ce ya yiwa fada a haka? Sosai kanta ya dauki hayaki ta cika ta batse, ina ai dole ta je ta ganshi gashi ga ita ya maimaita magangannun nan, zata je kuwa ko dan ta gani da idannuwanta abinda ke shirin samunta ita kanta, me hakan ke nufi? Shin yarinyar nan bayan yarta har ita sun gama da ita ko meye?

Da sauri ta mike ta yi dakin Zinaria dake kwonce har ta fara baci bayan ko salar isha bata yi ba wai ta gaji dan kawai an mata wankin kafa bama ita ta yi da kanta ba gannin tana baci ya sakata fitowa ta shiga kiran number babar yarta, ina ba zai yiwu ba, walahi ba'a yi su ba!

....... . . .. . ...........................

Tarin gajiyar da ya dawo da ita a yau ta hanna masa tunanin komai, yana gama dukan abinda ya zame masa jiki, ya gama waya da lauyan da ya dora kan binciken abubuwan da suka tsaye masa a rai, domin shi dai ba lauya bane, irin halin tsantsamtun da ya shiga ya hanna masa fita neman bayanan da kansa, domin a yanzun fitarsa sai idan ta zamo dole ne, ya daina fitar daren da yake ya dakatar har komai ya warware masa

Yana gamawa bayan ya gama nafilarsa sai kawai ya nemi waje ya kwonta dan samun hutu,
Sosai shara'ar da ya yi a yau ta caza masa kwakwaluwa, ya hadu da mutane ne masu matukar taurin kai dan kuwa du yanda ya so a gama shara'ar cikin masalaha da junna sai da suka saka shi mikewa da kansa ya kawo kur'anin da sam baya son yawan saka shi a garinsa ya ajiye a gabansu kan su rantse domin mutun ne kwonce ba ta yada yake, sai bin mutane da ido, bayaj a da shi din shi ake so da gani sai gashi a yanzu komai sai an masa, ga mata ga y'aya, rayuwa dai tai masu zafi sai hamdallah....cikin fadawa Allahn da ake ne matarsa ta tashi tsakiyar dare dan dauro alwallah sai ta ga babu ruwa baya zuwa, niyarta ta zagaya baya dan samun ruwan a butar makiciyarta, sai dai a nan ne ta ringa jin magangannunsa kan lalurar mijinta
Sosai aka yi rigima domin Abih kansa ya ja ya tsaya kan sai sun fadi komai idan kuwa ba haka ba kur'ani ya ci su

Ajiyar zuciya ya shiga saukewa a hankali wanda ke nuni da ya samu baci kennan

(Asuba ta gari SULTAN)

a yau ne ya kama ranar da iyayenta sukai mata alkawarin zata koma bakin aikinta zata je ta fara gabatar da aikin da ta fi kwarewa a shi wato harkar saloon

Shiri ta yi na mamaki, domin ta sha wata rantsatsiyar shada ne doguwar riga sannan da kanta ta aminta ta dora alkyabar nan dan ta san ba za'a bata lafia ta yi tafiaarta haka ba

Daurin da ya fi fitar da sirrin kyanta ta kafa a saman kanta simple sai jelar gashinta dake dan yawo a gadon bayanta wanda ta saka masa biboudi sai nanadewa yake a gadon bayan nata masha Allah
Takalmi ta kafa mai dan tsini, sannan kafa ciki bayan ta saka safa suka yada zango a falo sunna jiran yaya DAYABU su karasa wajen sannan daga cen su yi salama da Zahrau wace ta sha wani irin rantsatsen mak'up itama sai kyali take daidai da kalar fatar jikinta

Yana zuwa cikin shigarsa ta Gizner ya gaisar da iyayensa sannan suka tashi dan karasawa bayan sun yi masu adu'a

Cike da nutsuwa suke tafia, hakan ya sa du hankali ya yi kansu
Du inda suka zo sai an duka an kawo masu gaisuwa, sannan kowa so yake ya bambance wacece amaryar sarkinsu? Aman a yau sun kasa bambancewa dan irin kamar da y'ayan Abih suke, gashi sun saka Alkyaba ne su dukansu, haka kuma tafiarsu cikin tsari

Yaya Dayabu ne ya hango tarin takalma a kofar wajen hakan ya saka shi dan zaro idannuwansa ya ce" ke NAJEEBA hala mutanen nan du sunna cikin wajen cen?"

Najeeba dake sakin murmushi gannin irin yanda aka kawata wajen ta ce" yaya, sunna ciki, to aman bana gannin abubuwan hawansu fa?"

Yaya DAYABU ya ce" ai a kofar shigowa aka umarcesu ajiyewa, akoy dogarai dake baiwa abin hawan mutane tsaro, kema yaya za'a yi kowama ya shigo gidan nan da mota sai kace wani karamin gida?"

Murmushi ta kuma yi, lokaci daya droon din SULTAN ya ringa yawo a wajen, du kawunansu suka daga suka bi shi da kallo, haka kawai ta ji a jikinta kamar ana kallonsu ne, sai dai gannin yan uwanta basu damu ba sai itama bata damun ba

Karshe dai yaya Dayabu kasa shiga ya yi domin tun daga waje zaka gane fa yau sun hadu, mata ne birjik a wajen baba da babarta

Ita kanta ta yi mamakin wasu fuskokin mutanen da ta gani a wajen nan, ba dan komai ba sai dan da yawansu irinnan san junnan nan ne aman gaisuwa kawai ke hadawa, da yawansu irin sunna yiwa mutun kallon sun fi karfinsan nan ne, ciki kuwa harda matar ambasador da ta rangada guda lokaci daya tana fadin" gata fa ta shigo, Allah ya yi mana maganinta, Allah mun gode maka, yanzun kam sai dai a je a karata da Zinaria, Zinaria kuwa ta ci dubu sai ceto, zamu ga wa zai fadi a wasan"

Da mamaki Zahrau ke kallonta gannin irin yanda wajen ya bada kala daban daban, a ranta ta furta 'To fah, kar dai a dora daga inda aka tsata'

NAJEEBA na murmushi tana kara bin kowa da kallo, masu tafe dan taya murna ta gane haka kuma masu son ganewa idannuwansu komai a bayane yake dan haka sai ta cire alkyabar dake kanta, baki daya ta idasa cirera a jikinta hakan ya sa Hadimarta da sauri ta amsa ta yi dakin da aka ware dan hutunta ta kilace ta fito tana risinawa da tambayarta inda zata fara zaunawa dan hutawa

Murmushi ta yi mata bata ce da ita komai ba, ta shiga bin bakinta daya bayan daya tana gaisawa da su tanai masu lalle marhabin

Bayan ta gama ta umarci su Aida kan su bubude kayan aiki a fara aiki, aman aikin yau ba za'a amshi kudin kowa ba, sai dai zuwa gaba

Ai kuwa wajen ya idasa rikicewa da murna da gudar mata

Sai a lokacin ta ga Habu dan daudu, sai da ta zaro ido dan mamakin yaushe ya shigo,
Idannuwansa ya yiwa far far ya tafa hannu ya ce" ci ubansu kawata, takawarki lafia mata a wajen mai damagaram, karya ne a tankawa uwar dakina na kyale ko a gaban dubu sai nai motsi sai dai a dinken baki, kin san wanda ya gama tsorata da maciji ko igiya ya gani firgita yake, kin jijiga matan gwamnoni, kin tarwatsa zuciyar dakakiyar macen da take gannin ita mace ce, kin zaburar da yan mata, kin watsa kannanun kwari kin mike kin mana raf da wuyan MAI DAMAGARAM uban gidan ZINARIA, tabas ke din sai sarauta, domin manyan kaya kike janye da su da mai tuka su sai OGA, sitiyarin kan motarki ba kowani hannu zai iya juya shi ba, dole ki firgita mana fara mai takama da hakan, da Allah muka dogara ba da uban wani ba, mun tabara mun sha yasin mun motsa da adu'ar iyaye dan alkur'ani makiyanmu fadawanmu"

Ihun aka kuma sakawa hakan ya bata ran wa'inda akaiwa habaicin, ciki kuwa harda matar doctor wace itaka ta zo tataki ne yau dan ta ga wannan NAJEEBAR sannan ta san Habu farin sani ta ce" kai Habu habaici kake mana ne?"

Habu ya kuma juya ido ya ce" kar ki ce min kin ji kamar da ke nake?"

Zahrau ta girgiza kai tana kallon yanda wajen yake, ita ta rantse da Allah har a cikin zuciyarta baki daya ta tsorata, aman cikin ikon Allah NAJEEBA a tsaye take hannayenta sake fuskarta bata nuna alamun mamaki ko tsoro saima bin kowa da take da kallo daya bayan daya, ko shewar nan da ake du masu yi tana bin su da kallo, ga uban jus jus da ake rarabawa inda su Ummu ne suka ja ragamar rabe raben da sauransu,

A sanyaye ZAHRAU ta ce" ni dai dan Allah a bar wannan abubuwan haka, wai shin kaima kitson ka zo ne?"

Sai da Habu ya kaleta sama da kasa ya ce" ke kuwa baki san inda suke ina nan ba? Ai a jikinsu nake ci, sannan da kike cewa a bar haka kin taba gannin gidan kitso ba runguntsumi?, dubansa ya maida wajen NAJEEBA dake kallonsa, ita kanta a kasan zuciyarta uban mamakin ta inda ya shigo a yaushe ya shigo take, idan bata manta ba tun da aka dora masu zama da dogarai aka hanna masa shiga shagonta, Habu yana yi mata aiki ne ta hanyar kawo mata mutane sosai da sosai, idan ya zo waje kuwa zai zauna a sha hira da shi ne ya yi tafiarsa, bayan wannan ba wata alaka tsakaninta da shi domin ko irin biki nasu na yan daudu bai taba fada mata dan ta fada masa gaskiya itafa wannan abin baya bata sha'awa nema kwata kwata shima tana masa fatan shiriya

Sai da ta sauke ajiyar zuciya ta ce" to in bama gagawa irin ta dan adam ba, MUTALAB fa goma sha shida ya kyankyashe mata, ciki kuma biyu kawai ya kilace a dakin miji, suka san ko na tausayawa wahalar yan tsofafin mazajensu na mika masu wata jinnin MUTALAB din? Kun san abinda ya yi yaya shi ya yi kanwa"

Daya daga cikin kawayen Mardiya, wace ta bata wannan rana takanas tare da fada mata sirrin nan, bama kawarta bace kawar kanwarta ce wace ta turota takanas dan a kunna masu , rikakiyar yar bariki ce kana ganninta ka ga wace ta auri duniya auren zobe ta yi kas kas kas da cingan ta ce" kwarai kuwa hajiyata, ai MUTALAB ya iya haihuwa, aman ba ku goma sha shida babe matan, ku goma sha Bakwai ne ko kin manta wace aka samu *KYAUTA?* (irin sararsu ne, zaka ji an cewa yaron da Allah ya yi aka same shi haka KYAUTA)

Sai da Zahrau ta kusan faduwa daga tsayen da take, a tsorace ta kai dubanta wsjen wace ta yi maganar hakama su UMMUKULSUM ,
Najeeba kanta sai da ta rintse ido, aman kuma dama walahi ta shiryawa irin ranar nan, ta san da a irin yanda ta tarawa kanta neman magana sai an binciko sirikan rayuwarta dan a nemi tozartata, tama yi mamakin sirrin gidansu da ya jima haka ba tare da an jima da bankado shi ba, shi yasa ko ba komai take gannin ba laifi Mardiya fa ta yi hakuri, domin tsayin lokacin nan bata fada ba sai yanzu ai kuwa ta yi kokari

Kannanun magangannu ne suka shiga girmama, harma wasun na neman karin haske da maganar KYAUTA

Najeeba ta girgiza kanta ta ce" kai dan duniya, dan duniya bai yi ba, wato shi ko yaya ka yi da shi hakan take gareshi, kwarai kuwa mu goma sha shida ne kamar yanda na fada hakan ne, domin duniya ta san MUTALAB ya haihi y'aya goma sha bakwai ne, maza biyu, mata goma sha biyar, a yanzu da na gano munada yar uwa sai nake fadin sha shida, abin farin cikin alfahari nake da Ubana da bai zubar da yar kanwata ba, ya haifo abinsa santala sannan ta samu kilacewa wace zata yi min wuf da mijin daya a wajen nan alkawari ne........ta karashe tana mai sakin murmushi ta kai dubanta wajen Aida ta ce" ina take?"
Da sauri Aida ta shiga dakin hutun NAJEEBA ta fito da wata budurwa kyakyawa mai tsayi irin na yan uwanta, kamarsu daya sai dai ita din fara ce, sannan hijab ne jikinta yannayinta ya nuna tana da dan tsoro domin sai rarabewa take

Su kansu yayunta sun sha mamaki, a hoto suka san yarinyar yaushe Najeeba ta santa har ta kawota?

Da sauri Najeeba ta fincike hannunta da take jijimkewa ta ce" Jinnin Mutalab Allah kawai yake tsoro, jinnin Mutalab dokokin Allah yake karewa, haduwa da shi kawai yake tunani, idan ba dan haka ba da ya yanka dan mutun sai dai uwarsa ta haifo wani ba shi ba! Sakar min hannunki ki kalli du wace ta bi ki da kallo daidai misalin wanda ta yi maki, idan yar mutunci ce ki yi mutunci da ita, idan ba yar mutunci bace kika daga mata kafa walahi sai na tsinka maki mari, kema ganninki kika yi, suma wa'inda suka same ki daga ke basu kara wata ba hakan na nufin kadara ce ta afka masu wace ba yar shegiyar da ta fi karfinta, ina alfahari da ke, ZAHRAU na Alfahari da ke, Ummulkhair na alfahari da ke, Ummukulsum na alfahari da ke, mu kam muna alfahari da ke a ahalinmu"

Zahrau ta matso kusa da su su hudun, tana kallonsu ta lumshe idannuwanta ta ji wani dadi a kasan zuciyarta, burinta dama itama ta dawo cikinsu ashe yar rigimarsu har ta kawota gidan nan? Hannunta ta kama a hankali ta dan murza sannan ta sakar mata murmushi wanda ya sakata fashewa da kuka ta shiga rungumarsu cike da wani irin farin ciki, ashe zasu karbeta? Ta sha labewa ta kalle su tana son su a ranta aman kuma tarin tsoron ta kusance su ya saka kulun take kara hangensu daga nesa, tunaninta kar ta kusance su, su fatataketa dan ta kasance ba da aure aka haifeta ba, ko a message din da suke da NAJEEBA walahi gani take wasa ne, ashe dai da gaske ne? Ita kam ina zata saka ranta dan murna da farin ciki?

Habu ne ya ringa kikifta ido yana gannin yanda wajen yake kara daukan haramar rikicewa a fili ya ce" toh fa"

Zahrau ta dan zunguri keyar NAJEEBA a hankali ta ce" itace
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment