Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[04/12 09:41] Meela Adeel: 1⃣
° *ZUMUNCINMU A YAU* °
By Aysha Ya'u Kurah

*FIKRAH WRITERS ASSOCIATION*

'''BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM'''

Sadaukarwa ga mahaifi na kwarai *LATE ALHAJI YA'U KURAH* Allah SWT ya jikanka ya kai rahama kabarinka..

*SHIMFIDA*

"Assalamu alaikum" Ta faďi karo na uku cikin siririyar muryarta,
cikin ďaga murya taji ance,
"Wai wacece ta ke ta kwaďa mana sallama ne haka?!"
A hankali jikinta na rawa ta amsa.
" Ni ce."
"Tooo!! Sannu NI CE, me ya kawoki?"
Cikin rawar murya ta ce "Mamma ce ta aikoni in kawo muku abinci."

Daga cikin ďakin ta jiyo muryar dattijon wanda ya bata tabbacin shima yana ciki. "Toh ki ce an gode, je ki ďauki naira ashirin a saman tagar ďakina kiyi gaba."
A hankali ta sauke ďankwalin da aka ďaure kayan a ciki ta kwance ta fito da sababbin samirun tuwo da miya ta cire ďankwalinta tace "Nagode BAFFA, Allah ya saka da alkhairi." Ta ďauki ashirin ďin ta fita cikin k'unan rai.

A hanyar da zata sada ta da kofar gida taci karo da su Husna rik'e da manyan kuloli suna tafe suna nishi da kyar, rab'ewa tayi ta basu guri dan su wuce, suna karasowa dab da ita suka kwashe da dariya haďe da faďin "Nadiya roba-roba."
Badariyya ta ajiye kular hannunta ta shafi kayan jikin Nadiya tace
"Kaiii!! Wannan ba roba bace rai fess ce."
Suka sake tintsirawa cikin shakiyanci suka ce "Su Nadiya bana an samu canji, daga atamfar roba zuwa shaddar roba."

Cikin sanyin jiki tayi gaba tana jiyo ihunsu har suka shige cikin gidan.

Tana fita tayi tafiyar minti biyar sannan ta isa titin da zata roki masu mota su ďauketa da naira ashirin ďin da aka bata, dan in tace zata tafi gida a kafa sai ta kai yamma saboda nisa,
zuciyarta cike take da mamakin yadda zumuncin zamani ya koma,
tun tana karama ta ga mahaifiyarta na fuskantar irin waďannan wulakancin saboda kasantuwarsu talakawa, sau tari takan tambayi mahaifiyarta anya Baffa ne ya haifeta kuwa?

Acikin gidan kuwa, su Husna na shiga babu ko sallama suka faďa ďakin,
zabura Baffa yayi ya sakko daga kan gado yana faďin. "Lale da matana, lale-lale."
Badariyya ta faďa jikinshi tana faďin "Kakus, ina barka da Sallah na?"
Cikin rawar jiki yasa hannu a aljihu ya ciro yan ďari biyar-biyar sababbi ya k'irga goma ya bata,
yatsina fuska ta yi tace "Haba kakus, dubu biyar fa ka bani, ni gaskiya sunyi min kaďan Pizza kaďai zanci da su." Washe baki ya yi yace "To yar lele, an gama." Ya karo mata wasu biyar ďin ta mike a jikinshi babu ko godiya sai ma faďin "Ko kaifa, ai da na sake ka yanzun nan,,,
Husna ta matsa kusa dashi tace " Saura ni kakus."
Dubu goman itama ya bata saboda yasan sakon barka da sallan shi na tafe don tun safe y'arshi mafi soyuwa a gareshi ta kirashi tace zata aiko MUSADDIQ da sak'o, yasan sakon bai wuce na kuďi.
"Ina yayanku? Ko ba tare kuka zo ba?" Baffa ya tambaya yana gyara aljihu.
Badariyya tace "Ka ji kakus a kofar gidannan fa muka sameshi, yana fita muna shigowa dan ya riga Nadiya fita ma." Kallon mamaki yayi musu yace "Aiko bai shigo ba."
Goggo ta rufe kular da ta bude ta ce "Kasani ko ya manta da wani abu ne?"
"Hakane kuma." Ya faďi tare da basar da maganar.
Nan suka hau hira da ciye ciye, sun ma manta da samirun tuwon da Nadiya ta kawo saboda sunsan babu wani abun arziki a ciki.

Zaune take tayi tagumi tana jiran shigowar Nadiya dan tasan in Allah Ya yarda zata samu ko ďari biyar ce a gurin su Baffa na barka da sallah,
Zainab ce ta taso rike da robar abinci tace "Mamma zan kara abinci." Janyota ta yi jikinta tace "Yi hakuri auta, yanzu Anti zata dawo har madara ma sai kisha in kinaso kinji?"
Gyaďa kanta tayi cikin murna ta kurawa kofar gidan ido tana jiran b'ullowar yayarta.

A gajiye ta shigo gidan ta nemi guri ta zauna tana maida numfashi,
da sauri Zainab ta mike ta ďauko mata ruwa, karb'ar ruwan tayi haďe da janyota jikinta tace " Kin ci abinci?"
D'aga mata kai tayi, "Eh naci amma ban koshi ba. Mamma ta ce zaki kawo kuďi a siyo min madara."
A hankali ta ďago jajayen idanuwanta ta sauke kan mahaifiyarta, kallon tausawa juna sukayi sannan suka kau da kawunansu, cikin sark'ak'ak'k'iyar murya Nadiya tace "Mamma na kai musu, Baffa ya bani naira ashirin, ki tayani yi mishi godiya dan ya taimakamin, da a kafa zan dawo gida."
Cikin b'oye b'acin rai Mamma tace "Kai madallah!! Allah ya biyashi da aljanna, gaskiya naji daďi, tashi maza kije kiyi sallah."
Tana kokarin mikewa taji anyi sallama, juyowa tayi haďe da amsa sallamar, suna haďa ido tayi saurin kau da kanta,
Mamma ta mike cike da murna tace "Maraba da Musaddiq, yanzu kake tafe?"
"Eh Mamma ina wuni."
"Haba dai daga tsaye?" Ta faďi haďe da shimfiďa dadduma.
Zama yayi yana sosa k'eya suka gaisa sosai,
kuďi ya zaro a aljihunshi kusan dubu dari biyu yace;

"gashi inji mummy tace a kawo muku" bai jira jin me zata ce ba ya ajiye kuďin ya fice daga gidan da sauri dan yasan in ya daďe a gidan to asirinshi zai tonu..

Kasa tab'a kuďin tayi saboda firgici Kai anya Musaddiq yaji inda aka aikeshi da kyau kuwa?
Wannan kyautar tayi yawa dan tsakanin ta da yar uwarta bai wuce kyautar dubu biyar,

"Nadiya mik'o min wayar can" tace tana mai nuna ma nadiya wayar,
da sauri ta ďauko ta mik'a mata. Hannu na rawa ta fara neman lambar yar uwarta, sai da ta kusa tsinkewa sannan ta ďaga cikin isa da tak'ama,
murya na rawa Mamma tace "ina yini Hajiya"

"lafiya" kadai tace murya can k'asa, bata damu da amsawar ba dan in da sabo ta Saba, sai ta cigaba "yanzu Musaddiq Ya kawo min sak'o shine nace bar..."

Dakatar da ita tayi ta hanyar cewa "ina da abin yi Suwaiba nasan godiya kika kira kiyi, bakomai yiwa kai ne" tayi saurin kashe wayar, cikin mamaki ta ajiye wayar tana duban kuďin zuciyarta cike da farin cikin yar uwarta ta fara sanin muhimmancin zumunci....

Musaddiq na fita ya nufi motarshi ya kashe wayoyinshi ya ta da motar yayi gaba yana nazarin yadda zaiyi ya fahimtar da mahaifiyarshi da kakanninshi muhimmancin zumunci,

A kullum yana mamakin yadda zumuncin zamanin yanzu ya zama sai in kana da kuďi,
yana takaici matuka saboda irin wulak'ancin da Mamma suwaiba da ya'yanta ke fuskanta saboda kawai basu dashi, bashi da wani burin da ya wuce yaga kan zuri'arsu ya haďu, Mai shi ya taimaki mara shi, amma kullum abun k'ara lalacewa yakeyi saboda masu shi ďin basa taimakawa na jikinsu saidai na neman suna..

Mrs Tijjani Shattima...
[04/12 09:42] Meela Adeel: 2⃣
°ZUMUNCINMU A YAU °
BY Aysha Ya'u Kurah               

"Nadiya amshi maza kira min yayanku,
cike da murna ta karbi wayar ta latso number,

Yana zaune ya kifa kanshi a wheel barrow yana tunanin ta inda zai fara,
'Dan kudin dakon da ya samu na Sallah shi ya had'a yayi ma kannenshi kayan sallah, ragowar ya ba mahaifiyarshi tayi abincin sallah,
karar da wayarshi keyi ne ya dawo dashi cikin duniyar tunanin da ya tafi,
hannu ya zira cikin aljihunshi ba tare da ya d'ago ba ya danna ya Kara a kunnenshi,
Assalamu alai-- "hello Ya Hafiz ta katse shi cikin kaguwa,
dago kanshi yayi  cikin firgici yace "Nadiya Lafiya,?
fizge wayar mamma tayi tace "Hafizu kana Ina ne, duk abunda kakeyi ka barshi ka dawo gida, mikewa yayi da sauri ya Sanya silifas dinshi, ya kalli abokin aikinshi yace "Haladu dan Allah ka Mik'a min baron nan gidan oga lukman in har ban dawo da wuri ba,  Haladu yace "lafiya dai ko, "walhy ban sani ba mamma ke kira na, ya karasa fadi yana tafiya da sauri ,
"Allah yasa lafiya haladu ya fadi da karfi dan Hafiz ya kusa karya kwana,
zuciyarshi cike take da fargabar abinda zai je ya tarar a gida...

Hello Baffah, an yini lafiya,
baki har kunne baffah "yace lafiya lau ya sallar,
"sallah alhamdulillah,
"Dan Allah Baffa kace ma su Husnah su biyo MUSADDIQ na aiki Haruna driver,
to bakomai daga ya karaso zansa su taho saboda dare,
"kana nufin har yanzu bai zo ba baffah,
baffah yace "eh to sunce min sun ganshi d'azu amma ni har yanzu bansa shi a idona ba,
ikon Allah ta fadi hade da gyara zama,
ya rigasu fita gida fa, kuma saida na mishi kashedi akan yawo, Yanzu haka yana can gurin abokan banza, amma dai ya basu sak'onka ko? ,

"ko kusa bai basu ba, baffah ya fadi had'e da yak'e wanda yafi kuka ciwo dan ya kosa yaji makwafin kudin da ya ba jikokinshi da Karin wasu a aljihunshi,
"karka damu baffah bari in kirashi inji inda ya tsaya,
"too bakomai Kar dai ki matsa mishi kin San yaran yanzu saida lallami,
haka ne baffah nagode a gaida Goggo,"to zata ji Nima na gode,....

Kiran Musaddiq ta shiga yi, abin ya d'aure mata kai da taji wayoyin shi a kashe, lallai yau zan bala'in sab'a ma Yaron nan, duk fadan da na mishi akan shirman partyn nan baiji ba ko, Allah ya kawo shi gida wallhy Mai rabani dashi sai Allah ta wurga wayar cikin jaka ta d'auki gyale da mukullin mota ta fita...

"ji nake kamar a mafarki mamma, shafar kudin ya sake yi yace
"ban taba tunanin zan rike irin wadannan kudin ba a rayuwata,
Mamma da farin ciki ya mantar da ita damuwa da yunwa tace
"kaidai bari, Allah kenan maji rokon bawa, duk yadda mutum ya kasance cikin kunci da bakin ciki to in ya dogara da Allah sai ya samar mishi mafita,,
Hafiz yace "haka ne mamma, to yanzu ya zamuyi da kudinnan,
"shi nake tunani hafizu,
mu jira babanku ya dawo sai musan abin yi dashi,
  dubu biyu ta ciro cikin kudin tace je kayo mana cefane da wannan muyi abinci kafin ya dawo,

Zainab da ke kwance Kan cinyar Nadiya tace "anty Madara ta, Nadiya tayi dariya tace "kiyi hakuri yanzu za'ayi abinci muci,
mamma na jinsu tayi kamar bata ji ba tace,
"au Hafizu na manta ka siyo ma auta Madara kaji, Nadiya tayi murmushi tace kamar kinsan maganar da takeyi kenan, Mamma tace au haba, taho auta ta kinsan ni namiki alkawari kuma bazan manta ba,,                    haka suka kasance cikin farin ciki a ranar, ji sukeyi kamar babu kamar su a doron duniyar Allah SWT,                     Allah sarki, kud'in da bai wuce kudin naman wani gida ba shi ya Sanya bayin Allahn nan murna har suke Jin babu kamarsu......

Mrs Tijjani Shattima...
[04/12 09:42] Meela Adeel: 3⃣
°ZUMUNCINMU A YAU °
BY Aysha Ya'u Kurah

*******10:56pm******

Zaune yake cikin motarshi kafafunshi duk biyun na waje yana latsa wayarshi da ko minti uku baiyi da kunnata ba,
text din mummy ya karanta yayi d'an murmushi had'e da shafa kwantaccen sajenshi,
rufe wayar yayi ya sake duba agogo,…
gyara zamanshi yayi ya rufe motar yace
"na tabbata yanzu mummy ta isa k'asar Singapore ita da k'awanta cikin mafarki,
tada motar yayi ya karaso kofar gida,
kiran mai gadin su yayi a waya dan ya bud'e mishi gate,  yana tsoron latsa hon ya dawo da mummy cikin kasar Nigeria,
da sauri Mai gadin ya bud'e mishi,  ya shiga yayi parking a gurin da aka tanada dan ajiye Motoci,

Kiran waya ya shiga yi kafin ya karasa kofar parlon..

Badariyya na zaune tana buga game taji land line din dakinsu na Kara,
pause ta danna ta Mik'e tana tsaki,
"hello.. ta fadi cikin muryarta Mai cike da izza da isgili,
"hey Badar zo ki bude min kofa kuma kiyi a hankali Kar mummy ta jiki kin gane ko,
katse wayar tayi ba tare da ta amsa shi ba ta juya ta fita daga d'akin, 

d'akin mummy ta nufa, bud'e kofar tayi ta shiga ba tare da tayi sallama ba, dan a ganin Badariyya sallama ta talakawa ce,,
hasken da ya gauraye d'akin ne ya farkar da mummy daga bacci,
Mikewa tayi hade da mik'a tace "BADAR lafiya,
yaya Musaddiq ne ya kira ni wai in bud'e mishi kofa....

Bawan Allah yana waje yana jiran Badariyya ta bud'e mishi kofa,
ganin da yayi har minti 5 ta wuce bata bude ba ya fara mita cikin zuciyarshi, d'aga wayar yayi da niyyar sake kira yaji ana tab'a kofar,
tura wayar yayi cikin aljihu ya k'arasa kusa da kofar fuskarshi d'auke da murmushi,
"ina kika tsaya ne haka, har hakuri na ya fa---- maganar ta makale mishi a mak'oshi sakamakon ido hud'u da sukayi da mummy,
zaro ido yayi ya had'iye wani mugun miyau,
dariya ya fara yi yana fad'in mummy baki kwanta ba,
tun d'azu Ina nan k'ofar gida a zaune ni da Tinau Mai gadi yana bani Labarin k'auye,
sannan malam--- juyawa tayi ta barshi a tsaye,

shigowa yayi ya rufe kofar ya bi bayanta da gudu,
can gefe ya hango Badariyya tsaye tana mishi kallon raini,
harara ya jefe ta dashi yace "tun kina yar ficiciya kin iya munafurci da makirci Ina ga in kin girma, wallhy kinji haushin rayuwar ki idiot,,

tsaki taja ta wuce d'akinsu,,

Kofar dakin mummy ya karasa,
a hankali ya murd'a kofar ya shiga had'e da sallama,
kusa da ita yaje yayi kneel down ya kamo hannunta yace
"kiyi hakuri mummy, wallahi ba party na je ba, ina gidan su Mahmud tun da na fita daga gida,
sai dare na bar gidansu na dawo kofar gida na zauna,
Dan Allah kiyi hakuri banason wannan fushin please ya karashe a shagwabe,,

bata tanka mishi ba ta zame hannunta cikin nashi tace "bani,,

zuciyarshi na dukan uku uku yace "me zan baki?,

K'ara tamke fuskarta tayi tace kud'in Baffa da na aike ka dashi,

dakewa yayi yace "ni gidan mama suwaiba kika aikeni saidai ko driver kika aika gidan Baffa,

"karka raina min hankali Musaddiq,
kalleni da kyau banyi girman da zan fara mantuwa ba,

dubu biyar na baka ka kaima "SUWAIBA"

dubu d'ari biyu na Baffa, sai dubu Hamsin na k'anwar k'awata "Hajiya Nafeesa dake layin su suwaiba,

bud'e baki yayi yace "Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun,
mummy ai banji duk lissafin da kika min ba, ni dai sunan mama suwaiba kad'ai naji, na bata dubu dari biyu da biyar,
ga dubu hamsin nan a aljihuna na manta inda kika aikeni dashi,
karki damu gobe in shaa Allah da wuri zan kai mata, kika ce gidanta na kusa da gidan mama suwaiba ko?

Wani mugun kallo ta bishi dashi had'e da taune leb'enta,
matsawa baya ya fara yi dan yasan in mummy ta fara taune leb'e to abin da zai biyo baya bazaiyi kyau ba,

dai dai kofa ya tsaya kamar zaiyi kuka "yace mummy kiyi hakuri dan Allah,

cike da takaici tace "Musaddiq Anya rayuwar da ka daukarwa kanka Mai b'illewa ce,
ka zama almubazzari Wanda baisan darajar kudi ba,
in ba iskanci ba me suwaiba zatayi da dubu dari biyu harda d'oriya, wallhy tun muna mu biyu da kai gobe kafin goma na safe kaje ka amso min kudi na, kuma ka tabbatar ka kaima Hadiza kanwar Hajiya Nafeesa kana ji na ko,
gyad'a kanshi yayi fuskarshi da bata cika nuna fushi ba ta canza launi saboda tsananin b'acin rai,

Takalmin kafarshi ya cire ya kwanta yayi ruf da ciki yana tunanin yadda zaiyi ya samu dubu d'ari biyu gobe ba tare da yaje gidan mama suwaiba ba,

Sai karfe daya ya yanke shawarar Kiran yayyenshi mata ya fad'a musu komai yasan a cikinsu bazai rasa Mai bashi ba.....

Mrs Tijjani shattima....
[04/12 09:43] Meela Adeel: 4⃣
°ZUMUNCINMU A YAU °
By Aysha Ya'u Kurah

Kamar a mafarki yaji ana bugun kofar dakinshi, mikewa yayi akan dardumar da bacci ya dauke shi bayan sallar asuba,
mik'a ya fara yi hade da addu'ar tashi daga bacci,
kara buga kofar da akayi ne ya sashi kallon agogo,
goma saura kwata ya fadi da karfi yana mai karasawa kofar dakin,

murda kofar yayi a hankali  ya ja da baya hade da runtse idanuwanshi saboda tsoron irin kallon da zaiyi Karo dashi...

   *HAPPY 17TH BIRTHDAY BROO*

Muryoyin su ya daki dodon kunnenshi,
bude idonshi yayi da sauri ya bisu da kallo daya bayan daya,
wani murmushi ya saki mai matukar kyau, take ya manta da damuwar da ta hanashi bacci ya fara rungumarsu yana fadin "thank u so much sweeries,,

" Happy womb escape uncle" 
ya jiyo cikin siririyar murya,
''omg HINAD!! ya fadi da karfi,
murmushi tayi mishi hade da yi mishi nuni da hanyar shigowa dakinshi da idanuwanta,,

Ta madubin console din dake kallon dakinshi ya hangota tsaye cikin shigar jallabiya ta alfarma kanta yane da jan mayafi ta nade hannayenta a kirjinta tana murmushi,

ihu ya saki hade da kwasawa a guje ya nufi gurinta,
bude hannuwanta tayi ya fada kirjinta,

"Best birthday gift eva luvly sis, I love u so much,

dago fuskarshi tayi ta cire farin glass din Idonta tace
''Happy birthday little Diku nah, love you more,,

karasowa suka yi cike da mamaki suka ce ''saukar yaushe ANTY REEMA,

''yanzun nan!, ko gida banje ba, ta fadi tana maida glass dinta,

  waigawa musaddiq yayi gurin Hinad ya lakace hancinta yace ''cutie pie ina handsome?
yamutsa fuska tayi tace yana mota wai bazai shigo ba,
dalili? Musaddiq ya tambaya yana kallon Anty Reema,
''don't ask me kasan halin d'an naka,

kallon Sauran kannenta tayi tace mummy fa?,
RADIYA ce ta fara magana, ''muma zuwan mu gidan kenan, ina ga bata tashi ba,

hannun RAUDHA ta kama tace ''ina kika baro WALEED,?

''yana gidan Anty RALLY can yayi sallah, nasan suna hanya yanzu,, Raudha ta bata amsa cike da girmamawa,

falo suka koma dukkansu banda musaddiq da tuni ya fita gurin HILAL....

Maganata ta karshe kenan babu wanda ya isa ya sake dawo da ita farko,
bazan mishi party ba wannan shekarar FAKAT!!! mummy ta karashe fadi tana hararar musaddiq dake zaune kanshi a sunkuye,

but mummy why,?  RALIYA da shigowarta kenan ta tambaya tana karasowa parlon,

tsaki mummy taja ta tashi ta wuce kitchen,

Radiya da Raudha kuwa mamaki ne ya hanasu magana dan a iya rayuwarsu sunsan babu abin da mahaifiyarsu ke so sai bidi'a,
haka nan ma kirkirar party takeyi in kudi yayi mata yawa, babu d'a, ko jikan da shekara ta taba wucewa ba ayi mishi kwarya kwarya ba,
barin ma danta d'aya namiji tilo wanda partynshi ke banbanta da na kowa, shiyasa sukayi sammako dan ayi komai dasu, 

''wow MIRACLE ya sakko kenan,
yau mummy ce da kanta take cewa bazata yi ma little birthday ba,
iko sai Allah Anty Reemah ta fadi tana mai mikewa,

Raliya tace ''kedai bari anty na Kasa ajiye jaka saboda mamaki,,

'''Ba abun mamaki bane laifi yayi ma mummy'''

waigowa sukayi suna kallon ta inda maganar ta fito,

karasowa tayi rike da cup a hannunta tace
''kwarai kuwa, almubazzaranci yayi da kudin mummy,
ta aikeshi ya kaiwa Baffa shine ya kai gidansu Nadiya Roba Roba,
kuma kudin da yawa  har 200k,
mikewa musaddiq yayi a fusace yayi kanta,

rikeshi Anty Reemah tayi da sauri ta girgiza mishi kai alamar ya kyaleta,

Badariyya ta rike kugu tace da kin kyaleshi anty,
karya akayi maka, mtswww wanda bais----''shut up'' Anty Reemah ta katseta da karfi,,
''yaushe yarinyar nan ta fitsare haka,
Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun,
duka nawa kike Badar?, Musaddiq sa'an ki,

''Ba sa'a na bane amma abin da zaiyi ni bazanyi ba, dan Sam bashi da hanka-----

wucewar walkiya da tsayuwar ji na wucin gadi ne ya hanata karasa maganar,
rike kuncinta tayi ta Sanya kara mai firgitarwa,
cike da firgici su Radiya suka karaso gurin,
kallo anty Reemah ta bishi dashi yana huci hade da zazzaro ido,

cikin zafi yace ''I usually give people more chances dan dey deserve, but once am done am done,!
waye sa'an ki anan, tun dazu kina ta zuba rashin kunya an kyaleki shine kike kokarin wuce limit dinki,
ya kalli musaddiq cikin kunan rai yace
''kanwar kanwarka ta tsaya tana fada maka magana kai kuma kana tsaye kamar gunki, u'r pathetic wallhi mtswwwwwwwww, yaja tsaki hade da daukar wayarshi yace ''wannan dalilin ya hanani shigowa gidan nan,
kallon Anty Reemah yayi yace  ''plss lets go Mum,,

faduwa kasa Badariyya tayi tana ihu tana shureshure tana fadin ''Allah ya isa mugu azzalumi,
wayyo Allah na mummy ya tsinka min kunne,

da gudu mummy ta karaso ciki dan duk budurin da akeyi bata sani ba tana can bayan kitchen tana duba masu yi mata hidima.....

Mrs Tijjani Shattima....
[04/12 09:43] Meela Adeel: 5⃣
°ZUMUNCINMU A YAU °
By Aysha Ya'u Kurah

Ya ya, me yake faruwa? kukan wa nakeji kamar Badar,
da gudu ta ruga jikin mummy, Hilal ya bita a guje ya daga hannu zai kai mata duka mummy ta daka mishi tsawa, ''kulll karka sake ka taba ta, rasa kunya berar danga,

ko girgiza baiyi ba bare ya saurari abinda ta ce ya sauke hannunshi a bayanta,

wani ihun Badar ta sake saki kamar wacce ake yankawa,

kallon gurin da suke mummy tayi cikin bacin rai tace'
''Reemah dan iskanci kina tsaye danki zai raunata min 'ya, babu Wanda yayi yunkurin hanashi,
kuma saboda rashin ta ido ya iya Zuwa har gabana ya narka mata gudumar hannunshi a baya,
to wallhy bazan dauka ba, ko ki rama mata ko kuma ni in rama mata da kaina,

Raliya tace ' ''haba mummy, ya za'ayi mu shiga fadan yara,
Badar ce fa bata da gaskiya, rashin kunyarta kullum dad'a k'aburi yakeyi,
babu Wanda ya isa ya fada mata taji,
daga fitowarta babu ko gaisuwa ta fara magana cikin isa da rashin kunya,
thank God akwai Hilal a nan,  da dukan da zan mata wallahi sai yafi haka,

mummy ta saki baki cikin mamaki tace me tayi ne waiii,

Husna ta kwashe duk abinda ya faru ta fada mata,

mtswwwwwwwww mummy taja tsaki tace
''to karya ta fada, duk Wanda yaga
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment