Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

min rai*
Da sauri ta kawar da dubanta tana jin wani iri a kan jarumin uban y'arta, tunda ta rabu da aurensa bata taba yin wani auren ba, ita ba tsufa ba, ita ba rashin lafia ba, kawai zaman da ta yi da shi ya saka ta kasa gane wani yaren, ta saba sa rayuwa da shi da irin garajensa da fadansa da hayaniyarsa uwa uba da tsarin soyayarsa

Dubanta ta kai wajen DAYABU da Anmy da niyar tambayarsu wai zaman me suke ne? Sai ta ga tsuru ita suke kallo
Sai kawai ta daburce a dan rikice ta ce" Kai meye kake kalona?
Sai kuma ta sosa goshinta ta ce" ka yi ka kai min su makaranta ka wuce aikinka fa? Bana son shashanci ka zo ka wani zauna ana tausarka sai ka ga kanwarka da ka kai gidan miji jiya ba!

Tana fada ne tana kokarin shigewa ciki

Da ido suka rakata har ta shige kafin su kali junna su sakarwa junna murmushi

Zahrau ce ta fito sanye da hijab tana dan sauri ta ce" Anmy, ina zuwa zan je bangaren SULTAN

Anmy ta dan zabura ta kaleta sai kuma ta koma ta zauna a hankali ta gyada mata kai

Ficewa ta yi hankali kwonce ta nufi bangaren

A lokacin da ta shigo abinda ta ganni ne ya bata mamaki, auntyn Nadia ce rike da hannunta sunna tafe a hankali zasu bi ta corridor su shige ciki

Irin tafiar da take Zahrau ta bi da kallo kafin ta kai tsugune ta shiga gaishe shi

Kamar yanda ya saba amsawa hakan ce ta faru kafin ya yi mata nuni da dakinsa

Kanta ta kara sadawa kafin ta mike a hankali ta nufi dakin, zuciyarta kuwa cike da sake sake da son sannin abinda Nadia ta yi a bangarensa da irin tafiarta

Saurin korar abin ta yi a ranta dan gudun kar zargin ya yi yawa ta shiga dakin

Irin yanda ta yi karo da bra, da pant da rigar Najeeba ya sakata saurin shiga nemanta a cikin dakin

Idannuwanta ya sauka a fuskarta hakan ya sa ta nufeta da sauri tana kiran sunnanta a hankali

Najeeba ta buda idannuwanta da sukai mata nauyi ta sauke a fuskar yayarta

Zahrau ta yi saurin dago kanta cike da tausayi ta ce " NAJEEBA, sannu, sannu kanwata

Najeeba ta kara dora kanta a hankali saman cinyarta , a lokacin wasu hawayen suka kara balewa a idannuwanta

Muryarta a raunane ta ce" ban taba sannin Ahalin Mutalab zaku ki saurarena ku min auren nan bayan ina fadi a sannu ina fadi da ihu cewar kar a mun hatsari ne ga rayuwata ba, sai gashi a kaina an fara inda yaya ya nuna min idan na ki zai yi kuka, su ummu suka nuna min ai alkairin kennan, Anmy bata zauna mun zanta ba, Abih bai bani lokacinsa ba, ke kina nesa idan na kira bakya dagawa, sai ga bakuwar da ta zo ta wanken fuska da mari du a kan auren nan?

Zahrau ta ji zuciyarta ta karye, a hankali ta ringa shafa kanta ta ce" Najeebana, zafin ciwo ne ke damunki, idan kika shiga ruwan zafi kika sha magani zaki ji ki garas, ki yi hakuri kin ji? Ki daina fadin magangannun nan a kanmu, Najeeba ba zamu taba juya baya a wajen da zaki cutu ba, kuma iyayenmu ba zasu taba yi maki shiru da gabgan ba, sunna tsoron su saurareki ne ki ci galaba a kansu har su janye auren nan, Najeeba Ummu kuwa kin san halinta, idan tana waje ki kiyayi abinda zai kaita makura, kin mantata ne? Bata son irin halayan nan kin sani sarai a kan zumunci bata saurarawa, Ummu idan muka yi fada zata hade mu ne ta bamu punishment din da da kanmu zamu dawo nemawa junnanmu hakuri, kin manta a lokacin da yaya kan yi fushi da mu irin yanda take zaunar da shi ta ringa nuna masa mahinmancin junnanmu? Ki daina jin haushin ummunmu, domin uwa ce a wajenmu baki daya

NAJEEBA ta cije lebenta tana jin ciwo a zuciyarta ta ce" ba zaki fahimta ba, Zahrau, ba zaki fahimci abinda ke faruwa da rayuwata ba, kin ga, ashe shine muke zama a stade, kuma shine muka buga basket ball, Zahrau, ya wulakanta ni, ya nunan ba kowa bace ni, ya kawo Nadia ya kwo........

Rufe bakinta Zahrau ta yi, a hankali ta ce" ki yi hakuri

Iya kalmar da ta fada kennan kafin ta shiga kokarin kamata
Du irin abinda take Najeeba na kallonta ne kawai, domin a tunaninta wannan bacewar shinfidar da har ya bushe nata ne
Shirun ta mata dan ta lura bata so ta yi mata bayanin abinda ya faru,
Lebenta ta kara cijewa a lokacin da Zahraun ta fita dan zuwa ta samo wata suturar kafin ta tafi da ita

Aman Allah ya taimake ka, tun jiya ka bani amsar eh zan dauki abin shinfidar amaryarmu, dan me zaka hanna a yanzu bayan kai ka fada?
Muryar Zinaria ce kw bayani a sanyaye Shaheed kuwa na sauraronta

Wayarsa ta kara yin vibration din mesage
Yana dubawa ya ga sakwon eh za'a samu waje sosai a jirgin da zai shigo daga niamey sannan ya wuce agadez

Amsa ya turawa yaron nasa wanda ke kula da shagonsa na kayan gini cewar a je a ciro tiket na iya adadin mutanen da ake bukata

Dubanta ya yi yana karantarta,

A hankali ya ce" na wanke abin shinfidar, yana hankalce da ita

Da karfi ta ce" Meh? Ka wanke? Wani irin wankewa? Kai ne zaka yi wanki? Ko dai bata kawo budurcin nata ba?

Duban da ya sauke a kanta ne ya sakata saurin yin shiru da maganarta sama sama

Da sauri ta dan duka ta nemi afuwa sannan ta mike ta nufi hanyar bangarenta kamar zata fadi

Tana zuwa ta karasa da saurin jikin mahaifiyarta tana kuka ta ce" wai ya wanke, wani irin wankewa? Shine zai wanke?

Mahaifiyarta na shafa kanta tana cije lebenta, ya wanke? Idan har ba'a samu jinninta ta haka ba, bata tunanin akoy yanza zasu yi su samu
Sai dai zasu kwatanta ko yayane

Yana nan zaune har Zahra ta dawo ta shige ciki

Bata jima sosai ba ta fito sunna tafe a hankali kan Najeeba na saman wuyanta

Tsayar da ita ta yi ta karasa ta duka ta dauki alkyabarta ta dawo a hankali ta rufa mata kafin ta kara kamata su nufi hanyar fita

Idannuwansa ya dago daga kallon gefen da yake ya sauke a bayanta, wani yam yam ya ji a jikinsa hakan ya sa ya cire dubansa daga kanta yana kallonsu har suka fita sannan suka dauki hanyar coridor din da zai kaisu bangaren Anmy

Haka kawai ya dan kurawa waje daya ido, ba abinda yake gani sai abin nan da yatsarsa ta dangwalo
Nan da nan ransa ya ringa baci
Bacewa mai tsanani
A kasan zuciyarsa kuwa ya furta" *ta zo ta baka nutsuwa, shin haka ta mike a gabanka ka tana wajen da ka yi niya?* idannuwansa ya kara rintsewa da karfin gaske yana jin kansa na neman kwasan ciwo

Mikewa ya yo da sauri yana koran tunanin nan ya nufi hanyar fita

Rumfa zai je wace aka kama macizai har uku a cikinta a jiya,
Mugayen macizai ne masu baban dafi
Macizan na cikin gidan ne, a yau dai zai gansu da ransu, a yau zai dauki hannu na mai su

Tabas tun yana yaro aka koya masa harkar wasa da maciji, zai iya cewa a kusa kusan nan a cikin gidan sarautar du kalar macijin da aka yarje a shigo da shi to fa sai ya san wanda yake da damar iya kula da shi dan kar a shigo da wanda zai bace ya jiwa mutane

A kaf masarautar nan basu san cewa yanda ya lakanci abin har ya fi karfin tunaninsu, domin bayan koyon da akai masa ya kara zurfafa iliminsa ta hanyar karantarsu da komai ta computersa

Tun da ya fito ya ja turus ya tsaya sakamakon irin busar da aka kwasa

Ashe fa akoy hawa dawakai?
Irin yanda ya ga matasa na laye sun sha damara da manya manyan mutane harda datijai kowane na tsaye ne rike da linzaminsa ya saka shi sakin dan murmushi

Hannunsa ya daga ya yafito amintacensa dake tsaye kusa da wani ingarman doki ya sha kwaliya yana rike da linzaminsa, wato dokin da zai hau ne

Tunkaro wajensa yake yana karantar irin tsayuwarsa

*Hala har ya tare da mace ne a cikin matan?* shine tambayar da ya yiwa kansa

*HALA JAR YA SAMU NUTSUWAR DA YA HANA MASA SHI YA SAMU?*

yana karasowa ya kai kasa ya hade hannayensa ya sada kansa ya furta" *JA GABA KAKE JAN GWARZO, FARO KAKE MAI FARAR ZUCIYA, YA KAI MIJIN ZINARIA, MIJIN GIMBIYA NADIA DA GIMBIYA NAJEEBA, SANNUNKA DA FITOWA HASKE, HASKENKA HASKE NE MAI HASKA DUNIYARMU, SANNU DA FITOWA NAMIJIN MAZAJE, SANNU DA FITOWA MAI GIDAN RANA, SUN BUGU SUN BUGA SUN KASA, GURNANI KAKE MAI TARWATSA TARON MAZA, KAI NE DAYA TAK MAI WUKAR YANKA MAI DAMAGARAM SARKIN SARAKUNA, MATASHI NE MAI ABIN MAMAKI, MAI MOTSA ZUKATA KODA BASU SHIRYA BA*

Murmushi ya saki yana lumshe idannuwansa, kansa ya dan sada da dubansa ya sauke a kan Amintacensa
Namiji ne gabjejen gaske wanda yake ji da shi,
Wannan shine babar kyautar da masarautar Garin Agadez ta taba masa wace har gobe yake jinta har cikin ransa, kyautar Amintacensa kyauta ce da ba zai iya mantawa ba, a da soja ne, ya sadaukar da haka dan bauta masa, shi kam me zai iya bashi ne dan ya gode masa? Shi ba bawa bane, ya bashi sarautar dogaran Fada baki daya, yana da salary wace ta ninka ta sojojin har uku, yana da gida a waje da fada da mota har biyu kyautar sarki ne

Dan rage muryarsa ya yi da niyar ya tsokane shi kasa kasa ya ce" yaushe zan maka wankan ango?

Shima murmushin ya yi ya kara sada kansa hannayensa jimke bai daina yannayin kirarin da yake ciki ba

A hankali ya ringa takawa manya manyan dogaransa na yi masa kirari, da sauri amintacensa ya janyo dokin ya nufo shi da shi

Danndukawa ya yi dan ya taka ya hau kamar yanda aka saba

Sai dai ga mamakin duban jama'ar wajen wani uban tsale ya daka ya dane saman ingarman dokin nan
Ai kuwa zo ga ji wani irin busa da ihun gardawa da kirari, nan fa tsumi ya motsa aka haukace aka dane dokunna

Lalle Sarkinsu ya fito a shirye, dan haka du suka haye suka yi baban filin sukuwar Fada aka shiga gabatar da sukuwa cikin tsari da zaburar da zuciya inda wajen ya cika makil ana ta kai kawo ana murna


A hankali ta je ajiyeta saman gado, sai dai ta kasa zama ta kwala yar kara tana mikewa tana kara wara kafafuwanta da muryar kuka ta ce" Aunty, barkono a kasana, ki yiwa Allah mu je asibiti kar a je na farke

Auntynta ta juyo tana daria tana kallonta, a fili a bayane ta ce" sakaryar wofi, NADIA, kin bani mamaki, wai ki budi baki kina hauka gaban kishiya? Ni yanzu da Allah tsaya min na taimaka maki

NADIA ta kaleta da kyau ta yi murmushi ta ce" Aunty kennan, ni NAJEEBA ba kishiyata bace, kuma na rantse da Allah zan yi ta zuwa ina gaisheta ina neman afuwarta har ta sauko,
Aunty, ni ? Ba zaki turani na yi mata gaba ba, ni? Zan mayar da ita kishiya? Idan har na yarda na shiga layin kishiyarta kin ganni nan ko? Sai kin kasa gane wacece ni! , a jiya har fada kike ashe bata damu da shi ba?

Ni kuwa ina da tambaya Aunty,

*MENENE AINAHIN DASA TSANARSA A ZUCIYARTA?*

kin san menene? Aunty zan baki mamaki idan na furta maki dalilin madaukakiyar tsanar da ta fara yi masa harma ta ringa neman makusarsa ido rufe shine daga wani fada da suka yi da matarsa ta budi baki ta ce da ita *BAK'A, MAI BAKIN ANIYA, KIN MATSAWA RAYUWATA KAMAR WATA KISHIYARKI, BAYAN MIJINA KO A KAFARSA AKA KULA BAK'A ZAI CIRE YA YAR NE, BAKYA GABANSA HAKAN YA SA NAKE TAUSAYA MAKI!*

NADIA ta yi murmushi tana kallon Auntynta ta ce" a ranar da suka suka yi fada a kan abin nan sai da ta ringa maimaita kalmar nan sai sitin da uku ina irgawa

Hannun Auntyn ta riko ta ce"




Happy juma'at>ØzÝ

*Yan uwa ina k'ara gode muku, Allah ya bar k'auna.*>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



41


Ta ce " Aunty, a kan me zai mata zafi har haka?

Bayansa, su ranar da aka ce ana taro na gidansu zaki ga ta rasa me zata saka, a saloon ta saka wannan ta cire
Mitarta daya ce" ka je ya ringa hararanka kamar wanda ka fito tsirara

Auntynta ta girgiza kai ta ce" ke dai ta baki tsoro ne, ai Nadia komai isarka da tunanin kai din wani kwaro ne ai akoy gabanka, so nake y'ata ta kasance jarumar Sarki Shaheed, so nake baki daya ki doke su! Nadia, wai kin ga fuskarsa? Yaya kamaninsa suke?

Nadia ta yi wani irin tsam kafin ta saki murmushi ta saka hannayenta ta dafe kumatunta, a bayane ta ce" tabas rabo ya kaini zama matarsa, in ba haka ba ban isa na shigo layin wace zai iya duba ba

Me kike nufi? Auntyn nata ta tambaya cike da zakuwa

Nadia ta ce" Aunty, walahi rawanin nan da yake shine rufin asirinmu, da ace buda fuskarsa yake da kirarsa da mun shiga uku da mata, Aunty, Shaheed baki ba zai fadi kamaninsa ba,

Murmushi ta yi ta mike ta nufi bayi dan tara mata ruwan wanka da gashi

Da kallo ta bi dakin a karo na biyu, Ac sai yi yake dakin sanyi sosai

Aunty na fitowa ta ce" Aunty, ba'a kashe Ac din nan ba tun jiya?

Kamata ta yi ta mike suka nufi bayi

Sunna shiga ita da kanta ta cire zanninta ta ajiye, auntyn nata na jiranta dan ta san sai sun sha kokowar zama a cikin ruwan dumin ta ce" wato Nadia bacina na jiya, wani irin baci ne na yi mai salama
Daidaya nake fada maki Nadia na yi a dakin cen
Ac na hura kofofin fatana, Nadia baci ne na yi da salaba , lokacin sallah na yo tar tar a cikin kunnayena kiran sallar tamkar a dakin nan,
Na so na ki tashi na kara juyawa sai dai cikin ikon Allah irin karatun da aka yi tamkar a azumi ya hana min rintsawa
Nice yau da bin masalaci sallah? Lalle Nadia wannan gida baban gida ne
A yanzu na daina zagin dangin kishiyarki, koda kuwa suma daga gidan sarautar suka fito aman na daina zaginsu da suka zo wajenta suka tare

Nadia, ba yinwa, ba kishirwa, ba shara, ba wanke wanke, ba wanki bare guga, Nadia ba zagi ba duka, ba zafi, Nadia wajen kwonciya a gyare ga wani kamshin turaran wuta da basa gajiya da sakawa
Nadia ina mike ina shating ina hasko kaina
Haba ina, zan je na duka na yi masu salama na dawo na taya ki zama, Nadia ni dai ko cin uwar taki Najeebar zata yi ko? Ba inda zaki, maganar tafia ki bara mata mijima bata taso ba

Nadia na daria tana dan tsoma kafarta a ruwan da ta ji ya yi zafi sosai ta ce" Aunty, ni sulhu nake nema da Najeeba, ni kaina a jiya kafin na san waye shi nake fadin na bara mata
Aunty, ni kam zaman lafia nake so da Najeeba, aman ba zan iya barin SULTAN ba

Daria ta yi ta ce" ko ke fa yar, wato kin ga maza kin kasa kawar kai ko? Wahalar bata firgitaki ba?

Nadia ta ringa daria ta ce" ta firgitani, aman kuma ta kara min kwarin gwuiwar zama a shashena...
........................................

Ruwa masu zafi ta hada itama kafin ta yi kokarin kama Najeeba

Tun daga yanda take kin son cire doguwar rigar jikinta ta dan fara kokonto

Bata kawo komai kanta ba dai har ta talafa mata ta shiga ruwan nan

Irin zaman da ta yi a cikin ruwam ya saka gaban Zahrau mumunan faduwa

Da sauri ta mayar da hannunta na hagu ta kara taba zafin ruwan dake dauke da abubuwan kamshi

Tabas yana da zafin da ko lafiarka kalau zaka ji tsoron shigarsa bale ita da take tunanin miji ya zo mawa

Da sauri ta kalli Najeebar, abubuwan da ta gani saman shinfidar a bushe fa? Sannan ita kanta a jikinta ta ga abubuwa su fa na meye?

Duban fuskar Najeebar ta ringa yi kafin a sanyaye ta ce" gardama kikai masa Najeeba ko me ya faru da ke?

Najeeba ta kai dubanta kan fuskarta
Haushi ya sakata kin yin magana a wannan lokacin sai da Zahrau ta kuma fusta"kin ga, ki rufa min asiri ki bani amsar dake min yawo a raina, ki rufa min asiri ki bani amsa yaya zan saka ki cikin ruwan zafi haka baki ji zafi ba? Bayan na ga alamun da suka nuna min mijinki ya zo gareki?

Shirun da ta kara yi ne ya saka Zahrau kara shiga yannayi na damuwa, fuskarta na rikidewa zuwa kalar wace zata fashe da kuka ta budi bakinta a hankali ta ce" meye damuwarki? Hala ba ke ya zowa ba? Hala da wata ya tara a ranarki?

Najeeba ta yi rauraurau ta budi bakinta da yannayi na bacin rai kasa kasa ta ce" me kike son ji? Yawan maganana da bacin rai na? Me kike son ji? Na kuma maimaita maki shirmen da ba yanda zaki iya yi min?

Hannayenta dake kusa da nata ta riko ta dago tana kalonsu ta ce" ban taba gannin wulakanci irin na jiya ba, tabas ya gama anfani da Nadia ya dorani saman datin jikinta

Ido Zahrau ta rintse da karfi tana kawar da kanta

A sanyaye ta lumshe idannuwanta tana jin du wani waje da harshensa ya ringa bi a jikinta kafin ta ce" Zahrau, kin san wani abu?
*NA TSANE SHI!*

Zahrau ta lumshe idannuwanta itama kafin ta janye hannunta ta mike a hankali ta ce" ina jiranki, ki gama ki fito

Da sauri ta juya ta fita, ita kuwa ido ta lumshe ta kara zama cikin ruwan nan, tabas ya ci galaba a kaina a yau,
Ya bi min jikina da kallo,
Idanma da gangan ka lashi fatar jikina SHAHEED na maka alkawarin sai na saka ka son lasarta da hauka hauka, Idanma da zumar wani lamari na zuciyarka ka hade lebena da naka Shaheed, Na maka alkawarin sai na haukata yawun bakinka
Shaheed sai na zabura mafarkin ka,
Shaheed sai na hana maka sukuni!
Na rantse matanka ba su ne abokan gabana ba! Domin na yi imanin WA MAN TASHA'UNA ILA AN YASHA ALLAHU RABUL ALAMEN.

Zahrau na fita ta ci karo da Ummu zaune tana kallon kofar

Ido hudu suka yi da junna, Zahrau ta sada kanta ta yi niyar fita a dakin

Ummu ta yi murmushi ta ce" Zahra, zo mana

Zahrau ta fasa fitar ta karasa wajen Ummu tana kallonta

Ummu ta kuma yin wani murmushin ta ce" ina zaki je ki fadi matsalar yar uwarki? Ba dai Anmy zaki fadawa ba?

Zahrau ta dago tana son goge hawayen dake cikin idannuwanta a sanyaye ta ce" Ummu, tana cikin damuwa, yaya DAYABU ya fada mana sai mun kai zuciyoyin nesa mun kawar da kawunnanmu, inaga shima dan ya kauracewa haduwa da ita ne yake iya hakurin gannin hawayenta
Ummu, meye mai karfi tsakaninsu haka? Na zata Najeeba zata iya hakuri, aman Ummu aminiyarta Nadia fa ya aura, sannan a jiya Nadiar a bangarensa ta kwana, ba abinda ya faru da Najeeba

Ummu ta lumshe idannuwanta tana kokarin murmushi a bayane, a sanyaye ta ce" Eyah, shine zaki je ki fadawa Anmy haka?

Zahrau ta bar hawayenta sauka a fuskarta sosai ta ce" na gaji ne da gannin yannayinta a haka, kanwata ta kasance macen da a wajenta nake daukan darusan kecewa da daria komai bacin raina, ita ke kara saka min kaunar na rayu a zuciyata, ita ke kara saka min nutsuwa idan har hankalina ya tashi, Ummu, na gaji da ganninta tana hawaye a kan auren nan, na ga alamun shima ba so yake ba, itama haka to a kan me zasu yi ta wahala har haka?

Murmushi ta yi ra kamota ta zaunar da ita tana hangen yan kafafuwan Najeeba daga wajen kofar da alamu ta karu tana jin me za'a ce

A hankali ta ce" shine zaki fada mata ta raba auren?

Zahrau ta kuma sauke ajiyar zuciya harda yar shashekarta ta ce" ashe shine wanda ke tafia suke haduwa a stade wajen da take zuwa shan iska? Shin bibiyarta yake yi ko menene? Ummu, idanma aurensu ba mai mutuwa bane a sama mata yancinta, ba zan iya motsawa nan da cen ba har sai na ga abinda zai faru ya faru da kanwata, Ummu, a wajen Najeeba muke koyon murmushi komai bacin ranmu, ba zan yarda farin cikinta ya gushe daga rayuwarta ba, walahi su Ummulkhair jiya kuka suka yi kamar me, Ummu yaya kwana ya yi muna mesage da shi hakan ya sa tun karfe shida yana gidan nan , mun yi niyar yau mu hadu mu duka mu sakata murmushi sai gashi ya kara bata mata?

Ummu ta yi murmushi dai kafin ta ce" Zahrau, sai nake gannin kamar kun so kanku da yawa, idanma wani abu ya hada su fushi da junna me zai hanna ku yi bincike dan gano kusababin wannan rashin jituwa tasu ta hanyar zama ku tambayi kanku da kanku wacece kanwar ku? Wannene Sultan Shaheed?
Bara na fada maki waye SHAHEED,.SHAHEED mutun ne mai son kare martaba da mutuncinsa da na duk wani wanda ya sani bare na dan uwansa
Shaheed a duniyarsa ya tsani mace mai rawar kai da neman fitina
Shaheed ya kasance mai son mace mai wahalar ganni ga maza
Zahrau, Shaheed fa shugaba ne
Zahrau SHAHEED yana da dama da yawa a rayuwa, sannan idan yau ya ki kallon Najeeba meye dalili?
Inaga baban dalili a nan shine yana jin haushinta, yana jin haushin halayanta, a abinda na fahimta kennan
Ke kin san wacece kanwarki a fannin tara samari
Wayarta na hannuna , labarinta na kai mini daga inda na fito

Dan shiru ta yi ta ce" bama wannan ba, zaki fita kanki tsaye ki tarbi Anmy ki nuna mata Shaheed na takura yar uwarki Zahra ko kunya bakya ji bakya jin nauyi? Kin san irin yanda ta ci burin auren nan da irin lokacin da ta jima tana son haka ya kasance kuwa? Kin san burin anmynku kennan kuwa? Kin san baban tashin hankalinta a yau ta ji wani abu na faruwa tsakaninsu ne, bare har abin ya fito daga wajenku? Zahrau idan da amana ruwa ba zai ci gwani ba, idan har da kunya ba zaku iya daga kai ku nuna wani lamarin ba, Anmy wacece a wajenku? Ko kuwa sangartar da ku da tsananin soyayar da ta nuna maku ne zaku saka mata da shirme?

Najeeba ta lumshe idannuwanta a hankali ta ja jikinta ta koma wajen wankanta

Darzar jikinta ta shiga yi cikin nutsuwa

Sai da ta gama sannan ta koma gaban madubi ta yi tsaye

*ANMY* tabas idan har su din y'ayan halal ne zasu so saka alkhairi da alkhairi,
ANMY, uwa ce a wajensu mai kuka da damuwarsu ta yi farin ciki da farin cikinsu

Ta kasance mai sadaukar da farin cikinta dominsu mai rungumesu a kowani hali
Du irin fitintinnun su bata taba gajiyawa ba , takan tarewa ta dauki jifan da akaiwa kuka

Gashin kanta ta warware ta shiga yin wanka dan ta tsaftace jikinta

Sai da ta gama ta dauko dan karamin tawul ta nade kan nata kafin ta kurawa madubi ido

Murmushi ta yi a bayane tana gannin yanda fuskarta keda kumburin kuka da rashin wadatacen barci

Lale ta yi mantuwa guda, ta manta su waye Y'yayan mutalab, ta manta idan ta tayar masu da hankali sosai ba zasu iya rikewa ba, au kuwa zasu tayarwa da Anmy ne
Lale ta manta girman alkhairin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment