Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Compiled By Umar Dalha Funtua.

Copied By Aminatu Hassan Oum-Deed at.


[8/5, 8:19 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹

🌺🌺🌺🌺🌺

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~*

*Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat)

*Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat)

*Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare.

*Godiya*---- Ga Allah subhanahu wata'ala daya bani rai da lafiya na rubuta maku wannan littafin mai dinbin fad'akarwa da nishadantarwa, yanda nafara lafiya ina rok'on Allah yasa in k'are lafiya.

*Jinjina*--- ga 'yan Golden Pen writers association Allah ya k'ara hada kanmu ya qara mana zaqin hannu ya bamu ikon rubuta abunda zai amfani al'umma baki daya.

*Matashiya*--- wannan labarin qirqirarre ne banyi da niyyar cin zarafin kowa ba duk wanda ya ci karo da abunda yayi daidai dashi yayi haquri.

Page *_~1~_*

• ∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆•

Tsoro na Allah tsoro na muhadu dashi ahanya saboda ko ba komai dai ni nasan bana iya kallon cikin kwayar idanunshi,wani mugun kwarjini yakeman ta bangare guda kuma tsareni da idanunshi masu rikitar dani dayakeyi aduk lokacinda zamu hada hanya.

dukda an bashi shedar tinda ake dashi ba'a taba ganin miskili ta bangare guda kuma kamilin saurayi aduk fadin unguwar ba irin shi.

Unguwar da take cikeda 'ya'yan masu kudi 'yan gata, 'ya'yan masu fad'a aji a fad'in Nigeria, da yawa yawansu ma ba a qasar sukeyin karatu ba ta wani bangare kuma sha'aninsu sukeyi da 'yan matansu 'ya'yan k'usoshin gwamnati irinsu amman duk da haka acikinsu Ya Ameen daban yake.

mata dayawa suna sonshi amman shi Sam basa gabanshi Aikinshi da kasuwancinshi kadai yasanya gaba, acewarshi har yanzu ba'ayi yarinyar dazai tsaya b'ata ma kanshi lokaci akanta ba, kai shi soyayyar ma gabaki dayanta bai yarda da itaba.

Menene abunso a jikin mace? Kullum tambayar da ya keyi ma kanshi kenan.

(Nidai nace bakaje hannu baneba lol🤣)

""""""***************"""""

Ahankali nake takawa cikin natsuwata da tafiya ta mai ban sha'awa da burgewa, ni ahakan ma gani nakeyi sauri nakeyi saboda aiken da ummata tayiman kasuwa banaso na rasa adaidaita din da zai kaini duba da yanayin unguwar tamu, akwai drebobi har guda uku acikin tanqamemen gidan namu ko nace nasu amman dukda haka ummana ta haneni da shiga motocin domin kaini inda zani, a cewarta in tsaya matsayina na diyar mai aikin gidan mara galihu saboda gudun wulaqanci dukda cewa su drebobin ba zasu wulaqantani ba kasancewar mu dasu duk matsalar mu daya na wulaqanci da muke fuskanta daga matar gidan,

A wajen mai gidan da babban yaron gidan ne kawai muke samun sassauci amman ba daga su ba mudin da dabbobin dake gidan gonar bangare daya daga cikin gidan duk daya muke awajen iyalan gidan in kacire mutum uku rak cikin mutum bakwai daga cikin gidan watau Ya ameen Babban Dandan Gidan a maza, afnan watau autar gidan dashi kanshi kuma uban gayyar watau mai gidan Alhj Mustapha Dambulan

Ban aune ba naji nayi karo da mutum kasancewar saurin da nakeyi kuma da son kaucewa idanun drebobin saboda banaso su yiman tayin kaini din, lokaci guda kuma nayi baya zan fadi bankai ga kaiwa qasa ba naji an janyoni dakarfi har na fada faffadan kirjinshi da yake cike da haiba, lokaci guda dad'edd'en kamshin turarenshi da ke kara taimakawa wajen rikitar dani ya yiman sallama a hancina.

"Subhanalla" nace ina mai ja baya dasauri amman dukda haka damtsen hannuna na cikin nashi ba tareda ya sakeni ba,

"yi hakuri don Allah yaya..."

"Shiiii🤫" ya katseman hanzarin bashi hakuri da nakeyi, cikin isa da rashin son magana dinnan nashi ya bude baki dakyar yaceman "is ok ya wuce amman nan gaba ki dinga kula, bakyau ana tafiya ana tinani"

ya fada ahankali yanda nikadai zan iyaji dukda dai cewa dama haka yanayin maganar tashi take don in ba saninshi kayiba saima ka dauka maganar zuci yakeyi labb'anshi ke motsawa

Sakina yayi tareda zagayeni ya wuce kaman ma ba shine ya gama magana ba yanzu

Girgiza kaina nayi yayinda har yanzu ban koma normal ba bugun zuciyata ya qara gudu lokaci daya kuma ina kokarin daidaita numfashina domin ji nayi kaman ya wuce tare da numfashin nawa,

juyawa nayi nabishi da kallo har ya shige dan madaidaicin apartment din nashi da yake cike da kyau da qayatuwa a bangare guda na gidan.

Ci gaba nayi da takawa mamakin shi fal araina, na godema mahalicci na da ba aunty sauda ko nihal ce wannan tsautsayin ya faru akansu ba da na kade har buzuna,bani kadai ba ma har ummata da take cen tana masu iyakar iyawarta cewa zasuyi na bangajesu na daidaita kafada ta da tasu ubanwa ya haifeni,

oh "Allah ya soni" na fada afili ina mai sauke ajiyar zuciya daidai lokacin da na daidaita kaina ta gefen titi ina mai tafiya tareda waige waigen Inda zan hango abun hawa saboda inaso nayi sauri na amsoma ummana aikenta kada mukara yin laifi akan wanda mukayi dasafe wajen Hajiya matar gidan da muke aikatau.


_Muje zuwa Wannan shine mafari_

~Oum-Deedat ce~
[8/5, 8:20 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹

🌺🌺🌺🌺🌺

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~*

*Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat)

*Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat)

*Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare.

Page ~2~

•∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆•

*Ya kamata musan wannan gidan dakuma rayuwa dake gudana agidan*

_Wacece wannan yarinyar da takema kanta ikirarin marar galihu?_

_Wanene Ya Ameen?_

_Wanene Alhaji Mustapha Dambulan?_


"""""""""""""""**********"""""""""""""""



Alhaji Mustapha Dambulan asalinshi dan jihar Katsina ne A wani Local Government da ake kira kankiya, su shidda ne awajen mahaifinshi da mahaifiyarshi da suke zaune cikin rufin asiri daidai gwargwadon abunda Allah ya hore masu, mahaifinsu Alhaji Isuhu da mahaifiyarsu Hajiya zuwaira suma duk yan asalin karamar hukumar kankiyar ne.

Alhaji isuhu manomi ne rikakke, kuma irin attajiran qauyen nan ne saboda yana noma ga kiwo yanayi, kuma ta bangare guda yana ba mutane jari sudinga sana'a suna raba ribar, akalla mutanen da yake wannan kasuwancin dasu sunkai mutum goma koma fi,

sannan yana kasuwanci na auduga da kamfanin saqa kaya dake Lagos inda dakanshi yake siyen auduga da wadda yake nomawa ya hada yakai kamfanin a bashi kudinshi yazo ya sake juyasu kafin kakar audugar ta dawo.

Yaranshi maza biyu ayayinda mata suke su hudu dukda cewa ya aurar da guda biyu manyan yanzu saura biyu ke gareshi a gabanshi.

Dukda yake mutumin karkara Allah ya bashi matukar tinani hankali da basira, saboda alokacin karatun boko baiyi yawa ba azamaninsu amman ahaka yace insha Allah 'ya'yanshi duka mata da mazan sai sunyi tinda shi Allah bai bashi ikon yi ba,

matan na gama makarantar primary yake aurar dasu ga wadanda sukeso saboda shi babu tsarin auren dole ko hadi a rayuwarshi tinda yace shima ba'ayi mashi dole ba wannan shi yasa yake zaune da matarshi kwaya daya rak kuma uwar 'ya'yanshi duka guda shiddan,ayayinda mazan kuma suke wucewa gaba da primary Allah ya taimakesu kuma suna gamawa suka samu aiki tinda alokacin ko baka gama secondary ba ma in kaso zaka iyayin aiki kuma abiyaka albashi mai tsoka saboda alokacin kudin sunfi daraja ba kaman yanzu ba.

Aisha itace zuwaira tafara haihuwa daganan sai Fatima mai bimata sai kuma Auwalu daganan sai aka haifi Mustapha.

Haihuwar ta tsaya mata kusan wasu shekaru masu dan dama inda har sun gama makarantar primary dinsu sannan Allah yabata haihuwar 'yanbiyu mata aka barmasu sunansu watau Hassana da hussaina.

Kyawawa ne gabadaya gidan jajir suke ga hanci masha Allah wannan shiyasa ma yayinsu mata sukeda manema har Allah yasa aka aurar dasu sai kannensu mata da ake gab da aurar dasu suma kwana kusa.



Aikin da auwalu da Mustapha suka samune yayi sanadiyyar barowarsu mahaifarsu suka dawo cikin garin katsina ayayinda shi auwalu ya dogara da aikin da yakeyi kawai shikuma Mustapha dayake shi ya gado mahaifinsa sak Allah yayi mashi zafin nema sai yake hadawa da kasuwanci ya saro kaya ya dinga sararwa ga masu shaguna inda nan danan Allah ya yi mashi ludufi abun ya bunkasa

kawai sai ya fara gininshi a unguwa mai kyau saboda shi bayada ra'ayin zama gidan gwamnati ayayinda shi yayanshi auwalu bai damuba ganin cewa a albashinsu ake cire kudin

Ganin ya gama gidanshi dan madaidaici yasanya yaso iyayenshi su baro karkarar sudawo maraya, sukau suka kafe kai da fata alambaram bazasu bar mahaifarsu da danginsu sukoma wani wuriba subar noma da kiwonsu, saidai fa in aure zaiyi ya sanya matar acikin gidan, yayinda shikuma yace lallai ba aurene gabanshi ba yanzu ma shirin qaro karatunshi yakeyi a qasar waje amman tinda yayanshi yasamu wadda yakeso ya aura yasanya ta acikin gidan alabasshi sai su warware ahankali.

Lokaci daya akayi bikin auwalu da yan biyu inda su aka ajiesu anan cikin garin kankiya shikuma Mustapha alokacin ya ma dade da tafiya k'aro karatunshi, amman a gidan da Mustapha ya gina nan auwalu yasanya matar tashi maisuna Zainab alokaci guda kuma yana cigaba da aikinshi na gwamnati.



"""""""""""""""**********"""""""""""""""


Mustapha ya kammala karatunshi cike da nasarori ayayinda arzikinshi na Nigeria ya cika ya tumbatsa saboda koda yaje karatunshi baibar kasuwanci ba sai ya koma saro kaya irin na kasar wajen masu masifar kyau yana turowa kuma asaukake inda yakeba babban amininshi da sukeyin kasuwanci tare yana saida mashi yana tura mashi kudin yasake saro wasu.

Gininshi ya farayi tanqameme acikin unguwar GRA yayinda shikuma Auwalu yake layout amman gini ne na fada aji domin fintinkau yafi wanda auwalu ke ciki ya gina apartment guda uku manya aciki yayinda shifa ya kafe akan sai ya maido iyayenshi birni suma suzo su huta tinda suma sun kawo karfi komai zasu iya yima iyayensu harma su taimaka ma 'yan uwansu mata da suke gidan mazajensu da suka fara tara zuri'a


Ganin ya kammala gininshi ga kasuwanci ya habbaka ya gina manyan store store na kayan masarufi da kuma kayan electronics sai kuma motoci daya fara shigo dasu daga qasar waje manyan 'yan kasuwa da 'yan siyasa na siye ta bangare guda kuma bai daina kasuwancinshi na qasar waje ba inda har ya zuba hannun jari a wani babban kamfani a China dayake saqa atamfofi da k'era wayoyin hannu.


K'arin girma sosai ya samu saboda karatunshi da ya qaro inda ya hada digree dinshi na farko da na biyu afannin qere qere da kasuwanci wannan shi yasanya gwamnati tarayya tafara bashi kwangila ta gina gidaje da masana'antu abundai sai Sam barka ba'a cewa komai addu'ar iyayenshi tana binshi tinda Mustapha mutum ne nagari maison kyautata ma duk wanda Allah ya hada shi zama dasu kuma baya kyamatar talaka ko mara shi duk daya ne awajen shi saboda yasan Allah ne mai azurtawa kuma yana azurta wanda yaso alokacinda yaso. Wannan kenan


*KUBRA* d'iya ce ga hamshaqin d'an kasuwa Alhj Nura,
Alhj Nura tare suke kasuwanci da Alhj Mustapha dukda ba tsaranshi bane ko kusa amman dai shi harka ta kasuwanci babu ruwanshi da wannan ta bangare guda kuma yana damawa a siyasar qasar babban dan kwangila ne da Allah ya azurtashi da makudan kudaden da shi kanshi baisan iyakarsu ba saboda yafi Alhj Mustapha kudi nesa ba kusa ba, kubra kyakkyawa ce dukda bazata gwadama Mustapha komai ba, ahaka Allah ya hada jininsu suna soyayyarsu dukda ita taganshi tace tana sonshi wanda hakan tasa Alhj Nura yima Mustapha magana, baiyi qasa aguiwa ba ya amince duba da yanzu iyayenshi babu abunda sukeso dagani irin iyalanshi kada girma ya cimmashi ahaka batare da ya tara zuri'a ba.


Kubra na da wani hali na kyamatar talaka da marar galihu inda Mustapha bayason wannan halin har yana mata magana akai irin yadda yaga in yaje fira gidansu tanama ma'aikatansu bayajin dadi sai yake dan tsawatar mata lokaci lokaci,

to tana dai kokarin kiyayewa saboda irin son da take mashi saboda Mustapha kyakkyawane ajin qarshe ga naira ga Hutu dukda bazai nunama mahaifinta komai ba.

Acikin haka ne Allah yasanya akayi auren Mustapha da amaryarshi kubra suna zaune kalau, wannan tasa ya jama yan aikinsu kunne ya gaggaya masu halinta saboda su kula kuma suna kokarin kiyayewa.

Dangin Mustapha kaf sunason kubra (kundai San yanda akeson mai kudi) iyayenshi girma ya kamasu yayinda mahaifinshi ya koma ya zauna ya barma qaninshi duka hidimominshi tinda 'ya'yan sun kawo karfi, saidai fa Mustapha ya gyara masu gida ya maidashi na zamani tinda sun k'i baro mahaifarsu ya sanya masu masu aiki da masu gadi da dreba guda daya mai suna iro suna kula dasu tinda yanzu babu sauran kowa a gabansu in ka dauke jikokinsu yaran Aisha da Fatima harma da yan biyu dake zuwar masu Hutu kuma tinda akwai ma'aikata suke kula dasu don dai hajiya zuwaira girma ya kamata don ma dai jikin nasu ba irin namu bane ba 'ya'yan yanzu.


Mustapha yaba 'yan uwanshi kaf jari kuma dukansu ya tattara su bayan aurenshi sukaje qasa mai tsarki suka sauke farali harma da wasu daga cikin ma'aikatanshi dayake ya bude babban kamfanin markada qarafuna a jihar legas yayinda ya dauki ma'aikata daga jiharshi ta haihuwa dakuma saura daga saura jihohin nigeriya


Ahaka Allah ya azurta kubra da samun diya mace kyakkyawa aka sanya mata suna Nafisa suna cemata feena daga ita sai Al'ameen suna ce mashi Ameen sai saudatu ana cemata saudat sai mai sunan Hajiya zuwaira suna cemata Nihal saikuma namiji data haifa Yusuf ana ce mashi Abi sai autarsu mai sunan maman Hajiya kubra watau bilkisu ana cemata Afnan.

Yara ne sun taso cikin gata da kulawa,kuma ga karatun arabi dana boko gabaki daya Allah ya basu saboda mahaifinsu mutum ne mai tsantseni yaran wasuma ya tsaya ya kula dasu bare nashi, Sam bayason abunda zai bata mashi tarbiyya da karatun 'ya'yan nashi, wannan ce ta sanya ya tattara kan 'ya'yan nashi ya tafi qasar waje dasu bawai don ya raina tashi qasar ta haihuwa bane a'a saidai kawai irin yanda yanzu karatun kasar namu ya tabarbare

acen yasanyasu makaranta mai kyau da ta Haddar alkur'ani dasauran litattafai, ahaka nafisa tasamu miji a cen qasar ta Dubai inda akadawo nigeriya akayi bikin kasancewar shima dan nigeriya ne iyayenshi yan asalin garin zariya ne,amman acen yake kasuwancinshi dama karatu ya kai shi kuma ya gama harma ya fara aiki da wani kamfanin kera takalma da abaya irin na mata.

Gabadayansu sun gama karatunsu inda mohd Al'ameen ya karanta fannin kasuwanci da fasaha (watau dai ya gaji mahaifinshi) ya hada masters dinshi ya jona yanaso yayi doctrine dinshi ita kuma sauda tayi degree na biyu yayinda Nihal da abi suka kammala degree na daya itakuma afnan tana aji na biyu secondary wannan ne ya sanya Alhaji Mustapha ya tattara kan iyalanshi ya dawo qasarshi ta haihuwa domin qasar ta amfana da ilimin da 'ya'yan nashi suka samu

Amman sun baro afnan gidan aunty feena domin karasa nata karatun, suma su Nihal da abi zasu koma idan sunso su cigaba amman alhaji yace sai sunyi aure tukunna domin ya gaji da ganinsu haka zaga zaga dasu ba aure.

Inda moh'd Al'ameen ya wuce qasar america domin karasa karatunshi daya dauko ta fannin fasahar zamani domin kasuwanci ya iya harma ya fara da taimakon mahaifin nashi

Hajiya kubra tana nan da halinta dakuka Santa dashi tin farko saima abunda yaci gaba domin mahaifinta Alhj Nura Allah yayi mashi rasuwa bayan haihuwar Nihal aka raba masu gadonsu, kasancewar ta na diya daya tilo ta mallaki dukiya da qadarorin da suka kara mata girman kai da dagawa domin yanzu bata jiran Alhaji wajen komai saboda itama ta mallaki dukiyarta ta agani afada wannan shi ya qara sangarta 'ya'yanta dukansu in ka dauke yaAmeen da afnan da bama ta qasar gabaki daya saidai tazo Hutu

Gida na nunama sa'a alhaji mustapha ya qera masu a garin abuja suka tarkato daga gidanshi na katsina, ya ba yayanshi alhaji auwalu da ya tara zuriya shima da matarshi Zainab abun dai sai sam barka yayinda ya sake siyan fili ya k'ek'ara ma iyayenshi gida a cikin kankiyan tunda tsufa ya kamasu kuma sunki barin mahaifar tasu ya kuma Gina masu gidan gona Inda aka cigaba da kiwon dabbobi kama daga su kaji,talo talo dawisu,shanu,awakai da duk wasu nau'in dabbobi da kuka sani ya kuma bada ana masu noma tinda itace tushen arzikinsu shiyasa basu yada ta ba.

'Yan uwanshi mata duka ya gina masu gidaje ya qara masu jari kuma duk shekara sai wasu sunje hajji su da iyalansu
ya dauki nauyin karatun 'ya'yan gaba dayansu kuma sunayin karatunsu cikin kwanciyar hankali wasu ma ya fiddasu qasar waje suna karatun tinda Allah ya hore mashi yanzu duk fadin Nigeria babu dan kwangila sama dashi,ya gina ma'aikatu yana daukar ma'aikata ga sana'ar motoci da qarafuna duk ya nayi,kudi dai ko ta wacce hanya juyasu yakeyi wannan shine silar arzikin Alhaji Mustapha Dambulan din kudi kenan inda ya tara tarin masoya da mahassada arayuwarshi.

YaAmeen ya dawo daga karatunshi hankali kwance da tarin Alkhairai,qasar ta amurka taso rikeshi saboda kaifin hankali da hazakarshi, amman ya qiya saboda irin tarbiyyar mahaifinshi dakuma kishin qasar tashi nigeriya.




*Wannan Kenan Yanzu Aka Fara*

🌹🌺~Oum-Deedat ce~🌺🌹
[8/5, 8:20 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹

🌺🌺🌺🌺🌺

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~*

*Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat)

*Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat)

*Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, qanwa daya tamkar dubu,Allah ya barmu tare.


Page ~3~

•∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆•

Muje zuwa.......

Ahankali zanmaku wacece "Suhan" ya labarinta yake kuma me ya kawosu irin wannan gida dayake cike da tarin gadara, shagwaba, mutumci, halarci,dakuma miskilanci



"""""""""""""""""***********"""""""""""""""

Cikin hanzari na siya abunda duk nasan anada bukata na baro kasuwar da tarin idanu yayiman yawa,
adaidaita na hau tare da fada mashi sunan unguwar da zai kaini.

yayinda muka isa nace mashi ya ajiyeni nesa kadan da gidan, sanin danayi cewa YaAmeen yana gida, kuma zai iya tambayata dalilin dayasanya driver bai kaini ba, tinda shikuma ya hanani hawan okada, acewarshi drebobin basuda amfani in har wani acikin ahalin gidan zai dinga hawa hayis,

(oh ko su wanene ahalin gidan oho😵)

Ilai kuwa yana qofar gidan zaune bisa darduma, yana shan daddad'ar iskar dake busowa ta sanyin marece dakuma flowers dake busowa, a lokaci daya kuma yana latsa iPad din dake hannunshi, dagani wani abu muhimmi yakeyi,cikin sanyinshi da halinshi ko wayar ma sai an yi mata Jan aji da yanga?🙄

Suf suf na wuce, wuf na shige ta tamqamemen gate din dake kofar gidan mai double,

saboda har ga Allah yanzu nidai kunyarshi nakeji tun abunda yafaru dazu dani akanshi,wai nice yau kwance a k'irjin yaAmeen...k'irjin da kowa ke mararin ganin mamallakiyarshi shi, k'irjin da mata da yawa keson kasan cewa bisa shi,
ni nayi imani in ka kadauke kannenshi nice ta farko da na fara kwanciya bisa shi, nima fa a tsautsayi ne ba yin kaina bane ba tinda ko magana zamuyi bana yarda in kusanci inda yake kawai ina tsayawa ne ta inda zan iya jin maganar shi
Shima kuma yana k'ok'ari wajen ganin ya ma baya ga duk wata d'iya mace da ba muharramarshi ba.

( yo wa ma zai iya rungumewa wannan sarkin 'yan miskilan🤔)

Da wannan guntun tinanin nashige sashenmu damin isarma da ummarmu aikenta, nima inyi maza in hada ma aunty Nihal fruit salad d'in da ta ceman tana so,wanda saboda tsabar isa da taqama saidai tayiman text din in hada mata d'in.

Shi kau ta bangarenta yana lura da ita tin sa'adda napep ya ajiyeta da sand'on da takeyi kada ya ganta, bata san ta riga ta makaro ba,

murmushi yayi mai kama da an sanyashi dole, domin shidai lamarin yayinyar na bashi dariya, shidai har ga Allah ba shiga lamarinta yakeyi ba, amman ya kula mahaifiyarta na iyakar kokarinta wajen bata tarbiyya, ko motocin gidan ya kula mahaifiyarta ta hanata hawa.

bai gasgata ba saida ya tambayi malam mudi shugaban drebobin gidan yabashi tabbacin hakan, shikuma ya gargadesu da matsa mata kada su sanya ta bijirema umarnin mahaifiyarta, matar da yake girmamawa fiyeda tinanin kowa, yana sonta har cikin ranshi yake tausaya mata saboda ya kula akwai wani sarqaqqen Al'amari mai girma tattare da ita,


DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAN FI KARFIN TA BA
avatar
zakari-4

3 months ago

Reply

I really love the novel

Please Login or Register in order to submit comment