Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kamar uku tsakani kamar komai ya wuce, ba wai yan mata na daina yi ba, ba kuma take taken masu kudin zamani na daina ba kaina sama da isata da komai gefena ga hajiata tana kawar da kai ga jiginiyar y'ayana da suke dauke da wata irin tarbiya ta shakuwa da junna da soyayar junnansu bale DAYABU da ya kasance ya iya tafiar da tarbiyarsu daidai gwargwadon iyawarsa,
Wata ranar asabar, wace ta kasance ranar da ta kai bango, ina katon shagona na buga madara suka kawo mata ziyara da yar da aka haifa min da siyaya rigijib dan neman fitina

A lokacin tana da saurin rama mari, dan haka a gabansu ta masu dan karamin hauka, ta nuna masu halaya na mata, suka ringa raba haki har hayaniyar ta kawo inda nake

Kafin na mike sai da wani abokina elhaji Saley ya ce" lale kura ta yi lafia, yo ni mace ta isa ta ringa yi min abinda matar ELHAJ MUTALAB ke yi masa ban lakada mata duka ba na nuna mata ita ke kasa da ni na koya mata hankali ko dan gaba ba?

Da wannan hudubar ta shaci fadi da bacin na isa gidana rai bace jinnina a sama ga oga ya zo ga ogan da zai zartar da hukunci wato mai gida tamkar kububuwa na fada gidan

Ina zuwa ido rufe na tsayar da su,
Rai bace na dubeta, a matsayinta na wace na kilace matata mai daraja, a gaban mutanen da suka ci amanarta, ni kaina wanda na ci amanarta dan rashin kunya irin tawa na murje ido irin ga boss din nan na kai na kawo sunna bina da kallo kowace na jiran ta ji kalaman bakina sai kawai na dubeta ido rufe na daga hannuna na kai mata marin biyar zazafan da ya sakata dafe kumcinta cike da mamaki, da firgicin rashin adalcina na kuma daga yar yatsana na nunata na ce" banza jahila! Da ke kadai zan rayu hala da kike nuna halin mahaukata ne? Ke har kin isa ki tare min budurwara ki daka har ki cira mata riga? To wannan da kike ganni ki saka a ranki sai kun yi zaman kishi da ita domin sai na aureta na kawota gidana kun zauna kin dafa mata ta ci kuma ta je shinfidata a karo na biyu! Yau na ga matar balaki dan kawai na aureki ban isa na dubi wata ba? Ba'a auren ke na aureki ko ni zaki nunawa hauka a nan? Ke ki je inda zaki je na sake ki saki daya domin ni ba sakarai bane da zaki ringa zuba min shirme kin bi kin tatare min gaba da baya na kasa aure to yau dai asirin bokan naki ya karye sai a kara gaba malama!"

Hawayen da bata yi idan muna fada ne ya bale mata,
Tana dafe da kuncinta ta matso kusa da ni sosai,
A hankali ta ce" *sakayar soyayar kennan MUTALAB?, ka yanke min zama da y'ayana? Ka sake ni a karshe dai a kan son zuciyarka bayan ka san iyayena sun rasu ina kake so na je na yi zawarci? Ba asirceka na yi ba, kai ka hanna kanka aure, sai dai kash Mutalab, kash, walahi da ka san koda zaka maido ni ni ba zan dawo ba domin na haramta hauranka, Mutalab na rantse da Allah na kare da y'ayanka da du wani abu da ya fito daga hannunka! Kishi da wannan? Ta nuna matar, kafin ta tsartar da yawu ta kunce goyon Najeeba ta saketa daga tsaye hakan ya saka Najeeba zabura ta wawureta tana kukan MAMA, sai dai ina kuma hankadeta ta yi ban aune ba ta bala min mari ta kuwa ci damara da dan kwalinta ta ja baya ta ce" idan ka isa bismillah, walahi ko a da ban mari fuskarka ba dan kana dauke da igiyar aurena a yanzu da kai da bola du daya, Mutalab bismillah, da kai da dadiron taka sai nai maku jina jina a gidan nan*

Mamaki ya hanna min motsi, ita kuwa karambani ya sakata tunkararta, lalle kuwa sai da ta mata jina jinan ina tsaye tamkar gaula domin marin nan da ta min ya aniya maido min maganar sakin da na mata

Da gudu ta shige dakinta , dan kwali da dukan takardunta da jaka daya tak ta dauka ta fito
DAYABU na kuka yana riketa haka yan uwansa sai kawai ta kubce ta fice da gudu ta fita

Idannuwansa ya bude wa'inda sukai masa jajajir, ya ce" kun ji abinda ya faru tsakanina da NANA MARIAMA, tabas wani sa'in Allah kan baiwa mutun mace ta mutunci sai dai irin rikon da zai mata ke hadasa cenzawar lamarinta

UMMU dake dafe da kanta dake sara mata ta kalle shi ta kuma kalli yarwn sai kuka suke

Dubanta ya yi wannan karron maganar tata ce, sai da ya sanyaya muryarsa ya ce" bayanta na auri mata, daya bayan daya ina kara saki domin ido rufe uwar y'ayana nake nema wace zata kuma daukan dawainiyar gidana da y'ayana tamkar ita ta haifa

Tun ina saki da karfina har na dawo ina saki da hawayena

A hankali na ringa dana sani, har na je na zauna gaban kanwata na zayane mata gabli da ba'adin zamantakewar da na yi da matata,
Sai dai kash, a lokacin ta so ta maido min da farin cikina sai Nana mariama ta gindaya rantsuwar cewa" ai kuma ita da mutalab sai a lahira

Kuma sada kansa ya yi ya ce" walahi na sha wahala, ina cikin shan wahala
Ina ta kame kame ido rufe
Yarana na ta gararamba zuciyata na ciwo
Du irin tarbiyar da suke samu ba ta mace tsayayiya gashi na kasa bada su wajen kanwata kwata kwata domin idan na shigo gidana burina na ga layin motocinsu, na tsinkayi kwaramniyarsu na zauna mu yi hira mu yi goyo goyo da kannanuwan, manyan na daukanmu a hoto
Sai nake kwatanta irin macen da nake so, sai na fadawa Allah
Sai da na dangana da auren wace nake zaune da ita a yanzu, sai malan liman na baba ya ce da ni" *kar ka saketa, koma meye halayanta, ka jure, idan ka kuma sakinta wace iri zaka kuma daukowa y'ayanka? Kar ka manta y'aya mata masu barin gaban iyayensu da wuri ne, kai kuwa goma sha biyar gareka mata masu rai da lafia a ciki baka aurar da ko daya ba, shin wai baka tsoron sake saken nan a sako maka naka? Bana so ka ji ciwon sakin y'aya a zuciyarka, domin ba uban dake so ya budi idannuwansa ya ga yarinyarsa a gabansa na zawarci*"

A hankali ya kuma maimaita" *NA SHA FAMA, INA CIKE DA TSORON RANTSUWAR MARYAMA*

Da sauri UMMU ta kuma kallonsa, zuciyarta na kara dokawa,

Mikewa ta yi tsaye tana jin zata fashe da kuka
Kafarta ta daga zata gudu ABIH ya kuma furta" *Marayu ne mu, daga ni har y'ayana, walahi ba zan kuma rayuwar dadiro ba ba zan yarda na hada SIRRINA da dadiro ba*

Da gudu ta tafi wannan karron tana mai barin kukanta fitowa

Abih ya mike tsaye da sauri , sai dai riko hannunsa da ya ji an yi ya saka shi juyowa

A hankali NAJEEBA ta furta" *ABIH*"

idannuwansa ya lumshe wasu hawayen suka ci gaba da zuba a idannuwansa

Da sauri ya koma ya zauna kansa kasa
Dagowa ya yi ya ga irin kukan da suke
A sanyaye ya ce" da na san rayuwa haka take da daci, da na roki takaituwarta a kaina daga bakin lokacin da na rasa matar kwarai, Mariam ta kasance mai hakuri, da juriya da kawar da kai, ni sai na bazantar na ringa tunkudata har na kaita wajen da ta fashe ta kasa da ni, ni da kaina na yiwa kaina mugunta waye ba zan yiwa ba? DAYABU, UMMULKHAIR, UMMUKULSUM, ZAHRAU, NAJEEBA, *SHIN ZATA DAWO GARENI?*

Tabas tsakanin da da iyaye sai Allah, tausayin iyayen nasu ya saka su hawaye sosai da sosai kafin su aniyar kwontar masa da hankali
NAJEEBA jikinta a mace yake tana kallon Abinta
Gaskiya Abih ya aikata ayyuka kala daban daban sai hamdallah

Bata iya cewa komai ba har suka wawatse aka barta da zahrau

Zahrau ta ringa kwontar mata da hankali tana kara nuna mata cewar UMMU bata da laifi

Cike da hawaye ta ce" Auntu Zahrau, ashe shima ya tsani bak'ar mace aka aura masa ni?"

Da mamaki ta ce" wata irin magana ce haka, SULTAN din ne ya tsani bak'ar mace? Me aka yi? Me ya sa ya fadi haka? Wani abu kika ce masa?"

Sai da ta kara shahsekar kukanta sosai sannan ta ce" *Da karfi ya kwace min abinda nake tanadarwa waninsa Bayan wannan, ya ringa min hararan nan na tsana Na zata ya tafi ni kuwa kaina a sade nake fadin ai ba son farin mutun nake ba, mugu azalumi mai cin kudin talakawa*

Sai da ta zaro ido kafin ta zauna da sauro tana kallonta ta ce" ya ji? Kina nufin ya ji?"

Najeeba ta gyada kanta tana kallonta itama ta ce" ya ji, shine abinda ya saka shi fada min shima ai ba son bak'ar fata yake ba"

Cike da madaukakin mamaki, da ayar tambaya Zahrau ta furta" lalle akoy wani lamari a tare da shi wanda yake da girman gaske
Ke yanzu, kece kika fadi haka a gabansa sannan gaki a zaune daram da ranki? Lalle na tabatar da du wayonki wani sa'in baki da wayo, ko kuwa rashin hankali ne? ALLAH masani"

Zama ta yi gabanta tana kallonta ta ce" na zata zaki iya tafia ke daya ba tare da shawarana ba? Sai dai na kula a kan matsalar wani kika iya samo mafita a kan karan kanki kina zama wawa Najeebana"

Kuma kallonta ta yi gannin itama ita din kawai take kallo ta ce" abinda ya saka ya kasa tataka ki ko ya karya maki kafa sakamakon maganar da kika fada a gabansa ya shanye shi zamu dauka mu yi anfani da shi ta hanyar buga wasan nan"

Kumatun NAJEEBA ta dan riko ta ce" baya son bak'a? Zamu gani idan har furucinsa shine gaskiyarsa, idan har idanniyarsa ba zata karyata sakonsa ba, idan har gangar jikinsa ba zata rikita lisafinsa ba!"

Mikewa ta yi ta kama Najeeba ta ce" zo mu je ki kuma shiga ruwan da AMMI ta hada, domin babu ne kawai bata tanadarwa wannan ranar ba

Abih na fitowa ya karasa Fallon, nan ya kuma tarar da Mardiya zaune ta kumbura kamar zata fashe sai karkada kaffafuwanta take cike da balaki

Yana son ficewa ta mike da yannayi na raini ta ce" ji mana? Meye ka shiga dakin cen ka zauna tun dazu ana cin amanata ne ko meye? Hala ji kake ban san wacece wancen matar da ta wani ja su ciki ba? Malan na gaji da irin abubuwan nan gaskiya amanata za'a ci ido na gani?"







Good morning all>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



47

Alhamdulilah na dawo=ØÞ


Cike da kulawa, da yannayin da kwata kwata baya nuna mamakinsa a irin halayarta a yanzun, domin ta shayar da shi lamarin da lamarinsa ya fasa bashi mamaki ya dubeta duba na tsanaki ya ce" da gaske kuwa kin san wacece?"

Karasawa ta yi sosai kusa da shi tana dan jijiga jikinta, irin ga mata an batawa mata rai ta ce" eh mana, ba uwar NAJEEBA bace? A kan me zata zo.nan ta tare ko yar uwar BILKISSU ce? Ko kuwa dan kai take zaune?"

Idannuwa baki daya UMMU ta zaro daga wajen diner da suke zaune ita da Ammi , domin tun fitowarta Ammi ke zaune da ita tana tausarta, baki daya hankulansu ne ya dawo, irin rashin kunyar da matarsa ke tatawa ta saka UMMU zaro idannuwanta cike da mamaki

Abih ya ce" dama haka ne, dama ace zaman da take a nan nawa ne? Ke da na fi kowa farin cikin hakan, da ace zata kuma dubana bayan rashin adalci irin nawa da na yi farin cikin hakan na godewa Allah"

Yana gama fada gaba ya yi ya barta nan tsaye, maimakun ya nemi wajen su UMMUN sai ya bar gidan baki daya
Kwata kwata hankalinsa a tashe zuciyarsa bata da nutsuwa

Tunda ta fito daga wankan nan wanda ta ji dadinsa fiye da na dazu ta zauna ta saka pizzar da Zahrau ta kawo mata mai zafin gaske wace aka sarafata da naman kaza

Sai da ta koshi sannan ta kuma mikewa ta koma bakin gadon da Zahrau ke zaune tana kunce kitson da ala fara yi mata sannan ta mika mata abin kitson ta sauaka kasa ita kuwa ta fara kunce mata a hankali,

Basu yiwa junna magana ba har sai da ta gama mata ta caje kan sosai sannan ta raba shi gida uku cen saman ta fitar da kadan na tsakiya sai ma karshe ta dadaure kafin ta fara tsagawa a hankali ta kuma yiwa na gaban gida gida sannan ta fara daukan wani irin kananen kitso masu kwana kwana da shiga cikin junna sannan har karshe take kitse kitson duda irin yanda bata jin karfi sosai a jikinta aman ta ci burin sauke kitson a kan har uwarta

A hankali Zahrau dake ta harhada yanda zata bilo mata ta ce" tsoho ne?"

Najeeba da sarai ta san wa take nufi aman sai ta kasa bata amsa

Zahrau ta yi murmushi ta ce" matsalarsa dai farinsa da kuma sarautarsa ko?"

Najeeba ta sauke ajiyar zuciya, a hankali kamaninsa suke dawo mata , da sauri ta saki ajiyar zuciyar da ta kwace sakamakon irin yanda kamaninsa suka kawatu a idannuwanta

Wani murmushin Zahrau ta yi, domin a rubuce sai dai ta rubuta labarin kanwar tata ta baiwa wani tsabar yanda ko da ido ta yi magana take gane gaskiyar ciki da kuma wanda ta fada dai ne

A sanyahe ta furta" sai kike ce min na yawaita shiru a kan yawan magana, nan kika nuna min daga mijin da na aura har matansa kar na zake wajen buda bakina ina magangannun da ni kaina zasu gundureni domin kuwa a irin haka ina iya bada kofar da za'a gane raunina, tashin hankalina, sakarcina, jin tsorona"

Najeeba ta ci gaba da kitse gashin Zahrau, itama Zahraun sai ta yi shirun tana sauraronta dan kuwa ta san kitson nan ba na karewar yanzu yanzu bane
Sai cen kamar bata wajen, kamar ba zata tanka ba ta ce" Ban taba shiga halin firgici da tashin hankalin da na shiga ba,
Dan jan iska ta yi ta ci gaba da fadin" just ki kwatanta abin a gabanki, mutumen da tun bana biyewa maganarsa har ta kai min buga wasa daga ni sai shi,
Lebenta na kasa ta cije da hakoranta na sama kafin ta ci gaba da fadin" ya yawaita yi min tambaya a kan gidan nan, sai na nuna masa ni ban san gidan ba, ban san kowa ba, karshe na furta masa ni fa bai min ba"

Tsagawa ta yi da dan karfi har Zahrau na fadin" Aush"

Najeeba ta furta" Du a kan me ya min basaja yake hira da ni? A kan me ya ringa yi min tsmbayoyin da suka shafe shi? A kan me ya ringa hakuri da fadana? A kan me ya ci gaba da janyoni jikinsa ina fadin maganar da ta raya min a kansa?"
Sai da ta ja numfashi ta sauke , irin abu ya dake kan nan ta ce" sai kawai na ganshi a lokacin da ya shirya wulakanta ni shi ne a gabana da kamaninsa da komai sai dai fuskarsa na dauke sa kallon tsanar nan da ya zamo ayar tambaya a wajena!"

"Kun ban amsar hasashenku, sai dai zan kuma yi maki wata tambaya Aunty Zahrau, kasancewarsa baban mutumen dake mu'amala da mutane kala daban daban, har ya kasance ya iya basaja ya shiga gari ya yi lamuransa, shin bai taba sannin menene halayar yan matan zamani hade da samarin zamani ba ko kuwa yana nufin du yan matan yanzun ba soyaya ce suke yi da samarinsu ba aa zubar da mutuncinsu ne suke?, kina so ki ce min Aunty ya taba kamani da namiji turmi da tabarya ne ya saka shi wareni daban a cikin yan uwana ya sako lamarin tsana a tsakanina da shi? Ko tsabar rashin yancin kai ne zai saka matarsa marar tarbiya du haduwata da ita ko yan uwana da ita tun bana kulawa har ya kai kimarta da shakunta suka zube a idannuwa sakamakon mamakin kalar fatata da ta yan uwana da jifanmu da kalmar y'ayan talakawa ya saka har ta kaini da daga hannuna na fara jin dadin sauke iskancina a kan fuskarta shikenan mu ba zamu iya ramawa ba dan bamu da yanci? Shi mutun idan ba sarki bane shikenan sai ya zama talaka? Anya kuwa ta san menene talaka? Ba narar arziki bane talaka, mai mataciyar zuciya shine talaka! Aunty kina son ce min dan muna samun matsala da sakarya nunar ranar matarsa ce ya tsane ni ko me na tare masa ne ni? Na ga dai gidan nan wajen kawo kara ne, na tabata ban kasance wace aka fi kawo karana ko na rako gabansa dan shara'a ba a cikin garin DAMAGARAM! Ko shima so kike ki ce min shine dalili?, Aunty kadara cewar wai na bata rayuwar tawa, na zama fitinaniyar na gagari kowa a kasarnan, ina ruwansa da rayuwata da zai sakota gaba?"

Ta karashe maganar tana huci sosai ranta a matukar bace

Murmushi Zahrau ta kuma yi a hankali ta ce" NAJEEBA kitsa min sannu sannu dan Allah zafi fa"

Bata bata amsa ba, dan kuwa ta gama shaka mata ba dadi a ranta

Aunty Zahrau ta ce" Tambayata Najeeba a kanki shine: shin ke zaki tsara rayuwarki ne ba Allah ba?"

Najeeba ta ce" Me hakan ke nufi Zahrau, na isa na tsara rayuwata ne?"

Zahrau ta yi murmushi ta ce" Good, kin san da wannan shine kike haushi dan Allah ya wanzar da ikonsa a kanki? Daga ni har ke har Ummukulsum shin mun san rayuwa zata kasance haka a kanmu? Kin taba tunanowa cewar ni Zahrau zan auri sarki, sarkinma mahaifin ZINARIA kuma dansa namiji kwalin kwal ya tafka aikin da zai shigo zanen kadarar ahalina?, wa ya taba kawowa kansa cikinmu wace ta fi mu tsoron harkar maza take gudunsu tun karfinta hakan ne zai risketa? Me ta yi? *HAKURI* ta yi, tana kallon ikon Allah a lokacin da ta gane bata isa ta zana zanen rayuwarta ba"

Dan dago kanta ta yi tana kallon NAKEEBA ta ce" Kina nufin kina son nuna min cewar ke din daban kike a cikin halitun Allah da har kika kai matakin da zaki samu aure mai daraja mai mutunci dan kawai ya kasance mutumen da kike naki zato yana nasa kuma ya zama fari sannan yana da mata ciki harda wace haka kawai kuka tsani junna shikenan kin isa ki nuna ba'a maki adalci ba, Najeeba har ta kai da ke da bakinki musulma kike kina kallonsa dan kin rikice ki ce masa ya sake ki ko auri HUZAIFA?"

Najeeba dake kallon yannayin yanda Zahrau ke magana a sanyaye ta ce" Aman"
Zahrau ta ce" Aman me? Idan bamu isa ba, iyayenmu baasu isa ba, kina son ki nunan bakya tsoron Allah?"

"Aunty wani irin baku isa ba?" NAJEEBA ta fada tana dan nuno hannunta fuskarta na nuna yannayi na tashin hankali

Zahrau ta yi dan murmushi tana dan girgiza kanta ta ce" bamu isa ba NAJEEBA, meye bamu gwada ba? Meye bamu nuna maki ba? Ciki harda mamansa wace ta haife shi ta roke ki, ba wai dan kin fi sauran matansa daraja ko wani abin ba a wajen Allah, aa, sai dan tana yi maki so daya tak fisabililahi sannan ta rayu da son samun iri daga tsatson kawarta aminiyarta? Du kika watsa wannan, yanzun ta kai har kina kallon mutun mai daraja, da mutunci, mai nagarta, mutun wanda Allah ya daukaka, ke dan kin samu dama kike furta masa ka sake ni? Idan har da gaske kike ba zaki iya rayuwa da SHAHEED ba, gwara a yau mu samu Ammi a san yanda za'a yi, ki tashi kawai ki je ki sameta, ki fada mata gaskiyar cewa ke fa ba zaki iya zama da shi ba dan haka a sawake maki, kin san aure Najeeba idan ba so, ba yarda akoy matsala, idan har mace ta tsani namijin komai na iya faruwa, tunda har shi ya amince zai zauna da ke a gaban mahaifinki da yayanki da kuma mahaifiyarsa ke kuwa kin kasa hakura da hakan sai a dauki mataki, ya sake kin ki koma wajen Huzaifanki, mai yiwuwa shine abokin rayuwar taki aman sai kin bi ta kan Sultan kafin ki karasa hannunsa"

NAJEEBA kawai galala ta yi tana kallonta, 'ita? Ta tashi ta je ta samu Ammi da maganar nan? Sannan ita ta rabu da shi ta komawa Huzaifa? Ita kanta tana wannan furuci a kan Huzaifa ne a kan dalilin da bata sani ba, aman yau ko dan dan abinda take taka iya shegenta dan ta kwana da sannin a kilace yake da ya kwace me kuma ya mata saura?'
Kanta ta dukar muryarta a raunane ta ce" Aunty, shi din da ba so na yake ba fa?, ki duba ki ga wai ni ya cewa baya son bak'a, kuma ya auri Nadia Aunty NADIA fa?"

Zahrau ta yi murmushi ta dukar da kanta ta bata damara tsagawa sannan ta kuma daukan wani kitson
A sanyaye ta furta" me kika ji a zuciyarki a lokacin da kika ga wata fuskar a matsayin matarsa bale Nadiarki? Yaya kika ji da ya furta maki baya son bak'a?"

A hankali saurin kitsonta ya ringa ragewa sakamakon irin zafin da ta ji ya ringa dawo mata sannu a hankali,
Tabas ta ji wani irin zafi mai girman gaske, faduwar gaba, da jin an gama wulakantata

Ajiyar zuciya ta sauke tana jin irin yanda idannuwanta suka cika da kwallah, a hankali ta furta " *RAINA YA BACI SOSAI*

wani murmushin Zahrau ta yi a bayane ta kuma aiko mata da wata tambayar da ta sakata tsayar da kitson harma ta kurawa wajen da ta tsaga da tsirarun gashin kan na Zahrau ido,

ZAHRAU ta dago kanta tana kallonta ta ce" Tall me an mata, zaki iya beman sakin ki ne a hannun Ammi, ki fito ki yi zawarcinki, ki samu bakin mutumen da kike hasashe ya aureki a matsayinki na bazawara ku je ku samu irin rayuwar da kike tsarawa kanki ki barawa NADIA da ZINARIYA mijinsu?"

*MIJIN SU?*
Abinda ya fi tsaye mata a kasan zuciyarta, 'aman a kan me Aunty zata ringa yi mata irin wannan? Dan ta tayar mata da hankali ne ta sakata kuka ko dan ta birkita mata lisafi ne? Mijinsu? Ita har ya saketan ne da aunty zata kirayi namijin da ya gama karbar du wani tanadinta ya kare amshe du wani guzurinta sannan ya shiryata kafin ya sakata a jikinsa ya bata rungumar da ya kusan minti biyar a tsaye da ita a hakan ya furta mata kalmomi kamar haka :Ki kula da kanki, ki tsaftace harshen ki, Allah ya sa ki wuni lafia....: ya karashe yana mai kara matseta a jikinsa wanda tuna hakan da ta yi sai da ta ji wani irin yarrrrt a jikinta na ba gaira babu sabar

Du tunanin nan da take, sam bata san har Zahrau ta janye kanta tana kallonta ba
Kwalar da ta cika mata ido ce ta samu damar zubowa a hankali saman fuskarta

Zama ta yi kusa da ita hakan ya ankarar da ita

Dumin da ta ji a fuskarta ta laluba cike da mamaki tana kallon lema lemar da ta lalubo
Zahrau ta harde hannayenta ta ce " zan fada maki gaskiya, kin taki sa'ar samun miji haka mai tsada bayan kina zaune a waje daya, a gaskiyar magana a irin wannan zamani koda kuwa da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment