Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

bata gane komai ba sai itama Dariyan take ta Zata Shakiyancin Munari ne.
Tare suka kama Girkin sai gabda mangriba suka gama kana suka shiga Domin yin wanka da Sallah.
Bayan sun idar ne Inteesae tace Munari tatashi ta Rakata Gidan Mommy ta Dauko mganinta na Ciwom mara Data zo dashi Daga Gida Jin maranta ta dan Fara mata Ciwo kadan kadan,Munari ta sako Hijabi suka Fito a Falo suka bar Abba da Ya Yusuf shima sai da yayi musu Fadan Fita duhu ya Shiga Jin Mgani zasu Dauko yasa yace suyi sauri ko kuma su Tsaya wajen Maman su kwana.
Sum sum suka Fice suna zuwa Haraban gidan zasu Fita suka kusa Cin karo da Imu ya dawo Daga masallaci ba Wutan Nepa sai dai Wata ta Raba gari Tar.
Lokacin da suka Fahimci shine Sai da jikinsu ya Dau rawa kallonsu yake Cikin mamaki kafin yace"Ina zaku yanzu da Daddaran nan..?
Yafada yana kallonsu Cikin Dakiyarsa
Cikin In ina Munari tace"Gidan..Ma...ma zamu je..!
Inteesar dai batayi mgana ba sai Morema kallonsa take yi yana Lura da ita sai dai bai bata Damar ma ta Fahimci ya ganta ba.
Hade rai yayi kafin yace"Yanzu da Daddaran nan..?
Yafada yana kara Duba agogon Fatan Dake daure a tsitsiyan Hannunsa.
Kafin ya Cigaba da Fadin"Ammh baku da Hankali ko..? In akace ku Fita iyanzu sai ku fita..?
Munari kanta na kasa tace"inteesar ce zata Dauko mganinta..!
Tafada tana Zungurin Intee datayi mgana ita kuma taki cewa komai.
Kallonta yake cikin Mamaki yace"Mgani bata da lafiya ne..?
Da Sauri Munari ta gyadamai kai Inteesar din yake kallo ita kuma taki yarda su Hada ido cikin Dakiyarsa yace"Oya ku koma gida in dai kunsan ba Chan zaku kwanaa ba....!
Munari tace"ai yau anan zamu kwana..!
Cikin gajiya da mgana yace mata"to bazaku fita ba..Ku koma ke gayamin Inda mganin yake naje na amso miki..!
Imteesar tq Fara Wiki wiki da ido kafin tace"Barshi ma gobe da safe sai muje na Dauko..!
Tabe baki yayi kafin yace"Better..!
Sum sum suka wuce yana Bin bayansu Har Falo ganin su haka yasa su Abba sukasan ya Korosu ne Dariya sukayi kawai su kuma suka wuce Daki suna Tura baki.

Washegari Daddy bai samu Biyowa ta nan Kano ba,Saboda zai yi baya Ya yusuf da Abba da Imran suka Samesa a kaduna,Su Munari suna ta Barci koda suka tashi Tuni sun kusa isa kaduna Domin 6:30am suka Fita Suna Dawowa Sallar asuba Tunda Tafiyan Motace zasuyi Dukkansu sun Tsani hawa jirgi Tun Faruwar Lamarin Daya Faru.
Da kwatace da komai sai ga Abba agidan Daddy farinciki kamar me Wajen Daddy ya kama Abba da su Yusuf ya Rumgume Umma kuma Tana ta ina ta saka dasu,Basheer ma yazo Dayake Har dashi Za"ayi Tafiya za"a Tafiyu iya Tafiya shiyasa Dole su nemi Wanda zai taimaka ma Yusuf da Driving Tunda Imu dai ya Dade bai Taka Mota ba.
Sai da suka karya kana suka Mika Hanya,Wajen 10am na Safe Umma ta Bisu da Allah ya Kiyaye Hanya Yusuf ke Tuki Imram na Gidan gaba Basheer da Abba da Daddy na Gidan Baya sai da suka Tsaya suka cika Tankinsu da mai suka Dau Hanya Da guzurin Abinci su da kayan Snak a bayan Booth Wanda Umma tayi musu tunda Tafiyace ba kadan ba kila su da isa sai Cikin Dare ko da asuban Gobe.







*Shakira*
3/22/22, 23:15 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�11*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*

Basu isa cikin garin Lagos ba sai Misalin 3:30am na Dare suka isa,Saboda Shigar Dare sukayi ga Gajiya yasa suka kama Hotel suka kwana suka warware gajiya sai da garin Allah ya waye bayan sun yi wanka sun yi breakfast kana suka Dauko Hanya zuwa Ainihin gidan su Imran wanda suka barsa Shekaru uku da wani abu.
Abba da Yusuf Rauninsu yafi bayyana ammh banda Imran wanda ba wanda ya isa ya bayyana wani Hali yake ciki.
Duk da sauye sauye ya karu a Birnin na Ikko basu manta kayattaciyar anguwan masu hannu da shunin da sukayi Rayuwa ba wato Victory inland ba.
Gidansu na nan yadda suka Barshi Katon get garkame da katon kwado Sai dai saboda Dadewa get din duk yayi kura yana sun Rufe wajen alamun dai ma mallaka Gidan sun Dade basa rayuwa acikinsa.
Ba wanda ma zai iya Tuna ina key din kwadon yake Lokacin da suka Rufe gidan suka Tafi suna cikin yanayin da ba baza su iya su iya gane komai ba.
Sai da Yusuf ya shiga Cikin gari ya samo mai yanke kwado aka zo aka yanke shi aka Bude gidan suka Shiga Ciki.
Allh Sarki Rayuwa Duk mai Imani Dole ya koka ma wannan Ahalin Gabadaya Haraban gidan ya Cika da Kura kyakyawan Marbels din Dake Shinfide a Haraban gidan ya cika da Ciyayi duk sun bushe Flowers duk sun bushe sun mutu murus Yana duk ya Lullube ko"ina ga Motocin su na Zamani guda Hudu reras,Na Abba dana Imran dana Nura sai na Yusuf gabadaya sun Lalace sun yi kasa Saboda ajiya Tayoyinsu sun Faffashe ba kyan gani sun yi kura Har sun gaji sun Fara Kokewa saboda Zama Waje Daya,Domin kana ganinsu Zaka Fara Tunanin da wahala su tashi Har su iya Moruwa koma sun Morin sai sun Dade a gareji suna cin uban kudi.
Kuka Abba keyi Reras sanda suka Shiga Ainihin Falon gidan ba Kurar Daya bata gidan bane Damuwar ba yana Tuna each and Single Moment da suka gudanar acikin wannan kayattacen Gidan shi da iyalansa da Matarsa sai gashi komai ya Zama Tarihi.
Abubuwa Dadama agidan nan sun Lalace kama Daga kayan kallo Frigde da Sauransu kujeru ne sai gadaje basu yi komai ba ammh duk wani kayan Wuta ya gama aiki gidan yayi kura yana Duk ya Rufe ko"ina sai da Basheer da Yusuf suka rika saka Sanda suna Cire inda Zasu Taka.
Wasu Kofofin Dakunan ma Sun ki Budewa sun kame sai an kira masu Cire Kofa Imran ya shiga Dakinsa yana Kallon kowani kusuwar Ya Duba Cikin Wardrope dinsa da Gabadaya kura suka mamaye ka'ina kyawawan Suit dinsa na kamfanoni Dabam Dabam da ke shake Cikin Wardrope din Duk sun gama sauya kala Kama Daga Takalmansa na Kowani kamfani masu Tsada da yarari duk sun sauya kamanni da Dadewa da kura komai nashi acikin Perfect ne Lokacin yana amsa sunansa Banker Imran Abubakar malami ba yanzu da komai ya sauya ba shi kanshi yaji Tahowar kwalla yayi saurin kauda kai bai bari Hawayen ya Zubo ba yasa Hannu ya Dauke kwallarsa.
Haka bangaransu Yusuf da Abba Suna Bin ko"ina da kallo suna Hawaye Daddy da Basheer suna ta basu baki,Basu iya ko zama ba saboda ba Wajen zama suna dai Tsaye suna Zagaya Ko"ina na Gidan suna kallo Suna Tunawa da Rayuwar baya.
Daddy ya fara kawo shawaran bazasu Tafi su bar gidan nan hakan nan ba Zai kara Lalacewa Tunda ba su da Sha"waar kara Rayuwa aciki sai dashi Abba yace bazai Taba saida wannan Gidan ba Har Abada Ko ya Mutu ga Yusuf ga Imran ga Munari gidane mai Dimbin Tarihi zai barsa Kila ko watan Watarana Su rika zuwa Hutu ko kuma Yanayin Rayuwa zai iya maido da Daya Daga Cikin su Imran nan garin Tunda suna da Muhallin Abubuwan bazasu yi wahala ba Kowa yayi na"am da mganar Abba ammh sai aka Fara Tunanin yadda za"ayi Daddy yace Dole kafin su koma a samu wadanda zasu Zauna agidan nan da sunan gadi su kuma Rika gyarashi suna kula Dashi Domin barinsa ahaka shine Jidali.
Suna cikin Hakane sukaji Sallama Daga Kofar Falon gabadayansu sun ji mamaki Abba ne da Daddy suka Fita Haraban Gidan Ikon Allah Abba kawai ke Fadi na ganin Abokinsa Amininsa Dr.Isa Ali Argungun Abokin aikinsa ne shima Lecture ne a nan Lagos Universty,Sai dai shi yana Shashen Kimiya da Fasaha ne Wato Computer Science sannan kuma Makota suke da juna Domin gidansa da Gidansu Gida Dayane Tsakani sun yi Zaman Amana sosai da Amintaka Duk garin Lagos Abba bai da aboki kamar Dr Ali argungu Matarsa Hajiya Barira Kawar Anni ce Lokacin tana Raye,Sannan karamin Dansa Ibrahim Khalil,ma"ikacin Banki ne shima Tun alokacin da shi kadai Imran ke gaisawa Sama sama abota dai wacce bata Zama Takura ba yayinda shi Khalil ke aiki da Firstbank nan Reshen Jahar Lagos shi kuma Imran yana aiki da GT bank suna Haduwa Lokaci bayan Lokaci in Bankunansu ta Tura su wata Seminar Tunda dukkansu Zakwakurai ne abangaran da suka karanta ma"aikatan su na matukar ji dasu,yanzu ma Tare da Khalil suka shigo Abba suka Rumgume juna da Dr.Ali Argungun suna masu Hawayen Farincikin ganin juna jin shuru ne yasa su Yusuf suma suka Fito Haraban gidan nan suma suka ga Abun mamaki nan fa aka Shiga gaisawa Cikin Tambayan juna bayan Saduwa Dr.Ali argungun yaja su zuwa Gidansa Tunda nan yayi kura ba wajen Zama basu yi gaddama ba Sanin sa ai shakiki ne ga Abba ko su Daddy sun san Tunda Lokacin Rasuwar su Anni Har Dukku ya Taka Daga baya daya samu Labari shi da Iyalansa.
Alokacin da Abun ya Faru bai sani ba Har Suka zo suka tafi da Abba chan Dukku sai daga baya yaji Labari kuma garin Dukku ba boyayye bane sannan Gidan Marigayi Alkali Dukku ma haka da Tambaya da komai suka isa Dukku Lokacin Abba yana Halin Rashin Lafiya baya gane komai sai sambatu Dr.Ali argungu ya Dawo da Tsausayin Abokinsa matuka acikin Ransa kuma yasha zuwa Dubasa Har Dukku kusan Sau Uku Daga baya da suka Dawo Lagos kuma basu Dade ba aka nemesu aka Rasa ya Zata sun kara komawa Dukku ne sai da yaji Shiru ba waya ba komai Achan Jami"a ma ba wani Labari yasa yaje Dukku da kansa nan ya iske Labari mara Dadi an nemi Dr.Abubakar malami ko sama ko kasa Shi da Sauran yaransa ba'a gansu ba Lokacin ya gana Daada Tana ta kuka Tana Bayyanamai Damuwarta ya Dawo Lagos shima da Damuwar Abun kuma shima yayi ta Bincikensa ba wani Labari sai dai ba Cire rai ba
Suna da Lambar juna shi da Daddy yana Kiransa Lokaci bayan Lokaci yaji ko an ji Labarin Malami sai dai Shuru ne,Shima Daddy yakan kirasa yaji ko da wani Labari Lokacin da Abba ya Dawo Wasu abubuwan sun Doke wasu Shiyasa bai samu Damar Sanar da Abba komai ba.

Dr.Is Ali Argungun Koda yaushe zai shiga gida ko zai Fita sai ya kalli get din gidan nan ko zai ga an Budesa Shekaru uku da wani abu bai Taba ganinsa a Bude ba sai yau daya Dawo Daga Wajen aiki yaga Gida a Bude mamaki ya kamasa haka ya Shiga Cikin Gida yana Fadama Hajiya Barira Ita ma tayi mamaki suna cikin mganar ne sai ga Khalil ya shigo shima Dai zencen yake musu shine Dai Hajiya Barira tace su leka su gani ko yan"uwanshi Daga Dukku ne kila zasu samu wani labarin suna zuwa kuma sai suga Abba sai Sabon Labari ya tashi anan Falon gidan Dr.Isa Ali Argungun Abba nata bashi Labaran bayan Rabuwa shima yana gayamai Faculty dinsu tayi rashinsa Wlh kuma yana mai Tabbatarmai ko yau ya koma Zai koma da aiki Jami"ar Lagos bazata yi sakacin rasa Zakwakurin Malami kamarsa ba,Nan sukayi Lunch Cikin Farincikin kara Saduwa da juna Hajiya Barira ta Fito suka gaisa Jin cewa su Abba kano suka koma da Zama yasa Dr.Isa Ali argungun yace ma Abba ai kano gida ce Hajiya Barira yar Fagge ce dake kano ne suna zuwa kano Sosai Rashin Sani sun gaisa ta karamai gaisuwan su Anni ya Amsamata Cikin Jin Dadin karamincinsu yana ta godiya.
Hajiya barira bata da wani D"a gabanta sai Khalil shi kadai ne bai yi auree ba kuma shi kadai ne Namiji Sauran duk matane suna gidajen Auransu,Shiyasa Gidan Daga ita sai yan aikinta da Mijinta da Danta Khalil.
Sai da suka yi Sallar Azahar anan cikin Gidan Yusuf yayi musu Limanci,bayan sun idar ne kuma suka kara Tsinkewa da Hira Khalil ma da Imran Cikin Ikon Allah suna ta mgana kan abunda yashafi aikinsu Yusuf da Basheer suna ta mamaki duk da Daga Khalil din Har yusuf din Daya ne bama su son Hayaniya bane da yawan mgana ba.
Daddy shi yayi ma Dr.Isa Ali Argungu mgana kan wanda za"a Samu ya rika gadin gidan Abba,Dr.Isa Ali argungu yace Faduwa tazo Daidai da Zama Megadinsa Buba Dan BAuchi ne Bahaushe ne nan suke Xaune dashi Shi da iyalansa suna BQauters,Daman kaninsa yazo kwanakin nan Wajensa yake yana ta neman Aikin gadi bai samu ba in hakane sai ya koma Gida ya Dauko iyalansa su zauna a BQuatre suna Kula da gidan Allah barshi Duk wata sai arika Biyansa Abunda ya Sauwaka Duk da yaso Abba ya baro Kano ya Dawo Lagos kamar baya su Cigaba da aiki Tare Abba ya nuna a"a Shi Zaman Lagos ta Fitarmai arai kwata kwata bai mtsamai ba Tunda Daddy yace A Buk kano zasu neman ma Abba aikin su gani ko Za"a Dace Tunda Lokacin aikinsa bai Wuce ba..
Ba bata Lokaci akayi ma Buba Megadi mgana Shida kaninsa Lurwanu sun ji Dadi Matuka Abba yace yaje ya Dauko iyalansa su zauna agidan su Rike Amana su kula da gidan sannan Yusuf ya Dau alkawarin Biyansa Kudi mai Tsoka Duk wata wannan abun yayi Musu Dadi suna ta Godiya.
Aranar basai da aka kwana ba aka Fitar da komai na Gidan Daya Lalace aka Zubar Motocin kuma aka Saida su aka Karbi kudadensu kalilan ba masu yawa ba Aranar basu koma Hotel ba agidan Dr.Isa Argungu suka kwana Washegari da Safe Lurwanu ya dau Hanyar gida zai je ya Dauko Iyalansa Kudin Motan da komai Dr.Isa Argungun ya basa,Yana Tafiya shida Abba da Daddy da Ya Yusuf da Basherr suka tafi Jami"ar Lagos inda Abba yayi aiki Shekaru ashirin abaya Abba yaga Tarin Sauye sauye yaga wadansu wanda sukayi aiki Tare Lokacin wasu kuma sun bar Wajen wasu kuma sun Rasu,Shugaban Jami"ar da kansa ya Nemi Abba ya dawo ya Cigaba da aiki da inda ya Kwarewa Ammh ya nuna ya Gode bai kara Sha"awar Zama a Lagos,Basu damu ba sun mai Fatan Alheri sanin duk inda yaje Takardunsa da kwarewarsa sun isa yasa a kowata jami"a ta Daukesa ma Bama Buk ba.
Koda suka Dawo gida Imran da Khalil basa Gida kuma basu gayama kowa Zasu Fita ba,ba wanda ya Damu Sanin kila sun Fita Zaga gari ne.
Ashe abun ba haka bane Bankin da Imran yayi aiki Khalil ya Daukesa yakaisa Kafin ma Imran ya yarda Zai shiga sai da aka kai Ruwa Rana da Lallashi da ban baki Khalil ya nuna mai Hakan nada Muhimmanci sosai.
Tare suka shiga Har Ciki shima din yaga Tarin Sauye Sauye a wajen yaga wadanda sukayi aiki tare wasu kuma da yawa an sauya su wasu kuma Rai yayi Halinsa,wadanda suka sansa sai Turruwa suke wajen gaisawa dashi To alokacin Waye baisan Imran Abubakar malami ba kan kwarewa a aikinsa da Miskilancinsa iya Daukan wanka bama aiki Muhimmaci gabadaya Dokokin bankin shi nashi Dokar ma ya Take nasu shiyasa ba Ma"ikacin da Manaja ke ji dashi Alokacin Irinsa Saboda yadda ya maida kansa kamar wani bawa gwannati na amfana da Tarin baiwarsa da lafiyarsa.
Manajan Wajen ba"a Sauyashi ba wani Bayarbe ne Mr Tunde Abdulwasi yana ganin Imran sai da yayi wani ihu ya Rumgumesa Tsakani ga Allah sun yi Rashin Zakaran ma"aikaci kamar sa haka yake ta Fadama Imran da Khalil sun nemesa har sun gaji sun Nemi Wayarsa shuru sun ta Turamai Sako ta Email dinsa ma Shuru shi ko Imran yama manta yana da wani Email Tin bayan Faruwar abunda ya Faru ya Daina Mu"amala da Duk Abunda ya Shafi Socoal media ya koma Rayuwarsa yadda yake yanzu sai dai ammh yana ji ajikinsa kila Lokacin da Wannan Imran din zai sauya ne zai Dawo ainihin Imran Abubakar Malami A Banker,Manaja yamai Tayin Dawowa aiki kan Mstaayin da yafi na Baya Imran ya nuna mai A"a Baya Bukata Duk mganar da suke yi Cikin Rantsantsan Turacin kasar Amurka ne in kaga bakin Imran yadda yake Tsara mgana Cikin Harshen Turanci sai mamaki ya kusa sumar dakai ka Fara Tunanin Anya wannan Imran din ne mai Shan Taba..?
Khalil ne yayi ma Manaja Tunde Abdulwasi bayanin a takaice na Komawarsu Imran kano da Rasuwar Mahaifiyarsu da yan"uwansu bai ji Dadi ba ya Tsausaya musu,Ya kuma Dage Imran sai fa ya Dawo aiki ko ba anan Lagos ba zai yi waya da Manajansu na Gtbank din su Dake Reshen kano,zai Turamai Duka Bayanan Imran da Takardunsa ta Email Zasu kirashi da Zarar ya koma Zai Cigaba da aiki kamar baya bazai Taba barin wanda aikinsa ke da Mutumci Fiye da komai a idonsa ya Zauna haka ba ballatana tun abaya suna da kyakyawan alaqa da Imran din Hallayarsa na Burgesa rashin Shiga Mutane,baya da shiShishig baya Shiga Harkan kowa baya Hulda da mata sai yazo aiki ya Wuni har yammah ya tafi bai tanka ma kowa ba sai ya Zama Dole aiki ya Hadaku Mutane da yawa acikin bankin suna jin Haushinsa sai dai basu da yarda zasu yi dashi,Ko ya sani bai Damu ba Tunda bai isa yaasa su so ra"ayinsa ba Shidin Kaifi Daya ne.
Bashi da yarda zai yi ya karbi mganar sukayi Sharing din Lambar juna shida Manaja Tunde Abdulwasi,kuma bazai iya Turo Alfarma Khalil ba yana nuna Kulawa akansa.Daganan bakin Ruwa suka je suka dan Huta duk da ba wata Hira suke ba ammh yanayin yayi ma Imran Dadi yana gefe yana kallon Khalil Dake waya yana wani Narke Murya Kila da Budurwansa yake mgana Tsakani ga Allah Tsausayi ya bashi Namiji har Namiji ya Zauna Mace na Juyashi har yana neman mata kuka Duk da abaya yasan Khalil din kamar shine yana da Miskilanci Ammh jisa ya zauna yana wani marairacewa kamar zai yi kuka karamin Tsaki yaja yana kallon Daidaikun Mutanen Dake wucewa Idanuwansa yakai inda yaga wasu Beatifull Couple Duk da bai sani ba Zuciyarsa ta basa Ma"aurata ne,suna Rike da hannun juna suna Tafe Cikin Soyayya da kauna yana kallonsu yana jin wani yanayi kansu kawai yake Hangowa shi da Inteesar Tuna ta yayi sai da yaji wani Sanyi a fili ya Furta"Shababbiyar yarinya..Na kawota nan ai shagwabarta zata yi tamin..!
Yafada yana jin wani Annuri na Shigarsa Wayarsa ya Dauko ya Tura mata sakon

"Kin manta dani ko..?

Alhalin fa ko jiya ta Kirashi sun yi da Daddare data kirassa yaki Dauka Saboda suna Tare da Khalil sai da ya Turamata sakon.

"Oya ki kwanta ki barci..Bana son Damu..!

Shine ne wai yau ta manta dashi so yake yajata da Zence.
Bata kai ga Turomai amsa ba Kiran Sagir ya shigomai ya Dauka suna mgana yana Tambayansa yaushe Zasu dawo yace bai sani ba,basu wani dade suna mgana ba ya katse kiran Saboda Hankalinsa baya kansa yana Wajen Inteeaar ne.
Illah kuwa yaga Sakonta Cikin Shagwabarta Duk da baya ganinta tace.

"Laaaa...Kai ya Imu nice ma na manta Dakai kai da kaje Lagos ka manta Dani kaga yanmatan Birni..Au koda yake ai kana da Matar Abuja Sajida.."

Sai da ma yaga Sakonta ya Tuna da Wata Sajida Tsaki yaja jin tama batamai Mood dinsa Raini yagani Kirkiri Tsaakaninsa da Inteesar Wato Shine ma ya samu yanmata ko..?kiranta yayi kai tsaye tana Dauka ya Fara Fadin"Kin raina ni ko..?Wato nine ma na samu yanmata ko..?Ni sa"anki ne Intee..?
Yafada Cikin wani Salon daya gama Kashe mata Jiki Gabadaya sai ta Fara mganarta Cikin Shagwaba Tana kanunun kuka Maimakon ya Dakamata Tsaawa yace ta Daina sai ya kasa ya samu kansa da jin Dadin Duk Abunda tayimai shi kanshi baisan Yaushe ba yadai samu kansa yana Biye ma Duk wata Tabaranta Wai kukan Shagwaba take yi basu dawo ba alhalin yace mata kwana Daya Zasu yi sai ga Imran yana mata Rantsuwan Wlh ba Laifinsa bane Daga su Daddy ne.
Soyayya mai sauya Mutum ta Sauya Imran bai sani ba ko aikin Daya amince zai koma Saboda Inteesar ne,yasan Zataji Dadi sosai,Kamar ya gayamata sai ya fasa yafi so ya bata Mamaki ne suna cikin Wayar Khalil ya zo Inda yake yana ganin haka ya katse kiran,Sai gashi ta kara Kira Bai Dauka ba sai da ta katse ya Tura mata Sakon

"Kije kiyi karatu...We tok Later bana Gida ne.."

Haka ya Rubuta kafin yabi Khalil wani dan Cafe inda suka Siya Coffea da lemu Anan Imran ya siya Sigari Khalil yaji mamakin ganin Imran na shan Sigari har sai da ya Furtamai Bai ce komai ba amsa Daya ya basa da cewa Life kenan.
Imran yasha Sigarinsa sosai,Saboda Tunda sukazo bai shafa ba,Har da Guzurinta yayi Khalil sai mamaki yake da Tsausayin Domin ya Tabbata Rayuwace ta maidasa haka abaya ko Kusa da ita baya zuwa.
Da suka koma gida basu ma Kowa bayanin inda sukaje ba Suma ba wanda ya Tambaeyesu..
Sai gashi bakin da zasu yi kwana daya sai gashi sai da suka kwana Hudu Tunda sai da suka jira Lurwanu ya Dawo da Iyalansa,Matan sa Biyu da yaya Bakwai irin auran Wuri ne ayi ta Tara ya"ya suka shige BQuaters Matar Buba da ya"yansu suka Tayasu gyara Komai har Cikin Gidan ma suka share suka Goge suka gyara kayan wasa kuma nasu Imran dasu Anni duk afito dasu wadanda bazasu Mori ba aka Zubar masu kyan suka Dauka sauran kuma zasu Sadakar dsshi ga Mabukata ana Gobe zasu tafi acikin Gidan suka kwana Saboda an gyara komai,Daga Gidan Dr.Isa Ali Argungun ake kawo musu Abinci Washegari Tun Safe suka Dauki Hanya bayan Abba da Dr Isa sun karbi Lambar juna haka ma Khalil da Imran sun Rabu kan in an nemesa zai gayamsa Insha Allahu.
Sai Cikin Dare suka iso kaduna anan suka kara kwana Sai Ranar Alhamis suka Dawo Kano,abun da ya bama Abba Da Daddy mamaki Har sukayi wannan Tafiyar Baffa Kabiru bai kira yaji Ya akayi ba sai dai sune suka Kirasa Daada kuwa Hankalinta kwance Koda yaushe Tana Waya da Malami Jininta ya Daina Hawa sai Dai ma yana ta kara Sauka ne.
Abba ya wakilta Yusuf ya Turama Daddy duka CV sa na Takardunsa Shi kuma ya Tuttura ma abokansa na nan Jami"ar Buk suka kuma Tabbatar da za"a dace Daman ana neman Wadanda suka kware kan Abubda Malamin ya karanta ya jira Lokaci kawai za"a kirasa.
Intee tafi kowa Murnan Dawowarsu daman Rashin ganin Imu duk ya Ramar da ita da kuma Gidan ba Dadi basu Abba Mama bata nan Taje Kaduna Bayan Tafiyan su Daddy Lagos jikin Inno ya Motsa sai sukayi mgana da Umma Maman ta Shirya tatafi Wajen kwananta uku kenan Daman Tun kafin tatafi suka dawo nan Gabadaya Saboda Taya Anty Safiya Zama.
Har ya dawo basu Hadu sunyi dogowar mgana ba sai dai sukan Hadu su kalli juna tayi mai Dariya shi kuma ya Hde rai ya Harareta,Sun Dawo Alhamis Ranar asabar da Daddare bayan sun gama Dinner gabadayansu Imran daman ba Zaman Dinner yake yi ba Tea kadai yasha sai gashi ya Fito Daga Daki ya Duka gaban Abba yana Fadamai Gobe yana so yaje Dukku.
Sun ji mamakinsa sosai Abba cikin mamaki ya kallesa yana Fadin"Dukku..?.
Kai ya gyada batare da yayi mgana ba Ya Yusuf dake Zaune gefen Abba ya kada kai yana Fadin"Dukku..? kodai Abuja mallam gayamana gaskiya..Kana son ganin Sajida ka Fake da Dukku..,,!
Kamar ya watsamai Ruwan Zafi haka yaji kallon Ya Yusuf yake yana auna in ba Domin shi bane wlh sai ya Duramai Ashariya Saboda Haushin mganarsa.
Inteesar ya kallah Dake gefen Munari da Anty Safiya itama kallonsa take Gabadaya Sai taji Ranta ya baci da aka ambaci Sajida kenan da gaske wajenta Zai je.
Kauda kansa yayi bai ce komai ba Abba na Dariya yace"Ai kamar tana makaranta bata dawo ba..Barsa kila ganin Kakarsa ne ya tasomai in yaje ya Dawo sai ya shirya yaje yaga matar tashi Lokacin ta dawo gida Tunda Ya Kabirun yace min suna Test ne..!
Har Abba ya gama mgana bai Dago ba.
Abba ya kallesa yana Nazarinsa kafin yace"Kwana zakayi in ka tafi goben..?
Dakyar yace"In Dare yayimin sai jibi zan Dawo..!
Abba ya kada kai yana Fadin"Allah ya kaika Lafiya Daada nada manyan Baki..!
Imran yaji Dadi da Abba bai kara Cewa komai ba ballatana ya Tambayessa me zai je yi wajen Daada yana Haararan Yusuf
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment