Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kasuwa, ko ina numfashin karshe aka daura min shi zan mike na murje ido na ce bana so!

Gaba dayansu da mamakinta suka kura mata ido, lale ta cika mutun mai karfin hali,
Yanzu itane ke fadin haka a kan sarki?
Ummulkhair ta ce" aman an fadi ba nauyi, an ji kunya
Na tabata yau Anmy ba zata iya rintsawa ba idan ta ringa tunowa kin nuna kin fi son wani dan daudu a kan yaronta!

Najeeba ta yi shiru jikinta du a mace tana kallonsu idannuwanta suka ciciko da kwallah
A sanyaye ta ce" Ummu, Huzaifan ne dan daudu? Ummu Huzaifa ba dan daudu bane na rantse
Kuma kin ga, ban taba sannin yaro zai juri iya shegena sai da na zauna na ringa masa yana taro ni
Ummu, ina son Huzaifa har raina, ya jima yana fama da ni
Meye laifin Huzaifa?, saurayi tsayaye yaro mai jinni a jika
Ummu, Huzaifa ya iya sangarta ya iya hira ya iya yi min kallo irin na mutun mai daraja
Ummu me ya sa zaki zagar min shi bayan shi zan aura nake so na zama uban y'ayana?
Ummu, kin manta irin namijin da nake so?
Huzaifa du ya hada abubuwan nan Ummu, shine tsakani da Allah dan ki tayar min da hankali zaki zage shi ki ce da shi dan daudu kuma ummu dan kawai na nuna aa ba ni ba sai ki ce na tayarwa da Anmy hankali? Ni yaya kike so na iya yin bacin ne? Ummu aunty Zahrauna kan sadaukar da farin cikinta domina
Na tabata da itane ake magana a kanta, da ba zata taba kawo sunnana kusa ba dan ta san idan na tsani abu na tsane shi, zata amsa ne koda kuwa hakan na nufin karshen numfashinta
Ummu, a hannayenku ta barni ashe ta yi aikin banza shine kuke tayar min da hankali fisabililahi?
Ta karashe wasu irin hawaye na zubowa daga idannuwanta kafin ta juya da gudu ta yi cen ciki

Kafarta ta daga zata bita hankalinta tashe
Da sauri Ummukulsum ta riko hannayen nata
Maidota ta yi kusa da ita kafin ta bata kyakyawar rungumar da ta sakata itama fashewa da kukan tana girgiza kanta ta ce" walahi zan amshi auren nasa koda kuwa matarsa zara kashe ni, ta daina kuka ina sonta ban yo haka dan son kaina ba

Ummukulsum ta ringa sauke ajiyar zuciya a hankali ta ce" zata fito ne, ta yi mana haka dan ta saka mu, mu kwana muna kuka hankulanmu tashe
Barta zata fito ne ummu, aman in sha Allahu rigimar Sultan da mutanen dake tare da shi kaf cikinmu ba mai iyawa sai Najeeba

Shin baki ga tsarin tafiarta ba? Tamkar dawisu haka take tafia cike da takama tana baza albarkatun jikinta ba tare da tana yi da gangan ba

Shin baki ga irin yanda take iya saka idannuwanta cikin nasa ba? Waye yake da wannan kokarin bayan ita din?

Shin baki ga ranar da ta daga hannu ta wankawa Zinaria mari a gabansa ba? Hakan na nufin koda a gabansa ne ba zata taba bari a takata ba!
Tabas tsana, ko na ce wani baban lamari na faruwa tsakaninsu wanda mu kanmu mun kula da irin rashin daidaituwar yannayinsu dake faruwa a tsakaninsu
Aman wannan lamari kam, inaga na Allah ne!


Ummulkhair ta ce" idanfa suka yanke ni ce zan aure shi?

Ummukulsum ta ce" haka Allah ya tsara, koda ke ce zaki je ki rayu da su in sha Allah babu abinda zai same ki face wanda Allah ya kadaro maki!


Baki dayansu shi suka saka gaba a lokacin da suka roke shi shin ya amince su je su fadawa Allah kan zabi biyun nan Allah ya dora su a kan wada ta fi dacewa da shi

Ya san da sannin cewa ba zai kubucewa auren yar gidan Mutalab ba domin an rigaya an fadi maganar, abinda yake son bakinsa ya buda ya fada shi ne" *NA ZABI UMMULKHAIR* , sai dai lamari na kasancewarsa baba a wajen na mulki ya saka shi harshensa yin nauyi
Gannin abin yake wani iri,
Ba zai iya buda baki ya furta masu zabinsa ba domin shi, shine mai danne zuciyar wasu, shine mai daukan dukan wasu, shine mai shanye damuwar wasu
Abu daya ya san zai yi shine, zai roki cewar a saka auren da za'a masa tamkar wani yaro da zabinsa shima
Mahaifinsa ya masa auren fari
Ya yi na biyun da kansa ba'a je ko'ina ba ta rasu
Gashi mahaifiyarsa zata masa auren uku da matar da shi kansa yake cikin faduwar gaban kar ta masa zabin da zai saka shi mutuwa dan bakin ciki
Yana so a bashi damar daukan mace biyu a rana daya, zabin da suka yanke da wace zai zabowa kansa ya aureta a cikin sirri
Sam Zinaria ba zata iya da lamarinsa ba, so take ta kashe masa lamari yana da karfinsa da kokarinsa haka kawai
Auren da za'a daura masa kuwa idan Ummulkhair ce itama me zata iya masa? Yarinyar da shekarunta duka duka ba zasu zarce ashirin da hudu ba,?
Sam baima kawo maganar idan kuwa Najeeba ce ba, sai dai kura masu idon da ya yi wanda hakan ya saka Anmy sanyaya muryarta ta kara kallonsa ta ce" SHAHEED, ko kaima ba zaka auri y'ata ba?

Da sauri ya kalleta, sai kuma ya maida dubansa wajen DAYABU

Kansa ya kara sadawa a hankali ya buda bakinsa ya ce" ko wani zabi kukai min, in sha Allah zan yi biyaya
Sai dai, ina da wani muradin auren wata yarinya, ina fatan za'a hada su biyun a rana daya

Namijin duniya kennan, haka Dayabu ya fada a kasan zuciyarsa

Abih kuwa murmushi ya yi a fili ya furta" wannan ai abin murna ne, Allah ya tabatar mana da alkhairi

Su duka da amen suka amsa kafin su mimike Dayabu ya nufi dakin Anmy da Nusaiba dan ya shinfideta domin ba zai kula kannen nasa ba, ya kula idan ba ya nuna masa da zafi zafinsa ba zasu kawo raini a lamarin

A lokacin da suka zo tafia gida sai Abih ya shiga motar Dayabu

Har ya tayar ya fara tafia Abih ya yi murmushi yana girgiza kansa ya ce" ina hangen rigima a wajen yan biyuna, NAJEEBA, ko UMMU? sai dai da son kai irin nawa sai nake jin bana so a kara yi masu kishiya duda na kasance ni ina balawa mata tikitin zawarci bama na basu damar yin zaman kishin

Dayabu ya yi murmushi ya ce" Abih, ka manta Ummu, sun yi zama da maman Bilkisuu fa

Sai da ya lumshe idannuwansa a lokacin da ya ji sunnan *UMMU* mahaifiya a wajen NAJEEBA, shi yakan kirata da UMMU, sauran kuwa sukan ce mata mama
Murmushi kawai ya yi yana tuna lokacin, zamanin nan ya kasance tamkar wani zaburaran doki a tsakanin matan nan biyu
Ya ga rayuwa ya yarda cewa mata sunna suka tara
Murmushi ya yi a kasan zuciyarsa kuwa fadi yake" me ya yi zafi haka da aka guje ni an matana? Na kai zuciyar cikin duhun da ta kasa yafe min?
.............................................

Ba yanda bata yi da dogaran dake tsaron kofar bangaren ZINARIA kan su barta ta shiga tana da sako wajenta mai mahinmanci, sai dai sam suka ki amoncewa domin ita da kanta ne ta nuna ba zata karbeta ba tana hutawa
Haka dole ta samu ta kwana gefen fulani domin idan dare ya yi haka ba mai fita daga fada sai da kwakwaran dalili

.............................................
Sam bata samu ta rintsa ba, sakamakon maganar yar uwarta cewar ta saka Anmy a cikin bacin rai
Idan ta juyo daga kan gadonta ta hange su sai ta ji uwa ta je ta cicije su ko zata huce, sai kawai ta ji baki daya kewar yayarta ya hana ta rintsawa domin ta tabata da ita ce da ba zata taba yi mata fushi haka ba

Suma bangarensu sun matukar yi kokarin gannin sun watsar da fushinta gefe, domin idan har suka biya tabas zata saka su a damuwar da zasu kwana sunna kuka ita kuwa da safe ta warware ta yi tafiyarta!

Kiran salar fari a kunnayenta ya sauka
Dira ta yi daga gadon ta yi bayi ta dauro alwalah
Sai da ta zo ta saka doguwar riga saman ta bacinta sanann ta yane kanta ta shiga gabatar da sallah

Tana nan zaune har aka kira sallar asuba ta kuma gabatar da ita cikin nutsuwa ta shafa fatiha da sauri ta mike ta yi bangaren Anmy bata kula yayun nata ba

Tana zuwa ta shige da salama kasa kasa kafin ta karasa da dan saurinta wanda ita ganni take sauri ne take yi ta duka gaban Anmy wace ta gama sallah tana jan carbi

Kanta a kasa tana jin hawaye na son zubo mata ta kamo hannayenta ta dora a gefen fuskarta a sanyaye ta ce" Anmyna, wai da gaske na bata maki rai wai har kin kwana baki yi baci ba?

Anmy dake jin kaunar yar a ranta ta ce" in ji wa?

Najeeba ta ce" ba aunty Ummu bace ta fada?

Dan murmushi Anmy ta yi jin ta ce da ita auntu Ummu, yau ummun ce auntyn,
Kanta ta dan girgiza tana murmushi ta ce" aa, ma baby girl ba zata bata min ran da zan riketa haka a zuciyata ba,
Me ya samu idannuwanki suka kunkumbure haka?

Murmushi ta yi ta ce" ban yi baci bane Anmy

Anmy ta kara shafa gefen fuskarta a sanyaye ta ce" tashi ki je ki kwonta cen ki huta maza

Mikewa Najeeba ta yi tana jin hankalinta ya dan fara kwonci dan yannayin da Anmy ta nuna mata ta tabata an bar maganarta

Doguwar rigar ta cire ya mata sauran wata yar rigar baci baka wace bata idasa rufe cinyoyinta ba sannan daga saman mai gidan mama ne wada ake kira rabin nono ya kasance saman a bultse suke rabin ne suka rufe

Ba abinda ya shafeta dan ta san ba mai shigowa bangaren Anmynta, kuma gaban Anmy kuwa zir ne kawai bata yi

Hayewa ta yi saman lafiyayen bed din Anmy mai sansanyen kamshin turaranta ta yi kwonciyarta tare da rungume yar kanwarta dake ta baci
.........................................
Kamar yanda ya saba da duhu duhu yake shiga dan gaisheta
Hakan ne ya faru, a lokacin da ya daga labulen dakinta ya sanyo kansa
Idannuwa masu neman fitina suka sauka a kan fitsarariyar yarinyar nan wace ya yi mata kallon shari'a daya tak ya yi gagawar cire idannuwansa yana jin wani nishi na kwace masa kamar mai cutar athsma

Da sauri ya saki ya juya ba tare da ya shigan ba, domin gani yake sam bai dace ya shiga a irin wannan lamarin da mace ke kwonce da irin wannan shigar bayan ba muharamarsa bace!

A wannan rana Najeeba bata fita saloon ba, sai da aka yi salar magariba ta fito cikin shirin abayarta lurub har kasa ta cewa Anmy zata dan leka ta dawo a tsaitsaye

Da adu'a ta bita tana mai yin dan murmushi
Irin yanda yarinyar ta fi sauran yan uwanta kulawa da ita ya saka take mata so daya tak da babu irinsa
Kwana bakwai dai suka dauka zasu sake zama su dukansu tana adu'ar Allah ya yi zabi na alkhairi

Tun da ta zauna a wajen yau ya fahimci halin da take ciki

Shima zaunen da yake hotunnan tsala tsalan yan matan da aka turo masa ne yake bibiya yana son gannin wace zata iya da shi?

Kuma dago shanyayun, lumsasun, idannuwansa masu shige da na mashaya da kuma dauke da kwali ya yi ya kai dubansa a kanta a karo na bakwai
Haushinta yake ji sosai, ta zo ta wani zauna masa a wajen da ya rigayeta kamawa a nan yake zama, bayan yana cike da haushinta na har wani ta ja mahaifiyarsa na hada sunnansa da nata, yo shi Allah ya tuba idan aka ce za'a aura masa wannan yarinyar a ranar zai cire rigar sarautar ya je da gudu ya tari katuwar mota ta murje shi da ya ga takaici! Me zai yi da masifafiya, yar balaki, balagazar mace? Ai shi auren nan da zai yi na hutu ne ba na jazawa kai balaki bane!

Sai da ya dani zuciyarsa kafin a sanyaye ya furta" *wa ya taba ki? Sai nake ga hankalinki tamkar ba a kwonce ba, hakan kuwa kwata kwata ya dauke min nutsuwata*

Dagowa ta yi tana kallonsa, yauma da alama ya yi gudu ne dan da kayan gudun a jikinsa sai mahaukacin basket din takalmin dake kafarsa wanda yannayinsa zai tsadanta maka tsadarsa
A hankali ta cire kanta ta dan daga kanta tana kallon taurarin wajen
Muryarta a sanyaye itama ta furta" *ina cikin tsaka mai wuya ne, ashe haka zaman juran amsa yake? Ina cikin gararin rayuwar da kila wa kala ne idan har zan kai labari, domin kuwa da na yarda da abinda zai iya kasancewa da ni gwara a ce bana duniyar!*

Da matsanancin mamaki yake kallonta, aurensa ne take fadin da ya kasance a kanta gwara ta rasa ranta? Ita din wacece da har take tunanin tana da girman matsayin da shi zai yarda ta amsa sunnan matarsa? Ashe aurensa zai iya kuntata mata rayuwa har haka? Tabas da ace zai iya da ya je da kansa ya roki a aura masa ita ko dan ya ringa kallon yanda zata yi har ta mutun
Sai dai ina, irin yanda yake jin kyankyaminta ba zai iya wannan kasadar ba

Sai da ya dan cije lebenta na kasa kafin ya furta" me ya yi zafi haka NAJEEBA? wani irin abu ne wannan dake damunki mai tsanani? Ki fada min ni zan yi maki maganinsa domin Najeeba ina jin ki har cikin zuciyata yanda na dauki kanwata haka na dauke ki

Juyowa ta yi tana kallonsa
Sosai ta ji dadin maganarsa, wada ta so a ce yayanta ne yake fada mata dadadan kalamai haka

Kanta ta sada a hankali ta mike tsaye

Kuma dubansa ta yi a sanyaye ta ce" wannan rigimar cikin gida ce, ni din, bana iya fadin sirrin Ahalina

Tana gama fada ta yi gama cikin wani taku na ban tausayi domin gaba daya jikinta a sake yake hakama tunaninta ba a jikinta yake ba

...........................
Bayan sati daya

Da yamaci ne suka hadu a bangaren mai martaba,
A tsakanin wannan sati dayan baki daya y'ayan sun cika da zulumi da tashin hankalin abinda zai faru
Ko a yau basu san cewa za'a yanke abinda aka yanke shawara ne hakan ya sa suke cen wajen harkokin su, Najeeba na saloon, Ummu na wajen aure
Tun da aka yi maganar nan Dayabu da kansa ya dakatar da Huzaifa kan ya bari zai waiwaye shi idan hakan zata yiwu

Likita kuwa ba'a bashi damar shigowa bama sai dai a waya suna soyewarsu tamkar ba gobe

Abih du suke kallo a lokacin da ya gama adu'a, kafin a sanyaye ya dago dubanza cike da gamsashiyar amsar da zuciyarsa ta bashi, haka kuma malaman da ya rarabawa kan a taimaka suka shaida masa ya budi bakinsa cikin nutsuwa da kamala ya ce" ALHAMDULILAH,
ba wanda ya isa godiya sai Allah
Alhamdulilah da Allah ya dora mu kan amsar da ta tara mu a yau
Dubansa ya kara kaiwa wajen Anmy dake zaune tana sauraro a hankali ya ce" BILKISSU, du wajen wanda na yarda da kamalarsa, da datijantakarsa , da irin shaidar adininsa da na kaiwa maganar nan ya nuna min ya yi abin a cikin kwana shida, ya yi kwana uku da sunnan kowace
Wasun kuwa sunnan Ummu kadai na basu
Wasun kuwa na Najeeba

Tabas Allah ya kawo amsa,
Amasar nan kuwa ita ce

*NAJEEBA*





BALIN BALIN BALI
>Ø#Ý>Ø#Ý>Ø#Ý>Ø#Ý>Ø#Ý wata wakar indiya[2/12, 4:04 PM] Ummu Sadeeq: >ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



32


Irin yanda yayi wani dum a zuciyarsa na lokaci d'aya ya saka shi rintse idanuwansa da k'arfi.

"Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une! Me ke shirin faruwa a tarihin rayuwarsa? Shi? SHAHEED, shine da auren wannan yarinyar?"

Bud'a idanuwansa da suka rigaya suka cenza kala yayi da niyyar budar bakinsa ya furta masu magana kamar haka" *Aa, ba zan lamunci auren fasik'a ballagazar mace ba, ku yi hak'uri ku nema mata wani*."

Idanuwan nasa ya fara saukewa kan DAYABU

DAYABU kansa na sade ne, ya kasance zuciyarsa ta cika bugawa mai tsananin gaske domin ya tabbata ba zai amshi maganar Najeeba ba
yana da damar k'iyawar, kuma idan ya k'iyan ba abinda za'a yi
sai dai sai ya kasance ya had'e hanayensa biyu dake rawa rawa cike da tsoron amsarsa yana ta adu'a a k'asan zuciyarsa.

A hankali ya kai dubansa wajen Abih
Sai ya ga Abih ba a zaune dangalgal yake ba, shi bai san yar tsamar dake tsakaninsa da yarinyar ba hakan ya saka farin ciki ke kwonce a kan nitsatsiyar fuskarsa amsarsa kawai yake jira.

Dubansa ya maida kan Anmy.

Irin yanda ta bi ta marairaice fuskarta zaka rantse cewar jira take ta ji amsarsa ko ta suma ko dad'i ya sakata kai sujada k'asa, irin kallon da take masa na jiran jin amsarsa ne, hakan ya saka ta d'an langab'e kanta sannan ta k'ura masa ido tana sauraronsa.


Sau biyu yana k'ok'arin gyaran murya dan ya furta abinda ke cikin zuciyarsa cewar ba zai yiwu ba, Alkhairin ta kai shi wajen wani, sai dai ya kasa d'aga ya d'ora dubansa kan mahaifiyarsa sai ya ji du ya tsintsinke.


" *SHAHEED*." Ta fad'a muryarta har tana d'an rawa rawa.

A sanyaye tace "Sai nake ganin jinkirin amsarka tayi yawa SHAHEED, ko dai ba zaka auri yarinyata ba?"

"EH ba zan iya aurenta ba Anmy..." Zuciyarsa ke fad'a a lokacin daya kasa magana.

ANMY ta ta budi baki da d'an k'arfi tace "SHAHEED?"

Idanuwansa ya lumshe kafin ya kuma bud'ewa kansa ya cire daga dubansu da k'yar ya bud'i bakinsa ya b'amb'aro maganar dake ciki ya furta" Allah ya tabatar da alkhairi Anmy."

Ajiyar zuciya ta sauke tana maida dubanta wajen Abih da yanayin farin cikinsa ya fara raguwa.

A hankali ya ce" SHAHEED? Anya kuwa mun yi maka adalci a maganar nan? Ya dace ka fad'i ra'ayinka domin kai dai yanzu ba wani yaro bane da za'a saka ka gaba a tirsasa maka wani abin ba."

Kansa ya d'an girgiza cikin nutsuwa kafin ya ce" Allah ya sanya Alkhairi Abih."

Abih ya sauke ajiyar zuciya ya d'an saci kallon DAYABU ya ga yanzun ya d'ago kansa yana kallon sarkin.

ABIH yace "Yaya maganar d'ayar yarinyar?"

Saida ya d'an jik'a leb'unansa da suka bushe kafin yace "Insha Allahu idan kun tsayar da ranar d'aurin auren ita ma zan gabatar da danginta sai a yi komai a had'e."

Albarka sosai suka sakawa lamarin, Anmy ta k'ara dubansa , a sanyaye ta ce" Alkhairi ne, insha Allah SHAHEED."

Murmushi ya k'ak'aro mata kafin suke mik'ewa su masa sallama.

A baya ya tsaya sai da suka fita ya dawo da sauri.

Wajen da ya tashi ya koma ya zauna.

Kansa sade ya k'ara had'e hannayensa kafin ya d'ago yace "Dan Allah, ka amsheta da zuciya d'aya domin kai d'in mai zuciyar adalai ce, ka zame mata bango, ka zame mata uba, ka zame mata farin ciki ka zamo sanadiyar shiryuwarta, tabbas na san cewar kana yawan tuhumanta kan harda sakin hannuna a yanda take sangartarta, ka yi hak'uri, ka rufa min asiri ka dubi baiwar Allahn nan da idon rahama."

Saida ya gama maganar sannan SHAHEED ya lumshe idanuwansa ya k'ara gyara kwoncinsa a saman kujerar da yake hakan ya saka DAYABU k'ara godiya sannan ya mik'e ya fita.

Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une ya ringa maimaitawa a k'asan zuciyarsa.

Me ke shirin faruwa da rayuwarsa wanda bai tab'a hasashen kawowa a cikin tsarin rayuwar tasa ba? Meye wannan? Yarinyar nan itane zai aura? Waye bai ce yana sonta ba waye bata amsa tana sonsa ba? Waye bata yiwa kwaliya ta yiwa rangwad'a ba? Waye bai ganta da dan wando tana tsalen gudu da ball a hannunta wai ita ta tafi sport? Wani sakarai ne baya son tab'a jikinta? Wani irin zaman aure ne zai yi da ita bayan yana da dar da irin kasancewarta mace marar kamun kai? Aure fa aka ce,
Idannuwansa ya kuma rintsewa yana jin wani irin haushinta a kasan zuciyarsa
Me ya sa kika gama iskancinki zaki kare a gidana?
Har kansa ya ringa sarawa a irin wannan tunani da ya yi.

Kwonciyarsa ya gyara yana mai lumshe idannuwansa da suka yi ja sannan sukai nauyi yana tunanin rayuwa
A yau bama zai je wajen gudu ba dan baya tunanin idan ya fita zai iya aiwatar da wani abu

Tabas Anmy na cikin farin ciki madaukakin farin ciki, hakama yayanta da kuma DAYABU
Sai dai basu cika nunawa ba domin zaune suke sunna kara tsara ta inda zasu hayo mata

Anmy kan ji har gabanta ya fadi idan ta tuna yanda za'a sha fama da ita

Farko, harkar saloon,
Biyu harkar fita
Uku auren kansa da wanda za'a d'aura mata bayan tana tsalen fad'in ai ita ga wanda take so *HUZAIFA*

Abih ya dubi agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa na hagu ya kalli Anmy ya ce" Bilkissu, wai karfe nawa take dawowa ne, na ga lokacin ace ta dawo ya yi gamu dare dare a zaune shiru

Anmy ta kalli agogo itama, mikewa ta yi tana fadin" k'warai, zuwa yanzu ya ci ace sun dawo duba da tun da na dora mata dokar lokaci bata taba kaiwa lokacin bama take dawowa dan wataran har sai ta rigayi Ummukulsum wace ke zuwa wajen lesson da Professor

Wayarta ta gwada kira shiru, hakan yasa ta nemi layin SHAHEED.

Ta jima tana ringin kafin ya d'aga.

Anmy a tausashe ta ce" ALLAH ya taimake ka baci ka yi?"

SULTAN dake zaune saman sallaya ya d'an girgiza kansa yana fitar da hucin zafin dake cikin zuciyarsa ya dan girgiza kai tamkar tana ganninsa sannan ya d'an furta" Ummu."

Anmy ta k'ara tausasa muryarta ta ce "Dama, so nake ka bani number amintacenka, zan yi kiransa ya yi kiran dogarin dake tare da Najeeba, shiru basu dawo ba."

Idannuwansa ya k'ara rintsewa a k'asan zuciyarsa yana fadin" yaya zata yi ta dawo yanzu? Sai ta gama bi kwararo kwararo tana siyen naman bakin titi ta je wajen da ta nasa k'wai ta zauna daga cen kuma idan ta raya mata ai sai ta nufi wani wajen? Yanzu Anmy wannan ce kika zaba min matar aurena?.

Du a k'asan zuciyarsa yake bayaninsa kafin ya sauke ajiyar zuciya a sanyaye ya furta "Ina zuwa."

Kashewa ya yi ya mik'a hannu ya d'auko wayarsa mai d'auke da numbobin du wasu dogaran gidan.

Abin layo layo ne,
DOG NAJ ya kamo kafin ya danna kira.

Daga b'angaren da suke cikin tashin hankali kira ya shigo masa sam bai duba ba ya d'aga ya kai kunnnensa a lokacin kuwa d'an uwan nasa na fadin" Bayan nan ina zamu nufa nemanta? Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une."

"Hello? Hello?" Ya ringa maimaitawa.

Shaheed kuwa na sauraron irin yanda dayan ke ta ambatar" Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une." Hankali tashe yana fadin "Kuma wajen mai nama bata nan, mun je wajen mai ice cream bata cen, mun je stade bata cen, to wai ko dai tana cikin saloon d'in nata bamu duba da kyau bane."

Shima hankalin nasa a tashe ya ce" ba ka ga suturar da ta fita da ita bace a jikin yar aikin nata? Yaya aka yi ta fita bamu ganeta ba?"

D'ayan ya furta" baka gannin yau abin ya kasance da wani irin cinkoso gashi dare ya yi mutane wasu sai fitowa suke wasu na shiga ta yaya kake so mu ganeta bayan yau ko fitilar kofar saloon din ba'a kunna ba."

" *INA TA SHIGA?*" Ya fad'a a dake wanda sai a lokacin dogarin nan ya ciro wayar daga kunnensa da wani irin fad'uwar gaba ya lek'a sunnan da ya kira shi
" *GURNANIN ZAKI*."

Wayar ce ta sub'uce daga hannunsa yayi wani irin sama da hannayensa kafin ya furta "Mun mutu."

Wayar ya bi ya wawura dan kuma kaiwa kunnansa yana mai zubewa k'asa tamkar yana gaban Shaheed d'in hakama d'an uwansa na ganin wannan lamari yayi tunanin lalle wani babba ne a fadar yayi kira idan ba amintacen sarki ba to fa wani babba ne shi baima kawo cewar sarkin ne ba.

"A kashe , ya kashe, Attahir shikenan,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment