Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yace"Shikenan Sai na Dawo Take Care Of Ur Self..Zan Taho muku da Abinci..!
Da Sauri Safiya tace"Daga jiya kagama Siyan Abinci My Dear.
bai samu ce mata komai ba Farinciki ya Cika ransa Daganan sukayi Sallama.
Banganran Abba kuwa kamar Sabon Mutum haka ya koma yau ya Fita Waje yaga anguwan Dayake Rayuwa,,Iro megadi yasha mamaki ganin Imran da wani mai kama dashi da Yusuf Baki ya sake kawai Domin bai Taba Zaton akwai wani agidan ba Sai dai ko ba"a Fadamai ba zai iya Cewa Mahaifinsu Imran ne Daman suna da Uba..? Shifa ya Dauka Daga su Sai su acikin Gidan,Dayake Yusuf ne ya daukosa Gadi,Shima din Security din Ma"aikatansu ya ma mgana Shine ya Samo mai Iro,ba Saboda komai ba sai Saboda Abba suna Fita su barsa Shi kadai ga kuma Gida watarana Ake ji Tunda yanzu Mutune bana Allah.
Abba ya bama Iro Hannu suka Gaisa Cikin Fara"a Ganin kallon da yake ma Abba ne yasa Abba yamai Bayani da kansa Mamaki ya Cika Iro Cikin mamakin yace"Ammh Ranka ya Dade Alhaji ban taba ganin ka Fito ba Tunda Nake agidan nan..?
Abba ya Murmusa kafin yace"Eh ai Tun Dawormu bani Da Lafiya Likita ke Zuwa Gida yana Dubani..!
Iro yace"Kwarai kuwa anyi Haka..Likita kuwa na zuwa Lokaci Bayan Lokaci Ai bansani bane Sannu Alhaji Allah ya kara Lafiya..!
Abba ya amsa da Ameen Imran kuwa Gaba yaci yana Fadin"Abba an fa Tada Sallah..! Abba yabi bayansa yana Fadin"Mu zamu Tafi Masallaci..!
Iro yabi su da adawo Lafiya har suka Fice yana mamaki da Karin Al"ajabi A fili ya Furta"To wannan wani irin Cuta ce ashe Mutum Fin Shekarq bai Taba Fita ba..? Kuma naga Kafarsa Lafiya lau Oh..Ni iro..!
Haka yayi ta Fadi mamaki dai yaki Barinsa.

Haka achan masallaci ma Bayan an Idar da Sallah Sagir yaga Abba da Imran Daga Baya Dayake da suka Zo an Tada salla har anyi Raka"a Daya sai suka Tsaya Baya Tunda gaban ya Cika Bayan an idar suka Rama Sallar Farkon Abba na Zaume Bakinsa yaki Rufuwa sai da ya Share kwallah Mutane kuwa basu Damu ba Duk da basu Taba ganinsa ba suna Tunanin baki ne a anguwan Tunda ai Gari da Yawa Sagir ne har Zai Fice yaga Imran sai Chan yaga Abba Cikin mamaki yazo ya gaida Abba ya amsa mai Cikin Sakin Fuska Yana Fadin"Sagir ko..?
Sagir ya gyada kai Abba yace"Mu je Wajen masallaci..!
Mikewa sukayi suka Fice Abba kuma ya Tsaya gaisawa da wasu Daga Cikim Masallacin Sukuma suka Fita Waje Sagir ya kallesa yana Fadin"Abba ya samu Lafiya har ya Fara Zuwa masallaci..Na tayaku Murna Abokina..!
Imran ya jinjina kai batare Da yayi mgana ba sai ga Abba ya Fito suka kara gaisawa da Sagir,yana Tambayan Mama yace ya gaisheta,Tare suka Jero har Zuwa Bakin gidansu Sagir din ganin ya Tsayane yasa Abba ya Tambayeshi nan ne gidansu yace Sagir din ya nuna mai Shagosa Abba ya saka albarka Daganan sukayi Sallama ya koma Shagonsa Cikin Mamaki acikin Ransa yaji Dadi Sosai.
Safiya na Jera Flaks,kan Dinnig Su Abba suka Shigo da Fara"anta Tayi musu Maraba Imran dai Bai ko kalleta ba ya nufi Hanyar Dakinsa sai yaji Tace"Arm nace ba..!
Ya juyo yana kallonta Tacigaba da Fadin"Nace ga abincin fa..!
Imran ya kalleta kafin yace"ke kikayi Girki da kanki..?
Mirmishi Tayi batace komai ba Abba Dake Zaune yace"Ni kaina sai da na Hanata ta Dage sai tayi..!
Imran bai ce komai ba bayaso yayi mata gaddama Saboda karamcinta sai ya Kada kai yace"Later Zan ci..!
Kai ta kada mai Shikuma ya Shige Dakinsa Shirya komai tayi kan Dinning din Harsu Filet sai da ta Jera Ta je gaban Abba ta Durkusa Tace mai ga Abinci chan Abba ya rasa bakin mgana sai saka mata albarka yake karon Farko Daya Taba Zaman Dinning,ba kan gadonsa yaci Abinci ba Ita Safiya ita ta Yi Serving Dinsa ta Hadamai Cowslow daidai wanda Zai ci,Ta Daukomai Ruwa da Lemo Zata Tafi yace ta Zauna itama ta Zuba taci Duk da tanajin kunya ta kasa ma Abba Gardama Dole ta Zauna itama taci Sosai Abba yaci Abincin Sosai acikin Ransa yana sakama Safiya albarka.
Ranar Wuni yayi afalo Salla kadai ke Tadashi Safiya na Tare dashi suna Hira Kamar sun saba.
Yana bata Labarin Kazar kazar dinta kamar Asma"u Safiya Taji Rauni ya kamata ganin Abba na kuka ita Tayi ta Lallashinsa Tana kara Numamai Mutuwa ta Allah ce addu"a kadai suke Bukata,Abba ya Share Hawaye yace"Hakane Daugther Allah yayi miki albarka..!
Daga yau Addu"a ne Tsakanina da Matata da ya"yana Allah ya jikansu..!
Safiya ta amsa da Ameen.
Sai yamma Munari ta Dawo itama ganin Abba haka yasata Farinciki taRumgumesa Tana Murna ya gayamata yau Har Fita yayi Yaje masallaci,Kuma Duk Sanadin Safiya Munari ta Rumgume Safiya Tana Fadin"Thank u Bhabi..!
Munari bakinta yaki rufuwa ganin Dinnig Da kololi Shake da Girki ta Buga Tsalle Saboda Murna Abba nata Dariya sai kuma tarufe baki Sanin Halin ya Imu kada ya jita kuma ya jitan bai dai Fito ba Tsaki yaja acikin Ransa yace"nonsesss..!
Sai da taci ta Koshi Tana Santi
Daganan Munari ta jata Dakinta,Suka Zauna suna ta Fira tana ta Bata Labarin Makaranta Sai da aka kira mangariba ta barta ta koma Dakinta ta Sake wanka,Ta fito Tana Sallah Yusuf ya Shigo Gidan
Ya Tarar da Abba da Imran suna Masallaci.
Bai gama mamaki ba sai da yaga Aikin da Safiya Tasha Da Labarin da Abba ya bashi na Safiya yadda suka Wuni Hira yau ya ma kasa mgana Saboda Farinciki.
Yau agidan Rana ta Farko da suka Hadu Saman Dinning suka ci Abinci Munari da Safiya sun kara Shiga Kitchen sun yi Ferfesun kayan Ciki Imran Shima ya Fito Ferfesun Yaci kadan Yasha Ruwa ya koma Daki Abba Dai yaci Sosai,Da Yusuf da Munari bayan sun gama Suka koma Falo suka Dasa Hira Yusuf ya Dauko Jaridun Daya Siyoma Abba masu yawa Tundaga na Watan Daya gabata sai Littafan addini su azkar,Muwada Malik,Buhari da Musulim
Da Qur"ani izifi Siitin Karami na Karatu Abba ya Karba yana ta Godiya Safiya tace Saura Medicated glass Wanda Abba zai Rika sakawa in zai yi karatu Saboda karamai karfin gani.
Yusuf yayi na"am da Mganar Hatta Abban ma Saboda Zama Waje Daya Raunin Idanuwansa sun Ragu.
Da Sallar Isha"i Abba da Yusuf da Imran Tare suka Fita Masllaci Sagir Sai da ya bama Mama Labari Bakinsa yaki Rufuwa ita kanta Mama tayi Farinciki,Inteesar na gefe Tana Latsa Wayarta bata Saka musu baki ba Tunda ba da ita suke mgana ba.
Yusuf kuwa sun kwana Farantama juna Rai shida Safiya sun Riga sun zama Daya ya gama Gudartama Ransa Cikin Satin nan da anyi musu Albashi Zai Kwashe ya Dauketa suje ta Zabi Furture,da Zasu zuba ashashen da Zasu Zauna,Sai kayan sawanta Bayaso Wani nata yazo ya ganta tana Zaune a Dakinsa Hakan bazai mai Dadi ba Wlh Iyayenta sun gama mai komai da suka Kawo mai Haske acikin Gidansu.





*Kalma Daya akan Safiya..?kalma Daya akan Oga Ranka ya Dade Imu🤣Kalma Daya ga Inteesar Inteen Daddy da Ya Basheer Maryama Takwaran Daadan Alkali Dukku..!*




*Shakira....*
3/22/22, 23:04 - Ummi Tandama😇: *GIDAN MU..!*
_(Our House)_
*Book 1*

*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janafty❤️*

*DEDICATED TO:*
*Aisha alto(Sisinah)*
*Chubado muhammad(Uwar dakina)*
*Yahanasu Soupnass(Qawalli1)*
*Kausar salis(My jika)*
*Rahma Ladingo(Dota)*

        *🅿?16*

*Bayan Sati Daya*

Bayan kwana Bakwai da Auran Yusuf Da Safiya Abubuwa sun Fara Daidaita Gidansu Yusuf yanzu ya Fara Dawowa Daidai Tare da Mutanen Cikinta,kuma Duk a Dalilin Safiya Tuni ta Saka Yusuf ya kira mai gyara ya Saita Tv,Sai dai kaga Abba Zaune afalo yana Karatun Jarida Sanye da Gilashin sa mai karamai karfin gani ko kuma yana Karatun Littafin addini Safiya Dake kai kai da kawo Tsakanin Falon da Kitchen suna Taba Hira Sama Sama.
Ya kasance Duk Safiya Tare suke Breakfast,kuma Duk Dare suna Dinner Tare sai dai Imran ne bai Cika Zama Cikinsu ba,Ba wanda kuma ya Damu Sanin Halinsa Tun suna Lagos Shi yafi jin Dadin gudanar da komai na Rayuwarshi shi kadai batare da kowa ba.Mutane suna da matukar Muhimmanci a Wajensa,Bai yason Ka takuramai Shima yana Girmama Rashin Takura ga wasu koda su din Ahalinsa ne sai dai Kowa ya gansa yasan yana Cikin Farinciki Gidansu ya Dawo Gida irin na Kowa Bayan sunyi bankwana da Farinciki Da Dadewa.
Asatin Har Masallacin jumma"a Abba yaje Tare da Yusuf da Imran Cikin Farinciki kuma da Likita yazo Dubasa Yaji matukar Dadin ganinsa yace in Har Abba zai Cigaba da Tafiya haka Hakika Mgani bazai kara mai amfani ba Zai iya Dawowa Daidai  insha Allahu,Farincikin Haka yasa Yusuf yayi Shawara da Abba da Imran kan yana so ya gyara Shashen Dake Koridon Dakin Munari Safiya ta Tare acikinsa tunda wanda suke Zaune yanzu Ciki Dayane,sai kuma yana son Siyamata kayan sawa,Abba yaji Dadin Haka Saboda Safiya ta Chanchanci komai na Rayuwa Shi ya bashi Umarnin Ya taba Kudin Dake bankin Nura marigayi,Tunda akwai kudi Har yanzu yayi amfani Dashi Imran ma ya yarda da Shawaran.
Ranar Sati da auransu da Daddare suka Tafi Gidansu Safiya Shi da ita sai Tace Tare da Munari Zasu je Wanda Cikin Satin Daya sunyi matukar Shakuwa kamar yaya da kanwa In Munari bata je makaranta ba Suna Tare da Safiya aiki Tare suke yi Girki ma Haka wajenta tana ta kara koyin Abubuwa sosai Tunda ita Munari Da Karfi Da yaji ne ta iya girki,Lokacin Tana Karama Ba komai ta iya ba Sai dai ya Zaman mata Dole ne Tunda itace Macen Cikin yayyin nata da Taimakon Waya Online Clasess,Sai kuma Goggle yasa take kwaba Wasu abubuwan ammh Zuwan Safiya ya Kore mata komai,yasa ta gane ashe abaya Duk Shirme take yi.
Koda suka je Alhaji Alhassan Baya nan Ya Tafi Fagge,Mommy Tayi Farincikin Ganin yarta Cikin Kwanciyar Hankali Tayi Fresh na Amarci,Tasleem Ta Rumgumeta Tana ta Murna ganinta,Mommy bata Taba ganin Yusuf ba sai Ranar ta yaba Sosai da Zabin Diyar tata Domin a Fuska yana da Kamala da Cikar Zati Tayi musu Nasiha Sosai,Tasleem Taja Munari Dakinta suna Hira Mommy Taja Yarta Ciki Suka bar Yusuf da Labarai da ake Nunawa a Nta,gabansa Cike da kayan makulashe da yar aikin Mommy ta Cika Gabansa Dashi Ruwa Kadai ya iya sha.
Mommy take Fadama Safiya abunda yakai Abbun su Fagge kararsa ta kai Wajen Goggo,Bayan taje Gidansu ta Fadama Iyayenta Halin da ake Ciki Mahaifanta basu saka baki ba Sai dai sun Tausheta Datayi Hakuri Tunda aikin Gama ya Riya gamu,Yayartace ma Da ta ke binta Anty Saratu Dataji Ta Dinga Fada Dayake Tana da Fada sai Iyayensu suka Taka mata Burki Itace ta bata Shawaran su je Chan Fagge sun Fadama Goggo ko Yaya ne ai Mahaifiyarsace Zataji Rashin Jin Dadin Rashin Darajata da Yan'uwansa da Alhassan bai yi ba Shine sukaje ita da Anty Saratu suka Fadama Goggon komai sai da Tayi kuka Dataji Abunda ya aikata Shine ta Kirasa yaje yau Tun Dazu Kila Chan zai kwana Tunda Har Dare yayi bai Dawo ba,Daman Tun Bayan Faruwar abun Mommy ta Daukemai basu Dawo Daidai ba.
Safiya bataji Dadin Rashin Jituwan Dake Tsakanin iyayenta ba Har yanzu yasa ta Sanyaya rai ta Dafa Kafadan Hajiya Mero Tana Fadin"Mommy Sam bana jin Dadin Rashin Jituwan Dake Tsakaninki da Abbu..Don Allah ki manta Komai indai Saboda ni ne Wlh Tallahi bana Cikin ko Wata Mtsala Mijina yana sona Abba kamar Diyarsa Munari ya Daukeni Bana Cikin Wata Damuwa baki ga alama ba..!
Hajiya Mero ta kalleta ta Kada kai Tana Fadin"Ammh ai Da Farko shi da Kansa yace yayi Bincike basu da Kowa anan..Basa da wasu Dangi Anya Safiya Kina ganin hakan ba wata Mtsala bace...?kuma fa yacemin Mahaifin su Mahaukaci ne akacemai..,?

Safiya ta Murmusa Tana Fadin"Mommy wa kika Taba ganin ya Fado Daga sama bashi Da Dangi? Suna da Ahali da Dangi irin na Kowa Mommy kawai yanayi ne yasa kika gansu kuma Mganar Abba..,karya ne Mahaukaci bane Wlh Sharri ne..!Nan da nan ta Fara bama Mommy Labarin da Yusuf ya bata ba Domin komai ba sai Domin Hankalin Mommy ya kwanta,Agurguje ta gayamata komai ta Karishe da Fadin"Mommy Kinsan Rashin Uwa a gida Babban Gibi ne..Su kuma Rashin Uwa sukayi da yan"uwa Har Uku yaya zasu Fuskanci Wannan Rashin..? Abba kuma Yayi Rashin Mata ce Uwar yayansa..Kuma yayi Rashin Ya"yansa Har guda uku alokaci Daya..Yaya kike ganin Haka Amtsayin in ya Faru Dake Mommy..? Sannan kuma yan"uwansa suka ki Fahimtarsa Ballataa su Taimakesa kan Halin Dayake Ciki..!
Mommy ta Share kwallah Saboda Tsausayi tace"Allah Sarki ashe Hadarin Jirgin Daya kashe Mutane dayawa din na harda Mahaifiyarsu da yan"uwansu aciki..?Abun Tsausayi Allah ya jikanasu da Rahma..Wlh naga Kokarin yaran..Allah yayi miki albarka Safiya Yanzu Hankalina ya kwanta na Tabbata Mahaifinki bai kai Hannun banza kina Hannu nagari..!
Ina alfahari Dake Ki Cigaba da Abubuwan Dakike,Insha Allah ke ce Haske acikin Gidansu da yardan Allah..!
Rumgume Mommy tayi Tana Share mata Hawaye,Sun Dade aciki suna Tattaunawa sai da Yusuf ya kirata yace su Fito su tafi sun bar Abba Shi Kadai,nan ne ma Mommy ke mata Mganar Kayan Daki Take gayamta Yusuf yace shi Zai siya komai kawai abunda take Bukata Turaran TuraraGida sai na kaya,Sai abubuwan da ba"a rasa Mommy tace Insha Allahu zata kira Anty Saratu Zasu Shiga Kasuwa Zasu siyomata komai Sai Tajita,kafin suyi sallama sai ta bata leda guda Cike da kayan gyaran Jiki,Tace abunda bata gane ba ta Kirata Taji Takaichi yarda takai yarta Baatare da wani gyara ba Ammh ko Yanzu Lokaci bai kure mata ba Saratu Zata Hada mata komai Tunda itama Tana Taba Sana"ar kayan gyaran Mata..
Koda suka Fito Tasleem da Munari sun Gama Hadamata Duka kayanta Kadan suka bari akwati Uku suka Cikata Harda su Takalma da Takardunta na makaranta sai Littafan addu"o'inta,da Sauran littafanta na Karatu Novels na Turanci dana Hausa,Sakawa su kawai akayi a Mota Mommy da zasu Tafi Tayi ma Yusuf Gaisuwan Rashin da sukayi bai yi mamaki ba Sanin Safiya kila ta gayamata yaji Dadi sosai ya amsa yana Godiya Munari da Tasleen suka yi Sharing din Cantact din juna,Tace Sai tazo,Safiya tace ta na nan tana Jiranta suka Tafi suna Daga musu Hannu,Bayan Safiya ta bar Sallahun Agaidata mata Alhaji Alhassan in ya Dawo Mommy aranta taji bazata Fadamai ba Kuma Zata kwabi Tasleem So take sai ya Girbi Abunda ya aikata da kansa Tukunnah.

Washegari Ta kama Lahadi ne Tun Safe Yusuf yace Safiya ta Shirya Zasu je ta zabi Funutures,da Kayan sawa,Bata iya cewa komai ba Domin Ta Lura Yusuf baya son gaddama,yau Munari ce tayi aikin Gidan,Tace Safiya Ta Huta Tun Safe tana Daki Gaida Abba kadai ta Fita,ta Dawo Daki ta Kwanta,Dole tatashi ta Shirya Bayan ta Shirya ne tace Tana so suje da Munari Ta tayata Zabe ya bata Rai yace Shima ai ya iya Zabe Dariya Kawai Tayi ta bar mganar,Doguwar Rigar Wata atamfarta ta Saka Mai kalan Green sai tayi amfani da Bakin Mayafi da bakar Jaka da Takalmi,Shima Yusuf din Shaddarsa Mai Duhu ce,Sun Fito Cikin Shirin Fita Suka iske Abba Falo suna Kallon Arewa24 shida Munari ganinsu sun Fito a Shirye yasa Munari take Tambayan ina Zasu je..? Abba ya kwabeta yace ina Ruwanta Tsakanin Miji da mata sai ta bata rai Tana Tura baki Abba da Yusuf suna Dariya Sanin shi yasan Inda zasu je.
Sallama sukayi ma Abba ya Rakasu da adawo Lafiya,
Wani Kamfanin saida Kayan Funuture suka Fara zuwa Tare da Safiya suka Zabi Kalan Bedroom da Falo,Dayan Bedroom din Dazai zama nasu Brwon and White sukace a Hada musu komai ,Dayan kuma da Zai Zama ko na Baki suka Hada Black and White,Sai Falo suka Hada Blue and Ash..Komai sai da aka Hada musu Harda su Cafet,kayan kallo,Sun siya Fridge Da wasu kanunun kayan Kitchen Tunda akwai karamin Kitchen a Ashashen,Ta Bank ya Tura Musu Kudinsu ya bada addreess Suka kuma Jadadda musu kayansu zai isa Kafin Su isa Gida Tare da Ma"aikatansu da zasu Hada komai sukayi musu godiya Daganan suka Shiga Kasuwa Safiya ta Zabi Kaya kama Daga less da atamfofi da Materials,Sai kayan Barci Da mayafi da Hijabi da Takalma bada yawa ya Siya mata saboda bai da kudi yace Sai sun kara Dawowa..
Suna Shagon Munari ta Kira Yusuf Take gayamai ga Masu kayan sun kawo nan yace Ta Nuna musu Shashen Dake kusa da Dakinta anan Zasu Jera Kayan Ta tayasu a Share Dakin,Munari tace ai Ta riga ta Share Dakin Bayan Fitansu Tayi Mopping Abba yace tagyara,Yusuf yace Shikenan ta Nuna musu su Jera komai suma gasunan zuwa..
Toh basu Dawo da Wuri ba Tunda sai da suka Biya suka kai Dinki Wajen Telan Da Safiya take kai Dinki Tun Tana Gida Kana suka Dawo sun Iske Tuni har kamfanin Tagama Hada komai sun Tafi..
Waje yayi matukar kyau sosai Munari ta Tayata dashi kanshi Yuauf din suka Kara gyara ko"ina Har Tv aranar aka Hadashi,Munari sai santi take Ita ta Tayata suka Kwaso kayansu Daga chan dakin suka Maidasu nan,Har Abba sai da yazo ya gani ya saka albaeka Imran ne dai bai Shigo ba,Daga bakin Koridin kawai ya Tsaya Daganan yayi Waje Shagon Sagir yaje Domin yanzu Chan yake Wuninsa,Tun Mganar nan da sukayi da Sagir na Zai bashi Sana"a Shikenan ya addabeshi Da kira wai yana Jiransa Dole yake zuwa ba Domin komai ba,Sai Saboda Sagir bai zai iya Ture alfarmansa ba, ammh ba wai Domin Ya koyi Dinki kamar yadda Sagir din yake Bukata Shi Aikinsa Daya ne aikin Banki ya Zauna kan kujera tana Juyawa dashi Lokaci Daya yana Sarrafa Computer shi aikinsa akwakwalwa yake,Bazai iya yima Sagir din gaddama ba Shiyasa yake Zuwa Sai dai Fara Zuwansa Shagon ya Takurama Yaran shagon basu da Damar Sakewa ko Hira ko Dariya in Har Imran na Shagon ba umh ba Umh ne ko Mganar Rada kayi sai yace ka Dameshi ka Fita yanzu yar Yar wakar ma da suke kunna Saboda Nishadin Dinki ba wannan Damar domin Ranar da suka Kunna Mp3 Din gabadaya Imran ya Rotsata da kasa ta Fashe,Tundaga lokacin Shagon ya Zama sai a Hankali,Yaran Sagir din Haushin Imran suke ji sai dai ba Halin su Furta Shi kanshi Ogan zai iya Bata Musu rai kuma ba komai yake yi ba
Illah ya Zauna Kawai yana bin Wuri Daya da kallo in yaji Nishadinsa ya Busa Sigari ko baka san Warinta baka isa ka Fita ba kuma baka isa ka Toshe Hanci ba Dole ka Shaki Hayakinta.
Shi Kanshi Sagir din yayi Nadaman Gayatton Imran din Domin ba yaransa Kadai ba Hatta shi ya Hana mai Rawan gaban hantsi ko Dinki Costumer suka kawomai Cinikayya sai dai su Fita Waje,Indai Imran na Shagon bayason Hayaniya da Takura,Sai dai ba yadda Zai yi Dashi Fada ne Kullum Kaca kaca suke Rabuwa,Bai kuma Hana gobe in Sagir yaji Imran din Shuru ya Kirasa
Har kuma zuwa yau bai kara ganin Inteesar ba,Har ma ya manta da Babunta.

******

*Kaduna..*
Da misalin karfe 8:00pm na Dare.

Shigowarta Bedroom Din kenan Dauke da Karamin mug,Wanda Ruwan Shayin Na"aNa"a,Alhaji Mustapha ne Zaune gefen gado Sanye da Jallabiya mai Ruwan Madara,Ya Zabga Tagumi da Hannun Bibbiyu Har ta karisa kusa Dashi bai sani ba,Domin yayi Zurfi Cikin Tunanin Daya Tafi kan Side Drower din Jikin gado ta ijye mug Lokaci Daya ta Zauna Gefensa Tana Fadin"Abban Intee..!
Ta fada Tana Ciremai Tagumin Sai Lokacin ya Dawo Cikin Hayyacinsa ya Fahimci Ta shigo Har tana Kusa Dashi.
Ajiyar rai ya sauke kafin yace"Bansan kin Shigo ba..!
Tace Tana Kallonsa"Ina fa Zaka sani kayi Nisa Cikin Tunani..kuma kasan yawan Tunanin illah ne ga Lafiyan Dan adam..!
Sauke Dayan Hannunsa yayi Daga Tagumin yana Fadin"Umh..Tunani ya Zama Dole Sahala..Wlh na kasa Sukuni Tunanin Halin da muka baro Daada aciki ne ke Damuna..!
Umma Ta yi shuru kafin itama Tace"Wlh nima Abban Intee..Daada ta kasa fa..Yaya malami kawai take son gani..Kaji fa Baba asabe Tana Fadin ko acikin Barcinta sunansa take kira..!
Ta karishe Fada Cikin Bayyana Jimaminta.
Alhaji Mustapha ya Sauke Twagayen Numfashi kafin yace"Ko achan Baya Soyayyar Daada ke ma Ya Malami ta Dabam ce shi din D'a ne masu Soyuwa gareta Duk yafi mu sanyin Hali Shiyasa yafi Shiga Ranta Dole Daada ta Shiga Damuwa Saboda Rashinsa Kusan kwanciyarta asibiti Biyu acikin Satin nan fa..!
Umma tace"Ni Tsorana kada Hawan jinin nan ya Fadar da ita kasan fa Mugun Ciwo ne..Daman ta Amince ko ku saka baki kai da su Hajiya Bintalo ta yarda Tabi Baban Sajida Abuja In ma Baba asabe take ji Duka su tafi Tare nan Dukkun sai a Rufeshi In Allah yasa ta Samu Sauki sai su Dawo ni aganina Chan zai fiyemata ko kobamai akwai gilmawar Wani nata agabanta nan kuwa sai dai in an Taka an je..!
Har tagama Mganarta bai ce mata komai ba sai Chan yace"Ai Daada alkwarin tayi ma kanta bazata bar gidanta Dukku Da Ranta ba..Sai dai in Gawartane ta yarda a Fitar da ita..!
Umma tace"ai kaji kuma..Allah dai ya bata Lafiya Wlh jiyan nan da muka isa Naji Tsoro Hakama Basheer yace sai da nayi kwallah Lokacin Data Rike Hannuwanku kaida Baban Sajida Tana Rokon ku ku Sadata da Malami kafin ta bar Gidan Duniya..!
Yayi kasake yana jinta Cikin wani yanayi kafin ya Mikamata Hannu yana Fadin"Bani Tea din..!
Ba musu ta Dauko ta mikamai ya karba yakai baki Kurba Daya Zuwa Biyu ya Dakatana Yana Daidaita Zamansa Lokaci Daya yana Fadin"Baki san wani abu ba Salaha..Jiyan nan da Barrister ya kirani yana gayamin wai Dr.Zubaida Ta kirashi tace Daada na asibiti Wajenta Itama Tana gidan Baba asabe ta Kirata jikin Daadan ya tashi na Tsorata..Duka Duka ko fa kwana Hudu batayi da kwanciya asibitin ba ta Kwana Daya aka Dawo da ita gida..Ciwon Daada wlh yana Tadamin da Hankali akoda yaushe Ina Rokon Allah Duk inda ya Malami yake Allah ya bayyanashi Daada nada rai kada Sai ta Mutu Hakkinta ya kamamu..!
Ya karishe Fada yana kara Kurban Tea din Hannunsa Umma Tayi Kasake kafin Tace"Hakki kuma..? Ai naga kuna iya bakin kokarin ku Wajen Nemansa bai kamata kace in Kun gaza Hakan Hakkin Daada zai kama kuba sai dai in shi Yaya Malami Tunda ko Yaya ka Lalace Uwa Uwace Har Abada kuma Tana da Nauyi da Hakki akansa..
Bai katseta ba sai da ta gama kana ya mikata mata Mug din ta karba ta Maidashi inda ta Daukosa,Shi kuma ya Mikar da kafarsa Saman Cafet din Dake malale a Bedroom din yana Fadin"Me kika sani Salaha..? Ai Duka Alhakin Barin Ya Malami Gida da Iyalansa yana Wuyanmu ne..Musamman Barrister Domin kinsan da Zafi sosai Alokacin da Abun ya Faru Ya Maalami ya Samu Depression kan Abunda ya Faru da su Yusuf suma ba wani Hop kansu sai yake ganin kamar Rashin Hakuri ne da rashin Yarda da kaddara yasa komai ya Lalace Har Laluran tasa tana ta gaba Kullum Likitoci suna cewa ba Cigaba..Dalilin haka yasa yayi ta Fada gaskiya munyi kuskure Domin naga wani Shiri,Tv Kwanaki Wani likita na mgana kan masu Fama da irin Lalurar Ya malami yace Ciwon Damuwa ne Ba Hantara ko Fada suke so ba ajashi ajiki Lallashi da ban baki a Zauna dasu adaina bari suna Tuna Abunda Zai sakasu Tunani,arika yin Abunda Zai sakasu Farinciki akoda yaushe kuma Tsakani ga Allah Bamu yi wannan kokarin ba Mun kawo su Dukku Gaban daada Mun koma Garuruwan mu,bamu yi La"akari da Daada ta Fara Manyata ba, bazata iya wani Kokari ba..Sannan iyalansa suma Raunin ya Tabasu da Har baza su iya Taimakon kansu ba Ballatana Shi Yaya Malami Ahaka suka nuna suna son Komawa Gida kuma na Tabbata Saboda Wannan Dalilin ne sukayi nesa Damu bayan sun koma Lagos Sun ga ba wanda ya Damu dasu..Na Tabbata Yusuf bazai yi Tunanin Yin nesa da Kowa ba Face mai muradden Halin nan Duk Cikin Dangin mu Imran yaron yana da Zafi Daman Chan Tun Farko Bai da Shiga Dangi Sosai sai da ya Girma ne ma Ya malami ke Tarosa in zai zo Dukku..Ina da Tabbacin Shi zai ba Yayan Shawaran Haka Shi kuma Bashi da Zabi sai ya Yarda da komai Suna ganin yin Nesa Damun din Shine mafita..Tabbas muma da laifin mu..!
Ya Karishe Fada Lokaci Daya yana Saka yatsa ya Dauke kwallar Data gangaromai Umms Jikinta yagama yin Sanyi tace"Tabbas Hakane ba"a kyauta..Rashi ne sukayi Babba..Allah ya jikan Zuwaira Ya malami yayi Shuru Dole Ya Shiga Damuwa mace mai kirki Da Sanin yakamata Ga kuma Rashin ya"ya kai yaga Jarabawa Wanda bakowani bawa bane zai iya Tsallakewa Abban Intee in Wani ne sai ya kashe kansa..!
Yayin Saurin katseta da Fadin"Wlh Abun Allah ya kare..Hakama likitan yace ,Wani babban Likitan kwakwalwa ne
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment