Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

аЯрЁБс>ўџ   ўџџџ     

              џџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџьЅСg №П0ТbjbjкЊкЊ .’ИРobИРobmџџџџџџЗZZжжжжжџџџџъъъ8" .,ъ†LlZ&Z&Z&Z&Z&5'5'5'СAУAУAУAУAУAУA$ђMЖЈP\чAY
ж5'5'5'5'5'чAжжZ&Z&л@LAAA5'ДжZ&жZ&СAA5'СAAAAZ&џџџџ Ы^Jgйџџџџщ=jA­AVL0†LAQSA.QAQжA,5'5'A5'5'5'5'5'чAчAA5'5'5'†L5'5'5'5'џџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџџQ5'5'5'5'5'5'5'5'5'ZB œ: An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels __
=иЋм(' *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*<ип
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_>ин

& *[ T.M.N.A]* & =ижм=иŠнў

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/




>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп

Na

*SAJIDA*


1


Zaune suke baki d'ayansu cikin fada, a kasa suke su dukansu saman tankadaden reran (kasa fara tas) dake tsakiyar fadar baki daya ba saman tabarma ba

Su dukansu sun tantankwashe kaffafuwansu tun daga datijon dake zaune har zuwa yar karamarsu

Kamaninsu du iri daya ne, sun kwaso kamar mahaifinsu wanda ya haife su wanda yake zaunen cikin shigar shada ruwan toka mai cike da kamala
Sai matarsa dake zaune gefensa fara tas matashiya domin sam bata kai shekarunsa ba bayanta da goyo tana dan jijiga yarinyar dake dauke da wani irin gashi mai kyau a kanta wanda sun gado shi ne daga wajen mahaifinsu da yake bakin balarabe

Manyan malaman fadar ne zazaune kusa da kujerar alfarma wace sarki ke sama zaune ya kura masu ido daya bayan daya yana kallonsu
Dogarai ne hudu biyu gefe da gefen sarki, daya rike da wata irin bullalar dorina irin ta dukan rakumin nan murdadiya mai taurin gaske sannan mai lauyewa wace idan aka tsulawa mutun take zagaye jikinsa ta dannu da zafin gaske, dayan kuwa yana tsaye rike da wata jakar fata wace ke dauke da alkur'ani mai girma ya masa kyakyawan riko

A hankali sarki ya dan daga kansa ya dan juya kan nasa hakan ya sa baban malamin da ya fi aminta da shi sannan ya fi kowa tsufa a fadar ya gyara cikin nutsuwa ya ce" Allah ya ja da rai, Allah ya jibanci lamuran sarkin garina, Allah ya huci zuciyar matashin sarkina mai cike da kamala, na miko gaisuwata ina kara jinjina da adu'ar gamawa da duniya lafia

Sai da ya numfasa kafin ya ci gana cike da jin nauyin maganar da zai yin duba da abin na cikin gida ne ya ce"
Yaran nan ne suka shigar da karan da ka bada rana yau a zo gabanka zaka wanzar da shara'a kwana biyu da suka shige

Baki daya aka kwashi gyara kimtsi, sarki mai adalci, sarki mai zartar da hukunci a kan dukan wanda aka cuta

Sai da ya lumshe idannuwansa cike da wani irin jan aji da wani irin cika da kamala sannan da jin kunyar datijon dake zaune wanda ke tafe da iyalinsa baki daya sun zo a masu shara'a kafin ya daga yan yatsunsa yana kallon baban yayan yaran da suka kawo karar mahaifinsu da kuma matarsa kan a saka masu alkur'ani a masu shinge kan aikata mugun abu a tsakani kama daga maganin asiri , zagon kasa dai da sauransu dukan abinda zai zama na cutarwa ne

Da dan yatsansa ya yi nuni kan baban yayan nasu wanda kansa ke kasa yana cike da kunyar sarkin domin ya tabata ya shaka kuma a kansa zai sauke dukan haushinsa

Da sauri na kusa da shi ya fadi cewa" Sarki ya baka damar fadin abinda ke tafe da ku a matsayinka na ja gabansu

Sai da ya sada kansa sannan ya dago ya sauke ajiyar zuciya, shi kansa kana ganninsa ka ga jinnin sarautar domin maganar da zai yi sai da ya ringa motsa bakinsa kafin da kyar ya buda bakinsa ya ce" SUNNANa *DAYABU BINE MUTALAB,* mun kawo karar matar mahaifinmu ne wato MUTALAB da kuma matarsa MARDIYA domin muna so a yi mana shari'a ta adalci hakan ya sa muka nufo gidan adalci

Gaskiya ne jangori, gaskiya ne yaro jangori a nan adalci shi ke janye da ragamar komai

Ajiyar zuciya ya sauke ya ci gaba da fadin" ba wani abu ne ya kawo mu nan ba sai bukatar a yi mana tsakani da matar mahaifinmu wanda take uwa a wajenmu kan zamantakewar yau da kulun, kwarai muna fuskantar abubuwan dake gifata mana kala daban daban wa'inda suke saka mu a halin rashin nutsuwa da fadace fadace tsakaninmu da ita
Mun zo gidan nan ne dan kaine uban kowa kuma mai zartar da hukuncin da ya dace bisa tafiar adinni,
muna so a yi mana tsakani da ita kan maganar magani wato asiri, kar ta shiga tsakaninmu da mahaifinmu, kar ta shiga tsakaninmu da yan uwanmu, kar ta shiga hurumin aikinmu, ko matayenmu ko kannenmu kar ta hada su da lamari na rashin samun miji, a takaice dai dukan wani shinge da ake yi a gidannan mun zo da kokon bararmu kan a mana shi tsakaninmu da *Su* muma a yi masu tsakani da *Mu* koda wani ta ji zai yi idan bata tona ba, koda wani muka saka ya mana ya ci mu!

Wasu kai suke jujuyawa, wasun kuwa cike da mamakin yau shara'ar ta cikin gida ce aman suka yarda ake yinta a fili gaban kowa, Jangori ne da kansa sai y'ayansa duda aun kasance fitatu kuma sananu a duniyar rigima sai dai abin ya bada mamaki gannin ya amsa kira shi dinma da kansa
nan da nan labari ya fara fita waje harma yan jarida suka fara garzayowa suka cika kofar gidan sarki kowa na jiran fitowarsu domin komai abinka shara'ar gidan sarki baka isa ka fitar da ita waje ba sai dai ka tsinci abinda ka tsinta a waje

Murmushi mahaifinsu ya yi a lokacin da DAYABU ya gama magana kafin ya dago jajayen idannuwansa da suka rikide sukai ja sakamakon bacin rai ya kali y'ayan nasa daya bayan daya sannan ya ce" *Na yarda nima a min tsakani da iyalaina, Sai kuma ya rage muryarsa a hankali ya kalli sarki ya ce" Aman banda soyayarmu, ina nufin ni dai ta min na fuskana wanda zamu ci gaba da zama lafia*

Gaba daya aka shiga kallonsa, da yawa suka shiga sada kansu cike da kunya, wasun suka saki baki da jin abinda ya fada, matarsa kuwa ta rausaya kanta tana sakin murmushi tana jujuya kaffafuwanta
A lokacin ne itama ta dago kanta da wani irin sauri ta kai dubanta wajen mahaifinsu
Hannunta na hagu ta dago ta kai wajen bakinta da sauri tana mai ruruko manyan idannuwanta masu zagaye da kwalin kajal ta ce" *lah*

Sai kuma ta maida dubanta wajen sarki wanda ya sauke mata kallon da zata iya kira kallon tsana wanda kwannan duniya ita rayuwarta bata san me ta masa ta tsare masa ba ya tsaneta yake kuma kan tsanarta kamar ya fida mata rai , ba wani haduwa suke da shi ba sai jifa jifa ko idan shara'a ta kawota ko ta rako wani aman daga irin kallon kyamar da yake jifanta da shi ta tabata da ace mai magana ne shi ko mai zage zage da ya mata zagin da bata taba jin irinsa a duniya ba

Kanta ta yi gagawar mayarwa ta sada

Sarki ya dan yi gyaran murya yana mai duban dogari mai rike da dorina a hannunsa, sannan a zuciyarsa ya ayanna" *Dama yaya za'a zo wajen fitina banda ke ke dai kin saka kanki a uku, mai yiwuwa yanda fatarki keda baki haka aniyarki azaluma kawai!*

Da sauri mai rike da bulalar nan ya dagata ya mata wani irin duka a jikin wajen da na yi tunanin garu ne, ashe ba garu bane an masa wani irin tsarin shafa penti ne ya hade da garun

Karan da abun ya yi ne ya saka baki daya mutanen wajen sada kansu sunna masu nutsuwa harma da hade kafafuwansu sunna kara kimtsa zamansu

Sai da ya kuma dago kansa ya kara bin y'ayan da kallo lafin ya maida wajen mahaifinsu da kuma matarsa
Su su goma sha uku ne, cikinsu ba wanda suke uwa daya kowane da uwarsa sai dai wani ikon Allah kamaninsu baki dayansu ya zo daya sai dai daga fata ne wani ya fi wani haske
Kanta ya sauke dubansa, yanda take wasa da yan yatsunta kanta sade tamkar saliha
Haka ya kuma furtawa a kasan zuciyarsa kafin ya maida dubansa wajen mai rike da alkur'annin

Hannunsa ya nuna kansa

Da sauri ya buda alkur'annin ya ciro shi
Baki daya wajen suka kwashi kabara hakan ya sa du wanda ke wajen tsigar jikinsa tashi tana yam yam yam masu saurin hawaye kuwa suka shiga sharewa

Kanta ta dago a hankali ta kai dubanta wajen alkur'anin
Kafeshi ta yi da ido, har idannuwanta suka nuna mata abinda take zargi

Da sauri ta kalli yayansu, sai kuma ta maida dubanta wajen mahaifinsu wanda shima ita din yake kallo ya zabga mata harara domin cikinsu ba wanda baya jin haushi, su dukansu suun cira bata nuna ba kuma daya bayan daya sai ya rama!

Dan jan abin da ta ganni ne ya sakata tabe bakinta ta maida dubanta wajen sarki wanda ya gama hada gabas da yama kudu da arewa ya hade rai hakan ya tsoratar da dukan wani wanda ke zaune a wajen itama da gagawa ta sada kanta tana dan bubuga kafafuwanta kasan zuciyarta kuwa fadi take " *Azalumi mai wata fuska*

Baban malamin dake zaune ne ya gyara zamansa cikin kamala ya shiga koro bayanan saka layar wanda du idan ya yi magana wajen sai an dauki kabara

Irin abubuwan da aka gindaya habaici da baki ne kawai aka cire ciki kuwa harda duka aka saka hakan ya sa jikin DAYABU yin wani irin sanyi nan da nan dana sani ta ziyarce shi yana kallon kannen nasa da ya yi imanin du sai sun mutu ko sun kuturce a kan layar duka da aka saka masu dan wasu irin jarababun y'aya ne masu fadan balaki, domin idan ta hadoka da su har kirari suke yiwa kansu na idan baka jiyata mutumen ba kai ba jinnin MUTALAB bane!

Cike da tausayi ya ajiye dubansa a kanta, ya tabata itace gawar fari domin kaf cikin kannensa babu wace ta kaita fada , a haka kuwa kamaninta sam bata da siffar mafadaciya, sam *Kamaninta basu yi nuni da wace zata iya yiwa wani illah ba*

Ana gamawa wajen ya kwashi wani irin shiru,
Sai da ya kuma jifan DAYABU da kallon zamu hade sannan ya gyara rawaninsa hakan ya sa suka gane zai mike ne, domin dama wannan shari'ar ita ta fitar da shi, ita ta tsayar da shi, baya kananun shari'a sai idan baba ce ko wace ta shafi ahalinsu

Kowa kansa na kasa sakamakon tashin da zai yi
A hankali ya sauko kafarsa ta dama mai dauke da takalmin fata irin na jinnin sarauta aman yana da kalar fukafuken dawissu bayan ya yi adu'a a kasan zuciyarsa

Sai da ya gama sauke kafafuwansa sannan ya mike da wani irin isa da takama
Yana mikewa da sauri sauran dogaran da suka karu suka shiga gyara masa rantsatsiyar suturar da ya saka ta yau wace sak irin fukafuken dawisu ne, harta da rawanin da ya sha wani irin rawani ne da akaiwa adon dawisu hakan ya sa baki daya ya dauke hasken wajen

Da sauri suka lallayu shi kuwa ya shiga takawa a hankali yana bi ta tsakiyar mutanen da suka layu

Kanta dake kasa hakama idannuwanta tana kallon kasa
A lokacin da ya kawo kafarsa daidai ita ta kasan gilashin dake fuskarsa mai hasken fari ya ga yar igiyar abin sauraron kidan da ta saka a kunnayenta tana sauraro, hakan ya sa ya dan jima a tsaye a kanta har sai da ta yi saurin dago da dubanta sai dai bata karasa kallon fusakarsa dake lulube da rawani da gilas ta yi saurin sada tsumamun idannuwanta da kanta tana kallon takalminsa da ya tafi da imaninta baki daya

Wata ajiyar zuciya mai zafi ya sauke yana ayanna tabas idan tana tunanin ta gagari kowa zai taka mata birki, a kulun ya hadu da ahalin gidansu yana mamakin irin zubin Halitar salihan mutane da akai masu sai dai tarin jaraba dake ciciyarsu, bare ita dake dauke da irin idannuwan nan masu lumshewa da wani irin lumtu lumtu masu tudun gaske da wani irin kumbura

Kwafa ya yi a ransa ya ayanna: ita har ta isa ta saka abin sauraron kida a lokacin da take zaune a gabansa?

A hankali ya kuma daga kafarsa ya ci gaba da takawa har ya bar wajen wanda barin wajen kadai sai da ya dauki kusan minti talatin tashinsa zuwa tafiarsa

Sai da ya shige sannan dogarin ya shaida masu summa iya daga kai

Kanta ta dago hade da harara ta sauke a fuskar dogarim wanda yake ta lulube kujerar sarki baima san tana yi ba

Yayansu na mikewa suma du suka mimike , mahaifinsu kuwa ya duka sunna magana kasa kasa da malan

Cike da bacin rai ta fara fita
Tana fita ta saka dogon takalminta fari kal mai tsinin gaske ta rike tsatsonta tana girgiza

Yayanta da sauran kannenta ne suka fito sai matar babansu a bayansu dauke da yarinyarta a goye

Da wani irin sauri ta zagaye ta koma kusa da ita ta kama goyon da sauri ta kunce hakan ya sa suka shiga kokowar kar ta kunce mata goyonta ita kuwa sai da ta kunce shi ta yi sauri ta damkawa yayarta mai dan sanyin cikin nasu wace ke fadi" ke meye haka? Ki rufa mana asiri da laya tsakanninmu

Bata tsaya ta saurari abinda take fada ba ta juya da sauro ta karasa kusa da matar mahaifinta wace ke tsaye da yan uwanta suma dangin balaki ta daga hannu ta wankawa matar mari da wani irin masifa ta aniya shigarta da duka

Yan uwan matar babansu na gannin hakan summa suka shigeta da dukan domin ai laya tsakaninta da su aka yi ba da yan uwanta ba
Yan uwanta na gannin hakan summa suka kasa hakuri domin familynsu wata irin family ce mai wuyar fasara, a tsakaninsu sunna cin kansu kamar me sai dai koda wasa basa bari a cuci dan uwansu idan kuwa aka yi gigin hakan sunna iya haduwa su lalasa mutun

Wata irin kokowa ce ta kaure tsakanin dangin matar mahaifinsu da kuma su hakan ya saka baban yayansu dora hannayensa saman kansa a fili furta" shikenan, yau dai karshenmu ya zo, shikenan ta halakamu baki daya

Da sauri ya karasa ya shiga janyo kannen nasa du wanda ya yi gardama kuwa hannunsa yake dagawa ya wankawa mutun mari nan da nan sai mutun ya bar fadan, mutane kuwa sunna kallon ikom Allah basu shiga ba domin kana iya shiga dan rabiya abin ya juye kanka su kuwa basa fatan fada da wannan ahali

Yana damkar hannunta itane ta karshe sai da ya kaita kusa da motarta ya saketa
Tana ta maida numfashi bata ankara ba ya daga hannunsa ya dauketa da gigitacen marin da ya sakata jin wani irin kauuu har kunnayenta suka yi kamar sun rufe tsabar saukar marin da zafi

Cike da fada ya ce" kin kashe mu! Kin kashe mu! Ubanme ya kaiki marinta bayan yanzu aka mana tsakani da laya a gabanki aka dagata?

A firgice sakamakon zafin marin da ya dada mata da dago shanyayun idannuwanta masu matukar haske da girma ta kale shi, kamar an mintsineta ta kwala ihu tana fadin" *karya ne! Ba cikaken bane! Bilahilazi sun daukeka wawa ba cikaken Alkur.anin bane suka saka yaya DAYABU!*

Da sauri ya tsaya ya kura mata ido yanda aka yaga mata rigarta sai haki take tana hararan wajensu , sai da ya karyar da wuyansa ya sanyaya muryarsa ya ce"
>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп>иен<ићп


*Na*


*SAJIDA*


4




Tana murmushi tana kallon yanda sarauta ta karbi yaron nata, yanda sarauta ke kara masa wani irin nutsuwa da kamala a hankali ta ce" Allah ya tsare gabanka, Allah ya tsare bayanka, ya tsare makwoncinka, ya tasheka da kansa
Allah ya yi maka albarka

Idannuwansa ya lumshe sakamakon jin dadin adu'ar da mahaidiyarsa ke yi masa har sai da ta dasa Aya sannan ya juyo ya kara dukar da kansa ya furta" amen Anmy

Cike da tafiar kasaita ya fito daga bangaren mahaifiyarsa
Bai zame ko'ina ba sai baban dakin karatun da suke raba dare sunna karatu da kuma ayukan sirri shi da mutanensa na sirri ciki kuwa harda yayan mahaifiyarsa da baban liman din fadar baki daya


Sai da ta tsaya a baban wajen saida abinci ta sayi pizza wajen gida goma inda ta bayar da jaka hamsin cif aka zuba mata a cikin motarta

Tana tayarwa ta karasa gidansu,

Mai gadi ne ya bude mata kofar ta idasa shiga da motarta

Yabi daya daga cikin masu aikinsu ta saka kwaso mata pizzar tana kai mata bangarensu da kannenta mata

Sai da ta gama kwashewa ta rufe motarta da dan kwalin nan a hannunta tana dan wasa da shi ta shige cikin falon nasu

Ja ta yi ta tsaya sakamakon gannin yayanta na bangarensu sannan kannen nata da kuma yayunta har sun yi wanka sun sasaka kayan baci

Wani dan malalacin murmushi ta saki tana idasa shiga ta ce" aa, me kuke a zaune?

Dubanta sukai gaba dayansu, gannin sai wayancewa take ya saka yayarta mai sunna Umakhulsum girgiza kanta ta ce" ai dole ki ce haka, dole ki ce haka Najeeba bayan ke kin iya tankwalo masifa tana baci!

Da sauri NAJEEBA ta ce" toh fa

Dayar mai sunna Zahrau wace itace mai sanyinsu ta ce" yanzu Najeeba kennan nima kina iya daga hannu ki wanke ni da mari? Kuma kin sani sarai da ba barinki zai yi haka ba koda kuwa Anmy ta yi dabarar sakawa ta rama sai ya maki wata muguwar muguntar marin masa matarsa ko?

Da Sauri DAYABU na dan dago hannayensa ya dunkule guda ya ce" fisabililahi idan ba jarababiyar y'a ba bilahilazi da ta wanka mata marin nan sai na shiga neman na tashi ni ba fifike ba, NAJEEBA a gaban sarki ki mari matarsa dan kina yar yayan mamansa?

Gaban goshinta ta dafe tana karasa shigowa
Sai da ta zauna tana kallonsu ta ce" meye hukuncina? Cin uwani zaku yi yanzun ko yaya?

Tasowa yayansu ya yi da sauri ransa bace ya nufota

Da sauri ta rufe fuskarta domin wajen da bata so a kuma taba mata a yau kennan ,

Sai da ya karaso ya daga hannunsa ya yi ya yi ya bambarw hannayen nata aman sai kara shigewa cikin jikinsa take, nan fa tumurtu ya tashi gannin zata wahalar da shi a banza ya saka shi sakinta yana maida numfashi ya zauna ya ce" shegiya mai ilimin kokowa, kin ci sa'a fuskarki a boye da yau na fitar da sahun hannuna a jikinta

Kanwar NAJEEBA dake dariya ne ta ce" wai ku ji fa, kamar wanda yaya zai mata wani duka mai karfi abinda nan zaka ringa zanen idan ka kamata ka fara kwalo da ita, tana zuwa gabanka sai ka bige da yi mata nasiha

Da sauri ya kaleta yana zaro ido ya ce" kin ga wannan mai sunnan Gimbiyar sam bata da kirki, idan ta tashi magana sai ta ringa yiwa mutun shari ba gashi ba na jijigata kuma ki bari ki ga ta kuma marin matar sarki zara ga abinda zan mata

Su dai du murmushi suke ita kuwa NAJEEBA ta hade fuska sai kara turo baki take wai sun hade mata kai sunna mata fada

Sai da suka gama yi mata kashedin ta kiyayi yiwa sarki hayen nan ta sada kanta ta ce" kennan sai na kyaleta ko? Kun san me tace ne? Cewa fa ta yi *ke kauce yar talakawa*

Ido Umulkhair ta zaro ba shiri ta ce" kan ubancen, shi yasa na so zuwa na ji a kan me zata maida maki mari yaya ya rikeni ashe iyayenmu ta zaga?

Yayansu ya yi shiru shima ransa na kunna

Zahra ta ce" kin min daidai dan ubanta ya kashe mu!

Su masu yi mata kashedin kar ta kuma sai gasu sunna fadin ai ko sunne sai sun rama, nan da nan suka shiga zanen idan ya kama su ya kashe su sun yi, yayansu kuwa ya rafka tagumi yana kallon dan karamin kanensu wanda su biyu ne kawai maza sauran su goma sha biyar baki dayansu mata ne kuma ko daya ba'a yiwa aure ba tukunnan

Ajiyar zuciya kawai ya kuma saukewa ya janyo pizzar ya shiga bubudewa yana raba du gida guda a biyu yana mikawa yaran kannanu
Sai da ya yi sauran manyan ya basu guda guda har NAJEEBAR sannan suka shiga ci sunna dan taba hirarsu

Sai da suka gama yar karamarsu mai sunna lalla wace bata kai shekara shida ba ta je ta langwabe a jikinsa tana hamma, a hankali ta ce" yaya Dayabu, ina Abihna?

Gashin kanta dake dadaure da tsakiya masu shegen kyau wanda NAJEEBA ta mata kitso kananu sosai ta jera mata su ya ringa shafawa a hankali bai bata amsa ba

Kamar minti biyar har ta yi baci hakan ya saka shi sauke ajiyar zuciya ya kalli ZAHRAU wace ke bi masa ya rage murya ya ce" Zahra yau a dakinki zata kwana dan Allah dan ki kular min da ita, kin ga Abih fa fushi yake da mu baki daya yau ko ita bai nema ba

Kanta ta gyada ta mike da wayarta dake ringin saurayinta ne wanda aka saka masu rana ta duka ta dauke kanwar nata ta nufi dakinta da ita

Tana kaita ta shinfideta ta hade kitson cen sama ta daure shi dan kar ya dameta wajen baci
Ta yi mata adu'ar neman tsari kafin ta tsareta da ido a cikin ranta kuwa fadi take" inama Abih zai maido mahaifiyarki
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment