Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

hikima.

Murmushi Anmy ta yi kafin yayar Zinaria ta dauka ta je gaban Anmy ta tsuguna ta ajiye sak'on ta k'ara gaishe da Anmy din sannan ta koma mazauninta.

Dubansa ya kai wajen su Nadia,
Sai kici kici Aunty take da jaka ita batama san inda ta zuba chek din da ya bada Jakadiya ta kawo masu ba, sarai ya san a wannan wajen za'a so nuna hali na wulakanci shi ya sa ya bada chek biyu wanda ya tabata wannan uwar handamar ba zata taba iya ciro kudi irin haka ba.

A lokacin da ta fitar da takardun sai da ya lumshe idannuwansa sannan ya ci gaba da kallo

Sai a lokacin ta kalli takardar, sai da ta zaro ido tsabar kad'uwa har da yan yatsunta ta kara irga ziro din dan tabatarwa.

Ajiyar zuciya ta sauke ta nufi wajen itama

Tana inda inda ta ce" NADIA na godiya, sannan ta bada kyauta a baiwa kishiyoyinta kamar haka, million muraran million har million ashirin ashirin... *su ja jari* (kar ku manta ita ba sannin me ake fad'a ta yi ba, kokari ta yi ta kamanta)

Itama ta nufi wajen su Anmy, sai da ta duk'a da hannu biyu ta mik'a masu sannan ta mik'e ta nufi wajen Nadia da baki d'aya ta zaro idanuwanta da mamakin kud'in, kan ubancen kaya sa, wani abin sai manya, wani abin sai kishi, yo ita uban wa zai bata wannan kud'in ta yi wasa da su? Ko hauka take, ba dai dan ta birge kishiya ba walahi, kai, inama inama daga ita sai Zinaria ne suka shigo? Inama inama hakan ne?

Kwarai gwuiwar Zahrau ta yi sanyi a lokacin da ta tuna kudaden da suka zo da su kwata kwata million hudu hudu ne, suma Anmy ce ta bada chek din tana fadin akoy tadar nan, suma zamaninsu an yi, idan an kawo amarya kowa na yiwa kowa kyauta, sai dai su nasu da sauki domin zamaninsu idan ka bada million dayama ka yi kokari bare har sama, su kam ba ta nan suka zuba kishi ba, aman sai ga wani tashin hankali kiri kiri ana wasa da kudi kamar jaraba yanzu haka kowace iya abinda gareta ne ta kakabe dan kawai kar a rainata?

Anmy dake yaki da zuciyarta kan ita zata je wani duban ta kuma kaiwa wajen Sultan
Ta sani, farin sani cewar shi ya bada kudin Nadia

Aman why ya yi haka? Shin tsana ce mai tsanani tsakaninsa da Najeebanta har ta kai haka ko me?

So take ta shiga idan ya so sun dade basu ce ta zabi Najeeba a kansu ba! Sam ba zata iya bari a shiga da yan kudaden nan ba, lalle yau ta yarda yanzu irin tadar nan ta zama hauka, gaskiya mahaifiyar zinaria bata son zaman lafia , a kan me zata bada irin hanyar nan? Sai kuma shi kansa dole sai ta tuhume shi da kudaden nan idan kiwa shi ya bayar sai ya ba sauranma!

A hankali ta ajiye ambulope din ta dan mizguta zata tashi

Hannun da ya mayar da ita ne ta bi da kallo

Murmushi ta sakar mata kafin ta idasa mikewa gaba dayanta
Ina sam ba zaka ce matar nan ta haifi najeeba ba,
Doguwar riga ce a jikinta ta shada an mata makeba wace ake fitar da wuya kawai
Rigar ta sha handwork mai tsadar nan irin wanda ake yi a dubai
Rigar ta hadu, ita kadai abin kallo ce sannan aka yi mata dauri das irin na zara buhari a saman kanta
Ashe itama gashi ne da ita?, hakan ya sa daurin ya kawata sosai a kanta
Sam babu irin cikar nan irin tumbi daban mama daban, rigar ta bi shafafen cikinta sannan mamanta ta saka bra das sun zauna a muhalinsu

Kafarta kuwa sanye take da takalmi mai tudun gaske baki sidik wanda ya haska fatar kafar tata, Ummu ba baka bace tana da hasken fata aman kuma ba fara bace

Hannunta dauke da yar poss dinta ba kudi ba abin kudi ko daya a hannunta

Sai da ta tsaya a tsakiya kafin cikin harshenta wanda larabci ya kwonta muraran ta furta" Asalamu alaikum

Idannuwansa ya lumshe cike da jin kunyar wace ta fito mata, Ummu uwa ce a wajensa, ya so Zahra ta shigo dan ya kula da motsin son shigowarta, sannan ya ga Anmy ta so shigowa duda ya yi niyar dakatar da Anmy din domin a nan a yanzu ba a matsayin maman Najeeba take ba, aa , a matsayin mamansu su duka take, sai ya ga Ummu ta fito

Amsawar da suka yi sunna kallonta ya saka ta yi murmushi a hankali bayan ta daga idannuwanta da ta saka masu karin gashin idon da ya zame mata jiki ko a yanzu da ta baiwa shekaru arba'in baya sam bata sake da gyare gyare ko dan ta yi zaman saudiya ne? Ita dai bata sake
Cike da sanyin murya, dauke da tsararen murmushi har hakoran makarta biyu na azurfa suka bayana kansu ta furta" Alhamdulilah
Godiya ta tabata a gareku adalan yan uwa
Allah ya saka da alkhairi da kyauta masu girma da tsari

A hankali ta kai dubanta wajen Sultan.

Sai da ta k'ara sakin murmushi sannan ta ce" Allah ya taimakeka, kyautar *GIMBIYA NAJEEBA* zuwa ga yan uwanta su ne tagwayen gida da kuma shop place."

Shi da kansa sai da ya k'ara kallonta da kallo irin na *DA GASKE KIKE?*

Tagwayen gida dai, gidaje ne da ahalin sarauta suka kashe k'atuwar anguwa suke tanfatsa gidaje kala daban daban a ciki, mahaifiyar Najeeba ta yi dank'ara dank'aran gidajenta masu firgitarwa har k'waya bakwai, gidajen sun ginnu, k'asa ta ci kud'i
sannan shop place d'in nan wajen da ake gabatar da kasuwanci ne, shagunna ne a laye har k'waya shida kowane da sunan shop place ba abinda ba'a siyarwa suma malakinta ne.

Idanuwanta ta d'an bud'a masa sannan a hankali ta ce" har abinda ke ciki." (tana nufin kowace gida d'aya da shago d'aya da abinda gidan da shagon suka d'auka).

Lalle ta kai duka
murmushin nasarar da yayar zinaria ke yi na sun ci fadan sai ya ka ciki, ita bak'uwa ce, aman ta san gidajen nan babu na wasan yaro, sannan ta san shop place.

Ai Nadia gaba d'aya ta ji wani girma ya hau kanta, ita ina ruwanta da wani duka, sam bata san mahimmanci hakan ba, ikon Allah take kallo a dan kankanin lokaci ta zama hajia (>Ø#Ý k'awata kennan)

Murmushi ya yi daga cikin rawaninsa, tabas iyayensa sun gama magana, wato idan sauran sun bayar da kud'in jari da sarkar kwaliya, su sun bayar da muhali da uwar jari?

Kansa ya ringa dan girgizawa a hankali , du ita d'in nan ce suke tarawa kasa?
Da sun san, ko baki daya garin nan zasu bayar dan k'watar martabarta ita din ta gama zubarwa da basu yi wannan k'ok'arin ba, da sun san sun siyarwa kansu kunya ne kan kunya da basu yi irin wannan lamari ba.

Sai da ya bushi iska yana gannin ta koma wajen Anmy ta zauna, fuskar Anmy ta fad'ad'a da farin ciki da annashuwa ya sauke ajiyar zuciya.

Bayan sallamar nan, dama zai yi shiru ne du su gama gabatar da kyautarsu wa junnansu, idan sun gama mahaifiyarsa zata yi nasiha , sannan ta fad'i wace zata fara zuwa turaka kamar yanda abin yake a tsare.

Anmy ce ta bud'a bakinta cikin sanyin murya, da mulkin dake cikin jinnin jikinta , cike da aji, da aiki da ilimi ta shiga yi masu nasiha.

K'warai ta yi nuni da girman igiyar da ta rataya a kansu a yanzun, sannan ta yi masu nasiha da su yi koyi da kishi tsaftatace domin kuwa kishi halal ne aman idan har bai zarce ka'ida ba, ta yi masu nuni kan kowace ta girmama ta gaba da ita, su wanzar da zaman lafia a zuciyar mijinsu.

A hanki ta dago ta ce" a yau *NAJEEBA* zata fara tarewa bisa k'a'ida, sannan Nadia dake amarya."

A zabure ta d'ago dubanta da kanta dake kasa, ita kanta a cikin hali take na damuwa, tabbas ta lura idan ba da gaske ta yi ba tana cikin tsakiyar tashin hankalin ne da ake kira gaba k'ura baya damisa.

Rabonsu da wani magana ta shiga tsakaninsu tun a bakin titin nan, sai dai irin kallonsa kan isar da sak'on zuciyarsa.

A yau da ya d'auko mata Nadia a matsayin kishiya sam ta k'i aminta cewar soyaya suka yi, sai ta d'ora hakan a matsayin da saninsa, wata hanya ce ta ya nuna mata cewar ita ba kowan kowa bace, abinda take jin haushin kanta irin yanda abin ya mata ciwo, k'warai abin ya daketa harma fiye da kishiyar da take zaune cikakiya k'osashiya, fitinaniya wato Zinaria, Tabbas abin ya daketa, sam bata tab'a kawowa kanta cewar zata wayi gari ta ganta a irin rayuwar nan ba, yau gata ita najeeba zaune ga kud'i ga mulki aman sun kasa sakata kwaso shoki saima cikin tunani kala daban daban, shin tsoronsa nake? Shine tambayar da ta cika yiwa kanta.

Eh ina tsoronsa, domin tamkar dodo haka yake a wajena, ban san kamaninsa ba, ban san zuciyarsa ba, ban san laifina a gareshi ba, idan dan ina kallonsa ne, ba wani abu bane sai son ganin wai kullum shi sai ya saka kwali? Wani sa'in kuwa idan na ga ana ta magana shi bai yi nakan kale shi dan na ga wai yana wajen kuwa? Fad'ana da matarsa bai shafe shi ba, ita dake zagina da munanan kalamai fa? *SHIN ME NA MASA DA YA SAKA YA FI TSANATA DA KOWA A DUNIYA?*, ni nake da abubuwan da zan tsaneka har mutuwarka, ka d'oran karan tsana kana tsargina? Sannan ka haye dukiyar marayu kana wasa da ita? An ce wai kasuwanci yake, yaushe yake fita kasuwar? (Kam Najeeb, kasuwa zai je? To sarkin wasan karan yara ne ba?), an ci an tayar da kai!

Jin maganar bakin Anmy ya sakata jimk'e hannayen Zahrau,
Ita? Ita fa? Zata tare a ina? D'akin wa? Turaka? Saima kalmar turaka ta b'ace mata b'at a bakinta,tabbas aurenta aka fara d'aurawa kafin a d'aura na Nadia, sannan idan maganar wace aka fara kawowa ne ita a gidan ta kwana, sai dai sam ba zata tare a turakar kowa ba!

Idanuwansa a lumshe suke a lokacin da wannan magana ta fito daga bakin Anmy.

Rintse idanuwansa kawai ya k'ara yi yana jin yanda yanzun ne zuciyarsa ta fara tafasa da abubuwan dake faruwa.

A kan me za'a ce ga wace zata fara shiga d'akinsa? Shi sam, bai ajiye wannan a gurbin wace zata zo gareshi ba, ba an d'aura ba? Su barshi ya zartar da yanda yake so aurensa ya tafi.

Anmy ta k'ara gyara zamanta tana hangen yanda Zinaria ta jinginar da kanta jikin kujerar da take zaune.

Sosai take tausayin yarinyar, tana tausaya mata da irin kishin dake damunta, irin wannan kishi, abinda ya dace ta samu wace zata ringa tausarta tana saka ta a hanya tana tarota, sai dai ga dukan alamun mahaifiyarta wace ta fi kusanci da itan ba zata taimaka mata ba, sai yanzu ta fara cire zafin reaction d'inta na jin an d'aura auren Zahrau da mahaifinta, tabbas uwar gijiyarta na bada gudunmuwa wajen k'ara tunzura zuciyarta, tatanta d'aya ne, irin zargin da ya shiga zuciyarta a kansu ya zamo k'arya, idan har ya zama gaskiya ita kam bata da abinda zata iya yi sai zuba ido, kisa? Kisa fa?

*Allah ya baku zaman lafia*

A fili aka ringa amsawa kafin ta bada damar ana iya tafia.

Talafota suka yi suka fara bi ta corridor d'in da zai kaita falonta suka fara fita.

Sai su Nadia suma suka yi b'angarenta, sannan su Zahrau suka kamata suka fita da ita, ita ko b'angaren nata bata je ba suka nufi b'angaren Anmy da ita dan su shiryata a rakata.

Suna shiga ta zame ta zube a k'asa a baki bakin shiga falon kafin ta saki kuka mai zafi mai cin rai.

Wace ta yi mamaki kad'ai kishiyar Zahrau ce, domin ita bata san wannan launin kissar da ta gabatar ta dnane abinda ya daketa a cikin zuciyarta wato wai Nadia.

Hannayenta take yarfewa a rikice ta ce" Wai Nadia? Aminiyata? Me na masa?"


Da sauri su Ummu dake jira suka yo kanta, har rige rigen tambayar me ya samu Nadiar suke?

Najeeba ta k'ara d'ago kanta ta ce" walahi basa soyaya, yaushe rabona da ita? Da sunna soyaya nice ta farkon da zata fara fad'awa domin ita rayuwar nan birgeta take, na tabbata daga baya ya saka haka dan kawai ya k'ara wulak'anta ni."

Da mamaki kishiyar Zahrau ke kallon Najeeba kamar me.

Najib dake zaune cen yana game da wayar Anmy ya dakata tun da ta fad'i yana ta kallonta, yanayinsa na nuni da hankalinsa a tashe ya ce" aunty Najeeba zaki b'ata kwaliyarki fa."

Zahrau ta kalli kishiyarta ta sakar mata murmushi ta ce" aunty, ki je ki huta kin kwaso gajiya."

Itama dacewar hakan ta gani, dan haka ta sakar mata murmushi kafin a sanyaye ta ce" Najeeba, ki yi hak'uri kin ji? Idan harma hakan ne ki d'auka hukucin Allah ne kasancewarta matarsa, ki yi hak'uri ki sanyaya zuciyarki ki rage kishinta kin ji?"

Tunda take maganar bata wani baiwa abin importante ba, sai da ta ji kalmar *kishi*,
Nimporte quoi! Ita zata yi kishi dan kawai ya yi aure? Kishi? Na me? Auren so ake yiwa kishi, mutumen da aka sani ake kishinsa, mutumen da ya gama kafa soyayarsa shi ake kishi ba wai haka kawai ba, ita ba kishi take ba, sam ba kishi take ba, tana jin haushin a mata kishiya da aminiyarta ne, me ta yi? Meye laifinta? Nadia ba abokiyar gabarta bace aman shine za'a had'ata gaba da ita?

Wani ihu ta tak'ark'are zata saki sai dai abinda ya d'auke mata shi saukar yan yatsu biyar a fuskarta.

A firgice ta d'ago dan ganin waye ya mata wannan hukunci a saman fuskar da ta gama shan gyare gyare? To mema ta yi na marin?

Sama sama ta ji muryar kamar ba tata ba tana fad'in" Zaki min shiru ko sai na b'ab'ala maki k'afa a nan? Shirme! Shirmen banza! Maza mik'e ku saketa, maza mik'e zaki fice a kimtsaki ki je ne b'angarensa idan ya so dan Allah a kawo ki gunduwa gunduwa *Najeeba MUTALAB!* Yarinya an wani shagwab'aki kina iskanci? Ke kin san wanda kika bud'i baki kika yi magana sama sama a gabansa ko uwarki da ubanki ba zasu iya yi ba aman alfarmar Gimbiya ya biki da kallo? Au ke ga marar kunya, ga isashiya ga mai bakin magana ko?" Du a wannan lokacin kamaninta ne suka dawo wa Dayabu dake tsaye ya hard'e hannayensa.

Tabbas ba'a tab'a kawo mace mai laushin da ta ringa kwana da su a saman katifa d'aya tana cencana su ba irinta , sannan ba'a tab'a kawo macen da idan ka yi abin hukunci zata hukuntaka ko a gaban ubanka ne irinta
takan kashe dukiyarta domin baki d'aya y'ayan, bata tab'a ware tata ba, idan ta tashi wanka d'aya bayan d'aya take wanke y'ayan daga shekara zuwa shekara ne, da d'an girmansa yana hankalce da ita bata tab'a dan ta zo kan tata yar ta fi wanketa ko ta fi binta a laluma ba.

Hararan da ta sakar masu ta cire d'aurin da akai mata na zarah Buhari sannan ta dakatar da Anmy ta ce" Wallahi, walahi da ba dan idan na fita na tatakata ba nima na raba rashin kunya a gaban SHAHEED ba, da sai na tataka banzar yarr nan! Ke har tunani kike dan yana son ki ya aure ki?"

"Ummu?" Anmy ta fad'a da d'an k'arfi.

Ummu ta ce" Oho shiiiiit, Anmy pls ki barni haba, wai ita uban wa ta fi zuciya ne? Ke? Ke najeeba? K'anwar bayansa zaki bud'i baki ki wani nuna baki damu ba dan an maki kishiya Nadia? To ki yiwa Allah kar ki damun idan kina so ki k'aro masa da Barirar! Aman fa ki sani, ko Ubanki MUTALAB da ya d'aure maki gindi kike iya shege, ko uwar taki gata a tsaye, ko su yayun naki nasu isa sultan Shaheed gurnanin zaki na zaune su ringa iya shege ba! Yau na ga ikon Allah! Dan an d'aura maki aure da shi ba yana nufin har kin kai wajen da zaki masa iskanci bane! Ke ko murza namiji zaki yi ki murza a k'uryar d'aki aman ba wai a gaban mutane ki nuna ke kin isa ba!"

"Zaki daina bina da idanuwa kina wik'i wik'i da su ki mik'e Najeeba ko sai na nuna maki wacece *MARIAMA BIN ABDALLAH* *UMMU?*!"

Zabura ta yi daga zaunen da take a kasa ta mike tana kara zaro idannuwan da sauri ta aniya kokarin yin wajen Anmy sai kara kallon Mahaifiyar nata take>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



39




Har waiwayen Ummu take tana hada kafa wajen sauri

Anmy ta kamata ta juyo ta kalli Ummu ta yi kwafa ta jata suka shige ciki

Dama wace ta yi saura datijuwar nan ce kadai wace zata kimtsata wato Fadimatu

Hankali kwonce ta sakata cikin wani ruwa mai kanshin gaske da sanyaya zuciya

Tana fitar da ita ta kara bin jikinta da wani mai lalausa mai sanyin kamshi

Wasu kayan baci dake cikin kwalinsu ne ta ciro, rigar fata ce doguwa da pant dinta da bra dinta

Rigar mai shegen kyau ce abin ba'a magana, iein mai santsin nan ce hakan ya sa take bin jiki masha Allah

Cike da nutsuwa ta zauna ta kara gyara mata gyaran gashin da akai mata
Wannan uwar kwaliya baki daya an wanketa an zubar da hodar
Kamaninta natural shine a tatare da ita
Baby face dinta ta bayana, ga lebenta mai kyan tsari

Man lebe mai wani irin kanshi aka bi da lebunnanta

Kwali kawai aka saka mata kafin a rufa mata bargo wani sansanyan kanshin turaran wuta ya shiga bin jikinta baki daya

Har gashinta da kalar turaran gashin da aka mata anfani da shi

A yau dai Najeeba kanta ta san ko wa ya sameeta a haka ya samu gata mai matukar girma da tsayawa a zuci

Hijab fari kar, hade da Alkyaba wata kalar blue mai duhu sabuwa dal aka luluba mata a saman suturarta

Zaunar da ita ta yi tana kallonta

A hankali ta ce" Najeeba, ko me zaki tarar ki kasance mai yin biyaya da Hakuri
Ki sani ko me kike ji a zuciyarki ki dane shi, domin kuwa idan har kika ringa falasa shi to fa kece a matsala kin ji?

Kanta ta daga a sanyaye, domin baki daya jikinta ya gama mutuwa ne, wata faduwar gaba take ji, takan yi tunanin wai da gaske zata je dakin mutumen dake miji a gareta? Wannan shiri da ake mata shin hasashen da take ne zai faru da ita?

Wannan rakiya ba kowa ya yita ba sai Jakadiya

A lokacin da aka yi kiranta itace mafi datijantaka, ita ta raka Anmy, yau gata zata yi rakiya ta uku a matan sarki

Cike take da fargaba, ta so ta ti tambayar aa, yaya za'a raka masa mace biyu? Sai dai ba hali domin ta san idan da ba da sanninsu ba, ba za'a iya kai masa wata kuma a kara kai masa wata ba

A hankali suke takawa sunna kara kusantar dakin

Yanzu yanzu ta dawo daga rakiyar Gimbiya NADIA bisa umarnin amintace ya shaida mata umarnin mai wukar yanka ne
Ta shiga rudu, mace biyu zai tare da ita ko me?

Jiki sanyaye ta karasa da ita tafkeken falon da ya kasance shine falonsa na karshe wato na sirrinsa, wanda matayensa ke shiga, daga su sai dakinsa na baci

Ta jima tsugune kanta kasa tana jiran uban gidansu

Najeeba dake zaune saman kujerar da ta yiwa kanta masauki ta daga kanta cike da nutsuwa tana bin falon da kallo
Tabas bata taba gannin wajen da ya birgeta irin wajen nan ba

Tsarin falon nan ya sakata yin saranda cewar lalle sarkin Damagaram ba karamin mutun bane

Sanyin Ac din ya sakata yin lakwas tana sauraron yanda cikinta ya dan fara neman agaji domin a gaskiya yinwa take ji rabinta da abincin kirki har ta manta, sai kima mata abubuwa suke,

Dubanta ta maido wajen Jakadiya

Kanta a kasa tun gurfanar da ta yi,
Hakan ya bata mamaki tana dubanta ta ce" aman mama ki daga ki huta mana

Da sauri Jakadiya ta kara sada kanta ta shiga Fadin" ALLAH ya taimakeki ai ban gaji ba, Allah ya kara maki lafiya Gimbiyar Gimbiyoyi, sannunki da zama uwar gidan Mai damagaram

Murmushi Najeeba ta yi tana kara kallonta ta ce" to tashi ko tafi idan ya zo zan ce da shi kina gaishe shi

Jakadiya kam abin ya gama kasheta da mamaki, kai? Tana gaishe shi? Ita wa?

Kara sada kanta ta yi ta ringa neman afuwa da fadin ba sai an ce tana gaishe shi

Wannan lamari ya baiwa Najeeba Nishadi har kara kallonta take tana so lale lale sai ta dago kanta kamar wara wace take gaban sirikinta?

Ita dai Jakadiya cike take da tsoro da al'ajabin Najeebar, so take ta bata damar da zata kara gurfanawa aman Najeebar ta hanna

Najeeba ta kara sakin murmushi ta ce" ki tashi ko ki bata min rai fa? Na salame ki

Ai kuwa da sauri ta kara gurfanawa tana Allah ya huci zuciyarta, kafin ta mike ta yo waje da sauri

Najeeba ta zaro idannuwanta a fili ta furta" kai? To meye dan kin bata min ran? Lalle gifan sarauta na tare da wani lamari mai girma

Komawa ta yi ta kara zaunawa da kyau ta shiga tunanin rayuwa
Saloon dinta, yaya yake tafia?
Kudadenta ina aka kilace mata?
Kayan aikinta shin ana kular mata da su?
Domin fa, zata koma bakin aikinta, zata nemi kudinta kamar yanda ta fara, auren sarki ba zai hannata nema ba!

Kamar wasa zama ya sameta
Tun tana daga kanta tana kallon agogo har karfe dayan dare ya yi bata ga alamun kowa ba, bata ji motsin kowa ba

A hankali ta cire kafafuwanta daga cikin lalausan takalmin da aka saka mata na baci ta dora kafafuwan nata saman kujerar nan ta juya ta yi kwonce ta mike kafafuwan nata sannan ta sauke alkuabar daga jikinta baki daya dan ta ji dadin baci

A kasan ranta ta furta" ai da gannin jajayan idannuwan nan nasa na mashaya ne, mai yiwuwa an labe wani wajen ana aiki marar kyau
Kafadunta ta daga tana ayanna ta fi nono fari, sannan ita kuwa da ta mareni sai na fadawa Abih!

A hankali ta lumshe idannuwanta tana mai neman baci, baci take so ta yi ta huta, ta ajiye matsalolinta gefe zata waiwayesu ne daya bayan daya domin a yanda ta fahimci rayuwa zuwa yanzu idan ba ita da kanta zata daukarwa kanta mataki ba, to fa bata da wanda zata fadawa ya shige mata gaba

A hankali ta ringa lumshe idannuwanta tun tana cike da tunanin duniya da matsalolinta har ta fara gyangyadi

Cen cikin gyangyadinta ta ji wani ihu daya tak wanda ya sakata zabura a firgice har tana gurdewa ta fado daga saman kujerar da take kwonce
A tsorace ta kai dubanta wajen agogon dakin mai dauke da gilass

Karfe uku har da minti arba'in da bakwai, wato hudu dai ta kusa

A tsorace ta kara saurarawa dan jin shin ihun ta ji ko kuwa mafarki take cike da mamakin har ta yi bacin awa kusan uku?

Murya ce ta shiga kunnenta a galabaice ana furta" *wayo Allahna zan mutu, wayo na tuba ka sarara min haka, wayo dan Allah kar ka kara turawa zafi nake ji kar ka yaga ni biyu, innalilahi wa'ina ilaihi raj'une wahala*

A hankali ta kifta idannuwanta sukai mata dan luuuuuu sannan ta kuma budawa

Irin kalaman da kunnayenta suka kuma tsinto mata sune kamar haka" *ta fi karfina, wayo zan mutu wayo ni Allahna ka taimakeni Sarki*

Wani irin ras, hade da kamewar bayan kai ne ya sameta lokaci daya,
Mikewa ta yi tsaye ta juya wajen da ta fi jin magangannun na fitowa

Muryar kawarta ce, aminiyarta ce, wace take tamkar yar uwarta ce ke fitowa daga cikin dakin cen wanda ya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment