Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

na damunta sakamakon irin darzar da aka mata, abu da rashin sabo
Wani hadi ne ta nufota da shi wato APKI da MAN KADANYA cakude da wasu graine kannanu maroon

Hannayenta ta kama ta tayar da ita zaune
Cikin nutsuwa ta ce" cire rigar

Ido Najeeba ta kura mata da mamaki, bata yi magana ba aman yannayinta ya nuna kwari ba zata iya kallo ana ci gaba da wani yi mata zirr ba

Zama matar ta yi da abin a hannunta ta ce" kin san shekarana nawa? Shekarana sitin da biyar a duniya

Da mamaki Najeeba ta zaro ido tana kallonta, sam bata yi kama da wace take da wadinnan shekarun ba

Matar ta ce" wannan din, shine aikina, sannan ban taba yiwa koda yar sarki bane sai matar sarki, matar sarkin ma, sai wace Allah ya yi,
Dan sasautawa ta yi ta ce" SUNNA NA PRINCESSS FADIMATU MUHAMAD, nice yar farko a wajen sarki MUHAMMAD,

Na yi awani a jirgi dan zuwa nan dan mutuncin Mahaifiyarki da kanwar Abihnki
Bani da jiyar juyawa sai na gama abinda ya kawo ni

Kuma lumshe idannuwanta ta yi kafin ta dan buda idannuwanta da yannayin gargadi wanda sam a muryarta babu aman idannuwanta sun nuna ta ce" zaki cire rigar ko na cire maki?

Hannayenta ta saka tana jan rigar cike da mamaki, a hankali ta bada hankalinta kan macen ta ringa gannin yanda take du wani motsinta,

Wannan hadin ta kawo wajen mamanta ta shafa mata a yan mamanta da basu da girma sosai ya kasance ta shafa masu sosai sannan aka kawo wata bra wace ana iya rageta ko a karata aka daure mata su dam

Sakata ta yi ta yi ruf da ciki sannan ta ringa shafa mata shi a wajen duwawunta masu fadi da girma, duda haka ta kara mata domin shi anfaninsa dama shine ya kara cika waje, shi yasa aka shafa shi a mamanta dan ya jara girma sai kuma duwawunta

Wani pant aka bata ta saka sannan aka cenza mata wajen kwoncin

Dayar matar ce ta shigo da wani man mai tsarara ta shiga shafa mata shi a jikinta baki daya tana masaging din jikinta a hankali a hankali har kafafuwanta da tafin hannayenta ko'ina cikin nutsuwa da kula

Sai da ta gama lumdeta sannan aka kuma tayar da ita aka rufa mata wani abin rufa aka saka wani mahaukacin turaran wuta mai wani irin sanyayan kamshi ya shiga ratsata domin a saman wata kujera ce mai hudoji direct ya ringa ratsa jikinta yana hawa ko'ina na jikinta yana kamawa sosai da sosai har ya gama sannan aka ciro wata wata riga fara kar aka bata ta saka mai dan tsayi kafin a bata safar kafa da ta hannu duka ta saka sai hula aka rufe mata kanta da ita mai dan gashishika mai laushin gaske

Anmy ce ta shigo tare da dayar matar wace ita kuwa aikinta shine hade haden tsumi kala davan daban
Tunn da ta ga Anmy sai ta ringa binta da kallo
Anmy kuwa tana kiyaye abinda zai saka su kadaice har sai da ta amshi abinda matar ta daho tantabaru ne da wani sirri ta dawo kusa da ita ta zauna

Budewa ta yi ta saka hannunta ta ringa bismillah tana ciyar da ita tana kiyaye bata da kasusuwa har ta cinye sannan ta saka cokali tana bata romon nan a hankali har ta shanye shi
Wata madara mai dan dumi ce Anky ta miko mata cike da bol mai dauke da sinadarai ta bata ta shanye

Sai da ta shanye tas ta mika mata
Mikawa matar ta yi ta juya ta koma domin rubutu ne take a allo tana rubuta yusufa da kanta dan hadin kankanar da zata yiwa Najeeba

Anmy zama ta yi a kusa da ita ta kamo hannayenta tana gannin yanda fatar Najeebar har ta wani irin daukan harama ga abin man nan ya saka hannayenta sunna santsi

Idannuwanta ta lumshe a sanyaye ta ce" Najeeba, zaki yi hakuri da abinda Allah ya hukunta?

Najeeba ta ringa kallon fuskar Anmy hakan ya saka Anmy jin wani iri, so take ta san me take tunani a zuciyarta, kar ta dauketa mai son kanta da yawa

Matar nan ce ta dawo ta ja abin zama ta zauna tana kallonsu

Murmushi ta yi ta nuna anmy da hannunta ta ce" ki rungumeta a jikin ki, ki fada mata dadadan kalamai

Ta kai dubanta wajen Najeeba ta sakar mata murmushi ta ce" kunya, da tsananin soyaya su rinjayi rigimarki a irin wannan lokacin

Anmy a hankali ta rungume Najeeba a jikinta tana dan taping din bayanta ta furta" i love u Najeebana, kin san me? Mamanki na hanya yau ko gobe zata zo

Najeeba ta rintse idannuwanta wasu hawaye masu dumin gaske suka zubo mata, mamanta? Zata zo? Ta zo ta yi me? Rabonta da Niger shekarun da dama, ahine yanzu zata zo ta mata me?

Bata dai ce komai ba har Anmy ta gama ta shinfideta da kanta sannan ta mike ta fita

Wani baci ne kai nauyin gaske ya dauketa na gajiya da kuma rudani
Bacin bata yi mafarkai a cikinsa ba, hasalima kamar wace ta mutu bacin kawai take du jikinta a gajiye

.......
Haka ya kasance a wuni za'a yi mata irin gyaran nan sau biyu, da dare kuwa za'a ringa koya mata yannayin magana da kuma yannayin cin abinci, da komai da komai wanda a gannin Najeeba kallonsu kawai take bata san cewa tana daukan yannayinsu ba domin su sun ga sosai tana daukan darusan su duda ba amsa take basu ba

Bayan kwana hudu mahaifiyarta ta zo, sai dai tun da ta zo ko da wasa idannuwansu basu hadu ba domin kuwa idan ta shigo dakin Najeeba koda a zaune take zata lumshe idannuwanta ne, ita kuwa zata tsaya ta yi murmushi daga nesa kafin ta juya
Tana azabtuwa da yannayin yarinyar nata
Sai dai bata da wani iko na tirsasata,
Ta samu DAYABU ta roki idan an fitar da ita ya rokar mata sasauci, Abih kuwa sam baya son abinda zai hada shi da ita domin matar tana da tasiri a rayuwarsa, zata haye masa ne a lokacin da bai shirya ba


Yau sauran kwana uku daurin aure
A yau da sasafe ya saka aka kira masa Zinaria
Sai da ya gabatar mata da tarin abubuwan arziki irin na fitar kishiya kafin cikin nutsuwa ya bata hakuri dan gannin ya samu bata yi irin na wancen karon ba sannan ya shaida mata cewar zai daura aure da mace biyu nan da kwana uku

Wani abin aka ce ya girmi hawaye, sai kawai ta ji zuciyarta ta dauki wani irin suka da zafin da ta yi gagawar dukewa

Hannunta na dama ta dora daidai wajen ta damka sai kawai ta tafi numfashinta ya dauke

Sosai ya shiga wani yannayi na ganninta a haka, meye wai a su kishiya? Meye dan zai yi aure sai ta ringa fmhayacinta? Ta san bata so ya yi aure aman sam bata iya bashi kulawar da yake da bukata? Subahannalah, subahannalah shine abinda ya ringa furtawa a kasan zuciyarsa
Sai da ya kira docter ta dubata ta bata taimakon gagawa kafin take dawowa hayacinta

Wannan karon kam ta kasa dane kukanta da ihunta, sosai take kuka ta rikice masa tana neman a hayacinta ta zauna jikinta du yana bari ta ce" me na rasa? Me na gaza? Mutuncina, darajata zasu zube ne a kasata, me ya sa kake son sai ka zubar da dukan wani tinkaho namu a duniya? Mahaifiyata ka ja gaban yiwa kishiya, yanzu zaka kara yi min du a cikin shekara daya? Kishiyarma ba daya ba har biyu? Ba zan iya lamunce raba mulkin garin nan da wata ba, ba zan iya lamunce tunaninka da wata ba

Sai kawai ta sauka da gudu ta fita ta yi bangarenta tana jin kamar zata mutu dan bakin ciki
Wayarta da ta kashe ta kunna hannunta na bari ta shiga neman layin mahaifiyarta

Tana dagawa muryarta a hade ta shiga koro mata bayani
Mikewa tsaye mamanta ta yi daga zaunen da take har tana gannin wata innuwa innuwa na son rufe idannuwanta

Me ya shirya yiwa rayuwarta ne da ta y'ayanta? Tana nan tana fadi tashin yanda zata kawar da maganar auren danta daya kwal namiji da wannan bakar yarinyar, da kuma yanda zata yi da yarinyar da rabinta da ta ganta tun shara'ar da aka yi masu da Yarima domin ganninta ya zama aiki a gidan baki daya, sam bata zuwa gaisheta bake ta samu ta wannan hanyar ta gama da ita shine zancen za'a yiwa Zinaria kishiyoyi har biyu ya fado?

Kashe wayar ta yi ta nufi dakinta da wani irin sauri a bayane ta furta" *ka ci nasara a mu ta hanyar shigar da wasu cikinmu, sai dai baka isa ka sako mana wasun ba ta bangarenka, ko wadinnan din zan fitar da su ne ko ta wani hali!..............

Ta wuni cikin tashin hankalin da ko abinci bata ci,
Yayarta ce ta zo ta tare a wajenta suka shige daka sunna tsare tsaren yanda zasu fitowa lamarin

...........................................

Bayan salar Isha yana zaune da jarida a hannunsa Amintacensa ya shigo masa da wata ambulope

Dukawa ya yi ya bashi sannan ya fita daga dakin ya koma wajen da ya rasa me suke yiwa yarinyar nan a ciki, hasalima bai san wajen na meye ba bayan kuma a cikin gidan yake ba wanda zai ce ga abinda ake yi a wajen

Sai da ya gama komai sannan ya buda ambulope din nan mai girma

Hotunna ne birjik, hade da takardar haihuwa, da adress complet

Hoton yarinyar ya kurawa ido, masha Allah Nadia akoy cikar mama sosai domin ko a hoton ana ganewa
Ajiye hoton ya yi gefe ya dauki takardar da aka yi bayani a ciki

Tabas kawarta ce, kawarta kuma ta yarinta domin tun makarantar secondary suke tare

Murmushi ya yi ya ninke komai ya mayar kafin ya dauki wayarsa

Mesage din da ta bara masa sun fi karfin irgensa dan haka ya goge su baki daya kafin ya yi shiru da wayar a hannunsa

Irin yanda take zumudi da kayan da aka kai na aurenta du ta yada maganar duniya wanda sam bai so haka ba, sosai an dauka cewar itane matar da zai aura uwa uba irin yanda take neman aminiyarta ido rufe dan ta shaida mata wannan dadadan labarin sai dai kash ta rana ina *NAJEEBA* ta shiga

Sai da dare ya raba sosai sannan amintace ya yi satar hanya ya fice

Bai zame ko'ina ba sai fadar da HUZAIFA ke zama

Yana zuwa ya yi masu salama kafin ya nemi ganninsa

Mikewa ya yi suka yi nesa da mutane sosai
Wata yar karamar wuka ya shafa masa a gefen cikinsa cikin kakausar murya ya ce" ina wayarta? Wayar zata bani, ka kiyaye idan ka yi wani yinkuri na rantse zan huhuda hanjin cikinka na yanke harskenka har sai ka ringa rokon mutuwa ta daukeka!

Kasancewar du inda zai je da wayar yake yawo yana kirta iskanci da ita har ya yi saken da Sultan ya saka aka yi tracenshi aka san wajen zamansa da komai bisa tirsasawar Anmy ya saka a amso wayar a hannun Huzaifan

Jikinsa na bari ya ciro wayar ya bashi

Kafin ya ankara ya masa wani bugu a keyarsa hakan ya saka ya tafi kasa summe sannan shi kuwa ya juya ya hau babur din da ya yi bada sau yana tuki yana sin fahimtar abinda ke faruwa,
Kwata kwata Sultan yana nisanta kansa da shi domin shi kansa yanzu bai san shigarsa ko fitarsa ba, abinda ya sanni shine wani abin na faruwa wanda sarki yake boye masa
Bukatarsa ta gaba shine sannin meye? Sai al'amuran auren nan, sam bai san yaya za'a tafiar da komai ba! Abinda ya dace ya sani dan sannin abinda zai yi!


Yau ta kama sauran kwana daya jal daurin aure, wato gobe za'a daura auren

Cikin nutsuwa ake takawa da ita ita kanta bata san inda za'a kaita ba
A rurufe komai sannan ba waje aka nufa da ita ba ta wani lungu ake ta tafia mai nisa da ita har aka isa inda za'a kaita

Sanyin safia ne, su hudun nan ne suka sakota tsakiya hakan ya saka kanta ke kasa suke jan hannunta a cikin wata irin tafia tamkar yar yaye

Sosai a yau da ta kalli madubi ta firgita da irin cenjin da ta ganni a jikinta tun daga fatar jikinta, gashin kanta, mamanta, duwawunta, kamshin jikinta kai harta da laushi santsin jikinta sai da suka bata mamaki mai tsananin gaske
Ta tabata a yanzu suturunta ba zasu shigeta ba ta wajen duwawunta da kuma mamanta domin sun kara cika ne sosai mamanta har ya yi girman da zai kai girman mangwaro mai dan girma kasanta kuwa tabas ta fi Niki minaj

Shigar da akai mata doguwar riga ce ta lesh wace aka yi wani irin dinki mai jan kasa daga baya sannan aka dora mata wata irin alkyaba mai ruwan ashh kala mai haske ta fi lesh din haske domin shi lesh din duhu ne da shi

Wani irin dadadan sanyi ne ya ratsa fatar jikinta da wani irin nutsatsen kamshi
Idannuwanta ta lumshe dan rabonta da ta ji sanyi haka na ratsa jikinta tun satotan da suka yi

Ji ta yi sun kamata sun gurfanar da ita zaune kasa sannan datijuwar nan ta karaso gabanta ta kama hannunta na dama ta kara durkusar da ita ta fitar da hannun mai dauke da wani irin kunshi mai shegen kyau a sanyaye ta furta" *ALLAH YA JA DA RANKA, MUN ZO NE NEMAN ALBARKAR AURE, ALLAH YA TAIMAKE KA*

wani irin tsintsinkewa gabanta ya yi ya dagargaje ya fadi hakan ya sa ta fago kanta da sauri dan tabatarwa kanta wani ranka ya dade din ne?

Lokaci daya ta mayar da kanta ta sada sakamakon ido hudu da suka yi da shi, idannuwan nan nasa sam ba alamun hutu domin har yanzu a rikide suke da fitintinnun da Zinaria ke gabatarwa na tayar da hankalinta da ta yi, ga abubuwan dake kansa, ga tunanin auren nan kamar da wasa

Idannuwansa ya lumshe yana jin kamshin da suka zo da shi, wacece mai kamshin nan a cikin su?

Kuma buda idannuwansa ya yi yana kallonsu du kawunnansu a kasa a gabansa, su dukansu jinnin sarauta ne yaushe suka zo? Me suka zo yi?

Sai da ya furzar da huci sannan a sanyaye ya buda bakinsa yana kallon Fadimatu
A hankali ya daga yatsunsa biyu ya yi nuni da wata ambulop yar karama fara karrr sannan ya lumshe idannuwansa ya dan jimke hannun nasa ya dan jinjina mata

Mikewa ta yi ta dauko ta duka ta ringa godiya da abin arziki duda basu buda sun ga meye a ciki ba, wannan shine kyautar da zai mata kafin aure bayan akwatunnanta da sauransu

Sai da ta kara tabata sannan Najeeba ta buda bakinta da take ji ya mata nauyi a sanyaye ta furta" *AN GODE*

da sauri suka kalleta jin AN Gode din da ta ce tamkar wace take magana da wani sa'anta bayan a hardace suka koya mata irin gidiyar da ta dace ta ringa yi masa a gaban mutane

Ta buda bakinta zata yi magana ya daga mata hannu hakan ya saka ta sada kanta ta ringa neman afuwa
Da yan yatsunsa ya nuna su tafi

Du mikewa suka yi basu kamata ba, domin kuwa iya su ya yi nuni da su fita

Tana jin alamun sun tafi ya saka ta dago da sauri dan gannin abinda ke faruwa

A yanzun kam ba iya zuciyarta kadai bace ta fadi harta da ita kanta sai da ta ji zata zube a wajen kafin ta yi gagawar mikewa tsaye nufinta ta juya ta tafi, sai dai ta tsinkayo muryarsa kamar ba shi ba a hankali ya furta" zo

Jikinta ne ya kara daukan bari
Ta juyo tana kallonsa
A zaunen da yake bai motsa ba sai dai irin kallon da yake mata ya isa ya halakata da tashin hankali
Kafafuwanta ta ringa jin sunna kaita wajen da ta tabata zai summar da ita idan ta idasa

Tana zuwa ta zube kasa hakan ya saka dubansa sadawa wajen da take tsugune

Kallo ya kare mata, shi kadai ya san irin hukunce hukuncen da zai mata a rayuwa

Bai ce komai ba sai da ya gama yi mata kakausan kallon da ya sakata jin zata fashe da kuka kafin a hankali ya furta " *TAFI*

ai kamar jira take ta mike da sauri ta fita , tana fita ashe sunna jiranta suka kuma daukan hanya suka koma

Ambulope din suka mikawa Anmy da Ummu dake zaune kafin ta shiga tube mata shigar nan tana mai yi mata maganar shin yaya aka yi ta furta iya kalmar nan a gabansa?

Anmy ta saki murmushi a lokacin da ta gaakudan kudaden da aka rubuta a kan chek, da kyautar gida da kuma kyautar zinarin da aka fadi irin kirar kafin ta mikawa Ummu

Murmushi itama ummu ta yi kafin ta mayarwa Anmy domin sam bata rike komai Na Najeebar dan ba zai yiwu ta diro kai tsaye a yanzu ta nuna itace uwar Najeeba ba

Ita dai Najeeba shigewa ta yi ko tsayawa bata yi ta ga abinda suke mamaki da murnarsa ba, alwallah ta kara daurowa ta zo ta shiga sallah, kuka take har kanta da jikinta suka dume da wani irin zafi da ciwo, fadawa Allah take aa ita bata so kar a daura ........... (HOUM)


*BABAR RANA*






Ranar da zata haukata zukata da dama, ranar da yan jarida zasu samu abin yadawa, ranar da zukatan maza da dama zasu ji wani iri da madaukakin tashin hankalin jin inda ta fada
Lale da yawa zasu ji inama, da yawa zasu ce dama ai yannayinta sai manyan ciki kuwa harda ambasador da soja da likitocinta uwa uba HUZAIFA,
Ranar da labari zai hadu a waje uku, tun daga bangaren ZINARIA, NADIA, DA KUMA NAJEEBA,
Jin labarin daga sama zai gigita da yawa,



.........ku biyoni yar mutan niger

Idan comment ya cikan gida zan yi na gobe, idan bai cikan ba sai nace Allah ya sada mu da alkhairi i.a


*Masha Allah*>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



36



A yau ta kasance ranar asabar ce,
Garin damagaram bai taba daukan harama irin na yau ba
Samari da yan mata, datijai da tsofafi, kar harta yara kanana idan suka samu hanyar fita sun fece zuwa baban filin da ake babar tadar wasan kaho

An shirya wasan kaho da sukuwa takanas saboda auren nan
An yada maganar daurin auren nan ne a gidan redio da TV cewar Sarki zai kara auren yan matala tsala tsala kwaya biyu duda yan matan ba'a fadi ko su waye ba, sai dai maman NADIA da Nadia du sun baza cewar itace dayar, su kansu sun kasa kunne su ji wacece dayar

Gaya kuwa ba sai an gayata ba, domin wajen ya samu halartar manyan baki na mamaki gidan sarki kara cika yake tun a jiya har zuwa yau cikin bakin kuwa harda su *MAI MARTABA SARKIN AGADEZ, DA MATANSA BAKI DAYA, DA YARONSA YARIMA*

Tun da suka zo, GIMBIYA mahaifiyar ZINARIA ta tare a bangarenta suka kile tare da sauran y'ayanta mata suka shiga hada hadar sa ji sa ganni sai dannar Zinaria suke wace take neman ficewa a hayacinta maimaitawa take ba zata iya raba mijinta da sarautar nan da wata halita ba

Yayarta guda kuwa ta fita cikin mutane dan ta samo rahoton dayar kuwa yar gidan waye? Domin tuni Nadia ta tona kanta ita da uwarta wa'inda basu san tana cikin amaren da za'a kawo gidan sarauta ba daidaiku ne domin ta karbi abin da hannu bibiyu, bata taba tunanin ita Nadia zata tare a matsayin amaryar mai martaba, ita zata ga fuskar mai martaba, takan yi daria ta furta" Najee, ina kika shige, yau daukaka ta tardoni a gida ni zan zama matar abokin gabarki, kar ki damu kawata zan shirya ku!

Bangaren Anmy hankalinta ya so rabuwa biyu, sai dai mahaifiyar Najeeba ta kaleta ido cikin ido ta ce" idan har kika yarda shiriritar yarki ta saka maki damuwa to fa ta samu nasara a kanki, ki gane tana kara langwabewa du idan kin shigo ne, ki zo ki kula da baki ki barta ta gama shan karin ruwan, idan lokacin fitar da ita ya yi za'a fitar da ita koda a sume ne a jinginar da ita, ban taba gannin bataciyar ya irin yarku ba! Kun wani rikice dan tana abu nan Abihnta har ni yake fadawa magana wai ina ruwana da ita, han

Murmushi kawai Anmy ta yi, domin a lokacin da aka basu damar su shiga su duka su kara ganninta a jiya ne suka yi kicibis da Ummu, du daburcewa Abih ya yi sai neme nemen kys din mota yake a aljihun rigarsa har sai da Dayabu ya yi murmushi ya kama hannunsa ya ja shi, har ya gifta ta ya juyo ya ja tsaki kamar wani yaro ya ce" an ji kunya, me kuma ya maido ki nan? Ki koma mana wajen neman kudinki, ki barmin y'ata babu ruwanki da ita

*FADA* ta rikice, ta hautsine wajen ya dinke da jama'a, dogarai ne sun sha rawani daidai misali du sun bazu sunna bada wani irin tsaro sai sojojin da suka barbazu suma sunna bayar da tsaron

Tsaye yake a cen sama ta wajen window dinsa mai duhu wanda shi yana iya gannin na waje aman daga waje ba zaka iya hango shi ba

Bashi da riga a jikinsa, ya gama moysa jikinsa ne da wani dan tawul karami yana goge zufar jikinsa yana kallon du wasu shagulgulan dake kai kawo a cikin fadar

Hannayensa masu taurin gaske ya daga ya dan dora a jikin garun ya kara kurawa wajen ido

Tabas ya jima rabonsa da ya ga taro haka, ya tabata Anmy ta bada babar gudunmuwa dan tana aurar da y'a

Murmushi ya yi yana girgiza kansa ya juya cike da kadaita ya nufi bayi da kansa

Ya jima ciki yana wanka da dukan uzurinsa kafin ya fito

Agogo ya kaiwa duba, nan da awa daya da rabi za'a gabatar da daurin auren dan haka sai ya zarce wajen tarin kayansa ya buda ya tsaya yana kallo

Saka sababin kaya ba yau ya fara ba, sannan ba sai ana wani abin yake sakawa ba, sai dai na yau din a sabinma bugagu ne wa'inda suka amsa kiransu

Da hannunsa ya ciro su da sabon rawaninsu hade ya ciro duka ya ajiye gefen gadonsa

Zama ya yi ya dauki karamar wayarsa ya danna kira

Tana fara ringin aka daga ana mai aiko da salama da neman fara kirari

Da sauri ya furta" yi shiru, abinda nake so da ke ki saka a yiwa yan mata kamar goma kwaliya ya kasance an laya su a matsayin amaren nan da ake yi, ina so ku ringa gardamar ba zaku bayar da amarya ba,
Ina so ki saka mata simple shiri ki bata hijab da nikaf ta fara fita ta tsaya ki a cikin kwanar gidanku kafin ki sandi mutane ki fito
Akoy dan sahun da zai dauko ku ya kawo ku
Idan kun zo yau gidan ba'a hanna shiga ko fita, zaku samu hanyar shigowa
Idan kun shigo zan wakilta macen da zata sada ku da bangarenta sai ku gabatar da abinda zaku yi

Dan shiru ya yi yana sauke ajiyar zuciya kafin ya dago yar yatsarsa guda ya ce" ku kiyaye, rayuwarta ko nace rayuwarku baki daya ke cikin hadari, idan har kuka kuma falasa wani abin ko me ya biyo baya ku kuka da kanku

Yana gama fada ya datse kiran sannan ya dan dane lebensa na kasa

Kuma mikewa ya yi da tawul din dake jikinsa ya nufi wajen window din

Abubuwa da dama sun shiga idannuwansa, irin yanda ake waje waje ana kuskus daga inda yake ba zai fahimci komai ba sannan a yau ba zai fitar da droon ba har sai an fara hawa dokunna domin a yanzun ana cen ana hawan kaho ne ana ta zubda maza

Suturarsa ya ringa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment