Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

barta ita kadai ba in ba Damuwa sai na Rakata gidan naku..!
Yusif yaji Dadin haka da Sauri yace"Bakomai Mama mungode
Batace komai ba ta Nufi Ciki ta iske Safiya tsaye tana kuka Rikota Tayi tana Lallashinta,Hijabinta ta saka ita Maman ta kuma Dauki akwatin Safiya suka Fito sun iske su Sagir sun Fice suna Waje suma Wajen suka Nufa Safiya ta Shige Cikin mayafimta Tana kuka Kukan bakkn ciki irin auran Wulakancin da Mahaifinta yayi mata.
Mama ta rike da hannunta da alwatinta Imran na Waje tare dasu yusuf,Domin tunda yace Mama tace zata raka Safiya bai ce komai ba Mama ta Chanchanci komai.
Yusuf kallo Daya yayi ma Safiya bai kara ba a jin kukanta yake har Cikin Ransa Mota ya Shige Tunda Imran suje shi zai taho
Mama kuma ta juya tana barin ma Sagir Sallahu in Inteesar ta Dawo ya amsa mata Daga Maman har Safiyan gidan baya suka Shiga Yusuf na gaba Yajasu suka Tafi.
Suna barin kofar gidan ba Dadewa Imran ya Zaro Sigarinsa ya kunna ya Cigaba da Fesar da Hayaki Sagir na gefensa Yana kallonsa kai kawai ya kada bai ce komai ba.
Daidai Lokacin da mai adaidata ya ijiye Inteesar akofar gidansu Sagir din ta Fito Tana Duba Jakarta ta Daukoma mai Adaidaita kudinsa ta Mikamai ta Jiyo cikin Rangajinta Dauke da Jakarta da wasu Takardu a hannunta Idanuwanta sun kankamce saboda Gajiya Tunda ga Nesa Sagir yake washe mata baki Cikin mamakin gani ta gane Tunda Gashi har ta kawo kanta gida.







*Shakira...*
3/22/22, 23:04 - Ummi Tandama😇: *GIDANMU..!*
_(Our House)_
*Book1*

*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janafty❤️*


          *🅿?11*

"Itama tundaga nesan ta Hangoshi Tsaye sai wanda suke taren ne bata Damu Data kalli ko waye ba ammh Tabbas tasan yanatare da wani ne a Tsaye.
Kafin ma ta Kariso Sagir ya saki Mirmishi yana Fadin"Kai ashe kanwar tawa dai da gasken gasken Zata iya Dawo da kanta Gida kamar yadda tafada..?
Ya karishe Cikin Zolaya,Cikin Hararan wasa lokaci Daya Tana Dakuna fuska Daya Zame mata jiki tace"Kaji fa Yaya Sagir ce maka akayi bazan iya Dawowa ba..? Ai daman na Fadamaka ina da saurin Dauke waje in dai naje koda Sau Daya ne..!
Tafada Daidai Tana Gama Tsayuwa agabansu Cikin gyada kai yace"Ah Lalle naga alama kuwa..To ya makarantar..? Hop karatun ba wahala..!
Inteesar ta yi naka naka da fuska kamar ta Saka kuka Tana Fadin"Wlh yau kamar na Dora hannu akai nayi ta Ihu..Karatu ai daman akwai Wahala ya Sagir ga bakunta ga rashin Sabo..gabadaya Jikina Ciwo yake kamar anyimin Dukan Tsiya..!
Ta fada Lokaci Daya tana kara hura Kafofin Hancinta jin kamar Warin Data Tsana aduniya warin da in Ta Shaka yake Fitar da ita daga Hayyacinta Wato Warin SIGARI.
Sagir bai Fahimta ba yace"Ke dai kawai kice ke Raguwa ce..!
Inteesar najin Zuciyarta na tashi da Warin Taban Dataji kuma bata ga Sagir Dashi ba..Kuma Tunda tazo wajen Hankalinta bai bata tama kalli Barayin Imran ba kamar yadda Shima ko Sau Daya bai kalleta ba Karan Sigarin Dake hannunsa Tuni ta Kare sai ya Murjeta a kasa koda Inteesar tazo Warin kawai ta iske,Hankalinsa kwata kwata baya kansu yana kallon Gefe ne yana wani Tunani,Tunanin yadda komai na Rayuwarsu ke zuwa Daga wannan sai wannan.
Inteesar Da tsayuwar wajen ya Fara Gagararta Ga tashin Zuciya Tana jin kamar Zatayi amai Tunaninta bai bata Sagir ke shan Sigari ba Sai tayi Tunanin kila wani ne yazo yasha a wajen Shiyasa taji wari.
Cikin Dan Dauriya ta Harareshi kafin tace"Hakama yanzu Ya basheer ya gama Tsokana.munyi waya dasu sun kai gida tun dazu..Umma tace tana ta kiran Wayar Mama bata Daga ba.tacemin in na Dawo na Hadasu suyi mgana ni kuma 5:30pm muka Fito Lacture,sai na Tsaya na Tambaya aka Nunamin Classrep din mu na Karbi Lambarsa Saboda Shedules din makaranta Tunda bansan kowa ba kuma an wuceni Kafin nazo..!
Sagir yace"Daz a very Gud Idea...Hakan nada kyau kinga sai ya nunami ki inda akayi kafin kizo..Mama kuma Wlh ta Fita nan Makota yanzu bada Dadewa ba tace in kin Dawo abinci na kitchen har ruwam Zafi ta saka miki a Falas yar gatan Mama..!
Inteesar Tayi dariya tana Fadin"Eh din ko kaji Haushi ne nazo na kwace gwannatin ka..? Kamar mama ta sani na gaji wanka nake so..Ga yunwa duk wunin yau Cway ne kadai Acikina..!
Sagir ya zaro ido kafin ya samu Zarafin mgana Hayakin Sigarin da Imran ya Zuka ya fesar har Wajen Fuskar Inteeaar wacce taji abun kamar Al"amara nan da nan Hankalinta ya tashi Taja Baya Jikinta na kyarma Lokaci Daya tana Jan Gefen mayafinta ta Rufe Hancinta Tana Fadin"A'UZUBILLAHI MINAL SHEDANIR RAJIM..'
Haka ta fada jin yadda Zuciyarta ke tashi Cikinta na Hautsina ga Miyau ya Taru a bakinta tana gabda da Amai alokacin.
Sai a wannan Lokacin gabadayansu suka Kalli Juna shi Imran Bai san Inteesar na wajen ba har Lokacin Shifa Tun sanda ta Nufosa yaga Sagir na mata mgana ya Shiga wani Sabgan Aduk a tunaninsa sun gama mganarsu ta Wuce Imran Mutum ne da bai Cika Damuwa da Mutane ba Shi d'an i Dont Care ne.
Ta"awizin Data Sakarmai yasa yasan tana Wajen Har ya Dago yana so yaga wata Yarinya ce take Sakarmai ta"awizi haka Charaf kuwa Idanuwansu suka Hadu waje Daya wanda nan take Zuciyoyinsu suka buga atake tare da wani bakon Lamarin da basu gane ko na miye ba ammh dukkansu sun kurama juna ido Cikin Wani yanayin da suka,kasa Dauke Kallonsu Daga kan junanasu Tare da bugun Zuciyan da basu Gane ko na Miye ba,Ita Inteesar tana kallonsa zuciyarta nayi mata rawa sai take ji kamar ta sansa,yanayinsa bai yi mata kama da bakon data ta taba gani yau ba.
Shi kuma Kallonta yake da mamakin Furucinta Shi bazai iya tuna Yaushe Rabon Daya tsaya yana kare ma Wata mace kallo ba,Ammh yau sai gashi yana Kallon Inteesar Dayaji ya kasa Daina kallonta,Sannan kuma Ransa ya gama Kuna da baci da jin ta kiramai Ta'awizi,uwa uba kuma Tana Faman Toshe Hanci kamar taga kashi.
Ita kuwa Inteesar,Warin Sauran Sigarin Dake Hannun Imran ne ta isheta Gabadaya ta kasa Hadiye Miyan Bakinta ga Zuciyarta na Tashi Amai nataso mata,Yasa ta kauda kanta da Sauri ta Zubar da miyan Daya Taru a Bakinta sagir Dake Tsaye,Yaga abunda ya Faru,nan da nan ya juya yana kallon Imran yaga yanayinsa sai yaga ya Hade rai ransa Tamau kamar ma yafi koyaushe,Sai wani kallon Sama Da kasa yake Bin Inteesaer Dashi.
Ganin haka yasa ya juya ga Inteesar yana Fadin"Inteesar lafiya kuwa.?
Cikin kara Toshe Hanci tace"Ya Sagir Warin Sigari...Bana son Warinta sam..Amai yake Sakani Da Tashin Zuciya..."
Daga haka bata ma tsaya kara mgana ta kwasa da gudu zuwa Cikin Gida Jin Aman yana Kokarin Fito da kansa ganin Haka yass ya bi bayanta yana kiran sunanta,sai bata tsaya ba Har zai Bita cikin gidan sai kuma ya Tuna da Imran sai ya fasa sai dai me yana Juyowa shima Imran Din yaga Bayanan,sai ya hangesa ya mika Hanyar Gida baki ya Rike aransa Yana Fadin Allah ya Huci Zuciyarka Inteesar ta tabo wanda bata sani ba.
Sai ya koma Cikin Gidan nan ya iske Inteesar sai Sheka amai Take Duk Sai da Ta amayar da Cake din Dataji da Lemo Sagir Shi ya Taimakamata da Ruwa ta wanke bakinta,ya kuma kwasan mata Littafanta da Jakarta Zuwa Cikin Falon mama.
Sai da ta Zauna Tana kana ta Shiga Sauke Numfashi Sama sama.
Cikin Tsausayamata yace"Sannu..!
Da kai ta amsa Kafin tace"Yauwa..Yaya Sagir ina ka samo Aboki D'an iska..?
Sagir ya Zaro ido yana Fadin"Waye Dan iskan..? Wai Imran..?
Inteesar ta Dakuna Fuska Kafin tace"Oho..Ni nasan ma sunansa..Eh mana..Sigari fa yake Sha agaban Mutane bako kunya..!
Sagir yayi mirmishi Kafin yace"Ai Shan Sigari ba Iskaci bane Inteesar..Sai dai Kawai kice Tana Illah ga Lafiyan Dan"adam...!
Inteesar ta saki karamin Tsaki Kafin tace"Duk Daya..Ni Wlh Tun ina karamata Daukan masu Shan Sigari nake yan iska..Ballatana Warinta bama Sonsa amai yake sakani da Tashin zuciya.
Sagir yace"Sai don haka..Ammah shan Sigari ba Iskanci bane..Hakama Abokina ba yadda kike Tunani bane..!
Tabe baki kawai Inteesar Tayi bata kara Mgana ba,ganin haka yasa Sagir ya mike Tsaye yana Fadin"Bari na Leka Shago..Komai kike Bukata ki Duba Kichen ko kina Bukatar wani Abun ne..?
Inteesar ta girgiza kai kafin tace"Bana Bukatar komai..!
Daga haka sagir yayi mata Sallama ya Fice Daga Gidan Inteesar ta kwashi Jakarta da Littafanta zuwa ciki Tana kunkuni ita kadai Tana Fadin"Allah ya isa..ya sani amai duk naji ma bana jin cin komai..Allah ya isana Wlh..!
Haka take ta Mita ita Kadai kyan Jikinta ta Cire ta Duba Flas din Mama Taga Ruwan zafi ta Juye ta shiga wanka Dashi Ta Fito bayan ta Dauro Alwala jin ana kiran sallar mangariba Lokaci Daya Tana mamakin ina Mama taje haka..? Bata samu mai bata amsa ba,Ta Sauya kaya zuwa wasu Riga da Wando Marasa Nauyi ta Dauko Donut Din Da tazo Dashi Taci Kadan ta fito Falo ta Duba Fridge din Mama ta ga Lemon Cy,ta Dauka tasha Kadan ta Hada da Dunot din kana ta koma Ciki Ta tada Sallar Har ta idar ba"a Kawo Wuta ba Duhu ya Fara sai ta kunna Fitilar wayarta ta Fito Falo ta Dauki Tsintsiya ta Share Falon,Kana ta Dauki Littafanta da abunda akayi musu karatu yau ta Fito Falo Tana dubawa Lokaci bayan Lokaci Tana Duba Hanyar na ganin Dawowar Mama ba ita ba Sagir Kiran Daddy ya Dauke mata Hankali Daga Kadaicin Datake yi ita kadai.

******
Mama ita da kanta ta Shiga da Safiya Har Cikin Falon gidansu Imran,bayan ta Umarceta Data Shiga da kafar Dama Ta kuma yi addu"an Neman kariya da Zaman lafiya,Yusuf na Biye Dasu Dauke da akwatin Safiya yana Jinsa kamar yana Yawo a sararin Samaniya saboda Farinciki.
Gefe Daya kuma kukan Safiya na Tayar mai da Hankali,Sai kuka take Cikin mayafi kukan da bai isa ya Hanata yinsa ba yanzu.
Afalo yace su Zauna kafin yace bari ya Shiga Ciki ya gayama Abba Mama tace toh..Lokaci Daya Tana Zaunar da Safiya kan Kujera Itama ta Zauna Gefenta Tana kara Bin Falon da kallo Ko"ina Shuru da alamu babu kowa Babu dai abunda ya Sauya Daga yadda tasan Gidan
Ba jimawa sai ga yusuf ya fito Fuskarsa Cikin Fara"a yace"Mama Abba yace ku shigo..!
Mama ta mike Tana Fadin"Taso muje Safiya..!
Tafada Lokaci Daya tana Rikota Mikewa Tayi Kanta Har Lokacin Yana Cikin mayafinta shi yayi musu jagora Har zuwa Dakin Abba.
Yana Zaune gefen Makeken gadonsa,Sanye da Jallabiya mai Ruwan Madara ya Rame sosai gemunsa ya dan Taru Da Farin gashi,Yana Rike da Charbinsa yana ja Da alamu Alwala yayi Domin Fuskarsa akwai Dashin Ruwa.
Yusuf ne akqn gaba Mama dake Rike da Safiya na Binsu a baya,Gefen Abba ya Zauna yana Fadin"Abba gasu nan..Mama ku zauna don Allah!
Mama ta zaunar da Safiya saman Cafet a gaban Abba itama ta Zauna Gefenta Tana gaishe da Abba ya amsa mata cikin Sakin Fuska,Duk da bai da lafiya ammh yasan mai Gaisheshi Duk da bai taba Tsayawa ma ya kare ma Maman kallo ammh Tabbas yasan Maman Sagir abokin Imran Tazo Gaisheshi ba sau Daya ba Shiyasa ya amsata Cikin kulawa Duk dama Yusuf yamai Bayani komai.
Mama ce ta Dafa kan Safiya Tana Fadin"Ga Safiya nan na rakota..gidana kanin Mahaifinshi Shi Sagir din da Sukaje suka sama da mganar Nema ma Yusuf din aure ya kawo ta Bayan Mahaifinta ya Riga ya Daura auran kuma ya Hadosu da ita..Shine nace bazan barta Tazo ita kadai ba bari na Rakota..!
Abba ya jinjina kai Shuru kamar bazai yi mgana ba sai chan yace"Bakomai yusuf yamin bayanin komai..Mungode kwarai kiyi ma Kanin Shi Mahaifin yaron naki Godiya,Nagode kwarai Daya Tsaya ma Dana bawai Domin yq rasa masu Tsaya mai bane..A"a sai Domin wasu Mtsalaloli na Rayuwa..!
Mama ta Murmusa kafin Tace"Ayya Bakomai..Ai ya"ya na kowa ne Alhaji..!
Abba ya gyada kai yana Fadin"Hakane Duk da hakane Dole Zanyi Godiya Sabodq yayimin ni abunda ina da Rai na kasayi Saboda Rashin Lafiya ammh da Izinin Allah da Taimakon Ya"yana dana Likitan Dake Dubani na Fara Samun Lafiya na Dawo Cikin Hayyacina da Yardan Allah komai ya kusa Zuwa karshe..!
Mama tace"Allah yasa..Allah ya kara Lafiya..!
Yusuf ya amsa da Ameen Kafin Abba ya kalli Safiya Dake Duke kanta Cikin mayafinta Tana kuka Abba ya kalli yusuf kafin yace"Ya sunanta...?
Yusuf na sosa keya yace"Sunanta Safiya Abba..
Abba ya maida kallonsa kan Safiya ya Daga baki ya kira Sunanta Har sau Biyu ta amsa Cikin Dattako yace"Dago kan ki nan yata..Dago kanki ki kalleni Dakyau ni ba Surukin ki bane..Daga yau ni UBA nake gareki Safiya kamar yadda nake Uba ga Yusuf da imran da Maimunatu..!
Ba Safiya kadai ba Hatta Mama kalaman Abba sun kashe mata Jiki Cikin Sanyi Jiki Safiya ta Dago kanta ta yaye mayafinta Tana kallon Abba da Jajayen Idanuwanta,Lokaci Daya Tana ganin kamar Yusuf ne ya Tsufaa ga kuma Yuauf din a gefensa Tabbas wannan kamar har ta baci bazata iya Juran kallonsa ba sai ta Sadda kanta Dan Mirmishi Abba yayi kafin yace"Allah ya albarkaci Auranku..Dukkanku ya"ya na ne..Saboda Haka tare zanyi muku Faada..Ku Rike amanar Junanku Yusuf ka Riketa Amana Domin Tayi maka Hallaci,ni kuma nayi miki alkwarin Zan Tsaya Miki mtsayin Uba koda watarana Yusuf yayi miki Wani abu kada kiji komai kizo ki Fadamin Daga Rana mai kamata ta yau ni zan Dinga Tsaya miki Har karshen Numfashina..!
Kawai sai Safiya ta Kara Rushewa da wani kukan,Kukan Farimciki da wani yanayi Domim kalaman Abba Dagaji Daga Cikin Zuciyarsa ne.
Mama ne Tana Mirmishi tace"Ai kagama Mgana Alhaji..Allah ya basu ZAman lafiya..!
Abba da yusuf suka amsa da Ameen Ameen.
Abba ya kalli Yusuf yana Fadin"Yanzu ina Zaka sakata..?.dazu na Fita na Zaga ko"ina Gidan yana da Girma sai dai ba plan akan ginin.."
Mirmishi Yusuf yayi kafin yace"Komai zai koma Daidai Abba..Zamu zauna da ita adakina..Kafin na gyara mata Falo da Bedroom din Dake kusa dana Munari..!
Abba ya jinjina kai kafin yace"Hakan ma yayi kyau..Ammh dai Zaki Rakata Har Dakin Mijin nata ko..?
Mama tace"Me zai hana..? Sai na mikata.."Abba ya Gyada kai kafin yayi ma Mama Godiya ta mike ta Riko Safiya suka Fice yusuf yabi bayansu Abba ya bisu da kallo yana kokarin Shanye Hawayen Dake kokarin kawo mai.
Sun Fito kenan Falon Yusuf ya Dauki Akwatin Safiya yayi Musu Jagora Zuwa Dakin nashi Imran ya Shigo Kamar an jehoshi Ransa a bace yana Tafiya yana Wani Buda Jiki Daga Yusuf Har Mama ba wanda ya kallah Balanta su suka ran zai yi musu mgana,yusuf ne ma yake kiran Sunansa yayi kamar bai ji ba ya Tura Kofar Dakinsa ya Shige ya banko Kofa Baya ji,sai karan Ta"awizin Inteesar Dake mai amsa kuwwa cikin kunnuwannsa,Sai kuma ganinsa Gabadaya na Hasashomai Lokacin Data toshe Hanci ne da Lokacin Data
Zubar da Miyar Ransa ya gama Baci.
Bango ya Daka da Hannuwansa yana Fadi"Who is she..? Who is d Hell is Her...? Da har zata Toshemin Hanci ta kuma Zubarmin da miyau bayan ta Kirani Shadani..!
Waye ita.? Haka yake Fada Zuciyarsa na Tafasa yana Daga Tsayen ya Zaro Sigari ya kunnata ya Yi mata kyakyawan Zukan da sai da yaji Ya kware da Hayaki kana ya Dakata ya koma yana Tari Idanuwansa sun kala sunyi Jajir,Kan kujeran Kwara Daya Dake Dakin ya Zauna ya Dora Kafa Daya kan Daya yana Girgiza ta Hannu Daya kuma yana ta Zukan Sigarinsa yana Fesae da Hayaki.
Yana Tuna Ko Lokacin da yake amsa Sunansa na Natsattsen Imran Abubakar Malami ba wata macen Data Taba kallonsa Tayimai wadandan Abu uku da yarinyar tayimai ba..Tun ba yanzu ba ya Tsani Raini Shiyasa baya Hulda da mata Sannnan su da kafara Sakarmusu Fuska Zasu Samu Hanyar Rainaka..Ballatana da yanzu yake jin kansa na ya Ishi kowa Riga da wando..Ya ke jin kansa a Mtaayin roban Wando Daidai da kugun Kowani Shege bama shegiya ba..Shine wata Yarinyar karama Zata Kirashi Shedanu ta kallesa ta Tsitar da Miyau ta kuma Toshe mai Hanci ba bu Wanda ya taba cimai Zarafi irinta,Duk iya kokarimsa Na ya Cire Abun aransa ya kasa ji yake koda waasa abun bazai iya Wucewa a wajensa ba Har Abada.
Sai da aka kira Salla ya tashi Bayan ya gama karar da kwalin Sigari Duka Ya Fada Tiolet aranshi Yana ji in Sagir ya bari suka Hadu Wlh sai ya Nausheshi a Bakin da sai Hakoransa na gaba sun kama gabansu Saboda ko yayane Shi yajawomai Raini wanchan wannan kwailar yarinyar inda bai Ganta yayi mata mgana ba ba yadda Zatayi ta Tsaya Har ta Cimai Zarafi ba.
Yana wanka yana kwafa,ji yake kamar ya Daki kansa yana jin Haushin yadda ya iya kyaleta bai Tsinkamata marin Da Sai ta ga Taurarin Wuta Wanda nan gaba Ko bashi ba Bazata kara Kokarin Raina ma wani wayau ba ballatana taci Zarafinsa ba.

Mama Har kan makeken Gadon Yusuf ta ZAunar da ita bayan Tayi mata addu"a da yar Nasiha ita da Yusuf kana Tayi musu Sallama Tace Zata tafi Yusuf yace zau kaita Gida tace ya Barshi, yayi Zamansa Sai dai yaki jinta Sai da ya rakata Har Bakin get yana mata Godiya kana ya koma Cikin Gida ita kuma ta gangara Zuwa Gida acikin Ranta Tana addu"am Allah yasa Sanadiyar Safiya Chanji mai Girma ya Faru a wannan Gidan
Tafiyanta ba Dadewa sai ga Munari ta Dawo mai Napep ya Sauketa ta Sauka ta Bashi kudinsa ta Buga get Iro ya leko ganinta yasa ya Bude mata karamar Kofar ta ahigo yana mata Sannu da zuwa Bakinsa Cike da gulmar Shigarsu Mama da Safiya da Fotowarta ita kadai sai dai bai samu Fuska ba a gajiye take Ga yunwa ga Wahalan makaranta.
Tana Shigowa Falon dakin Abba ta Wuce Direct ta iskeshi Yana Sallah Kanta ta Dafe ta fice Zuwa Dakinta tasan Ya Yuauf ya Dawo Tundaga Motarsa,Yau tayi Dare Tun Dazu suka Tashi Ta tsaya Amsan Note ne wajen Classrep dinsu,Sai kuma Data Fito Bata Samu Abun Hawa da Wuri ba.
Dakinta ta yada Zango,Tiolet ta wuce Tayi alwala Tazo Tayi Sallar Tana Idar ta Fito Zuwa Kitchen ta Duba Flaak taga Da akwai Ruwwn Zafi sai ta Samu karamin Mug,ta Zuba ta Fito Zuwa Saman Dinning ta Fara Hada Tea sai ga Yusuf ya Fito Kamar zai Fita Cikin Hanzari da Sauri ta saka baki ta Kira sunansa ya Juyo yana kallonta Kafin yace"Munari yaushe kika Dawo..?
Ta Dauko mug din ta Nufoshi Take Fadin"Yanzu..Na shiga wajem Abba naga yana Sallah..naga Motarka sai nayi Tunanin kana cikin Dakin ka ne..!
Yusuf yace"Yauwa..Gwara ma da kika Dawo..Gama Shan Tea din nan ki Shiga ki Zauna da Safiya..!
Munari ta kallesa Sakaka kafin tace"Wata Safiyan kuma Yaya..?
Kansa ya Dafe kafin yace"Kash..Is a Long Story..Atakaiche dai Matatacce Dazu aka Dauramana aure...Ayanzu hakama Tana Dakima..Ki Zauna da ita Zan je na Dawo..!
Munari mug din Hannunta ya kusa Subuce mata Cikin Mamaki tace"Anty Safiya ce matarka Ya yusuf..? Am so Comfused how Comes..?
Kai ya gyada kafin yace"Lilsiy..Ki bar wannan mganar zamu yi ta Daga Baya..Yanzu dai juz go..!
Munari tace"Oly..To dafa abinci zan Doramana kaga Tun Safe bana nan kuma Abba bai ci komai ba..!
Yusuf Daya kosa da mganarta ya kama Hanyar ficewa yana Fadin"Who tell u..?Zan yo mana Takeaway in zan Dawo..!
Munari tace"to ina shi Ya Imu..?
Karamin Tsaki yaja ya fice yana Fadin"Check him..In his Room mana..!
Daga Haka yafice Lokaci Daya yana Laluban key din Motarsa.
Tsalle Munari ta Dakata bata ma Tsaya Shan tea din ba ta maidashi Saman Dining ta Fada Dakin Abba ta Iakeshi ya Idar da Sallah yana Azkar Rumgumesa Tayi ta baya tana Murna da Ihu yana jinta yasan ta samu Labari Allah Sarki.
Shi Munari ta Tasa da Tambaya sai da ya gamayata yadda Yusuf ya gayamai da Abunda ya wakana,Munari Ta Washe baki ta Mike Tana Fadin"Wlh mu muna sonta Abba..Indai zata Zauna Damu..Zamu zameta komai da komai ko Abba..?
Kai ya gyada mata yana Jan Cashaba Lokaci Daya yana Fadin"Da yardan Allah..!
Ficewa Tayi tana Fadin"Abba Let me Met my Sister Inlow For d First time..!
Tafice ya Bita da kaallon Tsausayi Munari mai son Mutane ne ya Tabbata Batajin Dadin Zaman da sukeyi Daga ita sai yan"uwanta acikin Gidan nan

Safiya na Zaune inda Mama ta Zaunar da ita Har yusuf ya Fita ya barta bata Motsa ba Duk yace ga Tiolet nan ta Shiga Tayi Alwala Tazo tayi Sallah kafim ya Dawo ammh ta kasa Tashi Abubuea ne ke Dawomata Daki Daki.Na yarda auranta ya Faru kamar almara Allah Sarki mommy,ta Tuna Sadda take kuka tana Rike ta Tasan Laifin Abun su ne da Ta Mommy ce bazata bari ayi haka ba,Anfi karfinta ne Tuna Haka yasa ta Dauko Wayarta Dake Jikinta ZAta kira Mommy sai ta iske Missed call dinta ba adadi Jikinta na Rawa ta Bi bayan kiran,kira Daya taji an Daga kiran lokaci Daya Taji Muryan Tasleem da Mommy alokaci Daya suna Tambayanta ina ta Shige ne suna ta kiranta bata Daga ba.
Safiya taji kuka ya kawo mata Cikin kuka tace"Ina Gidansu Yusuf Mommy..Wayata Tana Silent Banji ba..!
Tasleem ta Saka kuka itama Tana Fadin"Anty Safiya..Nadawo naji Abunnda Abbu ya aikata Miki..Nayi kuka Mommy ma sai kuka take Kuma munso mu Boyoki Abu ya hana yace ba yanzu ba..!
Safiya na Sharan majina tace"Kada ki Damu Ina nan lafiya Safiya..Kuma Zaki zo inda nake Abbu zai barki kizo Insha Allahu..!
Tafada Tana Sharan kwallah kafin Tasleem din Tayi mgana Mommy ta karbe Wayan Tana Fadin"Safiya zan zo na Tafi Dake..Bazan yarda da wannan auran ba..!
Safiya na Zubar kwallah tace"A"a Momny kada ki yi abunda Abu zai Yimiki Abunda mu bazamu mu manta ba ....Kinsan Halinsa fa kiyi Hakuri Insha Allahu ba Mtsala..Gidan Maman Abokin Kaninsa suka kaini Ba Dadewa yusuf dun yazo ya Daukeni zuwa Gidansu ita Maman abokin Ta Rakoni zuwa Gidansu Yusuf din..Mommy kada ki Damu ki barni nayi Zaman aurena Abba mahaifin Su Yusuf yace min kamar ya nake garesa zai rikeni kamar yar daya Haifa ta Cikinsa..!
Mommy ta Sauke Numfashi kafin tace"Shikenan..Ammh bazan yarda ya aurar dake a wulakance ba..Sai na kwatan miki yancinki..Ki rika barin wayarki kusa Dake zamu Dinga kiranki..!
Ta Bude baki Zatayi mgana kenan Munari ta Shigo Dakin Tana Fadin"Hello Bhabi..!





*Shakira...*
3/22/22, 23:04 - Ummi Tandama😇: *GIDAN MU..!*
_(Our House)_
*Book 1*

*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janafty❤️*

          *🅿?12*

"Safiya tana ganin Shigowar Munari Ta Sanyaya Murya Tana Fadin"Mommy zan kira ku zuwa Gobe..Ki lallashi Tasleem Plz..!
Hajiya Mero Dagachan bangaran ta share Hawayenta Tana Dafa Kan Tasleem Tace"Shikenan Ki kula da kanki Don Allah..!
Safiya ta gyada kai Lokaci Daya ta katse kiran bayan ta dago Fuskarta Tana kare Munari kallo ko da bata Taba ganinta a Zahiri ba a kallo Daya zata gane Ita din Jinin Yusuf ce Ballatana Ta taba ganinta a Hoto a Wayar yusuf ya nuna Mata kuma Labarin Munari da Imu har Ta gaji da ji Ta Haddaceshi Saboda Karya ne Yuauf yazo wajenta ko ya kira Wayarta su gama Hira bai ambacesu ba ko bai Fada mata ba ta Tabbata su din sune Jinshkin Mijin nata.
Shiyasa ta Saki Fuskarta kamar yadda Itama Munarin ta Washe mata baki Gefen gadon ta Zauna Tana Fadin"Anty Safiya Wlcm to Our House..Ina miki Fatan Alheri..Sunana Maimunatu Abubakar malami ni lilsister din Mijinki ne ya yusuf..Ina Farimcikin Zamowarki Daya Daga Cikin Ahalin gidanmu ayau..!
Tafada Lokaci daya Tana mika mata Hannu alamun Musabaha.
Safiya Tayi Mirmishi kafin ta mika mata nata Hannu suka Sarke lokaci Daya tana Fadin "Nagode Sosai Munari..Nima ina Farincikin Haduwata Dake sosai..!
Munari ta Washe baki kafin tace"Waya Fada miki ana kirana Munari.?
Safiya tace"Wazai Fadamin banda Yayanki..? Abakinsa naji Sunanki mai Dadi munarin Abba Auta ko.?
Munari taji Dadi sosai Soyayyar Dan"uwanta na Ratsata tace"Yes..Haka kirarin yake..Ina jin Dadin sunan sosai Saboda Abba ne ya Sakamin Sai kakata wacce ta Haifi Abba na Daada Dayake Sunan Autanta su Abba naci Goggo Maimuna..!
Safiya tace"Allah Sarki..Duk suna ina..? Ita kakar taku da goggon taku..?
Sai Munari taki Cewa sanin ba Huruminta bane safiya na Nazarinta Sai ta Waske Kafin Tace"Yanzu dai ba wannan ba..Naga Abba Sauran Imu bangansa ba ko baya nan ne..?ko shi ne Dazu muna Falo ya Shigo a Fusace ya Shige Daki ya Bugo kofa..?
Munari ta kalleta Har Lokacin Suna Rike da Hannun Juna tace"Bansani ba ko ya Dawo..Nima ai yanzu na Shigo Gidan Tun safe ina makaranta Buk nake Karatu Fanni Economics..!
Safiya ta jinjina kai kafin Ta gyara Zama Tana Fadin"To dawa kuke barin Abba in kika Tafi Makaranta Yusuf ya Tafi wajen aiki..? Kuma meke Damun Abba ayadda na Fahimta a labarin da Yusuf yake bani kullum yana Daki baya Fita ko"ina ko Bai da Lafiyan Kafa ne..?
Da Sauri Munari tace"Lafiyar Kafarsa Kalau..Bashi da lafiya ne Shiyasa Su Yaya yusuf basa yadda ya Fito ko Falo
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment