Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

da yake idannuwansa a kansu har AMMI ta rufo ta dawo ta tsaya nesa da shi tana kallon ikon ALLAH

Sai da ta sanyaya muryarta daga inda take ta ce"






















Saura =ØÞ=ØÞ=ØÞ=ØÞ=ØÞ=؃Ü<Øûß=؃Ü<Øûß=؃Ü<Øûß=؃Ü<Øûß=؃Ü<Øûß=؃Ü<Øûß=؃Ü<Øûß
[3/31, 11:36 PM] BAK'A CE: >ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



64





A sanyaye AMMI ta ce" Haba Shaheed, kai da kanka ne yau ke marin fuskar Najeebana? Bayan ka san ko musulunci yayi hani da marin mutun? Mari fa cin fuska ne, wani irin laifi ne ta yi mai tsanani haka? "

Idannuwansa ya lumshe sakamakon zafin da yake ji a cen kasan zuciyarsa kafin a hankali ya zauna yana mai kara jimke hannun nasa

Rawaninsa ya idasa warwarewa ya yar a nan kasa sannan ya ja babar rigar da yake jin ta masa nauyi a yanzu ya sabuleta daga jikinsa

Hannun nasa na dama ya kuma kurawa ido, wani irin haushin hannun yake ji a kasan zuciyarsa

A hankali ya kara sauke ajiyar zuciya ya dago idannuwansa da sukai masa jajajir, muryarsa a sanyaye ya ce" So take sai ta kashe ni ido rufe ne? Me na yi mata da zata ringa hada ni da wani dan iska? Me ya fi ni da shi da zata ringa cewa wai tana son sa? Ammi sai kawai ta ringa ce min an mata auren dole itama ba so na take ba? Me ya yi zafi tsakani da Allah da take so sai ta kashe ni cikin ruwan sanyi? Me ya yi min saura? Ta amshe komai, ta gama amshe komai, ran nawama so take ta ga ya fita ko so take na ringa daga hannu a kanta , ko kuwa so take na je na halaka yaron mutane ne? AMMI bana iya yawan maganar nan, ashe ba zata gane yarena ba? "

AMMI ta kai dubanta wajen UMMU da ta taso ta taho, a hankali ta karasa ta zauna itama a kusa da su

Ammi ta ce" Me ka yi mata da ta fadi haka? "

UMMU ta ce" haba Bilkissu, harma tambaya zaki yi abinda aka mata? Fitsaririyar yarinyar nan shin bata san darajar girman igiyar dake kanta bane da zata ringa magana irin na jahila? Inma me ya mata ina hadin ta kwara masa ba sonsa take ba? An fada mata shi son nata yake? NAJEEBA ba sonki yake ba biyaya ya yiwa iyayensa dan an isa da shi, fitsararoyar malan! "

SHAHEED ya kalli UMMU da mamaki, ba sonta yake ba fa ta ce? Kansa ya dan girgiza ya rage muryarsa ainun ya ce" UMMU ba haka zaki ce mata ba, kin ga yanda hankalinta ya tashi da marinta da na yi fa, ni bama wannan ba daga tambayarta ne fa sai ta kama fadan nan, ko sun yi fada da wani ne ni zata tada min hankali haka kawai? "

Tausayinsa ne ya kama AMMI, kwarai yanzun bata da dar cewa yar tata ta gama yiwa yaron nata illah a zuciya, ransa a matukar bace yake, hankalinsa a tashe yake, baki daya jikinsa rawa yake aman kuma ya ji za'a fatataketa ya tare, kar a mata haka, kar a ce da ita haka

A hankali ta ce" MARIAM, wace irin tambaya ce ya yi mata ne? "

Ummu ta sada kanta, tsakaninta da Allah Allah tausayinsa take ji a kasan zuciyarta, kuma ba wai dan ita ta haifi Najeeba ba ko wani abun, sam kawai bata so ya zurfafa har Najeeba ta gane dan kuwa ta san wacece Najeeba

Kansa sade a kasa ya ce" daga tambayarta abinda take sha ta taimakawa yar uwarta dan ta gyara kanta shine ranta ya baci har take fada min wasu magangannun banza"

Su dukansu da mamaki suka kuma kallonsa, sai kuma kunya ta hanna masu hada ido da junna

A hankali AMMI ta ringa murza gaban goshinta cike da mamakinsa, dama haka ne ko likita idan abu ya shafe shi ne yakan rikice ya kasa gane gabas bare yama, kudu bare arewa, to ita yanzu mai zata ce da shi ne? Ta ina zata fara kwatanta masa lamura ne?

A hankali ta ce" SHAHEED, wannan wace irin tambaya ce zaka yiwa macen da ta san darajar kanta? Ai ko mace bata son ka zata iya jin zafin tambayar nan, kaima menene haka da girmanka? "

Kallon AMMI kawai yake cike da mamaki, to wai shi menene laifin da ya aikata haka ne?

UMMU ta ce" aa AMMI, shi din ko ba mijinta bane ai yayanta ne kuma ubanta, bai isa ya yi magana da uta ba dan rashin kunya zata mike tana nuna shi da muciya? Sa'an yinta ne? Ko mahaifinta ya isa ya nuna shi da muciya, ai daraja ce, Allah ya daraja shi dole a bashi darajarsa "

Ammi ta yi murmushi tana girgiza kai ta ce" haka ne, ban ki ba domin a yanzun ko ni da wahala na yi garajen nuno shi da muciya, sai dai dan abin danki ne kina son takewa ki rufe harma ki dorawa yarinya laifi salon gobe ya kara dora hannunsa a jikinta? Idan shi Allah ya bashi darajar kasancewa sarki, ita sai Allah ya bata darajar zama matar sarki, kina so ki ce min itama mulkarta zai yi? Da kuwa na yi tir da ita harma na rantse cewar ba jinnin mutalab da Mariama bace ita! "

UMMU ta ce" AMMI, kar ki yarda ki fadi haka Najeeba ta ji, ki murje idannuwanki walahi a kan Najeeba, to ita waye da ba za'a hukuntata ba? "

AMMI ta kara sada kanta kafin ta dago ta ce" zan fadi gaskiya, iya abinda nake gannin shine gaskiya a kan zancen nan
Ku dai kunna so ku take sanni ku take gaskiya ne bayan ba'a kyauta mata ba, na yarda matar mutun kabarinsa aman an yi wasa matuka da yarinyar nan, an dora mata auren nan ta amince kuma aka hadata kishi da aminiyarta? Nadia fa ta sha kwana a dakin Najeeba, itama haka, su yi fadansu su shirya, shikenan dan ya kuntata mata a laifin da ban san ko na meye ba sai ya aikata haka, duda na san matar mutun kabarinsa, ama Najeeba ta yi kokari kuma har ga Allah ina gannin girman hakurin da ta yi dan kuwa ban zaci zata iya cire kanta ta mayar da komai ba komai ba da sauki haka , dan haka gaskiya a daina, sam bans so, idan kana haka zaka iya hadasa rigima fa tsana a tsakanin matayenka, sannan zaka rasa kwonciyar hankali a wajen du wace ta ji zafinka a zuciyarta, ina kara fada maka mace fa ba hula bace, ka daraja mace, ka kara mutunta mace ! "

Ajiyar zuciya yake sauke a karo na ba adadi, a yanzun so yake ya ganta gashi iyayen nasa sun saka shi tsakiya sun ki barinsa


Najeeba kam AMMI na kuleta sai ta samu kanta da yin shiru na dan lokaci hannunta dafe da kuncinta kafin ta silale kasa ta fashe da wani irin kuka maran sauti mai cin rai

Kanta ta dora saman gwuiwowinta, idannuwanta rintse kukanta take kashirban ta kasa baiwa kanta hakuri
A hankali cikin kukan nata take fadin" Why me?, me na rasa Shaheed da zaka ringa nuna min iyakata? Ka san cewar nima ba da gangan na shigo rayuwarka da matayenka ba, ka san cewar ko da na shigo rayuwarka ban so wata shakuwa ta shiga tsakanina da kai ba, aman shine zaka saka na ringa jin tamkar ni kadai keda kai kana wulakanta ni? Menene na nuna min ka tara da wata bayan ni? Na san dama tunda ka kula matar cushe ai wace ka aura dan soyaya sai inda tunaninka ya tsaya a kanta, na san cewar zaka kulata harma ta ji tamkar ta haukace, aman me yasa zaka nuna min hakan a bayane? ........" Wani kukan ta kuma fashewa da shi har tana girgiza kanta dake sara mata , sai wani irin yamutsawa da cikinta ke

A hankali AMMI da ta baro su da UMMU ta idasa shigowa cikin kicin din

Da sauri ta je ta kashe gaz din dake ci tukunyar ruwan ta tafasa sai bori take tana dan kukan nan dake nuna tukunya ta tafasa

Wajen Najeeba ta karaso da sauri ta duka tana kokarin dagota

Cike da tausayinta ta ce" Sorry baby am, sorry hearty am, ba zai kuma dukanki ba in sha Allahu, ba zai kuma gigin taba min fuskarki ko wani bangare na jikin ki ba"

Kanta saman hannayen Ammi, sai ta shiga tariyo marin, kwata kwata ita bama marin take tunawa ba, mari dai ba yau ta fara sha ba, duda wannan marin sai da ta ji kamar ta fara sakin fitsari sai dai wani takaici da ikon Allah zafin maganarsa ta gyashe zafin marin da ta shigo tana juwa dan jinsa
Bata yarda cewar ta zama jaka a duka ba sai yau

A hankali ta kara lafewa a jikin AMMI tana ta sauke ajiyar zuciya, me ya sa? Me ya yi zafi? Me ya sa yake son yi min haka? Marin nawama da ya yi dan ita ya yi? A kan Nadia?

Idannuwanta ta rintse tana jin dacin hakan a kasan zuciyarta, ba dai matarka ba? SHAHEED na yarda ni bani da wani power ban isa ba, kuma in sha Allah zan tatare tabarmata na daina yaudarar kaina na baiwa masu waje su shinfida, domin bani da karfin kokowa da kai, Shaheed ka gama yi min ilar da idan na tsaya jin bakaken magangannunka ina iya macewa bani da ja da zabinka, in sha Allah zan tsawatarwa du wani banzan tunanina a kanka!

Jin jikinta da zafi ya saka AMMI lalabawa ta mike da ita a jikinta

A hankali ta kama hannunta da kyau ta ce" Na jefa maki dan waken zaki ci? "

Najeeba ta yatsine fuskarta ta girgiza kanta a hankali ta ce" Na daina jin yinwar Ammi, zuciyata ke tashi"

Daidai sun zo fita daga kicin din Ammi ta dan kura mata ido tana kallonta, sai kuma ta cire dubanta tana jaye da hannunta a hankali suka ratsa suka wuce dakinta

Tun da suka fito komai ya tsaya masa, kwata kwata ya daina gane yaren UMMU da irin tataunawar da suke, a hankali yake kallonta har suka bacewa ganninsa kafin ya sauke ajiyar zuciya, Kuka? Kuka ne ta yi fa , kennan marin ya yi mata mugun zafi a jikinta da har ta yi kuka? So yake ya mike ya bi bayanta ama ya kasa wani motsin kirki bale ya iya aiwatar da hakan

Ummu ta ce" SHAHEED "

Dagowa ya yi yana kallonta ya kasa amsawa ta ci gaba da fadin" Ka gane, ba zamu iya tunkarar matarka da wata magana ta gyara ba, bama haka, a nan ba'a haka, aman kai ke aurenta, kaima cikin dabara zaka iya kwatanta mata ba kai tsaye zaka fada mata komai ba, domin idan ka fada mata kai tsaye komai na iya faruwa tana iya daykan maganar ta kaita du inda fahimtarta ta nuna mata, hakan kuwa sam bashi da dadi, sannan ko da wasa ka kiyaye fadawa wata maganar wata, mata matsala ne da mu , kamar yanda ka ga kana fama da shara'ar kishiyoyi kala daban daban wace a kowace safia kafin dare ya yi sai an sha shara'ar abokanan zama to hakan ne, wata rigimar bata taka kara ta karya ba ama take zama baba a yi ta yinta har sai Allah ya yi mata tsawa, baban abinda ke daukaka kiyayar mata idan Mijinsu na nuna bambanci, fifiko, ko ya ringa zancen daya a gaban daya haka kawai, idan kana gaban daya ba ruwanka da takalo maganar kowata mace "

Dagowa ta yi tana kallonsa, kawai waje daya ya kurawa ido, kuma cikin ikon Allah har zuwa yanzu a cikin yannayinsa barin jikin nan ne kawai ya daina aman baki daya yannayinsa ya cenza baya cikin nutsuwarsa

Ajiyar zuciya ta sauke ta mike ta dauko masa ruwa masu sanyi ta mika masa

Ruwan kuwa ya kwonkwade kafin ya kuma dubanta ya ce" Umani ai ita ta ja har na mareta ko? "

Shi fa dama ba damuwa ba ya iya, idan damuwa ta shafi cikin zuciyarsa yakan rasa madafa, idan abu ya shafi AMMI yakan rikice ne, ya iya dakewa a gaban mutane ama idan ya samu wanda zai iya fayacewa damuwarsa fila fila to fa yakan manta waye shi ya kasa rikewa, bare ta tabata Najeeba ta shiga wani hali ne, ta tabata a yanzun Najeeba ta afka a ramin da bata shiryawa hakan ba, ita kanta tausaya masu take su dukansu, dan sun zurfafa tsanar junnansu ne hakan ya haifar da zazafar soyayar da suke aikatawa junna aikin fushi da fasara maganar dan uwa

AMMI ce ta karasa shigowa, rigarsa dake yashe a kasa ta dauke babar rigar sai fitar da fitinanen kanshin turarensa take , dakakiyar shadar mai tsadan gaske ta sha aikin sarakunna milk color ta ajiye gefe ta zauna ta ce" tashi ka je bangarenka SHAHEED "

Duban da yake mata tun da ta fito sai yanzun ya kifta idannuwansa, ya je ina? A cikin wannan halin da ya wankawa Najeeba mari har ta yi kuka?

Ammi ta kuma kallonsa tana hade rai sosai kamar wace bata taba yin daria a rayuwarta ba ta ce" ka tashi ka tafi bangarenka lokacin sallah na gabatowa kuka yaren nan dan wake ne zasu yi ka ga har kwabin nasu ya hadu "

Wajen kwabin ya kai dubansa, robar da Najeeba ke tukawa da kwabeben abin da bai san ko meye ciki ba, sai muciyar da ta saki nan kasa sanadiyar shigar zazafan marin da ya sakar mata, sai kwalbar yaji da abin kwai da mayonaise da lemun tsami da magi

Mikewa ya yi dan bin Umarnin mahaifiyarsa, cikin nutsuwa yake takawa har ya idasa ficewa aman ya bar rawanin nasa da babar rigar tasa a nan

UMMU ta girgiza kanta ta ce" Gaskiya kawata kina takurawa Sultan haba, gaskiya ki daina biyewa wancen sangartaciyar yarinyar, meye lagonsa kuka samu ne zaku fara bashi wahala ko me ? "

Yar daria AMMI ta yi, cike da farin cikin da ta fito da shi, da farin cikin gane idanma SHAHEED na cikin halin matsananciyar soyayar Najeeba to fa itama ta kamu da ita , domin abubuwa da dama sun nuna mata haka tun kafin su samu wannan sabanin, idan ka dauka irin yanda ta yi hakuri da maganar fita saloon, ta yi hakuri da fita yawo, Najeeba ce ke yawan murmushi idan ana maganar shaheed maimakun da, abinda ta fi tsana a yi maganarsa, uwa uba yanzun tana shinfideta saman bed ta bata goro ko zata daina jin tashin zuciyar sai ta yatsina fuska ta ce" AMMI, to ai ba sai ya ringa nuna min ya fi son Nadia ba ko? " sun taru sun sakata a farin ciki, AMMI ta ce" wai kin san wani abu nana, anya yarinyata ba tana da wani abu ba? "

Ummu ta yi murmushi tana gyara zamanta ta ce" Ba yarinyarki kadai ta harbu ba, harta Nadia, dan a zaman da muka yi a dakin cen tare na tabata tana da wata kama "

Idannuwa AMMI ta lumshe sakamakon jin wani irin farin ciki na lulube zuciyarta, Alhamdulilah, Alhamdulilah, Alhamdulilah, ta ringa ambata a fili,
Shekaru nawa sunna dakon jiran samun wannan kyauta?, ashe dai bayan Aliyu marigayi yana da rabon samun wani? Ashe dai ba zai biyota ba daga shi dif haihuwa ta dauke ko sama ko kasa? Najeeba na dauke da junna biyu, hakama Nadia? To ita me zata ce da Allah ne da irin ni'imomin da yake lulube ahalinta da su? Zata kara ninka ibadarta ne, zata ringa barin goshinta a kasa ne tana yiwa mai gaya mai duka kirari, zata ringa kai gaisuwa ga fiyayen halita, sannan ta kara rokar Allah kan ya bara mata yan tayin nan, duda hasashensu ne a matsayinsu na datijan da suka ga yau suka ga jiya suka iya bambance abubuwa da dama na rayuwa

Ammi ta mike tana fadin" Mariam, ki zo mu kira docter ya auna min ita Maryam "

Kamo hannunta UMMU ta yi tana girgiza kanta ta ce" ki kyaleta Bilkissu, idan shi din ne da zai bayana kansa, sam bana so ta san da wani abun a yanzu kin fa san shi kansa cikin baya tashi ciwulwutarsa sai an ambace shi, yanzu zo mu jefa masu dan waken nan sun yi gudun tsira "

Daria AMMI ta yi itama ta shiga tatara kayan tana fadin" Allah ya shiryi Shaheed, ka zo waje maimakun a ringa ihun murnar zuwanka aa, kowa fashewa yake abinsa, kuma ba wata magana yake masu ba da ido ne zai ringa bin su uwa ya samu sabuwar hakita "

Itama UMMU dariar take, nan suka shiga shapter abinda ke faruwa idan yana waje da yaren sunna shan daria

A wannan rana sallah kawai ke tashin Najeeba daga nanauyan bacin da ta ringa yi, sai dan waken nan da ta wuni ci, domin baki daya kwadayinta ya taru ya tare a kan dan wajen

Cen dare wajen karfe biyu ta ga message da numbersa, abinda aka rubuta a ciki shi ne *NA KASA BACI* , ta karanta ya kai sau hudu kafin ta tabe bakinta ta kashe wayar ta ajiye ta juya ta ci gaba da bacinta hankali kwonce

Da asuba ta makara domin har an gama sallar asuba sannan ta iya mikewa jiki du a mace ta shiga wanka
A lokacin yan uwanta du sun fara aiyukan gidan da ya zame masu jiki, kowace ta kama aikinta, da farko tana jin hayaniyarsu dan sun share dakin sun cenza abin shinfidar, sai dai daga baya sai ta ji diffffffff a lokacin kuwa Ummulkhair na kakaba daria muryarta sama sama

Idasa broshing din bakinta ta yo, dama ta yo wankanta ta daura alwallarta ta juyo a hankali ta fito daga bayin ta juya tana rufewa ta idasa shiga cikin dakin

Turuss ta yi sakamakon ganninsa zaune bakin gadon, cikin doguwar bakar riga irin ta sallah, rigar ta kara haska shi ya yi wani freshh da shi, sajen nan nasa lufluf sai dara daran idannuwansa dake kabta kikam yana mai binta da kallo

Cire kanta ta yi a sanyaye ta furta " Morning "

Bai iya amsata ba, duda mamakin jin ta gaishe shi da ya yi bayan tana fushi da shi, yana kallonta ta karasa wajen kayansu ta buda ta ciro rigar sallah da pant da bras
Bata saka pant da bra din ba rigar sallar ta fara sakawa sannan ta dauki turare ta shashafa du wani sasa na jikinta kafin ta shinfida darduma ta shiga gabatar da sallar asubahi

Sai da ta gama salarta cikin nutsuwa sannan ta mike ta dauki pant dinta

Juyawa ta yi ta duka ta saka wanda hakan ya saka shi kara yi mata kuriii yana kallonta

Sai da ta gama sakawar kafin ta ciro doguwar riga ta atampa, rigar kuwa ba'ai mata gidan mama ba dan haka take son saka bras

Rigar sallar nan ta dan sasauta ta kaita daidai kugunta sannan ta juya masa baya hakan ya sa dogon bayanta shafafe wanda baya dauke da lungu lungu ya tsatsare shi sai dan fadin mamanta kadan da yake hangowa har ta saka bra dinta sannan ta sabule rigar baki daya
Dukawa ta yi irin dukawat rakumi kansa kasa jikinsa sama ta dauki rigar wanda hakan ya saka shi sakin ajiyar zuciya yana kara gyara zama yana mai binta da kallo

Rigar ta saka ta juya tana jan zif dinta sannan ta dauko dan kwalin rigar ta daura saman kanta ta kashe irin daurin nan na ture ka ga tsiya

Rigar bacinta da ta cire ta dayke ta ninke ta mayar da ita wajenta sannan ta koma wajen dardumar itama ta nade ta kaudata ta karasa gaban madubi ta ja ta tsaya tana bin kayan kwaliyar su Ummu da kallo

Murmushin mugunta da neman fada ta yi kafin ta shiga uda turarukansu

Ai kam wani irin wanka ta shiga yiwa jikinta da turarukan nan tana harhadawa har suka fara hawan mata kai dan tsabar barna ama bata daina ba sai da ta ji ta jika da turare sannan ta ajiye

Juyowar da take kanta ya kusa gwaruwa da kirjinsa hakan ya saka kirjinta bugawa ta ja baya kadan ta dora hannunta kan abin madubin nan da ba kwari gareshi ba, gannin hakan ya saka da sauri ya sa hannunsa ya taro kugunta ya rikota jikinsa har sunna jin numfashin junna na garwaya waje guda
Muryarsa a shake ya ce" Ni zaki nuna tamkar bana waje BEEBAH? "

NAJEEBA ta hadiye busashen yawun makwogwaronta, so take ta masa rashin kunya ta mumurguda masa baki, sai dai walahi tsoron marin nan nasa na jiya ya mata katutu a rai, ama idan ya san wata ai bai san wata ba
Fuskarta ta yatsine a hankali sai kuma ta saki wata irin shagwababiyar murya ta ce" Haba SHAHEED, me kake so? Ko na kara fada maka sirrin abinda nake sha dan samun ni'ima ka kaiwa kawata? To SHAHEEED abunuwan ne da yawa walahi, da ka je wajen su Ammi su suke bani sai su harhada maka ka kai mata ta ringa sha may be a dace "

Bakinta ya kurawa ido da mamaki, furucinta yake aunawa bisa mizani, a hankali ya yi niyar yin magana sai dai bugawar da zuciyarsa ke yi ya saka shi lumshe idannuwa yana ayanna yau ya ga tashin hankali, ya yi gwa da gwa da maza masu abin tsoro basa kayar masa da gaba sai wannan ficiciyar yar?

Najeeba ta dora hannunta saman nasa ta shiga kokarin kwace rikon da ya yi mata idannuwanta saman fuskarsa tana tsinewa zuciyarta da dukan wasu burikanta, yaya zuciya da buri zasu yi mata haka? Dama su din masu cenza ra'ayinsu ne suka sakata hawa kan turba yanzun suke son sakinta a tsakiyar filin daga? Wannan wani irin tashin hankali ne da bata shiryawa haka ba? Rayuwarta da shi ta dauri niyar ko a yaya ta zo mata hamdan, idan da dadi idan babu oho, sai gashi banzar zuciya da banzayen burika na k8n fari mai mata sunna neman tarwatsa mata shiri? A hankali ta kuma kallon kyakyawar fuskarsa wace ke wartar du wani tunaninta da nazarinta, murya a shake ta kama hannun da dan karfin da take tunanin tana da shi ta ce" KA CIKA NI NA KARA GABA! "

buda idannuwansa ya yi da wani kallo mai tafe da sako, sakon ya kunshi magangannun ban hakuri, da rarashi, da roko irin na ki ji kaina ki tausaya min,

Bakinta dake mutsu mutsu tana rike shi dan kar ta yi abinda zai kurumtata ta kuma budawa ta ce"








Barka da juma'a jama'atul musulmi

A gaskiya ba zan iya kwatanta maku irin farin ciki da nishadin da kuke sakani yan gidan Mage Grup, walahi na wuni ina shan dariar chafterku, harda masu rrrrrrrrrrr na ce ku yi hakuri kar ku yi amai=Ø Þ=Ø Þ=Ø Þ=Ø Þ=Ø Þ
[3/31, 11:36 PM] BAK'A CE: >ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß>ØÕÝ<Øûß


*Na*


*SAJIDA*


=Ø«Ü(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<Øß
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ØÝ

& *[ T.M.N.A]* & =ØÖÜ=ØŠÝþ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



65

*SAKO ZUWA GARE KU JAMA'AR CIKIN GIDAN MAGE, JINJINA, GAISUWA, FATAN ALKHAIRI, ADU'AR GAMAWA DA DUNIA LAFIA, HAKIKA ADU'O'INKU SUKAN SAKANI NA RINGA JINA CIKIN MATSANANCI FARIN CIKI, UWA UBA IRIN KOKARIN DA KUKA RINGA YI
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment