Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kike masu cewa kin fi baki daya iyayensu jimawa da ni zai zo karshe
Walahi bana hada y'ayana da kowa!

.............................................

Kai kawon da yake ya fi a kirga, hankalinsa a matukar tashe, ransa sai suya yake yana kara gwada number da ta dora masa

Wayar ya wurga jikin bango yana dafe kansa

Yaronsa dake nemo masa mata ne ya yi gagawar zuwa ya dauko wayar yana kallon ogan nasa da tarin tambaya da kuma mamakin irin budurwar nan da ta dauki hankalin ogansa har haka

Da sauri ya ce" oga, ka yi hakuri ka kwatanta min kamaninta, ni kuwa zan bazama na samo maka ita koma yar waye na kawo maka ita ko na kawo maka numberta na gaskiya dan da dukan alamu ba numberta bane ta baka dan ana fadin number nan babuma ita wato ba'a dorata daidai ba

Sai da ya sauke huci ya dago kafcecen bakin hannunsa ya ce" isa, yarinyar idan ka ganta tama dauke da idannuwan mage
Ka san yaya idannuwan mage suke? Sunna da girma da wani irin lu.u lu.u a cikinsu wanda idan har ka shagala zaka iya zubar da salabe tsabar kyansu da dukan zuciyarsu
Bakinta madaidaici ne, lebenta na kasa ya dan fi na sama girma sannan lebenta yanda ka ga ruwan kasa haka yake yana sheki kamar wani diamonds
Fuskarta yar doguwa ce, mai dauke da gashin gira wadatace wanda yake gyare kamar na yar tsana
Hancinta dogo ne sosai sannan da dan fadinsa kadan
Gashinn idannuwanta dogaye ne sannan bakake ne sidik ga cika wa'inda suka karawa fuskar nata wani irin kyau da haske
Gashin kanta wanda ya leko sosai ta kasan dan kwalinta baki ne sidik yana wani irin kyalkyali
Wani kanshi da take shi ya kara fuzgata zuwa gareta
A zaune take a cikin mota ba zan iya fadin yannayin jikinta ba aman abinda na sani ta tara hips domin irin yanda cinyoyinta suka baje a cikin bakar doguwar rigar dake jikinta
Fatarta kalar bak'a ce, bakin nan mai hasken gaske, ta shafa mai mai dan maski wanda ya saka fatar nata yin wani mus mus tana kara fitar da sirrin kyanta

Da mamaki ya ce" oga bak'ar mace fa kace? Aman oga ina ce ka tsani bak'ar fata domin ka sha fadin kai ko haukacewa ka yi ba abinda zaka ci da bakar mace dan ba zaka iya kayan haushi ba

Murmushi yana girgiza kansa ya ce" to ka dauka na sheka maka karya a wancen karon, ka dauka du da nake fadin hakan ban hadu da ainahin mace bak'a wace ta san darajar bakinta harma ta saka min sha'awarsa daga kallo daya
Ka dauka cewa wannan yarinyar ko nawa zan biya dan ta zama malakina zan iya biya
Ba soyayar shan minti ko na dare daya nake so da ita ba
So nake na kawota gidana ta sama min iri irinta na hada da jajayen buzayena na cika gidana da jarina

Shiru ya yi yana tunanin irin kukan shagwabar da ta dan sakar masa hakan ya sa tsigar jikinsa baki daya tashi da karfi karfi ya ce" rashin bani cikaken numberta kuwa ya nuna min cewa ita din mai tsada ce, kuma na yarda na siya

Shi dai baki daya ogan nasa yau ya rikita shi, dan haka ya ce" Oga na ji kace a mota take ko? Wace irin mota ce?

Juyowa ya yi ya ce" hilux ce baka sidik, sabuwa ce mai number Nigeria dan ko awo bata mata ba

Da sauri ya kale shi, ido ya zaro ya ce" Oga, ko dai *NAJEEBA* kake magana a kai?

Ogan nasa ya ce" wacece haka?

Ya ce" Najeeba mai saloon NAJEEBA MUTALAB, wannan baban saloon din da ake magana baki daya garin nan
Da kace mota baka Hilux sabuwa na tuna ba'a yi sati biyu ba da zakariya ke fadin ta dauko sabuwa domin budurwar uban gidansa ce

Da sauri ya ce" kana nufin yarinyar da na gama zana maka ce budurwar csp Jibril?

Da sauro ya ce" oga ai idan dai *NAJEEBA* ce, ita da kanta *MAGE BA, MAI KWONCIYAR DAUKAN RAI* wannan shine kirarinta
Budurwar juju isma'il ce,
Budurwar Elhaj razak ce wannan baban dan kasuwan

Shiru ya yi sakamakon irin yanda ogan nasa ke kokarin bige shi

Bakinsa mai dauke da hakora mai tsawargna ya hade da kishin NAJEEBA cikin zuciyarsa ya ce" kana nufin yar hannu ce? To koma yar hannu ce ni zan kwasheta
Ai allura ce cikin ruwa
Ka je ka samo min asalin numberta ni kuwa zan nuna masu su kauce idan basa iyawa

Wata daria ya yi ya ce" zan yi mata bulala da tarin kudina
Zan wanketa wankin da zai haukatata
Zan gabatar mata da maganar aure na shinfide mata sadakin millions goma
Zata gigice ne ta amshi aurena ta kawo kanta dakina

Da sauri ya juya ya fita , shifa nan take ya ji tausayin ogan nasa ya kama shi
Sai kuma ya daga kafadunsa yana fadin" mai yiwuwa y'ayan mutane da kake lalatawa ne kaima zaka hadu da ciwon zuciyarka, dan na tabata baka taba haduwa da mai wanke aljihunka a lokacin da kai kanka baka ankara ba sai yanzun dan tas zata cinye maka tanadinka


Wuni ya yi yana yawo yana bin kama daga yan matan garin masu ji da kansu har zuwa yan daudu
Aman du wace ta santama bata bada number sai dai ta fada masa ya je ya amsa

Cike da gajiya ya dawo yana tunanin yanda zai yi

Yama na yi ya shirya da wuri ya fita wajen gudu, wajen da ake basket ball, da hand ball, da dai sauransu

Ya jima zaune, harma an fara buga kwallon har an tafi sallar magariba an dawo
Har ya cire rai da zuwanta sai hango bak'ar motarta ya yi ta danni kai

Hamdallah ya yi ya kara gyara zamansa

Daga cikin motar bayan ta kashe ta ziro kafarta guda

A hankali ta ziro dayar kafafuwanta dauke da wani takalmin basket fari tas mai nike ja
Kana gannin takalmin ka san babar harka ne zai kai dubu tamanin a kadan

Karasa fitowa ta yi daga cikin motar hannunta dauke da ball dinta ta rufe marfin ta shiga takawa

Yawancin samari da kuma yan matan wajen sun bada hankakinsu kanta wasun kuwa satar kallonta suke
Da yawa samarin sunna jin inama ace budurwarsu ce?
Wasun kuwa sunna mangarin irin kayanta na sport wa'inda ko wace rana zata zo da sabin yayi masu motsi
Da yawan yan matan wajen sunna mangarin irin yanda idan ta saka kaya ke mata kyau, wasu na son yin kawance da ita wasu kuwa na matukar jin haushinta da kishinta duba da irin yanda take dauke hankalin manyan mazan dake wajen manyan ma'aikatan dake fitowa motsa jiki da yawansu sum girmeta girma ba na wasa ba aman kuma ta fi su farin jinni
Idan kudin ne akoy wa'inda suka dameta suka shanye aman an fi hangota kansu

Da tarin nutsuwa ta karasa jikinta sanye da dogon wando wanda ya kama duwawunta dan irin girmansu sai dai ya saki daga kasa
Sai rigarta ta gudu mai dogon hannu wace tana zuwa ta cireta sai ta kasa ja wace ke dauke da karamin hannu

Baki daya kalar fatarta iri daya ce kama daga wuyanta, fuskarta, hamatarta idan ta daga dan amsar ball din a aske tas kuma ba wani baki kirin ko yannayi mai nuna rashin kula tas tas tas haka take

A hankali ta shiga gudu dan ka'idane idan ka zo sai ka zagaya terrain din sau hamsin kafin a raba da kai a hau buga basket din

Tana gudun ne tana dan buga hannunta da du wanda ta tarda dan gaisuwar ne haka, sai dai idan ta tardo namiji bata hade hannunta da shi sai dai ta daga masa hannun kamar zasu hade sai ta wayance ta kauce tana daria

Sai da ta gama aka raba da ita ta hau saman filin basket din

Sun kora da bugawa, ball din na hannunta tana gudu tana dokata da kasa ball din na dawowa tana neman wanda zata ba kawai sai ji ta yi an rukunkumeta daga bayanta wanda sam ba haka a basket idanma amsar ball ne zaka yi sai dai ka tinkari mutun idan ka yi sa'a ka amshe halas idan kuwa ka kasa wani ya kuma tarbansa ko ta gefen mutun aman sai gashin an rukunkumeta kuma namiji ne domin daga hannunsa da irin rikon da kuma warin zufar da yake ya shaida mata hakan

Da wani irin firgici ta saki ball din, tana juyowa ga mamakinta dan wajensu ne bama dan dayan bangaren bane
Wato ya yi haka da gaya ko?

Ranta ne ya yi kololuear baci duba da yau itace wannan bakon ba'adaren ya tabawa jiki harda kwonto mata a jikinta ya dora hannunsa afatar jikinta harma saman hannunsa ya goge kasan mamanta

Baki daya jikinta ne ya dauki rawa....ka ku manta NAJEEBA nada rashin ji, aman fa ba ta inda ake zato ba

Ba zato ba tsamani ta daga hannunta ta.......









>ØÕÝ>ØÕÝ>ØÕÝ>ØÕÝ>ØÕÝ>ØÕÝ>ØÕÝ>ØÕÝ
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



6





Ba zato ba tsamani ta daga hannunta ta sauke saman fuskar garjejen ba'adaren da ya rungumota jikinsa

Bako ne, shi bako ne sannan dan baba da rai ne
Ya saba life, yana gannin NAJEEBA ya yi tunanin yar life din ce hakan ya sa ya fara isar da sakonsa ta haka dan ta gane ta yi sabon kamu
Sai dai abinda ko ubansa bai taba yi masa ba ya ziyarce shi a lokacin da bai shirya ba

Idannuwansa ya waro da karfi da mamaki wanda sakamakon marin ya saka baki daya hankali ya yo kansu

Bata taba tunani ba, bata taba shiryawa ba sai ta yi ya daga dafkekiyar kafarsa ya daga mata bugu a cikinta

Wata irin razananiya kara ta saki kafin ta tafi luuuuuuu a sume

Gaba daya wajen hautsinewa ya yi ya hargitse

Zaratan mazan dake son malakarta suka hayayako inda zaratan yan matan dake hasada da ita suke kokarin tare masa

Shima cike da sangarta ya kara fitar da idannuwansa yana fadin" ni bani da rai da ta mare ni ne?

Da wani irin sauri wani baban soja dake wajen Captain ne ya daka tsawar da ta saka du suka fara shiga taitayinsu harma wasu suka shiga silalewa dan kar abinda basu taka ba su kwashe

Hannawa ya yi a tabata, ya kirayi ambulance sannan ya tsare wanda ya yi dukan ya yi kiran police dan shi soja ne baya kamu sai police

Nan fa wajen ya hargitse aka shiga yada maganar ta waya da kuma wa'inda suka rigaya suka silale

A lokacin DAYABU na zaune a katon falon SARKI , sun gama cin dadadan abincin da aka gabatar masu , ya kwontar da muryarsa yana kokarin kara bashi hakuri kan ya manta marin da NAJEEBA ta yiwa Zinariya

Sai da ya surbi lipton din da aka hada masa mai dauke da lemun tsami da na.a na.a sai turiri da kanshi yake kafin ya kale shi

A hankali ya ce" kana nufin na manta, na yi kamar ba'a yi ba?


Da sauri DAYABU ya gyada kansa ya ce" mun mata fada sosai, ita da kanta ta yi nadama, tana kuma bada hakuri sosai

Bakinsa da ya dan leko dan shan lipton din ya dan tabe ya yi dan murmushi sai da ya jima sannan cikin magana kasa kasa sosai da ba dan yana sauraronsa sosai ba da ba zai ji ya ce" to ta zo ta duka ta baiwa Zinariya hakuri

Kallonsa DAYABU yake, lokaci daya kuma yana tunanin maganar , yana shirin yin wata maganar wayarsa ta shiga vibrating a aljihunsa

Da sauri ya saka hannunsa ya lalubo ya fitar yana duba wanda ya yi kiran

Gannin sunnan abokinsa ne ya saka shi dagawa

Abinda ya fada ne ya saka shi zabura ya tsaya, a tsorace ya ce" what? Yaushe? Ita da wa? Me ta masa? Ina take?

Dukan tambayoyin nan a tare ya jero su kuma hankalinsa tashe hakan ya saka SHAHEED kafeshi da idannuwansa masu kalar na zaki yana kallonsa

Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une ya fada hankalinsa tashe yana fadin" gani nan tafe

Da sauri ya kashe kiran ya juyo wajen SHAHEED dake dubansa da duba irin na tambayar meye

Hankalinsa tashe ya ce" NANANAJJEEBA ce , sukai fada da wani ya daketa a ciki a wajen sports, yanzu haka dai an tafi asibiti da ita a summe

Irin duban da ya yi masa , ba tare da ya nuna alamun zai tanka ko zai tayar da hankalinsa a kan lamarin NAJEEBAR ba ya saka DAYABU dubansa da duba irin na haba dan uwa

Dan zamewa ya yi ya zauna yana kallonsa ya ce" haba SHAHEED maimakun ka zabura ka tashi ka bada umarnin a fitar da motar sirri a ja mu je ka ga yar uwarka sai ka yi min duba irin na tamkar an daki makiyiyarka ko tankawa ba zaka yi ba?

Duban da yake masa dai ne bai daina ba, hakan ya sa DAYABU mikewa ya kara kallonsa ya girgiza kansa a hankali ya ce" da hakuri, da kawar da kai, da adalci aka san saraki, sannan basa bambanci a kan kowa, sukan talabi mai ji da marar ji, sukan yi yafiya a kan kowa
Sasautawa ya yi ya ce" ban san me yasa taurinka ya tsaurara a kan yar uwarka ba

Sada kansa ya yi ya ce" Allah ya huci zuciyar sarkina, a huta lafiya

Yana gama fada ya juya da mugun sauri har kamar ya kifa ya fice daga fallon wanda dogarai ke tsaitsaye a kofa sunna gannin fitowarsa suka shiga yi masa fatan alkhairi da adu'ar sauka lafiya

Sai da ya ga tafiarsa sannan ya lumshe idannuwansa, tun da ya lumshe bai kuma budewa ba sai ajiyar zuciya da yake saukewa a hankali ya afka duniyar tunani


A firgice ya karasa asibitin
Sai dai abinda ya bashi mamaki ya kuma dakatar da shi kafin ya shige shine gannin docter Jibril da kuma mala'ika wato baban sojan da NAJEEBA ta baiwa banzar number a hanyarta na dawowa sunna tsaye kowane na muzurai

Ganninsa ya saka su saurin tarbo shi sunna kokarin rige rigen gaishe shi

Fuska hade sojan ya ce" ai na hana kowa shiga sai na kusa da ita, ta farka kuma wanda ya daketan yana hannunmu ko uban waye ubansa sai ya amsa laifinsa na dukan matana!

Doctern ya kale shi da sauri da mamakin matarsa kuma?

Shima a matsayinsa na docter ya matso ya ce" barka da karasowa yaya, Alhamdulilah ana kawota na saka manyan docters abokannan aikinmu sun yi mata dukan kulawar da ya dace
Yanzu haka maganar da nake maka ta farfado cikin hankalinta, sakamakon dukan ya mata a cikinta wanda take nisawa kuwa mun saka a yi mata dukan gwaje gwaje, ka san dare ya yi du an tashi da aikin gwaje gwaje aman da yake asibitin tamu ce ita kuwa matar docter ce ya saka har gadonta aka ringa turo kayan aiki ana aunata yanzu haka dai ana iya tafia da ita gida dan ta fada min bata son kwana a asibiti bata san irin halin da yan uwanta zasu kasance ba ya sa na bada damar a tafi da ita gida ko mu bada sabuwar ambulance a kaita har kifar dakinta

Wata uwar harara sojan ya watsa masa
Shima ya yi masa wani kallo irin na shiga gabankan nan

Murmushi DAYABU ya yi yana kallonsu daya bayan dayan kafin a hankali ya ce" Allah ya saka da alkhairi

Ba'a hana shi shiga ba domin docter na tare da shi
Sunna shiga ya karasa da sauri wajen bed din da take kwonce idannuwanta lumshe gashin idon da ta saka sun yi mata luf luf sun kara girman idannuwan nata
Lebenta kuwa du azabar da ta sha yana dauke da kalarsa na pink color iya na kasan na saman kuwa da dan duhunsa

Karasawa ya yi da sauri yana yaye abin rufar da aka rufa mata har daidai kirjinta yana talabota

Nan danan tabararta ta tashi, shagwabarta ta motsa ta langwabe masa ta saki kukan shagwaba tana kara langwabe masa
Cikin zazakar muryarta take fadin" ya, cikina, a cikina ya dakeni bayan shine da laifi haka kawai ya taba min cikina da hannunsa dan na mare shi ya dakan kafarsa a cikina

A hankali ya kara riketa ya ce" NAJEEBA, sannu, sannu kin ji?

Kuma langwabewa ta yi tana wani irin far da idannuwanta ta ce" ba zan iya yafe masa ba

Kansa yake gyadawa kafin ya bata amsa muryar sojan nan ta daki kunnayensu yana fadin" ni kaina ba zan iya yafe masa ba tunda ya taba min kafiarki, ashema shine marar gaskiyan? Ya dauka jikin ki abin banza ne da kowani banza zai iya tabawa?

Likitan ya kale shi da sauri, sai ya girgiza kansa ya juyo yana kallonta
Har kasan zuciyarsa yake jin kishinta sannan baya so ko da wasa ace tana son wani fiye da shi
Shifa sonta yake kuma ba son a watse ba
Gannin hankalinta ba a kwonce ba ya saka shi yin hakuri ya shanye kishinsa ya kara dudubata ya rubuta magungunnan da zasu kara kwontar mata da ciwon cikin da take ji ya fita da sauri ya bada a amso masa a cikin asibitin kafin ya zo da kansa su kamata da likita daya su dorata kan gadon marar lafia na turawa a tura gadon har wajen ambulance aka daga aka sakata dan tsabar gata ba dan bata iya tafia ba

Sai da ta ga da gaske ciki aka sakata ya saka ta mike zaune tana yatsina fuskarta ta kalli yayanta dake ta aikin jera mata sannu hankalinsa a matukar tashe

A hankali ta ce" ya, da sauki fa ni kar a kaini a cikin ambulance din nan hankalin Abih ya tashi, duda yanzu ya tsane mu

Murmushi ya yi ya kamata ta sauko daga bayan a hankali yana rike da ita suka karasa wajen motarsa ya buda baya ya sakata sai kokarin riketa suke son yi shi kuwa yana tarewa ta kwonta a bayan sannan ya juya ya amshi magungunnan da aka kawo

Kudi ya ciro a aljihunsa masu yawa ya mikawa likitan

Da mamaki ya girgiza kansa ya ce sam shi ba zai karba ba

DAYABU ya dube shi da kallo irin na yana son ya fahimce shi ya ce" ka yi hakuri, ni ina matsayin tamkar uba ne a wajenta
Da sanina, ba zan yarda wani ya yi dawainiya da lafiar kanwata wace na raina bayan na san ba'ai maku baiko ba
Alhamdulilah in dai inada rufin asiri zan yi iya yina a kan rayuwar kanaina
Ba mayar da kyauta ko kyautatawarka na yi ba
Ba raina maka na yi ba
Hasalima na ji dadin irin kulawar da kuka bata baki daya
Sai dai ka sani hidimar tsakaninku na soyayarku daban wanda ko shi da zata ji maganana ba zata amshi kudin saurayinta ba har sai ya zama miji a gareta
Sai dai zamani ya zo mana da abubuwa daban daban, a yanzu dan saurayi na yiwa budurwarsa hidima ba wani abin bane, hasalima shi ke kara aminci tsakaninsu
Sai dai ba zai kai har fannin lafiarta ko cimar da zara ci ba
Ka yi hakuri ka amshi wannan a je a cike dukan abinda ya dace a cike

Murmushi sojan nan ya yi da jin dadin abin a ganninsa an wulakanta likitan da ya bi ya kanainaye masa waje run dazu ya ce" aa yayanmu, ai kawai ka mayar da kudadenka, shima ba shi zai biya ba, wanda ya daketa shi zai biya komai dan shine da laifi shi ya fara shiga huruminta har ta mare shi

Ita dai idannuwanta ta lumshe tana jin haushin ubanda ya fadawa malaikan nan cewa tana asibiti
Lale ta fara yarda cewa an saka mata ido a garin nan
Idannuwanta ta kuma budewa ta kalle shi
Bakinta ta tabe a ranta ta ayanna" anya kuwa yana sallah? Yo sam ba annuri a tatare da fuskarsa sai duhu da warin baki!

Jin haka ya sa shima likitan sauke ajiyar zuciya domin shi dai ba zai karbi kudin nan a gabanta ba, haba shi da yake so ya yi mata wanka da kudi ta yanda sai shi

Shima sojan murmushin da yake yi yana ayanna ina zan yarda ka yi bajinta ka biya bayan na zo ne na rufe baki daya bakin yan gidansu da shagun? Ai zan saki bakin aljihunna na wankesu da yayan banki ta yanda zasu miko min yar koda ba fatiya na je na kara buda rigar nan nata na kali na cikin rigar nan dake hararena da kyau

Salama DAYABU ya yi masu bayan ya yiwa sauran likitocin da kuma masu tsaron kofar urgence din alkhairi wanda suka ji dadi sosai harma suka shiga bayanin ko shi waye cewar yan uwan sarki ne fa, kowa kuma ya san waye sarkin wanda idan ka samu kadaicewa da shi ka warke da izinin Allah

Sunna zuwa gida tun a hanya ya yi waya cewar a kawo masu Burger adadin da ya san zasu koshi kafin ya karasa shiga da motar

Talabeta ya yi a jikinsa har suka karasa shiga cikin falonsu sai kara kwontawa take tana raki tana rigima shi kuwa sai sannu yake mata tamkar ya fashe da kuka

Sunna shiga hankalin yan uwanta dake zaune ga abinci da yawa sun kasa ci sakamakon jin shiru yayunsu uku basu dawo ba wato DAYABU, NAJEEBA, DA ZAHRAU

Gannin Najeeba langwabe tana kara sakin kukan tabara ya saka su tashi a firgice sunna rige rigen karasowa wajensu

Hankalinsu tashe suke tambayar me ya sameta, ahin ko accident ta yi? Ita kuwa sai kara lafewa take a saman kujera baba ta ki amsawa

Abincin da aka kawo ya kalla
Bakinsa ya tabe ya tambayi ummu kamar haka" ke ummu wa ya kawo abincin nan?

Sai da ta tabe bakinta itama ta ce" mai gidan ce ta kawo

Bai ce komai ba sai zama da ya yi ya shiga balo maganin Najeeba ya amshi ruwan da Bilkissu ta dauko ya bale ya mika mata

Fuskarta ta yiwa takwaf takwaf hakan ya saka shi fadin" Najee, kin ga ki amshi magannin nan walahi idan kuwa ba haka ba zan dura maki shi katuwar banza kina yin amai kuma zan kara maki wani

Rauda ta ce" ya wai me ya sameta ne? Ko ciwon cikin ne? Na ga kuma ai ba karshen wata bane

Yayansu ya ce" a wajen basket aka daketa ta summa

Ido du suka zaro kafin karaminsu mai shekara bakwai ya bushe da daria ya ce" yaya an rama min dungure min kan da ta yi a school

Hararansa ta yi ta ce" NAJEEB zan wanka maka mari

Da tausayi kulsumu ta zauna gefenta tana dafa gefen wuyanta ta ce" wani dan iskan ne ya dakar min ke bayan ba'a dukan min kanwata

Langwabewa ta yi a jikinta ta saki shashekar kuka ta ce" bako ne, kuma walahi na daku baki ji yanda har yanzu nake juwa ba, ya kashe min kwayayen haihuwa

Khairy ta kai hannunta ta buge mata baki ta ce" shegiyar banza mai mugun fata, idan ya kashe maki kwayayen haihuwa ni ba sai na rike mar makogwaro ba?

Yayansu da ya shigo da manyan ledojin burger ya ajiye inda yaran suka fara tsale, sufa a dasha dan du idan manyan sukai fushi haka ake koda yaushe zasu ringa cin dadi ne, duda na gidansuma mai dadin ne aman kun san irin gashin nan na waje mai tonka akoy motsa kunne (aminiya kawar arziki maman jaririna ga kaza>Ø#Ý>Ø#Ý>Ø#Ý)


Dubansa ya kai wajen magannin gannin bata sha ba ya saka shi yin wajen da sauri da niyar dauka ya dura matan

Sai dai bai kai ga karasawa ba Zahrau ta shigo da gudu tana kuka sama sama tamkar ranta zai fita

NAJEEBA dake langwabewa tana kamar ba zata iya tafia ba tana raki ita ta fara zabura ta yi wajenta hankali tashe

Baki daya suka zagayeta sunna tambayarta meye ita da, wa ya mutu, me aka yi take kuka?

Cikin wani irin kuka tamkar zata sike ta budi bakinta ta ce" *wai wai wai an fasa aurena*

Ta karsashe tana mai kife kanta a kirjin NAJEEBAR da ta fara karasowa sannan ta fi kusanci da ita a durkuahen da take






Shin kuna so? Idan kuna so ina comment ne mai nunan kuna bi? Free ne mutanena
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment