Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

saman diner ne

Ko yanzu Zahrau ce kwonce kanta saman cinyarta ita kuwa tana shafa mata gashin kanta
Daga kasa kuwa Najeeba ce ke gyara mata akaifunta tana ta kankare mata su tana yanke mata duda ba wani datin dake jikinsu aman ta saba idan tana zaune ko ta dora rigimar sai ta yi mata kitso, ko ta kama gyare gyaren mata su akaifu ne da sauransu

Komawa suka yi wajen suka zauna domin wajenma waje ne mai alfarma dan ba kasa ne dabas ba aman duda haka ita ta so ta hau kan kujera dan a ganninta ai ita matar yayanta ce

Yayarta ta fara mika gaisuwa, kafin itama ta buda bakinta cike da yatsina ta ce" Fatan kun wuni lafia, yaya aka ji da hakuri?

Gimbiya ta dan dauki lokaci kafin ta lumshe idannuwanta, hakan ya sa Jakadiya fadin" Alhamdulilah, Gimbiya ta amsa Hakuri an gode Allah

Da kallo ta bi Jakadiyar sannan ta sauke kan Gimbiya
Sai ta ji shakarta ta shigeta domin irin kamalar dake tatare da fuskar gimbiya ba zaka iya takata kai tsate ba komai rashin kunyarka dan ba lalenema ka ji muryarta ba idan ba hakan ta so ba

Idannuwanta ta dago ta sauke a fuskar Zahrau wace ke iya gannin hakan

Dan mukewa Zahraun ta yi tana gyara gashin kanta ta bi kannenta da kallo baki dayansu, kallon nan da ake kallonka kuma a kalli mutun

Du yawanci sai da suka dan turo baki kafin a hankali da daidaya suka shiga gaisheta, gaisuwa kamar haka" barka da yamaci, fatan kun zo lafia?

Bakinta ta tabe tana dan jijiga yarta dake bayanta wace ke ta ihun a sauketa tun da ta ga yan uwanta aman uwar ta ki kunceta dan haka sai take kukanta irin kannanun kukan nan

Basu wani jima sosai ba, ko gaisuwar yaran ba yanda ya dace ta amsa ba yayarta dai ce ke amsawa kafin su mike su juya su fita

Sauri sauri take har suka karasa fita waje sannan suka shiga cikin motarta da suka zo da ita

Sai da ta kama hanyar gidan iyayenta dan cen suka nufa tana ta jan wani uban tsaki

Ita dai yayarta tana ta jijiga yar da ta ki yin shiru tana kiran sunnan yayanta dan saurayin

Sunna karasawa suka sauka suka shiga ciki

Mamansu dake shanya hijab din yar yarinyarta ce ta dago tana dubansu ta ce" aa, me ya samu kishiyar ne haka take wantsala kuka tun daga waje?

Yayar Mardiya ta mikawa mamansu yarinyar ta zauna tana dan tabe bakinta ta ce" mama, anya kuwa Mardiya ba tana hada mu da y'ayan mijinta da kanwar mijinta dan ta kasance mai son kanta bane?

Da sauri Mardiya ta dubeta ta ce" wani irin ina hadaku da su?

Hararanta ta yi ta ce" kwarai kin ji abinda na fada! Mardiya du irin rashin mutuncin dake tsakaninki da yaren nan sai na ga da sauki tunda har zasu budi bakinsu su gaishe ki, sannan ke maimakun ki yi masu amsa irin ta uwa ko dan idannuwan mamansu sai kike wani binsu da harara
Ke dai kece mai neman fitinar a bayane domin ni dai ba fada min aka yi ba ni na raka ki

Mardiya ta zaburowa Nusaiba tana fadin" zaki min shiru ko sai na ci uwarki a nan yarinyar nan?

Yar ta yi shiru tana kwontar da kanta saman kirjin kakarta ta kai dubanta wajen yayarta da yannayin fada ta ce" malama kar ki wani fada min haka dan ke baki san abinda nake ciki ba!
Yanzu dai a gabanki zuwa muka yi zamu hau kujera aka hanna mu aka nuna mana kasa muka zauna
Sannan kina ganni mu muka buda baki muka fara gaisheta bayan mune ya dace ta gaisar! Da kike maganar yaran ba sai da ta harari katuwar guzumar ba sannan suka gaishe mu ba?

Itama idannuwan ta ruko mata ta ce" kin fa san bana tauye gaskiya ko a gaban waye, ba zan boye gaskiya dan kina kanwata ba
Me kike so? Ki hau kujera ki layu da Gimbiyar Damagaram? Uwar sarki ce fa Mardiya baki da hankali ne? Ke ki kasance da ita a waje dayama ai arzikin arziki kika ci! Kuma maganar kujera ba a kasa aka sauke mu ba, na lura wajen saukewar an dora mu mafi karamci ne a cikin waje uku ne
Da kike maganar sai da ta harari yara sannan suka gaishe ki inaga ashema da tarbiyarsu yaran dan har an isa a sakasu ko a hanna su duda kuna cikin haki na gaba da tsanar junna?
Ke ki rufawa kanki asiri ke kin san cewa Allah ya baki dama, na rantse da Allah da ace kin sada kanki da matar nan da na tabata kun samu kusanci da fahimtar junna yanda ya dace, da ke ya dace a je a yiwa gaisuwar nan ba wai na tirsasaki na kaiki mu yi dan zama mu tashi ba
Haba Mardiya, ke kin san waye mijinki, igiyar aure daya ta tsinke tsakaninku, ke kin san kafin ki shiga gidansa da manufarki ta yin hakan, kin shiga gidansa ne dan ki rama kwace maki saurayi da y'arsa ta yi, kin shiga ne dan ki muzanta rayuwarta ki hanna mata zaman lafia da kwonciyar hankali
Baki shiga dan ki haihu ba
Baki shiga dan ki jima da shi ba,
Da biye biyen abokansa suka shunna masa ke ya aura
Ke kin san kina cin ribar baba malan ne
Ki kiyaye Mardiya, ki kiyaye dan wannan kadai ya isa ya shaida maki cewar Allab na tare da shi, kwarai kina haye masa da izgili kala kala aman Allah ya hanna rabuwarku, ke kanki nan da ya sake ki saki daya a nan kika ringa zuba mana hauka sai da muka neme shi aka mayar da ke
Kin je kin saba da rayuwar gidansa idan kika ce zaki balo ki fito kece da shan wahala
Ki duba ki ga jikina, kwoncen kayan da kika bani ne aman ni kaina na zama abar kwatance a cikin sa'a dan kina bani su ina ketawa ina shiga cikin jama'a har fadi ake kanwarta ce ke auren MUTALAB fa, me kika rasa a gidanki? Mijinki ba ke ba ko mu idan ya tashi tsokanarsa zai sako mu gaba ne sai an sha wasa da daria,
Kudi sai dai ki ba wani
A wajen kwonciya ya gaza maki ko a me? Mardiya idanma muzgunawar ne fa kin masu , ya dace ki gane cewar kece da faduwa idan kika ci gaba da rayuwa a haka domin ko a irin yanda kansu ke hade zaki gane mai shiga tsakaninsu fa walahi ba dai mutun ba sai dai Allah!

Mardiya ta zauna tana hucin maganar yayarya bayan baki daya gaskiya ta fada mata

Sai a lokacin mamansu ta kawo kujerar zama irin tayani tsegumin nan ta zauna tana kallonta ta ce" ke kuwa, rashin wayo ne ko rashin hankali ke saka ki aikata abubuwan nan?
Jiya yayarki ke ce min wai kin yiea yaren iyaka da taba Yarinyar nan
Ashe baki da hankali? Ke din kin isheta tuwo da miya ne? Ke yau ace mijinki na raye har ta kai aure yaran nan suka fita a harkarku yaya zaki ji? Ko macen nan ta isa ta yiea yarki kayan daki idan kina da hankali ai y'ayan miji abin so ne abin a jawo a jiki ne domin baka san waye wane ba, koda baka kwadayin lada ai kana kwadayin duniyar tunda ita ta rufe maki ido har kike tafka iskancin nan
Mardiya zan fada maki, ba zan kuma barin yarana shiga fadanki na iskanci ba
Da ace kece da gaskiya kin san wacece ni ko ni ba zan yarda a wulakanta min ke ba, aman na lura dadi ne ya maki yawa kike ihun Allah ya kasheki ki huta
Bana son ki yi nadamar haka,
Aman kuma dahuwar mutun mai kosai

Ita dai sauraronsu kawai take, ita ita ta san me take ganni da yaren nan
Yaren dake tunanin ita tsararsu ce? Yaren dake kiran sunnanta kai tsaye?

Muryar yayarta dake idasa shanyar mamansu ta ji da haushi haushi tana fadin" wai wani ita ya dace ta gaishe mu, matar da idan haihuwa ne ta haife ki dan kawai kina auren yayanta kuma tana matsayin shugabar garinkima sai kawai ta wani gaishe ki? Ai da na rainata kennan, ke da ko bakinta ta buda ta ringa mana zuba ni sai na raina mata wayau!

..........................................

Tsuru ne ta yi sanye da hijab baki har kasa mai hannu ta saka Anmy a gaba tamkar ta fashe da kuka tana kallonta

Muryarta na rawa ta ce" Anmy mana, dan Allah a bar tafiar nan na yafe

Anmy ta juyo da mamaki tana kallonta ta ce" NAJEEBA, a kan me za'a bar tafia gannin likita bayan zuciyarki na maki suka? Mai martaba zai yi fitar boye dan dole sai ya ga wani bincike a tsaye a gaban idannuwansa dan bai yarda da kowa ba, gashi kuma clinik din daya ne zaku je shikenan da daren nan sai na barki ki tafi ke daya ko a fasa? Ki fita a idona na rufe ba za'a fasa ba kuma tare zaku je kima dauko alkyabarki dan kin san ba zaki bi shi haka daga ke sai hijab ba ko?


Gabanta ne ya kara tsinkewa ya yanke ya fadi har tana dafe gaban nata, ita? Ta shiga motar sarki? Ta zauna a ina? Wato ya makure mata wuya ya karya mata kai ya halakata ya kasheta dama abinda yake nema kennan ya ga ta mutu? Bama wannan ba, ita da zata je wajen cen dan ta yi neman magana ta hanyar samun kula alakar soyaya da mijin matar nan idan suka je aka yi mata binciken a gabansa aka shaida masa lafiyarta kalau yaya zasu kwashe?
Ita kam ta rasa meye aikin wannan jarababen! Idan ba jaraba ba ko abin aunawar ka nemi a kawo maka ai kawo maka shi za'a yi har dakinka na baci ka yi aune aunen aman shine zai wani je da kansa?

Fuskarta ta kara shagwabewa ta ce" Anmy, to ya bani sakon mana na yo masa ni, ko kuma ki ce da shi ya tafi kawai ni fa na warke

Anmy ta dago daga danna watar da take tana magana da mahaifiyar Najeebar kan Najeebar ne kuwa uwar na so ta hasko mata ita a hoto ta ganta aman ta rasa ta yanda zata daukar mata ita ta harareta ta ce"



















YAU NA YI DA YAWA=ØÞ[1/27, 7:59 PM] Ummu Suhan=Ø
Þ: >ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



19





Sai da Anmy ta harareta ta ce" NAJEEBA MUTALLAB, tashi ki dauko min alkyabarki

Najeeba ta kara turo bakinta ta mike jikinta a sanyaye ta dauko alkyabarta fara aman kuma adon baki ne ya fi yawa a jikinta ta saka sannan ta bade jikinta da turare ta dauki yan cenji da wayarta ta dawo falo

Jakadiyar dake duke ne ta shaifa mata cewa har sun fito ita suke jira

Kollan Anmy ta kuma yi, sai ta ga Anmy din ta dauketa hoto da wayarta tana dan murmushi ta ce" ki fan saki fuskarki mana kema an mata

Bakinta ta kara turawa gaba ta juya tana tafe a hankali tamkar wace kwai ya fashewa a ciki jakadiyar na biye a bayanta tana nuna mata inda zata bi din hanyar da zai bi ya fita ba budadiyar hanya bace

Gabanta banda faduwa ba abinda yake, har sai ta fara jin da gaske wani zazabi na son kamata da karfin gaske ba da wasa ba
Ita dai ta san ya tsaneta, duda bata san falilinsa na tsanar nata ba
Takan kama mugun kallo daga gareshi, harma da kallon da zata iya kiransa na kyama

Tun fa ta nuna mata motar sai ta ja ta tsaya kanta sade

Najeebarma ta tsaya tana kallonta, muryarta na dan rawa rawa ta ce " mu, mu je mana

Da sauri Jakadiyar ta dago, sai kuma ta mayar da kan nata tana dan girgiza kai ta ce" Allah ya huci zuciyarki amintacen sarki kadai ke shigowa wannan waje ko ZINARIYARMU bata taba saka kafarta a wannan hanya ba, domin hanyar boyayiyar fita ce ta sarki

Sai ta ji ta kara tsorata da bayannin jakariyar, hanyar boyayiyar fita? To a kan me za'a zo da ita nan? Ko dai a nan ne ya yi niyar kasheta ya huta?

Idannuwanta ta rintse tana jimke wayarta a hannunta
Najeeba mana, meye haka ne? Ki je, ki je kawai, ki yi tawakali da Allah, ba zai kasheki ba ......zuciyarta mai karfin ke karfafa mata gwuiwa, nan take matsoraciyar shawararta ta ce" aa, ki rubuta message ki bari a wayarki, idan aka ga kin bace shine! Dan mutumen nan shi kansa kama yake da aljannu!

Hannayenta na rawa ta fitar da wayar ta rubuta message ta yi seving a wayar nata sannan ta shiga karasawa jimin motar jikinta du a mace

Mutumen dake tsaye ne ya saka gabanta yankewa ya kara faduwa
Wani irin girma ne da mutumen tamkar wanda ya fi ka'idar tsayin dan adam
Gashi da wani irin jiki mai abin tsoro, fuskarsa kuwa zata rantse bai taba sallah ba dan ba annurin hasken sallah a tatare da ita ko daya!

Bude mata motar ya yi ba tare da ya furta ko A ba

Da sauri sauri ta daka dan tsale ta shige motar gabanta na faduwa ta zauna tana ta waige waigen tsoro

Wata kwalba ce ajiye saman kujerar daga tsakiya haka, kwalbar mai duhu ce sannan ga duhun cikin mota hakan ya saka sam bata gane ko meye a ciki ba
Cikin motar ba kowa sai wani irin sanyin AC din dake kunne da kuma wannan dadadan kamshin turaran nasa

Hannayenta ta dora saman cinyarta ta jingina da jikin kujerar ta saki wawuyar ajiyar zuciya da tarin sarewar dake adabarta
A hankali ta ringa furta kalamai kamar haka" ke kuwa ta haka zaki mutu ashe Najeeba? Koba motar zai yi ya ce na yi hatsari ko wannan katon zai saka ya dane min hanci sai na daina motsi? Wayo su auntyna zaku yi rashina, wayo yayana kana ina? Yau du ban ganka ba kuma ban nemeka ba, yayana ka yafe min irin rashin jin da nake maka
Wayo Anmyna ki gafarta min ba zan kuma yin karyar ciwo ba kin ji?
Ya Allahna ka bani ikon mutuwa da kalmatus shahada ,
Allah ka yafe min laifukana ka rufa min asiri

A kadan ta dauki wasu mintina talatin gaba daya ta gama hada zufa ta gama ficewa a hayacinta harda yar kwalarta, jira ai ko na result din exam bashi da dadi bale jiran kila wa kala za'a kasheka ne ko za'a wujijigaka a yarda banza? A yan sekwanin sai ta samu kanta da wata irin nadamar rayuwa,
Yo ita me ta masa?
Duk irin sufanta shi da take da abubuwan da ba su ba sai ta ringa fadin" wasa ne, ban taba tunanin hakan a cen cikin zuciyata ba, na tabata kai ha barawo bane kar ka kasheni ka rufa min asiri

Bude gefen damar da aka yi, da murya kasa kasa ana fadin" takawa sannu sannu dan sarki jikan sarki, takawa sannu sannu mai damagaram ikon Allah, gabanka haske, bayanka haske d'a daya kake mai ja da arne

Kamshin turaran nasa da ya fara shigowa motar mai yawan gaske ya sakata sauri kara buda idannuwanta sannan ta rabu da jikin kujerar ta yi gagawar gyara zamanta ta nutsu ta sada kanta tamkar wace ta zo makaranta

Kafin ya daga kafarsa ya shiga motar ya jima kamar wanda zai hau mahaukacin doki
Shigowa ya yi cikin motar ya yi wani irin zama irin na hamshaki sannan aka mayar da marfin aka rufe

Mutane biyun nan sune suka shiga cikin motar , gabjejen nan shine amintacen sarkin shi ya ja motar a hankali sai wanda ke dan kurarin a gefensa rike da abubuwan makamai kamar wanda zai yi artabu da mugun abu a gabansa

Kwalbar nan dake ajiye wace ta gaje wajen harma tana gogar jikinta ya dora fari kar din hannunsa mai dauke da jijiyoyi a jikinsa manyan gaske ya bude marfin kwalbar

Hannunsa ya zirawa safar hannu ya saka cikin bakin kwalbar ya janyo abinda ke ciki

Wani irin kuuuuuu da cikin Najeeba ya yi a lokacin da wutsiyar macijin ta dan hau gefen cinyarta har tana wani irin yawo da dan karfi tana neman a saketa

Wuyansa ya rike raf sannan ya dan gyara muryarsa kasa kasa sosai ya ce" *bani matacen*


Da wani irin gagawa na gefen direban ya buda wata kwalbar, ashe ita kuwa tana dauke da abin sanyi ne wanda zai hanna macijin rubewa ya yi tsami ya lalace ba tare da an yi binciken da ake son yi da shi ba

Amsa ya yi ya dago kansa ya daidaita da mai ran

Irin yanda yake dilo harshensa yana yi masa tamkar giftawar mashi ya sakata sakin wata wawuyar ajiyar zuciya gaba daya jikinta ya dauki rawa
Irin yanda ya rike macizan a hannayensa sai shi kansa ya zama wani abin tsoron a gabanta

Kamar mai cutar asthma haka ta ringa jin numfashinta na yi mata rawa

Kallon macijin yake kallo irin na tsanaki
Sai da ya gama a kasalance sannan a gajarce ya ce" *aman yaya aka yi shi wannan yake da kiftu a gefen kansa dayan kuwa bashi da shi?*


Allah ya huci zuciyarka wannan kiftu da kake ganni shine kawai abinda ke bambance macizan da aka kyankyashe a rana daya
Shi kiftun nan kala biyar ne,
Irin wannan dan siririn shi ya kara shaida min cewa shine abokin haihuwarsa sannan kalarsa ne tak tak , du abinda wancen zai yi wannanma yana iya yinsa, Allah ya kara maka lafiya
Ya karashe yana dan kara dukawa

Bai kuma yin magana ba sai mika masa matacen sa ya yi ya karba da hannu bibiyu yana gagawar mayar da shi cikin kwalbarsa, sannan ya kara dago mai ran yana yi masa kallo irin na kurullah

Tabas idan a da wasa ta yi karya ta yi cewar zuciyarta na suka a yanzun kam sukar take, gaba daya jikinta ya mace ya yi mata nauyi har bata iya daga dan yatsarta
Idannuwanta kawai take yawo da su a kansa ta yi wani kasangar tana hangen gashi har ya sakar mata macijin ya kasheta
Aman dan me yake son kasheni da maciji? Ya kasheni da hannayensa mana?

Take tambayar kanta a kasan zuciyarta ga zufa ta gama wanke mata duban wani waje na jikinta

Wutsiyarsa ya kara dokawa a saman cinyarta yana neman a sake shi ya kwaci kansa, irin yanda maciji ke wutsil wutsil dan kwatar kansa
Hakan ya saka ta saki ajiyar zuciyar da ta kara sakata jin tamkar cutar nan mai shanyewa mutun jiki ya zama baya jin yana iya anfanar da komai na jikinsa da kansa ne ya sameta wato cutar hawan jinni da ilolinta

Sai da suka yi tafia mai dan nisa suka samu wani waje mai dan duhu duhu sannan direban ya taka birki ya tsaya

Wani shirun ne ya biyo baya na kamar minti goma,
NAJEEBA ta ringa maimaita kalmar shahada daga yannayin da take dan ta dauka an zo wajen da za'a kashetan ne

Gannin yanda take wani ringeshe a cikin motarsa ya kara bata masa rai, me ya sa Anmy ke yi masa haka ne? Yau da ace cikin kannenta ko yayunta ne bashi da damuwa sai ya fita da su a cikin motarsa da su din ya yarda da su cewar koda basa jin magana to fa basu wulakanta kansu ba
Aman sai ta saka shi daukota a motarsa mai tsafta, ta shigo masa mota tana garwaya numfashinta da nasa mai tsafta haka kawai ta zauna a wajen da yake ringesa kansa dan ya huta?
Ya zama wajibi ya batar da motar nan sunna dawowa domin ba zai kuma shigarta ba
Da ta san irin yanda yake kyankyaminta, da bata yi gigin yarda ta shiga wajen da yake ba
Halayenta sam basu yi masa ba
Muguwa ce, azaluma ce, makaryaciya ce, mazinaciya ce!
Idanma bashi da tabas shi zai samowa Anmy shaidar da ba zata iya hanna shi hukuntata a bainar nasi ba! Ya yiwa kansa alkawarin a kanta zai tsoratar da matasan samari da matasan yan mata da manyan yan iskan garinsa domin sai ya yi mata hukunci bulalar da ta hau kanta na zina da aurenta komai yawanta shi yasa yake so ya yi mata damka irin na gani da gani

Muryarsa a dake ya ce" *ki fitar min a mota!*

Maganar nasa rairai a cikin kunnayenta domin dama sauraro take

Dan zabura ta yi ta dago tana ta zarar ido

Amintacensa ne ya fita dan bude mata bangarenta domun dama bai hude bane dan yana jiran umarni

Yana budewa SHAheed ya watsa mata damin kudi a jikinta muryarsa still a dake ya ce" *nan da awa biyu ki tabata mun sameki a nan*

Yana gama fada ya kuma komawa ya gyara zamansa

Ai da wani irin sauri ta fita a motar da kudin a hannunta dan a saman cinyarta suke, ita a yanzu bata da bakin da zata iya budawa ta ce wani abu ko ta meni yin wani abu na rashin kunya


Tana fita ya mayar da mitar ya rufe ya zagaya da sauri ya shige suka daga

Gaba dayanta ta idasa zaro idannuwanta ta dora hannayenta saman kanta a fili ta furta" wayo wayo wayo innalilahi wa'ina ilaihi raj'une yau na ga masifa ido da ido yau na yi mota daya da arne marar mutunci marar tausayi mai cin danyen nama! Na rantse macijin nan ka fito da shi ne dan ka je ka kashe wani, yo waye bai sani ba cewa kashe kashe kuke a tsakaninku dan kujerar nan da kuke sama
Allah ya isana da ka tsoratani, kuma na rantse sai ka sauka sarki mai adalci ya hau kujerar nan annamimi mai ido kamar na mujiya!

Sai a lokacin ta kalli kudin da ya zuba mata
Dami guda ne na manyan kudi sabin bugawa domin yanda suke mike suke hade zai nuna maka cewa sababin fitowa ne daga banki yan jika goma goma je da zara iya rantsewa ba karamin kudi bane

Abin dake jikinsu ta kunce ta watsar a nan sannan ta bi su da yawu tana cire alkyabar nan da ta hana mata sukuni tana ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Allah ya tsareni da cin haram! Kai ko abincin fada ina cin wanda na san Anmy ta bada kudin aka kawo domin ban taba cin cimar da ta shafi shinkafa, ko wani abin da na san daga aljihunka zai iya fitowa!
Yanda ka tsane ni, ni nama fika tsanarka azalumi kawai mai cinye kudadenmu mu talakawa

Ta saman kudin ta bi tana tafiyarya da dan sauri dan a lokacin da ta duba agogon hannunta har ta ci minti goma a kan wanda ya barta

Saloon dinta ta je suka gagaisa da masu yi mata aiki sannan ta kara duduba komai ta ware kudadenta ta bara masu na anfannin yau da gobe kafin ta dawo nan da kwana hudu

Daga nan sai ta nemi mai babur ta dane tace da shi ya kaira wajen Hashimu mai nama

Agashe ta bashi ya amso mata mai ruwa ruwa har na jaka biyar tukunya ce sannan ta suka kuma daukowa suka nufi wajen saida ice cream

Haka take murmushi gannin yau zata sha mutumen nata wato ice cream dan ta kwana biyu bata sha ba domin Anmy bata barinsu yawan shan sanyin nan ko zaki

Siya ta yi har roba biyu tace da shi ya kaita stade

Yana ajiyeta ta dauki har jaka biyu ta bashi sannan ta ringa takawa a hankali a kafarta har ta karaso wajen mai gadin wajen suka gaisa da mutunci sannan ta samu ta shige cikin nutsuwa ta nufi wajen zamanta wajen hutunta

Tana zuwa ta zauna tana gannin yanda daidaikun mutane kowa ke sha'anninsa, a wajenfa babu yaku bayi, du manya ne kowa kuma na sha'aninsa

Ledarta ta buda mai dauke da naman nan ta fara ci a hankali tana lumshe idannuwanta dan tana mutuwar son tukunya

Sai da ta ji ta yi hani'an sannan ta dauko ice cream dinta roba daya ta buda
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment