Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

koma yaya ne ya mana in sha Allahu "

A hankali Najeeba ta maida dubanta kan Nadia, zata iya rantsewa bata taba jin wani abu ya tsirga mata mai kama da wanda ya tsirga mata a yanzu a kan Nadia da furucinsa ba
Idan bata manta ba a
Jiyama ya yi maganar sai ya karo aure aman bata damu ba, sai a yanzu da ta lura da furucinsa kamar irin na serieus din nan ne sai ta ji wani irin lamari na kamar bata ji dadin jin hakan ba, sannan tana kallon Nadia sai ta ji wani iri, wai yanzu Nadia ce kishiyarta? Wace suka hada miji tare? Yanzu abinda ya yi mata a shekaran jiya Nadiama ya mata? Akoy wasu manyan kalamai da ya furta mata wa'inda har yanzun idan ta tuna sai ta ji wani irin yar yar yar, shin itama Nadia haka yake fada mata? A hankali ta fara watsi da kalaman, ta fara kushe su da rage masu karfi a zuciyarta bale har su lahantata

Kuma duban Nadia ta yi, ta san wacece Nadia, a da Nadia kan cewa ita burinta ta auri mai mace ta yanda zasu gwabza rayuwar kishi, kowa halinsa ya kwace shi, ita kuwa sai tace bata son mai mata domin bata taba tunanin wani ya tauna nama ya bata ta tauna itama

Idannuwanta ta lumshe, haka kawai sai ta ji wani irin abu na sukarta a cikin idannuwan nata, a hankali ta dago jin ya daga waya muryarsa kasa kasa yana magana da alama da Yaya Dayabu yake wanda ya shiga garin Niamey a jiya kafin ya ajiye ya dago subansa su yi ido hudu

Janye nata idannuwan ta yi cike da jin haushinsa, haka kawai ta ji wani irin haushinsa ya tsirga mata, wai yanzu zaunar da su ne ya yi yake fada masu zai kara aure? Me yake so su ce da shi? Da su suka saka shi hukunta matarsa ne,?

"Ohk, fine" abinda ya fada kennan kuma ya yi shiru na wani lokaci kafin ya dora da fadin" ki fada min yanda kike so Nadia "

Kanta ta dago ta kuma kallonsa a karo na ba adadi sannan itama ta sauke ajiyar zuciyar, ta maida dubanta wajen NAJEEBA ta ce" dai daya ya yi ko Najeebana? "

NAJEEBA ta lumshe idannuwanta ta komar da bayanta a hankali ta jingina jikin kujera, kanta ta iya dan dagawa a sanyaye sannan dake

Sai Nadia ta ce" Alfarma nake nema Allah ya taimake ka, kafata bani da lafia bana iya komai da ita dole sai nai jinya, idan har da hali ina so idan auntyna ta zo mu je gida tare, ba dan na raina kokarin AMMI ko gazawarku ba, MAMA yanzun ba zata kuma zama da mu ba, ni kuwa na tsorata sosai, ina neman alfarmar na je koda sati daya ne na kara warwarewa....."
Ta idasa maganar tana sada kanta kasa

Shaheed ya kwashe minti biyar yana nazarin maganarta, ta gama sarewa cewar ba zai bata amsa a kan hakan ba, sai ji ta yi ya ce" wani wajen maman ta ce da ke zata tafi ?"

Da sauri ta dago kanta tana girgizawa, sai kuma ta mayar ta sada cike da tsoro, ita a ganninta an maida auren mama me zai sa ta kuma zama a nan kuma?

Shaheed ya lumshe idannuwansa yana kallon NAJEEBA, haka kawai yannayinta sai ya ringa taba nutsuwarsa, wannan dakewar da ta yi sai yake so ta dago koda tsokana ne ta yi yana kallonta

Dan ya kara kular da ita, wanda ya tabata sai ta kale shi , haka kawai jikinsa ke bashi idan ya fadi haka zata kale shi
Sai ya ce" Ni kuwa na yi baci ta yaya bayan kina nesa da gidana ? "

Da wani irin madaukakin mamaki NADIA ta kai dubanta kansa, a lokacin kuwa ya yi iya yinsa ya cire dubansa daga cikin idannuwan Najeeba ya dora kanta ya sakar mata san murmushin da ya sakata jin wata irin nutsuwa a cikin zuciyarta

Tana sada kanta ya maida dubansa kan fuskar Najeeba, ya ci gaba da fadin" idan ta zo zaku tare a bangaren da ba'a bude ba, na kusan bangaren BEEBAHH, a cen za'a baki dukan kulawar da kike so, sannan zan saka jakadiya ta kai maki kati biyar kina iya rabawa wa'inda kike son su ringa shigowa gannin ki, aman fa daga satin nan zaki dawo nan ladanki "

Murmushi ta saki tana kara rage tsayi daga zaunen da take ta ringa gabatar da godiyarta

A hankali ta kai dubanta wajen NAJEEBA, sai dai gannin idannuwanta a lumshe sai ta shiga kokarin mikewa dan zuwa ta amshi maganinta, sanan ta tabata zai bukaci yin magana da matarsa

Tana tafia a hankali ya maida dubansa sosai kan NAJEEBA, kallonta yake da kallo irin na son dole ya karance ta

A hankali ya ciciba daga inda yake ya koma kujerar dake kusa da ita ya zauna

Hannunsa ya dora saman nata dake jimke kadan saman cinyarta hakan ya sa ta buda idannuwanta a karro na biyu sunna kallon junna

Muryarsa ciki ciki sosai ya ce " sai na ga kamar ranki ya bace dan na yabi matata "

Dan yawun da take tunanin ta bari a bakinta ta tatara ta hadiye da kyar sannan ta fuskance shi, itama a sanyayen ta ce" anya ba sai ka je asibitin idannuwa ba kuwa? Domin dai idannuwanka sun fara baka gannin da ba daidai ba "

Kallonta yake bai bata amsa ba

Sai da ta ja hancinta a hankali ta dora da fadin" yaya zaka yi tunanin zan bata rai a kan auren da biyaya nake kawai?, kamar yanda baka so inaga nama fi ka so, dan ka san yanke min nishadi aka yi rana tsaka "

Bata karasa maganar da take ba ta ji saukar lebensa a kan nata, idannuwansa kulle sosai ya kama lebenta ya shiga basu wani irin horo mai zafin gaske wanda ya sakata saka hannunta tana ta son ture shi, aman ko gezau saima da ya ga dama dan kansa ya sake ta
Bai yi nisa da fuskarsa a jikin tata ba ya tsatsareta da kakausar murya ya ce" dan ki gane idan mai wuri ya zo dole mai tanarma kan nadewa, beebah ko kina mutuwa kina farfadowa ne kin harmatarwa wani, koda kuwa zaki hadiyi zuciya ne sai kin dandani azabar da kika kwashe shekaru kina dandana min, beebah meye samari basa fada maki, wayarki a hannuna sakon tsohon cen ya shigo cewar ki bashi nutsuwa?, sannan baki dadara ba kike ci gaba da neman fitina a gare ni, ba zaki gane ba, ba zaki taba gane komai ba, aman ki sani ina daf da dauke numfashinki ki dawo na kuma dauke shi ta hanyar hade bakin ki da hancin ki na rufe ki suma harma ki leko kiyama idan ta kama, domin ni narka min dalma da kike a wajen da ba zaki taba hasashe ba a sannin kanki ya fi karfin sumarki, beebah ina maimaita maki ki bar balaki ya yi baci, idan ba haka ba zaki haka mana ramin da zamu rufta ya halaka mu !"
Ya karashe maganar da kakausan murya tare da dantse lebenta na kasa da dan karfin da ya sakata fashewa da kuka ta saka hannayenta bibiyu ta shiga dokawa a kirjinsa ido ryfe ta ce"













My kaina=ØÞ
[3/31, 11:30 PM] BAK'A CE: >ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



60



Hannayenta bibiyu ta shiga dokawa a kirjinsa idannuwanta rintse tana jin wani irin tashin hankalin take sukar mata kahon zuciya, meye wannan? Me ke damunta haka? Me ke kara gudun zuciyarta ya dada mata zafin jiki ya hasasa mata fitar numfashi da sauri ya sababa mata bacin rai a kan furucin farin mutun mai mata SULTAN SHAHEED ne? So take ta buda idannuwanta ta samu karfin gabatarr da fushinta a kansa, aman a irin abinda take ji da zufar da take fitarwa sai ta fara tunanin idan har ta buda idannuwanta tabas idannuwansa masu dauke da zanen kwali zasu hadiye nata hadiya irin wace maciji kobra ke hadiye dan uwansa a lokacin da suka tsinci kansu a waje na rashin abinci, zai hadiye su ne murus ta yada zata rasa idon duba a gabannan

Tsoron hakan ya sakata idannuwanta a rufen nan muryarta a zafafe ta ce" Ni balakin nake so na tayar, ta yanda zamu rufta a ramin nan kasa ta rufe kawunnanmu kowama ya huta " ! Sai kuma ta sanyaya muryarta a hankali ta kai kanta saman kirjinsa, wanda ke rufe da riga ta ciki da malun malun sai fitar da dadadan kanshin nan yake, muryarta a sanyaye wannan karron ta ce" Kana shigo min da garaje, kana taka ni da takama, shin meye ya sa kake son nunan takama ne bayan ni ban san wani sarki ba a miji? SHAHEED na san cewa kake bani da kunya, na cika tsauri, bana so ka daina tunanin hakan domin bana tunanin zan kasance mai yi maka kirari" a sanyaye ta idasa tana mai dora dayan hannun nata a saman kirjinsa wanda hakan ya saka shi lumahe idannuwansa yana jin kalamanta,

Wani irin yannayi yake jin kansa, tun daga kan kwakwaluwarsa har zuwa zuwa cen kasan zuciyarsa, lamarin mai girma ne mai tafe da abin kunce balakin da yake mata ikirarin ta barshi ya yi baci, wannan lamari ya kire ahi balaki ne tun daga ranar da ya samu fasarar abinda ke damunsa game da wannan yarinya mai halayen yan nanaye, sai ya dauki lamarin nan ya yi wani irin katon akwati mai matsatsen ciki ya saka shi, ya saka katon makuli ya rufe shi, ya yi ta kara jibga masa jibga jibgan laifukanta ta yada zai kara matsanancin nauyin da babu mahalukin da zai iya tashinsa harma ya bude shi ua falasa sirrin da ya boye a cikinsa

Sai dai kash, gashi nan rana tsaka, a irin lokacin da bai shirya ba bayannuwarwa a rufe ruf ya watsar da kaso saba'in a kan dari na laifukanta, hakan ya sa du wani kusanci nasu ke girgiza laifukan nan harma ya fara jin barazanar dake son mayar da shi wani dan yaro,

Lebensa na kasa ya dan cije a hankali yana jin yanda take sauke ajiyar zuciya, a hankali ya dan lumshe idannuwansa da sukai masa ja, ya kara bata kyakyawar rungumar da ta sakata yin lamo a jikinsa

Bai ce da ita komai ba, sai mikewa da ya yi da ita a jikinsa
Idannuwansa ya sauka a kan iyayen mazaunanta, masu wani irin tudu da fadi hakan ya saka shi lumshe idannuwansa a hankali ya kara riketa a jikinsa ya shiga dan tafia da ita ba tare da ya dauketa ko ya takura tafiar tasu ba

Batai masa musu ba, haka kawai ta kasa yi masa musu din, ta yarda da binsa cikin zuciya daya har suka shige hanyar da zata sada su da bangarensa

Bai zame ko'ina da ita ba sai saman kujera mai zaman mutun daya
Shi ya fara zama kafin ya dorata saman cinyarsa ya kuma likata da kirjinsa ya mayar mata da kanta irin yanda ta yi da farko ba tare da ko ya cire malun malun din jikinsa ba

A hankali ya ringa shafa ualwatacem gashin kanta, muryarsa ciki ciki ya ce" Yaya kike tunanin zan yi wasa wajen kawowa rayuwarki cafka?, ido rufe abokiya nake nema, koda kuwa zamu ringa fada ne, wace zata dube ni ta ce da ni SHAHEED nake marari, rashin kunyar NAJEEBA sai ta ringa sakani...........,
Sai kuma ya yi shiru na dan lokaci wanda har shirun nasa ya sakata dan fara budaumsasun idannuwanta tana dan son dago da fuskarta dan ta kale shi, sai dai bai bata damar hakan ba ta hanyar mayar da kan nata a hankali ya ce" Ki yi komai ba komai yarinya "

Dan murmushi ne ya subuce mata wanda daga cen kasan zuciyarta ne ya fito, harma aka ji dan sautinsa

A hankali ta ce" zaka sakar min abokina? Bashi da wani laifi a fadan da aka yi ka sake shi, domin shi ke ciyar da mahaifiyarsa "

Shiru ne ya biyo baya na lokacin mai dan tsayi harma ta cire rai da zata ji amsarsa sai ji ta yi ya ce" na tura shi daukan soja, idan ya fito sai na aura masa mata hudu, kin san ina son mutun mai son farantawa iyalina rai "

Baki ta saki dan mamaki harma ta dago baki dayanta, irin yanda yake binta fa kallon kasa kasa ya sakata turo bakinta a fili ta ce" yanzu dan daudun ne ka kai daukan soja?"

Bai bata amsa ba, a yanda yake kawai yake bin du wani motsinta da kallo har ta idasa mikewa gaba dayanta ta kara turo bakinta sosai a fili ta ce" Ba dai rigima kake so da ni ba? Zamu yi, zan fadawa Ammina a sako min aboki haka kawai? Malan walahi ni bana son tashin hankali, bana son fada da maza haba, ni kaucewa mutun nake aman ana bi na, garinka a dake yake a tankade daga kai har Nadiar , hasalima ba zan iya zama da mijin kawata ba! "

Murmushi yake ta dokawa a kasan zuciyarsa, a hankali ya dan muzguta dan yana son cire babar rigar nan ya samu damar kallon drama girl din nan tasa hankali kwonce, sai dai hakan ya tsoratar da Najeeba a tunaninta mikewa ne zai yi a kanya sai kawai ta juya ta fala da gudun balaki ta shige dakinsa tana kokarin danno kofa

Yar daria ce ta subuce masa ya raba bayanta da kallo har ta shige tana son rufewar, kansa ya ci gaba da dan jujuyawa a hankali a kasan zuciyarsa kuwa fadi yake 'yarinyar ba dai kujera ba, ka ga sun hanna mata gudu yanda ya dace sai kwana take abinta yar rigimamiyar'

Yana kokarin tashi ne wayarsa ta kuma daukan tsuwa

Sai da ya cire rigar ya ajiye ya koma ya gyara zamansa a hankali ya ce" NAJEEBA, ki fito ki ciyar da ni na shigo da yinwa "

Bakinta ta turo daga wajen da take, tana ta ayanna yanzu tsakani da Allah magana ne ya mata a hankalin nan kamar zata ciro daga bakinsa? To ita ta yayama yake so ta fito ta bashi wani abinci bayan yanzu ta gama zanenta hankali kwonce? Sai kawai ta yi mukus tana sauraron irin yanda ya amsa salama cikin nutsuwa kafin ya dan saurara

Cen ya mike tsaye domin baya so ko da wasa su ji wani damuwa tsakanin junnansu, dan kawai yana gudun lamari na kishin mata ne

A hankali ya ce" Allah ya ja da kwana, haka ne, kwarai laifin Zinaria ya kai wajen da ta ja har na bata saki "

Ajiyar zuciya da wani huci mai dan zafi na takaicin gurbataciyar tarbiyar da y'ayan nasa mata suka samu daga wajen mahaifiyarsu,
Muryarsa a dake ya ce" Gimbiya ki daina min ihu a kaina, idan ba haka ba zan dauki mumunan mataki a kan ki! "

Shiru SHAHEED ya yi, domin ya fahimci muryar kukan da magana sama sama da yake ji na mahaifiyar Zinaria ne

Sarkin Agadez ya ce" Alhamdulilah, Allah ya sa hakan ya zame mata izna da ita da dukan wani mai halayanta ko wanda halayenta ke baiwa sha'awa,
Dan saurarawa ya yo kafin ya dan kara karya muryarsa ya ce" ina rokom Alfarmar a sasauta fushin, idan har da hali ta koma dakinta koda nan da shekaru ne "

Sai da SHAHEED ya dan saki dan murmushi a hankali ya ce" in sha Allah, burina ta gane rayuwa, ta gane abubuwa kamar haka : Dan adam ba abin wulakantawa bane komai rashin arzikinsa ko mumunan kamaninsa, ina so ta bambance mahinmancin zaman aure da zama domin ta birge kawayenta, ina so ta koyi sannin cewa mulki ko sarauta kafin ta hau dubanta sula hau, kuma suka sauka suka bari, a yanzu a matsayinta na yar sarki matar sarki tana iya amsa kiran mai duka, za'a kaita ne daga ita sai farin likafani sai hali sai sallah, ta gane ita ba kowa bace ko a wajen Allah daga bakin sa'in da ta dage kai da fata ita ba zata bi dokokin Allah ba, ina so ZINARIA TA SAN RAYUWA : , ya dan nisa ya dora da fadin " hakan ne ya saka ni mikata ga gidan horo na ahalin cikin gida "

Murmushi ya saki mai sanyi , kafin ya furta" Dama na san kai din adali ne, mai nazari ne, mai sowa dan uwansa abinda yake soea kansa, tabas na yi imani da cewa da ba dan ta samu gurbataciyar tarbiya ba da ta jima da fahimtar cewa adali, zababe, managarci ne Allah ya wanke ya bata, da ta jima da fahimta ta karba harma ta koyar da wata waye mijin da take aure, sai dai kash, sannan a gaskiya ka yi hakuri SULTAN SHAHEED, gidan horon Damagaran yar karamar aljannar duniyar mabukaci ne, ba zata taba shan wahala ba domin kuwa abubuwan da ta rasa kadan ne a ciki, zata dan hakura ne har a fitar da ita ta ci gaba da daukan banzayen hudubobi, ama idan har ta samu kyakyawan horo, zata je ta hada labari ne harma ta kwabi bakin du wani mai sakata aikata mugun abin, dan haka daga bakin lokacin da za'a samu sakamakon bincike cewar ba hannunta a rasuwar marigayiya da kuma kokarin son kashe yar uwarta za'a miko mana ita ne sai mu bata horon da ya dace ga marar kunya! "

Wani murmushin SHAHEED ya yi, kafin ya shiga mika godiyarsa cikin jin kunyar sakar masa y'a da ya yi aman kuma shine har ya fahimce shi haka

SARKI na ajiye kan wayarsa ya maida dubansa wajen mahaifiyar Zinaria dake ta rufe bakinta dan kar ta saki kuka tun karfinta domin kuwa bata so ko da wasa kishiyoyinta su yi gaba da ita

Kai ya girgiza a kausashe ya ce" wato bawa ba zai taba yin asara irin ta yayi asarar uwar y'ayansa managarciya, tabas asarar kudi ko wata kadara ba zata taba kamo asarar rasa mata ta gari ba "

Kansa ya dan girgiza a hankali ya warware nadin dake kansa sai da ya sauke ya ajiye ya ci gaba da fadin" meye wannan nadin? Me ke tatare da shi bayan tarin hatsari da tarin tashin hankali?, a wannan nadi bawa na iya haduwa da halakarsa, a wannan nadi kana iya kwonciya cikin fushin ubangiji, a wannan hadin zaka iya rasa lafiyarka, nutsuwarka, wadatacen lokacin kanka kai idan ka yi wasa harta sa ibadar ba zaka tsayar ba.....tabas nima wannan nadi ya min ilah, daga bakin lokacin da ya dauki girman kai, neman fitina, izgili, hayewa a kan matata da y'ayana mata, haka kuma ya hanna min wadatacen lokacin da zan ringa hankalta da irin abinda ke wakana da ahalina ta hanyar fahimtar yaya mu'amalarsu take da talakawana, da jama'ar garina koda kuwa sunna boyewa a cikin gida, a tunanina matar kirki nake aure da ita harma na kasa tunanin cewa tarbiya fa ba iya mace kawai ake sakarwa ba, dole ka kama a matsayinka na namiji, dole ka rintsa tsawatar da abubuwa da dama ciki kuwa harda iyalan naka....."

Shiru ya yi ya sada kansa, cen ya dago yana bin su da kallo ya ce" sai gashi nima na baiwa mulki madaukakin darajar da iya shi kawai yake da lokacina, shi kuwa sai ya samu wannan damar ya yi min ilar da ya lalata min tarbiyar y'aya, ya kara baiwa matata kofar lalata tata tarbiyar ita kanta "

Sai da ya share zufar dake keto masa sannan ya kausasa muryarsa ya tsatsare su da duban da du suka kara shiga hankulansu ya ci gaba da fadin"" Sai dai ba zan kuma sakacin nan ba, ina mai tabatar maku zan yiwa mulki rashin kunya ta hanyar kiyaye masa na yi masa jan ido na nuna masa mahinmancin iyalaina, da ni kaina, yarinyata mace ta aikata laifin da ya fitar da ita daga gidan miji, sanadiyar hakan zan kaita dakin horo na cikin masarauta cen cikin bangaren bayi! "

Gaba dayansu abin ya dake su, ciki kuwa harda Zahrau da ta san da maganar rigimar aman bata san saki ba da kuma decision din mijin nasu

Ai kam a yanzu sai Gimbiya ta kasa rike kukanta, a bayane ta fashe da wani irin kuka ta budi bakinta ta ce" me na yi da tsanani haka?, me ya sa komai ke son juye min kuma ake gannin laifina? Haba adalina, haba uban gidana me yasa a yanzu kake yanke hukunci mai tsanani a kaina? Haba aban yarimana, me ya sa kake son ido rufe sai ka wulakanta ni a gaban makiyana?, ka duba ka ga matar yarima yanzun ta sameni da kukan wai ya tafi Damagaram, shi SHAHEED din maimakun ya fara kiranka ya maka bayanin laifin da ta yi sai takardar saki ya turo maka maimakun kaima ka sakar masa kanwarsa sai ka bige da wani rarashinsa?, shin meye laifina ko na y'ayana dan mun ki kishiya?, kishi haram ne? "

"Ki min shiru ko na sabauta maki halitarki na saba kamaninki na gigita kwakwaluwar ki a wajen nan ke Baratu!" Muryar Sarkin Agadez ta karade wajen ransa a bace ya dora da fadin" tir da matar dake takama a kan kowa, BARATU ni ne sarkin ama ko ni da kin samu da kin mulke ni, kar ki yi tunanin a zaunen da muke ban san komai a kanki da kan irin rayuwar da y'ayanki ke cakulawa a gidajen aurensu ba, idan baki manta ba a zaman da kuka yi a dakin Zinariya nazajen y'ayanki sun masu magana cewa idan suka kai gobe su kam kar su dawo masu gida, baki yi tunanin maganar mai tsauri bace? Ni na tura masu da sakon hakan aman sai kika kasa ganewa domin ke din banzar uwa ce!, kin kai ni wajen da zan dauki mataki a wajenki BARATU! Tabas ba zan zuba ki a cikin dakin horon bayi bisa hujata na kin yi sake da tarbiyar y'ayana ba, ama zan tura ki gida ki nuna masu halayanki, ki gwada masu wacece ke, su ga irin wulakanta sun da kike yi, na tabata mai martaba sai ya mayar da ke baiwa kaskantaciyar baiwar da bata da wata daraja domin kuwa sam baki da halayan y'ayan sarauta!"

Yana gama fada a kausashe ya mike ya bar komai a nan ya nufi cikin uwar dakansa

Gimbiya, wato BARATU ta rasa wani tunanin zata yi a zaunen da take, tabdijan, za'a turata gida? Da tsufanta gode gode da ita? Zuwa gidanma a matsayin a saka ido a halayanta? Ita kam ita ce zata he gidansu a haka? Lalle da ta gane bata da wayo domib kuwa yayanta dake kan sarauta sai ya nuna mata bata da wayo, mahaifiyarta kuwa dama mace ce da sam basa shiri tun bata kawo yanzu ha domin kuwa tun da ran mahaifinta take alwashi a kan halayanta, a yanzu haka sai su yi kwana uku basu gaisa ba, ba dan komai sai dan tana kiranta zara kama yi mata fada a kan rayuwa

Tana nan wajen zaune har su Zahrau suka mimike suka bar wajen, domin su dai koda sun so rarashinta su nuna mata hanya ita din ba mai sauraronsu bace, idanma bata ce sun mata magani da mijinta ana son rabasu ba ai da kyau, hukunci sarki kuwa ya aiwatar da shi daidai yanda ransa ke so, dan kuwa kwarai hakan ne giyar sarauta ta dauki zuciyar Gimbiya da wasu daga cikin y'ayanta ta hura su ta yanda sun samu wani irin hauhawa da tunanin kaf duniya babu wanda zai iya kamo su ciki kuwa harta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment