Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

subuce masa ya ringa dan gyada kansa cike da kasaita hakan ya sa dogarai sada kawunnansu sunna miko gaisuwa da kirari dan gannin Saraki na murmushi ya tafi duniyar shauki (=ØÞ)

Gimtsewa ya yi yana mai kashe kiran tare da sauke ajiyar zuciya

An watse taro lafia, bayan watse taro ne mahaifiyar Nadia ta zo har wajen Ammi ta duka ta nemi alfarmar Nadia ta je gida ta yi wanka, ba dan komai ba sai dan ita likita ce kuma Nadia ta karu sosai wajen haihuwar nan tana son kulata da kanta

Duda ba'a yin hakan, ba'a zuwa wanka a gidan sarauta, ama sai Ammi ta yi mata wannan alfarma, domin kuwa tun saran da maciji ya yi mata suka so hakan aka hanna a yanzun kam sai ta basu wannan dama domin ko ba komai iyayenta ne ai kuma suna da karamci da kawar da kai

_________________________

Shirye shirye ya kankama, Ummukulsum ta shige dakin gyara, inda Najeeba ke makalewa itama ana bata gyaran nata na musaman domin du wani abin da Ummu zata sha tare suke sha, harma ta fita mayar da hankali domin a yanzun ta fita sannin darajar abin

auren kara karasowa yake , bai fi sauran kwana biyu kadai a daura auren Yaya Dayabu da amaryarsa ba, sannan na su ummu da Yarima

A wannan rana ne su Zahrau, su Yarima ango da baban amininsa mai sunna Idriss suka yada zango a garin damagaran tare da yan rakiyarsu tun karfe goma na safe cikin jirgin air france da ya wuce dan sauka a garin Niamey

Sunna sauka hadewa suka yi da yan uwanta suka harhada abinda suka ajiye a grup din da suka yi create iya su yan matan sukai shawara dan bada gudunmuwarsu ga yayansu abin alfaharinsu

Zahrau kanta da take babarsu wace komai ya shiga hannunta sai da ta yi mamakin irin kokarin da suka yi, nan suka samu Ammi da Ummu wace itama ta zo gidan a yau domin a nan masarautar za'a gabatar da shagulgulan auren duka biyu suka zube masu tarin kudin da takardojin adu'o'in kananun da suka rubuta ciki kuwa harda takardar Najeeba inda ya rubuta kalamai kamar haka "YAYANA, INA MAKA ADU'A KA SAMO MIN BABIES MATA DA YAWA YAWA YAWA"

Du daria suka saka , a lokacin da aka yi kiransa aka gabatar masa da irin kokarin kannen nasa sai kawai ya hade su baki dayansu a jikinsa yana dan bubuga bayansu, tabas ya ji wani irin dadi mai sanyaya zuciya sannan ya kara ji a cen kasan zuciyarsa cewa ahalinsa ahalinsa ne, jinnin Mutalab ba zasu taba zubar da dan uwansu ba

A tsaye suke kan kafafuwansu kan shirye shirye

Rana na yi suka kwasa a cikin motoci tare da dogarai yan rakiya wajen motar dogaran kanta mota hudu ce suka saka su a tsakiya cikin shiga ta alkyaba a rurufe masu ko'ina suka yada zango a gidan su amaryar yaya Dayabu

Irin tarbar da suka samu sun ji dadinta sosai, iyayenta ba wasu masu arziki bane ama mutane ne masu wadatar zuci, an masu dahuwa an gyara masu waje an shinfida masu tabarmu da darduma an kawo masu sansanyan tukudi wanda ya ji damu da sansanyar solani ya sha siga da kayan kanshi ga uban cikwui din dake ciki
Ai kau suka baje tamkar ba matar sarakai bane a wajen suka sha abinsu ana wasa ana daria inda mutane ke ta son su samu damar ganninsu aman dogaran nan sun kasa sun tsare dan kuwa kiran da sultan ke yi yana karawa ya kara saka sarkin Dogarai tsayawa kikam a kofar shiga sai muzurai yake ya kasa ya tsare domin uwar dakinsu na ciki

Abinda ya kawo su suka shiga yi, wato kitso da kunshi, sun raraba aiyukan a tsakaninsu inda kanwarsu mami itama ta kware a wajen zana kunshi kamar wata aljannah haka ta ringa zane masu kafafuwa Najeeba kam ta cire alkyaba ta ajiye ta shiga yaryarawa Auntunsu kitso wace ta sake cikinsu take kara karantarsu da jin kaunarsu a cikin zuciyarta domin ita a duniya ta tabata Allah ne ya wanke ya bata wannan bayin Allah da ake tsoro a cikin gari, ita kam sam bata ga abin tsoro a tatare da su ba, abin kaunarta ne, farin cikin zuciyarta ne, mutanen rufin asirinta ne tunda suka nuna mata kauna du irin arzikinsu da sarautarsu suka rungumeta a jikinsu sai kawai take ji a kasan zuciyarta lalle adu'ar samun miji na gari da dangi masu saukin hali da ta taso tana yi tun tana yar karamarta ne Allah ya amsa mata

Ba su su bar gidan nan ba sai kusan salar isha'i, shima kira ne ya shigo wayarta tana dagawa a dake ya furta" Zaki ja abinda zaki shiga kule ke da fita sai na maki wani cikin kin haihu, kin manta jariran da kika bari a gida ne?"

Murmushi kawai ta yi tana sakawa kitson da aka kusan gama mata ribom suka mike sukai masu salama
Nan suma suka yo masu bajintarsu daidai karfinsu inda aka hado su da uban tukudin nan cike da katon kula har biyu da kayan damunsa wanda hakan ya masu dadi dan kuwa sun ji dadin gumbar nan sosai walahi

Sunna zuwa gidan ba zama ba suka yi, a nan aka gamawa Najeeba kitsontsa suka tarar UMMU ta ci karfin kitson Ummukulsum wace ake mata wasu irin kannanun kitso masu shegen kyau
Ummukulsum ta yi wani irin fresh da ita, ta kara fitowa das da ita, dama du ta fi su hasken fata sai fatar ta kara haske sosai da santsi, ko a ido ka kaleta zaka so kuma kallonta domin abar sha'awa ce, a zaunen da take daga kasa wata yar kujera ce ta tsuguni wace balarabar ta ajiye mata, ana mata kitson tana kawo turaran wuta na tsuguni lokaci zuwa lokaci tana saka mata, wannan turaran da irin gyaran kasan da akai mata 6a saka ko yar yatsarta bata gigin gwada sakawa a jikinta domin kuwa ta yi wani irin matsewa abin ba'a cewa komai

Nan Najeeba ta zauna bayan ta watsa ruwa ta shayar da yaranta, sannan ta mikawa masu kula da su ta kama kan AMMI ta shiga kitsa masu du kuwa da irin tarin gajiyar da suka shigo da ita Zahrau kuwa ta shiga kunsa mata lalle namu na hausa

Ummulkhair ce ke ta turo baki tana hararar wayarta ta dago daga saka farcen da take yiwa Ummi ta kalli Ummukulsum ta ce" AMMI kin ga ba, walahi na san ita ta ba Yarima numberna ya ba wannan mutumen da suka zo tare, ni su fita a harkata ba zan iya ba gaskiya"

Ammi ta ce" to wai meye aibunsa? Dan kawai yana nesa da gari Ummulkhair ai idan abin ki ga gidan ya kama zaki zo ki ga gidan ko? Ni walahi nutsuwar yaron ne ta birge ni, gashi kyakyawa mai ladabi da biyaya to meye aibunsa? "

Dan bakinta ta kara turowa tana jin Najeeba na gyara zamanta tana tsaga kitson kan AMMI ta ce" Ammi, balema kudi ne da shi na rantse, kin ga fa a Abujar da yake zaune a cen aka haife shi, mahaifinsa ya rasu da wuri ne ya bara masa tarin dukiyar da shi kansa bai san adadinta ba, a haka mahaifinyarsa itama ta rasu, shine ya ki kula kudin ya je karatu , a waje suka hadu da Yarima har suka kula abota ke kam an yi solofiyo "

Da mamaki Ummi ke kallon Najeeba wace itace bakuwarta, ba komai ya bata mamaki ba kuwa sai ta yanda aka yi Najeebar ta samu information a kan mutumen

UMMU ta ce" Idon naira ta ce ki amince ke meye ki amince mana?"

Ammi ta ce" kin ga dai kar ki yiwa y'ata, ai gaskiya ta fada, to tsakani da Allah meye aibu dan ka so kudi? Ke yar albarka kudi abin so ne ehe!"

Ita dai mesage ta tura masa kamar haka" Ni dai ba zan iya auren mai yaren inglish a bakinsa ba, kai da baka da RRR a harshenka, kumama ni bana son mai kyau gaskiya "

A lokacin da ya karanta sai ya saki murmushi yana kallon Yarima dake yi masa mitar shi bai ga anfanin hanna masa gannin mata da aka yi ba wai sai an daura aure bayan matarsa ce, ya dora yatsunsa ya rubuta mesage kamar haka" Ma ji ma gani, aman mai yaren RR din nan sai ya zamo uban y'ayanki da izinin Allah domin ba inda zan je Sarkin Damagaran uba ne ga kowa, ya kuma bani daki"

Haka suka yi ta raha tsakaninsu har zuwa shiga kwonci kafin kowace ta labe da waya tana dan taba hira da mijinta, ciki kuwa harda Najeeba wace a irgenta bai fi kwana takwas zasu koma bangarensu ba, wato zata fara daukan duty
Hotunnan dinkunnansa da aka kawo ne take ta bi daya bayan daya tana kallo, bakinta ta turo ta danna voice tana shagwabe muryarta ta ce" Ni du kayan nan na rasa wanda kyansa bashi da yawa, Ni gaskiya haka kawai ka saka masu kyau ka fita daurin aure Har ka samo mana wata? "


Murmushi ya yi daga kwoncen da yake yana mai jin dadin irin yanda lokaci zuwa lokaci take nuna kishinsa a fili wanda hakan ke saka shi jinsa wani gingirigin, kafin ya danna ya shiga bata amsa daidai da maganarta

Asubah alkhairi Fari mijin Najeeba

A ranar dake gobe daurin aure sun wuni ne sunna tsaye kan harkar tsare tsaren tarbar baki da irin abincin da za'a girka wanda baki daya girkin larabawa ne za'a yi a wannan taron aure na y'ayan Mutalab

Sai da magariba ta yi suka kile a baban filin dake zagayen wajen AMMI ya su ya su suka shiga gabatar da sister Days, wanda ya dauki larabawan da suka zo da tsuma su Ummu, da su Ammi da Ummu, sai yan matan da su Najeeba

Kwaliya ce suka dauka irin ta larabawa, sun shirya shiri mai tsarin gaske ga turaran wuta sun jojona waje waje sun zuba uban turaren da ya ringa game masarautar ba iya nan ba, a wajen kuwa harda DAYABU wanda yake tare da kannen nasa tun da yama, sallah kawai ke tashinsa
Raguna har uku aka gasa masu,
irin gashin nan mai fita daidaya, aka gabatar masu da komai da komai sunna shan kidan larabawa sunna cin gasashen ragon nan sunna korawa da jusss

Ai kau rawa suke sha abinsu iyayen na shan dariya

Daga inda yake ringeshe da computer a kunne a gabansa da tablettt dinsa yana bin yanda suke gabatar da bikin nasu ya fi kurawa Najeeba ido, wace kugunta ke daure da irin abin nan na larabawa wanda sunna rawa yana bada sautin cas cas cas, hannayenta rike da wata yar igiya fara, gabanta kuwa wani kwanon silba ne karami, sai kafarta da ta dora kafa daya kan daya ita kuwa dauke da sarkar kafa mai walwali, kasancewar wajen da wadatacen haske sai ya zamanto komai yana ganni
Hirarta take hankalinta kwonce, sannan ba abaya bace a jikinta, sket ne budade da wata bak'ar riga wace ta bi lafafen cikinta wanda ko shi da ba dan ya san shine ya yi mata cikin da ta raina a gabansa har ta haife shi ba da shi zai fara karyata cewar ta taba haihuwa a wannan shafafen cikin, sannan ko a zaunen da take duwawunta da cinyoyinta sun kara wani irin bajewa wanda ke nuni da kibar haihuwar a cen ta tare, sai mamanta da suke cike bam ga ruwan nono na shayarwa ga asalin halitarsu

Ajiyar zuciya ya ringa saukewa yana jin wayarsa na ta tsuwa, kiran nan ya kai na tara a kadan, tun da magariba ake kiransa aman wannan da ya zamanto a kusa kusa sai kawai ya mika hannunsa ya dauko yana mai duba sunnan dake sama

Dan kara kurawa sunnan ido ya yi da dan mamaki, dan gannin Gimbiyar garin agadez ce,
Yana da numberta a wayarsa, ama kira bai taba hada su kai tsaye ba, koda jaje ne ko gaisuwa takan bi ta kan y'arta ne

Rage sautin kidan ya yi ya dan gyara kishingidarsa da wayar a hannunsa da kuma tablettt din yana kallo ya amsa kiran ta hanyar salama cikin nutsatsiyar muryarsa mai kamala

Mamaki ne ya dirar masa jin tana gaishe shi, bai idasa mamakin ba ta dora da kara neman afuwarsa sannan ta fara magana a sanyaye kamar haka" yara sun zo Damagaran wajen auren, aman mai martaba ya hanna masu sauka a fada cewar su sauka a gidan kanwata da safe zasu zo baki dayansu harda Zinaria , dan Allah a kara nema mana afuwarsa ko zai sasauta mana fushinsa"

Shaheed ya dan kara buda idannuwansa a kan yan matan AMMI da suka fara tashi sunna yin rawa yana dan girgiza kai yana murmushi a hankali ya bata amsa da fadin " In Sha Allah "

Gimbiya du sai ta kara dirircewa tama rasa ta inda zata bi dan fada masa abinda matar Yarima ke shirin yi, aman shi kadai ke iya tsawatarwa a masarautarsa dan haka fada masan ya zama wajibi

A sanyaye ta dora da fadin" sai yarinyar nan ta wajen Yarima, wato matar tasa, itane ta tafi ashe itama, kuma da niyar rigima ta tafi dan haka ina neman alfarmar a katse hanzarinta "

Shaheed ya kara buda idannuwansa da kyau, rigima? Zata zo wajen auren? Uhum

Karshe dai haka suka yi salama bata samu wata gamsashiyar fuskar da zata kawo masa dayar maganar dole haka ta yi hakuri da kudurin cewa idan da rabo zata koma dakinta

Shi kuwa ido ya zubawa Najeeba da ta dauki dan kwanon nan ta dora shi saman kanta bayan ta cire dan kwalin
Ido ya kara zarowa yana kallonta a lokacin da ta mikar da hannayenta ta shiga kada kugunta su kuwa larabawan nan me zasu yi banda yi mata ruwan turare da buda sama sama

Da sauri ya lalubo wayarsa yana cije lebensa na kasa yana mai furta" ya isa haka neman maganar, a watse tun muna shaida junna!"

=ØÞ=ØÞ=ØÞ=ØÞni ban ga laifin rawa ba wollah haka kawai a dai ringa jin tsoron Allah.....ah tom=Ø
Þ=Ø
Þ=Ø
Þ=Ø
Þ=Ø
Þ=ØÞ=ØÞ=ØÞ=ØÞ=ØÞ=ØÞ

___________________________


An daura aure lafia, duban jama'a sun shaida bisa wakilcin Sarkin sarakuna Mai damagaran, da sirikinsa, amininsa, babansa sarkin garin agadez, da manya manyan sarakunnan da suka halarta bisa gayata da suka samu domin kuwa shi din mai zuwa taro ne hakan ya sa idan yana taro ake zuwar masa ta ko'ina ba iya Niger kawai ba

An wuni cikin shagulgula, shagalin da ya dauki salo kala daban daban
Matansa du sun halara, kwaliya da shiga ke ware yayar wane ko uwar wane=Ø
Þ

Zinaria ta halarta tare da yayunta ko ba komai auren dan uwansu ake suma sannan masautar biyu sun zama yan uwa hakan ya sa suka shiga mutane duda irin tarin mamakin da ake na ganninta irin yanda ta rame sosai ta kara wani fari fat kamar wace bata da jinni a jiki tsabar saka damuwa a ranta, sai dai ta ji dadi da iyayen mijinta basu nuna mata komai ba, kai harta da yarinyar da ta sako gaba da zagin cin mutuncin bata wani nuna mata wani abin ba saima gaisuwar mutunci da suka yi a tsakaninsu

Bayan magariba du an fitar da tarin jama'ar nan sai na jiki sosai ke shigowa falon, su kuwa sun yayada zango, Zinaria na rike da Abdallah tana dan jijiga shi cike da begen yaron a kasan zuciyarta Najeeba na gefe guda lulube da wani jibgegen hijab mai nauyon tsiya wanda fitowarta kennan daga wanka ta hau kan yar kujerar tsugunon nan da jimkin abubuwanta da ta harhada ta ringa zubawa a hankali yana bin jikinta hankali kwonce tana hangen Zinaria daga zaunen da take, dan bakinta ta dan tabe, ita fa ba za'a hanna mata jin kishin mijinta ba, domin ya isa ne

Tana gamawa ta shige ciki dan kwontawa, ta gaji, gajiyartama ta gaji, sai dai maimakun ta samu bacin sai kiran da mijinta ya yi mata na vidio call ya sakata kura masa ido tana kallonsa ta saman screnn din

Bakinsa da yake dan dantsewa ta di baiwa hankali, kafin ta saki murmushin jin abinda ya ce , cewar ta zo gareshi

A hankali ta ce" Na ki "

Ido ya zaro yana kallonta ya dan nuno karamar yatsarsa ya ce" Beebah, satinki nawa rabonki da ni? Ke tunda cikinki ya tsufa kika ysane ni, a yanzun da kika haihu har kika fara sallah shikenan ba zaki zo gareni ba? Nine fa? "

Murmushi ta kara yi a sanyaye ta ce" Kwana nawa ya rage mu hadu ne SHAHEED?"

Idannuwansa ya kausasa jin ta kama sunnansa, kit ya kashe kiran yana kumburi, hakan ya sakata tashi ta zauna da sauri ta shiga doka masa kiran tana kallon wayar, ama fir ya ki ya daga hasalima kamar baya nan haka ya mata shiru bayan yana kallo

A hankali ta koma ta kwonta ta shiga yi masa message sansanya mai sanyaya zuciya, ta dora da fadin" Fushinka na iya hanna min baci khalb, na tuba abin kaunana "

Murmushi ya yi yana mai bin kalaman da shauki a cikin zuciyarsa, a hankali ya sake kiranta,
Tana dagawa ya kura mata ido na dan lokaci har sai da ta kashe masa ido daya sannan ya yi murmushi, shi kadai yake ayana irin abinda zai mata, wato har sati take tunanin zata kara shi kuwa yana nan uwa wani sakarai ko? Zata gane bata da wayo, ta dai yi gigin zuwa bangarensa

A washe gari tun karfe tara suka tashi da hayaniya, ba ta komai bace sai ta matar Yarima wace a yau ta shigo da sunnan ita din matar yariman ce harma ta samu sadawa da bangaren Ammi

Kuka take cikin harshenta da baya fita da kyau tana mai nuni da Ummukulsum zata shigar mata gida ne dan ta rabata da mijinta kamar yanda yayarta ta raba sarakuwarta da mijinta hakama kanwarta ta raba Zinaria da mijinta

Ba wani nan sulhu ba take, fada ne take wanda ya baiwa Najeeba daria tsayen da take cikin shiga ta wani danyen lesh mai kalar orang da ratsin fari ta dora farar alkyabarta har kasa sai baza kamshi take fuskarta dauke da nitsatsiyar kwaliya , hakama yan uwanta da du sun riga da sun dauki kwaliya sun shirya dan bikin da ake a cikin gidan du sunna kallon ikon Allah, sai hakurin da ake bata na ta zauna a yi magana , gefe AMMI na tsaye itama sai UMMU da ta tabe bakinta ita kuwa ba alkyaba bace a jikinta bubu ce ta babar atampa ta kashe dauri ita kanta fuskarta da mak'up simple, uwa uba Amaryar tsarin kwaliyarta ba'a cewa komai du sunna kallonta

Karar buda bangaren shigowarsa ya sakata saurin kai dubanta wajen, haka kuma du wani mahalukin dake falon sai kake jin tsitttttttttt ya yo, yan matan har sun kai kasa dan girmama mai girma, wa'inda basu rigaya sun zube ba AMMI ce da Ummu da Najeeba, da matar Yarima,
Ita Najeeba ta ki dukawar ne dan bata so ya bayana a cikin tsarin da ba rawani, a yau tana jin kishin du wata mace ta gane mata shi ba rawani ciki kuwa harda matar Yariman!

Kanshinsa ne ya fara rufe kofofin hancinsu, kafin sandar girmansa ta fara shigowa baka mai lankwasa da adon zeba sai farin hannunsa mai dauke da zoben azurfa da agogon azurfa sannan jijiyoyin sun mimike rado rado ana ganni a jikin

A hankali yake kara bayana lokaci daya ta ji wani irin abu na mata yawo a jiki da kwakwaluwarta da zuciyarta,
Bayanuwarsa cikin shiga mai duhun haske ya sakata sada dubanta kafin itama ta zame ta kai kasa ta dukar da kanta cike da jin shayinsa da matsananciyar kaunarsa

A SARKINSA YAKE, SARAKI NE, MANYANMU NE, MASU MULKINMU NE, UBA GA ABDALLAH DA MUHAMAD, BABA A WAJEN YAKUB MIJI A WAJEN NAJEEBA DA NADIA, cike da kasaita ya dan juyo da kansa bangaren mahaifiyarsa wace ta kai zaune itama cike da sada kanta domin kuwa ita ta kawo shi duniya aman ko ita takan bambance lokutan da take iya kama kunnensa ta ja, da kuma lokutan da take sada dubanta a kan nasa dan kuwa daukaka ce daraja ce da Allah ya bashi,
Kansa ya mayar wajen UMMU, itama kan nata a sade yake a kasa
Matar Yarima na idasa gane komai itama ta zube a kas wajen da su Ummu suke duke, AMMI kuwa a kan kujera ne take, Ummuma a kasan take kanta kasa

Duban kowa yake daya bayan daya har idannuwansa suka sauka a kanta,
Yana kallon nata kallo na kurullah, kallo na soyaya, kallo na bege,

Salamar Yaya DAYABU da ya kwana a gidan amarya ne ya saka shi kai dubansa inda yake shigowa, yana karasa shigowa ya duka shima nan kasa da sauri yana mai kawo gaisuwarsa

Shiru bai amsa ba, hakan ya sa ya kara sada kansa kasa

A haka mutun uku suka shigo da salama, wato ABIH, YARIMA, DA AMININ YARIMA

Bayanuwar yannayin wajen ya saka su zubewa suma sunna mai gaishe da MAI DAMAGARAM MAI WUKAR YANKA GURNANIN ZAKI

Da sauri ya cire dubansa daga kansu bayan ya gama gannin bakin Yarima harda shi a wajen da matarsa take, ta dauki wannan kwaliyar da ta tsintsinke masa zuciya, tana baza kanshin nan da yake matukar kishi, sai kawai bakinsa ya kara yin nauyi ya kasa amsa gaisuwar sirikinsa da yariman da abokinsa

A hankali ya kuma cirw dubansa ya dora shi kyam a saman kanta

A hankali ta ringa dane idannuwanta dake son dagowa dan dubansa, har matse hannunta ta yi du dan ta hannawa kanta kallonsa sai dai ina, abinda ya zame mata jiki, ya rigaya ya zame mata sabo bata tunanin akoy wani hargagin da zai hanna mata dago da kan nan nata da take jin yanai mata balin bal

A hankali ta idasa dago da dubanta ta zuba idannuwanta cikin nasa

Irin TSADADEN kallon nan da ya saba yi mata wanda a da take dauka da na tsana, kallon nan mai yi mata nuni da tsantsar kaunarta da matsanancin kishinta da madaukakin bukatarta, kallon nan mai tsuma zuciyarta ya sakata lumshe idannuwa koda bata shirya ba ne ya kafeta da shi ko kyaftawa baya yi

A hankali ta ringa jin zuciya da gangar jikinta na mikar da uta tsaye daga zaunen da ta yi

Tana gama mikewa ta ringa takawa da kafafuwanta dake dauke da farar safa kal kal da alkyabarta har ta karasa gabansa
Sakamakon ya darata a tsaye sai ta dago dubanta tana kallon idannuwan nasa
Gannin a yau yan sarautar aka tashi da su, ga shara'a ta samu a irin wannan lokacin sai ta saka hannayenta a hankaki ta dan ja rawanin nasa kasa kadan ya kasance lebunansa a waje sannan da girarta ta yi masa tambayar menene?

Ajiyar zuciya ya sauke, a hankali ya dora hannunta na dama daifai kahon zuciyarsa sannan saman labansa ya furta" *KISHINKI NAKE, SON KI NAKE, ND I NEED U A SAMAN GADONA* "

Murmushi ta sakar masa mai tsada kafin ta dube shi da kyau itama a kan lebenta ta ce" *BURINA NA DAWAMA A CIKIN JIKIN KA, ZAN JE NA YI JURANKA HAR ALLAH YA KAWO MIN KAI....* hannunsa ta ja ta dora a wajen mararta ta dan shafa ta kara tsura masa ido ta ce" *Marata a shirye take da daukan ajiyarka ko da kuwa mace na iya dauka sau billion a rayuwa.......zan amshi ruwa daga mai dauke da ruwa, zan baka hardar karatun da kake koya min fila fila KHALB* "

Har ga Allah sai kawai ya ji jikinsa ya fara bari bari, yana kallonta kamar wani wawa har ta shige ta kofar da ya biyo

Ji ya yi tsayuwa na neman gagararsa, da duba ya ringa bin jama'ar dake wajen du kawunnansu a kasa

Wani yawu mai santsi ya hadiye ya ja ya mayar da rawanin har wajen bakinsa

Muryarsa na crakin ya kai dubansa wajen Yarima ya dan limshe idannuwansa a kasam zuciyarsa kuwa fadi yake 'Ina, koda na ce zan gabatar da shara'ar nan ba zai yiwu ba, ta lalata komai ta tsatar da komai sannan ta tafi da komai', sai kawai ya dan kara gyara tsayuwarsa ya ce" *YARIMAH ABDUL JABAR, KA GABATAR DA SHARA'A WA AHALIN GIDAN SHAHEED ALIYU DA MUTALAB NA BAKA WUKA NA BAKA NAMA*


Yana gama fada ya juya da dan hanzari ya shige ta hanyar nan,

Ai kau ta dan dage alkyabar dake jikinta ta juya da niyar kwasawa da gudu
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment