Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Illan Auran yara kenan Yanzu in babba ce Taya ya Zaka Xauna ma kana mgana..?ai tasan abunda ya Dace da ita Soyayya batayimai adalci ba Data saka ya Fada soyayyar yarinya karama Datake Neman ta Sauya shi Daga Imran dinsa Zuwa Wani Imran din na Dabam
Yana Jinta Tana kuka yayi banza da ita In bai rika mata haka ba Watarana Da mganarsa Zata Rika ja tana yarda taga Dama Kwanjinsa bai Hana in Anyi ba Daidai ba ya magantu Soyayyat taci kaza kazanta alokacin in Komai ya Dawo Daidai sai a Tuna.
Yana Aiki Bisa Laptop dinsa yaji Har Tana jiniyan kuka kamar Wata karamar Yarinya.
Da Sauri ya Mike Ransa na Baci ya Shiga Dakin afusace kan gado ya ganta ta Dunkule Tana kuka kamar ya Daketa Cikin Fusata yace"Na Dake ki ne..?Kukan Dadi kikeyi kinsan Allah in baki min Shuru anan Wajen ba Na Tako Inda kike sai nayi kwallo Dake Nagani kukan Jini Zaki yanzu ko na Hawaye..!
Ai jin haka yasa Kaji Inteen Daddy Tsit Tasan zai aikata Kyafci yayi ya Fice Daga Dakin Ta rakasa da Harara Damam kukan Tabara ne afili Tace"Ko ma ya Lallasheni ina kuka.!.tafada Tana Tura baki Ranar Bai kara ganinta ba da Safe mahar ya Fita bata Fito ba aransa yace in na Nemeta zata Rainani ne gwara na Kyaleta ai itace Tamin Laifi da Wannan Tunanin ya Fita Batunta mai Dade a Office Dayake asabar ne wani aiki ma ya karisa Daganan Shagon Sagir yaje suka sha Hira bai bar Sagir yayi Salama ba sai da sukaje suka karbo Dinkin Hijaban Inteesar matar mallam Imu ce yadi Hudu Hudu ne Har yana jan kasa Mama Tayi Danwake ya Shiga Har Ciki Suka gaisa suka ci Danwake shida Sagir yana ganin Gidansu yaso kamar ya Shiga sai kuma ya fasa kada Intee taji tace Ita ya Hanata Shiyasa ya Fasa shiga ammh sun Hadu dasu Abba a Masallaci Ya Yusuf nata yimai Tsiyan mai Yaji ya Daka Borkunu Imun Abba..
Bai ce komai ba ya Kara Hade rai kamar an aikomai da Sako mara Dadi a an anguwar yayi sallar Isha"i kafin ya Koma Gida Inteesar na Cikin Daki bata Fito ba ya Damu Yana so yaji Lafiyarta ya barta itaa kadai agida Tun Safe.
Ya Kirata bata Dauka ba ya Turamata sako.
"Kina lafiya..?.
Ta karanta Ta Sharesa Wata Zuciya Tace ka kama kanka Imran da Girmakka Yarinya na neman janka a kasa da wannan Tunanin ya Fita Batunta ammh fa Tana Ransa Ranar Lahadi ba aiki yana Gida yana Daki yaji Fitowarta da Safe ta Shiga Kitchen yana jin haka ya Fito Falo ya Zauna Saboda yaji kamar Girki take yi Sai da Ta gama ta Fito Dauke da Filet Shake da Indomie,Ko Gaisheshi batayi ba Bakinta agaba ta Shige Daki Dauke da Goran Ruwa ta kasan ido ya Kalleta Dariya ta kamsa afili ya Furta"Imu ka Tabo Autar Daddy sai Allah..!
Kitchen din ya shiga yaga iya Cikinta ta Dafa,Cikinsa ya Shafa ya Lafe sosai yana jin yunwa Inteesar Muguwa ce ko Ta Dafa dashi in bazatayi mai mgana ba ko acikin Kitchen din ta ijiyemai yazo yaci bakomai.
Hakanan ya Dafa Ruwan zafi yasha Tea sama sama ya Dawo Falo Laptop dinsa ya Dauko ya Fara aiki Domin ya Daukemai Hankali.
Ranar haka suka Wuni Inteesar Har Kai take kaudawa bata son kallonsa Imran shima ya Mazaye baya bari Ta gane ya ganta shima ya nuna mata ya Fita Zafin kai.
Washagari Monday Ranar ne Last Paper dinsu,Karfe 10:00am suke da Jarabawan Zai Rigata Fita Shiyasa da Safen ya Taka Har Dakinta tana Kudundune Cikin Bargo ta Rufe ido kamar mai barci batasan ya ganta ba Tana Danna Waya tana jin Sallamarssa Ta Tusa wayar Cikin Bargo Tana Barcin karya.
Bai bi ta kanta ba ya Ijiye mata Ledan Hijaban yana Fadin"Ki yi amfani dasu..Bana son na kara ganinki da Mayafan nan..!
Yafada Lokaci Daya yana Dora mata Dari Biyar saman ledan Ya kama Hanyar Fita yana gyaran Zaman Briefcase din Dake hannunsa.
Yana Fadin"Kiyi maneji ba kudi a Hannuna..!
Daga haka ya Fice ya Turo mata Kofar sai da Ta Tabbatar da ya bar Gidan kana ta Mike Zaune ta jawo Ledan Tana Dubawa ai data Gwada sai da ta Rike baki Tana Fadin"Tabdijam..Ni ce Zan saka wannan kamar wata Malama..!
Tafada Tana kallonta ta Madubi,Wata Zuciyar tace"Kuma ki ki sawa..Abu ya Zama Bala"i..Kila ma wannan karon Har da duka!
Tuna Haka yasa ta bata rai Hijabin kala Goma ne kala kala gashi an yi musu Dinkin Zamani.
Bata bar gidan ba sai ta Soya kwai tasha Da Tea da Buredi wanda sai da ma suna Hanyar dawowa Gida Ranar tagani tace su Tsaya su siya kana ya Tsaya ya siyan musu shi ba ci yake yi ba ballatana Yayi Tunanin siyowa.
Dakyar ta samu Daya daga Cikin Hijaban ta saka Kalan pick Zanen Material din Jikinta Har kasa ya kaimata ya Rufemata Diga digi ya ta iya Matar Imu take in batajin mgana Mganinta Zai yi a Dake ka kuma a hanaka kuka kuma aki Lallashinka sai dai ka gaji kabama kanka Hakuri..!
Lokacin da Munari taganta a makaranta Sai da ta Kusa Kaiwa kasa Saboda Dariya Inteesar sai kwal kwal kuka Cikin Shagwaba tace"Duk ban yi kyau ba ko..?
Ba yaya Imran bane ya kawomin wai kada ya kara ganina da mayafi..!
Munari na Dariya tace"Tab..Mrs Imran Abubakar Malami..!
Take Fada Tana Dariya wayarta ta Fito da ita Tana Fadin"Bari nayi miki Hoto naji Dadin Bama su Nasara Labari..!
Daman Kiris take jira sai ta sakamata kuka ganin haka yasa Munari ta Daina Dariyan afili Sai da Taga Inteesar din Idanuwanta duk sun kumbura alamun tasha kukabata Tambayeta ba sai da suka Fito Paper Course mate din su suna ta Murna Final Suka samu Waje suka Zauna Munari ta kalli Inteesar Dake Fama da Hajibi Tana Fadin"wai ya imun dukan ki yayi ne naga Idanuwanki sun Sauya..?in dai kuwa ya Dakeki Wlh Tashi muje office din Abba ki Fadamai kan me..?aure ai ya wuce wasa..!
Inteesar ta Dago tana kallonta kafin Tace"Wlh bai Taba Dukana ba..!
Munari tace"To me ya yi miki..?daga ganinki kin sha kuka wannan i don naki..!
Inteesar ta kauda kai batayi mgana ba Munari tace"Shikenan Tunda baki san Gayamin ammh Zan Fada miki gaskiya in baki Mike Tsaye ba Wlh Ya Imu Wahala Zai ta baki kafin ki gano kansa Kingama Jigata..!
Inteesar ta Juyo tana kallonta Kafin tace"Uhm..Naga alama..Ranar da naje gidan nan..!.,
Nan ta shiga bama Munari Labarin abunda ya Faru ta Karishe da Fadin"Haka ya dinga min tsawa da Fada ina kuka bai Lallasheni ba yace ma in na kara Damunsa yazo nan sai yayi kwallo Dani..Ni ba ance Miji na Lallashin matarsa ba ni Wlh Ya Imu bai Taba Lallashina ba Munari in ma Fushi zan yi baisan inayi ba sai don in nagaji na Hakura dakaina anya Yana Sona..?
Munari ta gyara Zama anzo Wajen Data ke son zuwa Cikin Hikima tace"Wlh yana sonki..So mai Tsanani ma Daya kai ku wannan Mtsayin in da baya Sonki ko sama da kasa Zasu Hade bazai Aure ki har ya Zauna dake ba Baki ga Sajida da baya sonta ba ya Saketa.ba..?haka Ya Imu yake Dan kafiya Dan Ra"ayi bamai Turasasa yayu abu Dole sai Abba ammh ko shi baya yarda yasakashi ya Zauna da abunda baya Ra"ayi..!
Inteesar ta jinjina kai alamun gamsuwa kafin tace"Ai bai taba Cemin yana sona ba..!
Munari tace"Ai bazai fada ba..Ke ce Zaki Sakashi ya Fada ma bai sani ba..!
Inteesar tace"Ta yaya..?
Munari tace"Baki gane ba..?tsaya ma wai Kun Fara amarcin ne ko kuwa Dai kina nan kina Jiransa..!
Inteesar ta Rausayar da ido Tana Fadin"Bama mu taba fa kwana Daki Daya ba Tunda muka yi aure..!
Munari ta Zare ido Tana Fadin"No Wonder shiyasa bai yi Laushi ba Har yanzu..ke kuma kika yarda..?baki cemai kina jin tsoro ba..!
Imteesar tace"To ya zanyi..?dakinsa yake Shigewa fa sai na Bishi..!?
Munari tace"Sosai ma.irinsu ya Imu sai da Tarko..Ki bisa ki Danamai Tarkon da zai kawo kansa da kansa yana Magiya..!
Inteesar tace"Ta yaya hakan zai Faru..?kamar fa baya son abun ne ni ko irin Romance din nan bamu taba ba..!
Tafada Abun na fitowa Daga Karkashin Ranta Munari tama kasa mgana Inteesar ta Cigaba da Fadin"Ina Fadamiki sirrina ne saboda Ke Kawatace kuma yar"uwata wacce banda kamarki..ki bani Shawaran ya Zanyi..?
Munari tace"Insha Allahu Inteesar Zan baki Shawara kamar yadda Zan bama kaina..!
Nan Munari ta Zauna Tana ta karanta mata Yadda Zatayi da Dubarin mata Inteesar tayi Kasake tana ji kafin tace"Kina ganin...kin fa san Ya Imu..!
Munari tace"Ai shima Mutum ne kamar Kowa kuma Namiji mai Lafiya Wlh karyansa ya Ture Kiran wannan Majalisar Dinkin Duniyan in kuma ya Fara Dandanarta To zai so kullum ya Dinga Ninkaya aciii ina nan Zaune Zamu gani Ya Imu yayi Laushi sai yadda kikayi Dashi..!
Inteesar tace"Allah yar"uwata..!
Munari tace kina wasa ne Dariya sukayi lokaci daya suna Tafawa Inteesar na Fadin"Khalil ya Shiga uku..,!
Munari na Fadib"Ai yama shiga Goma ne..!.
Dariya suka saka gabadayansu sun dan jima acikin makaranta bayan sun gama Sallama da Course mate dinsu suka Tafi Office din Abba suka gaisheshi bayan sun gama shan A.c da Lemo suka Mai Sallama suka Tafi Daga Bakin Get suka Rabu kowacce ta hau adaidaitan da zai kaita inda zata suka Rabu Da Inteesar kan Zata gwada Shawarwarinta.






*Shakira..*
3/29/22, 14:31 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�27*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*

Inteesar ta koma gida da Kudiri Tare da Niyyar gwada Shawarwarin Munari da kuma amfani dasu.
Tana komawa Gida bata Zauna ba Bayan ta sha Complex tayi alwala Tayi Sallar la"asar Domin sunyi Sallar Azahar a makaranta ita da Munari.
Daganan ta Fara gyaran Gidan bata gyarasa Koda yaushe sai Ranar Datake Gida shima Daga Falo sai Kitchen sai Dakinta ko Hanyar Bedroom din Imran bata Taba kallah ba.
Sai da ta kal kale ko"ina Har Bedroom din nashi ta shiga ta gyaramai Duk da ba wani gyara saosai bai da kazanta Duk Abunda yayi amfani Dashi yana Kokarin Maidashi Muhallinsa Har Tiolet sai da ta wankemai Tas yana Tashin Kamshin Turaran Dakunan Data Turara Gidan dashi a Burner.
Tana gamawa Ta Fada Kitchen ta Fara Sarrafa abunda Zata Dafa Saukkan Abinci Tayi Farar shinkafa da Miyar ganye Da Kifi sai  ta Soya kaza Tayi mata Pepe Chicken da yaji albasa da kayan Kamshi,akwai Fruit a dayawa a acikin Fridge Saboda Imran baya bari ma ya yankemai Wani Lokacin da yawa yake siyowa Tana sha ammh ita dai barta Da Cin kayan Fulawa da Zak'i.
Kayan Lambun ta yayyanka tayi Fruit Salt ta saka afrige Lokacin Data gama an Fara Kiran Sallar mangariba Bata Shiga Daki ba sai da ta Jera komai Saman Dining kana ta shiga Ciki.
Wanka Ta Farayin kafin ta Dauro alwala ta Fito Sallar ta Farayi kafin ta Shafa Man shafawarta na Olive Ta Fara kokarin neman kayan da zata saka Wadanda zasu ja Hankalin ogan akanta.
Cikin akwatin kayanta na Gida Wanda Nasara ta Hadamata,gabda Biki ta Bude Tasan Tana da wanduna da Riguna Lokacin Tana Gida da Zata Taho kano ne Umma ta Hanata Tafiya Dasu Taji Dadin ganinsu aciki Batasan Umma ce ta saka su ba,Domin ai Tasan Zasu yi mata amfani Tunda Gidan Miji Zataje Daman ko Gidan Maman abunda yasa Umma ta Hanata Zuwa Dashi Saboda ba kamar nan bane Da ba Kowa Daga ita sai ita sai Daddy Ya Basheer na Gidansa ba Kullum yake zuwa ba,gidan Mama kuma akwai Sagir kuma shi ba Muharraminta bane Shiyasa ta Hanata tafiya da Wandunan datake Sakawa su Lameta sosai suna Fitar da Surar Jikinta.
Wani Wando ta Samu Red Colour Daga Kasa ya Tsuke sosai iyakarsa kuma daga gwiwanta Kadan ya Wuce sai Wata karamar Riga mara Hannu Itama Ja ce sai dai Tana da Zanen Baki a Jikinta an yi Rubutu kanana daga gaban Riga Data Sanya kayan Ta Tsaya gaban Madubi sai ta Fara Tunanin Anya Zata iya Fita gaban Ya Imu haka..?kayan Tun Tana gida bata cika sakasu ba sun kamata sosai Wandon ma Dakyar ta saka Gabadaya Shafaffan kugunta ya Bayyana Kirjinta ya Cika rigar ta kamata sosai da Har Shatin Cibiyarta ana gani sannan kuma Da kadan ta Wuce Cibiyarta Data Daga Hannu Lafaffan Cikinta Zai Bayyana Waje ne.
Sumar kanta Da bata Kitse ba Ta Tattara ta Daure Daga kasa ta Sakamai Band kafin ta Samu Wata Hula red itama mai adon kamar Love ta gaba ta saka bayan ta Saka wani Saukakkan Dan kunnen da bazai Dameta ba kara kallonta Take ta Madubi kafin Wata zuciya tace mata"To ke Intee keda zaki burge Miji ai bakya Bukatar wannan Hular..!
Tafada Tana Cire Hular kanta Sake Sauya yanayin Band din Tayi ta maidashi ta Tsakiya duk da ba wata Doguwar suma gareta ba Tana da Cika da na Zaman Falo.
Karan Bude get taji Tasan ya Dawo kenan Tanaji ya Shigo da Motarsa ya koma ya Rufe get din Wanka Ta Fara ma kanta da Hunra da Turaruka masu Kamshi Da Fitar ma da Duk wanda ya Shake su Hankali yau akwai jan mgana.
Kugu ta Rike Tana Sauke ajiyar rai a Fili ta Furta"Zan Burgesa..?
Allah yasa ma ya Kalleni Nasan Halin Wanda na aura ba komai ke Burgesa ba..Zan so Tarkon na ya kamashi Can"t Wait naji Ya Imu ya Kalleni yana Fadin I Love u Inteesar..Bazan iya Rayuwa bki ba..!
Tafada Hartana Kwakwaiyon Salon mganarsa Kafin ta Tsintire da Dariyan Farinciki Bakinta Ta Rufe jin Motsin Shigowarsa ya shiga Dakinsa kana ta Sauke ajiyar Zuciya gefen gado ta Zauna Tana Kara jiran Fitowarsa kamar yadda ta Tsara sai ta Fita Ta ja Fada daman ai basa mgana suna Fada ne.
Yayi matukar mamakin ganin Dakinsa Tsab yana Tashin Kamshi Sai dai yasan Intee ce ta gyaramai Daki Mirmishi yayi yana Fadin"Allah Sarki..Yarinyar Tana da Hankali..Allah yayi miki albarka..!
Yafada kafin ya ijiye Briefcase din Hannunsa ya Sabule kayan Jikinsa ya Shiga Wanka Har ga Allah yaji Dadin Ganin ko"ina na Tashin kamshi Sosai yayi wanka cikin jin Dadin Da Annushuwa aransa yana Fadin Ta Daina Fushin kenan..?
Bayan ya Fito bai Tsaya Shafa mai ba Ya Saka Karamin Wandonsa baki 3Quater da vest wacce ta Dan kamasa Ya Tsaya a Hanya yayi Sallar mangariba Kishi yake ji sosai Gefe Daya yana jin yunwa kuma yau din ba Na Shan kayan Marmari bane na ya samu Abinci mai Rai da Lafiya yaci ne.
Laptop dinsa ya Dauka akwai wani aikin da Manaja zai karba Ya fito Falo yana Takunsa Wayarsa Rike a Hannunsa kamar Dole yaki Sauya waya,Kan Daya Daga Cikin Kujerun Falon ya zauna Lokaci Daya yana Ijiye Laptop dinsa saman Center Table din glass din Dake Tsakar Falon Kamshin Girkin da kamshin Turaran Wutan Daya Gauraye Falon bai sa ya Zauna ba yanufi kicthen ya Dauko Ruwa a Fridge kafin ya Nufi Dining kai Tsaye ganinJerarrun kololi masu kyau da yarari a jeri Cikin Sha"awa da Burgewa
Yana Daga Tsayen ya Bude Ruwan ya Kwankwada Rabi kana ya Sauke yana Sauke Numfashi kan Dining din ya ijiye Goran Hannunsa Lokaci Daya yana Bubbude Warmers din Da Pepe Chicken ya Fara cin karo Kamshi ya Dakesa Tuni Miyansa ya,tsinke sai kuma ya ci karo da Fruit Salt yana Turirin Sanyi ai Imran baima Tsaya ba yaja Kujera ya Zauna ya Zari Filet ya Diba Wannan Naman kazan Ya samu karamin Mug ya Diba Fruit Salt din Bata saka siga ba Shi ya saka ya Fara Lodama Cikinsa aransa yana Fadin"Yau Intee an sauko ba Mugunta..!
Acikin Ransa yana Dariya yana Tsaka da CinNamansa ta Fito Daga Cikin Dakinta Cikin yanayin Takun Wahainiya Kowani Taku Daya Kirjinta na Shaking Tare da Kugunta Dayake karyawa duk inda tabi bai ji Fitowarta ba sai dai Kamshinta ne yamai Maraba ya Dago kansa yana kallonta Daidai Lokacin Dayakai Cinyar kaza bakinsa itama Shi Take kallo Direct suka Hada ido Gabadayansu sai da sukaji wani yam acikin Jikinsu Imran da gabadaya ya Kafeta da manyan Idanuwansa yana Kallomta Daga sama har kasa Ita kuma ganin haka yasa ta Kauda kanta Ta Kara Kaimin Takunta da dan Sauri Ta wucesa zuwa Kitchen Galala kamar Wani Sakarai haka ya Juya yana Binta da kallo Har ta bacema ganinsa.
Nannauyar ajiyar rai ya Sauke sai Lokacin ya iya Tura Naman Daya Dauko Bakinsa yana jin wani Dum Dum a Tsakar kansa gabadaya Wani iri yake ji Inteesar ta Taimaki kanta Data Bacema ganinsa Domin ya kusa sume mata cikin yanayin Daya kasa gane Meyake Faruwa dashi.
Bata jima ba sai gata ta kara Fitowa Dauke da Filet da Cokali nan ma ya Sake Binta da kallo yana mamakinta Yasha ganinta ba Hijabi ammh bai Taba ganinta da kayan da suka bayyana Surarta ba irin haka.
Bai Taba Tsammaninhaka take ba yasha ganin mata Masu Cikar Hallita suna Mu'amala da mata a banki kuma yanayin Shigarsu mai bayyana Komai ne bai Taba ganin Macen da Cikar Hallita ta Dace da ita ba irin Inteesar ba Duk da bata da wani kiba kallon Kitse yake ma Rogo Tsab Ta mallaki mayan kayan da Kallon awajen Manya mata yake Tunanin Samu ashe Ashe Yana mata kallon yarinya ta Wuce da Duka Tunaninsa.
Tasan yana kallonta shiyasa ta kariso Har Dinning cikin Tafiyarta ta yanga Bata yarda ta kallesa ba ta Duka Har Tana dan Bege Cinyarsa da Zata Diba Shinkafar da Miyar ganye ta Duka Sosai har Matsatsun na Shanunta suka Bayyana Daga sama Imran ya Hadu dasu sai kaji Mukut Sautin Wucewar Abu a makwogwaronsa Batare daya Shirya ba Inteesar na Jinsa Da ba domin ta Daure ba babu abunda zai hana bata Kwafsa ma kanta Wajen Kwashewa da Dariya ba Saboda yadda yayi Lokaci Daya yana Wani Zare ido kamar yayi karya.
Fruit Salat din ta diba cikin karamin Mug ta saka Siga da yawa saboda Tana son Zaki sosai.
Tana Shirin wucewa Dauke da Filet din da Mug din batare data Kallesa ba ya Daga baki yana Fadin"Inteen Daddy ba gaisuwa..!
Yafada yana kallonta Cike da karim mamaki.
Kai ta Dan kadai kafin ta Juyo Tana kallonsa irin sai ma yanzu na ganga ta Wani Tabe baki kafin tace"Oh..Sannu da zuwa..ai bansan ka shigo ba..!
Tafada tana wucewa kan Daya Daga Cikin Falom ta Zauna yadda Zai Rika Fuskartata Galala yayi yana kallonta yadda ta Dora abincin Saman kujera batama kara kallonsa ba.
Aranta ya Furta"Lalle yarinyar ta karo Wulakanci..!
Kai ya Kada kafin ya sha Fruit Salat din Daya debo bai ma Cinyen Naman Dayasa ba ya goge Bakinsa da Tissue ya taso zuwa inda ya zama Wajen Zamansa Duk Dare ya Zauna suna Fuskarta,juna shi da ita Cikin Kufuluwa ganin yadda tayi wani kamar Bata gansa ba yace"Inteesar kin Rainani ko..?kina abu kamar baki ganni ba..?
Dagowa tayi Tana kallonsa Lokaci Daya Tana saka Mug din bakinta ta Kurbi Abun Zuuu..kamar irin na yara Tana Tande Lebe batayi mgana Karkace kai yayi yau yaga Karshensa yarinya karama Zata Birkitasa Gabadaya ya kasa Daina Kallonta Duk abunda take yau Direct yake kare mata Kallo kamar Wani Maganadisu.
Kansa ya shafa yana Fadin"Uhmm..Saboda kawai nayi miki Fada..Shine kike Fushi Dani..?shikenan ke baza"ayi miki Fada ba kenan..?
Yafada yana Sakarmata Idanuwansa da suka Shanye saboda kallomta Cikin Bakkm yanayin da bai Taba Riskan kansa ba.
Sai da takai abinci bakinta ta Hadiye Kana ta Dago Kanta Tana kallonsa Cikin Basarwa tace"Fushi kuma.?ni ba Fushi nake yi ba Fushi kuma ai sai manyan mata da suka san Ciwon kansu Ni karamar yarinya Dani bansan komai ba..Maganar Fada kuma ai ka Isa kamin Fada ko baka da Mtsayin Mijina kai din Yayana ne..!
Tafada Lokaci Daya Tana wani Far da idonta kafim ta Dauke kanta.
Burauba Imran ya Fada Aransa sanda yaji kamar ya tashi ya Riketa acikin Jikinsa a yadda yake ji Wato yarinyarnan mgana ta gasa mai ko..?illar auran yara kanana kenan wani Lokacin kai da ya kamata ka Zama dan Lallashi kai ne zaka koma kana Lallashinsu suna maka Iskanci Kiri kiri.
Ballatana yadda yaga Intee na wannan abun in yace zai Sakarmata Fuska Tsab zata ci Ubansa Hankalinta Kwance shiyasa ya Hade rai aransa yana Fadin Imran ka kama Girmaka ka Daina kallomta hakanan.
Da sauri ya Janye idonsa yana wani Dakuna Fuska Lokaci Daya yana Fadin"Better..!
Laptop dinsa ya jawo ya Budeta ya Kunna bari ya Fara aikinsa ko Zai Daukemai Hankali Dakai kansa Inda Sauran Girmansa zai Zube Inteesar tabi ta Tattaka.
Yana aikin yana Satar kallonta yarinya kamar yar Tsana sai ka Taba katabo ma kanka Duk Tana kallonsa sai dai bata nuna tasan yanayi ba.
Saboda Takalan mgana yasa kalleta yana Fadin"Ammh dai kinsan Cin Abinci akan Kujera ba Ladubban cin Abinci bane..Ga Dining in baki son ci anan sai ki Sauka kasa ki ci saman Cafet is ok..!
Mikewa tayi Dauke da Filet da Kofi Tayi mika Cibiyarta da Cikinta suka Bayyana Waje kafin tace"Alhamdulillah..Ai nama Koshi..!
Tafada tana wani kara bankaro Kirji Ta wuce Ta gabansa kamar Zata Fadomai
Saura kadan Laptop din hanmunsa ta Subuce ta Fadi kasa yayi Saurin Tallabowa da Kallo ya bita kafin ya Fitar da Numfashin Daya Sakesa..!
Umh....!
Yafada afili yana jinjina kai baisan me ya Shiga kan yarinyar nan so take yau ta Kuresa..!
Bata jima ba ta Dawo ta Zauna inda Ta tashi Hade rai yayi yana Dakuna Fuska wai kada taga Fuska ta Rainasa ammh gabadaya Hankalinsa baya kan aikinsa yana kan Intee ita kuma ta Lafe Kan kujera Tana ta Muskuce muskuce Tana mikar karya Datake kara Kwancemai kai bata sani ba Gabadaya ya Rasa Natsuwarsa Kuzarinsa na neman Kwacewa Daga Hannunsa dukkan wani Juriyansa da Kaifinsa yana Neman Bashi kunya ayau dinnan.
Inteesar Tana so ta Tsokane sa yasa ta gyara Zama Tana Fadin"Ya Imu plz ka kira mai hada Kayan kallo nan su Hada mana ni ina so fa..!
Kallonta yayi cikin Dakuna Fuska yace"Anki salon ya Dauke miki Hankali Daga Karatu ko..?
Tura baki Tayi Cikin Shagwaba Tana Fadin"To ba mun yi Hutu ba yau..!
Yana Kokarin Daidaita kansa yace"Uhmmm!!!!
Kamar wanda aka Shake ta Wutsiyar ido ta kallesa aranta tace kadan ka gani baka Rainani ba zaka sha mamaki.
Mikewa tayi zumbur kamar wacce aka Tsira Tana Wani Tsalle tsalle Komai na Jikinta na Motsawa Kirjinta suna Shaking suna Dukan juna
Imran ya gaji gabadaya Inteesar Zata Tina mai asiri in ya tashi Domin gaban Wandonsa ta Cika Tana Harbin Iska in har Intee taga Girmansa ai ya gama yawo.
Cikin Kaushin Muryan Data Shake yace"Miye kuma haka..!?
Cikin Shagwaba tace"Wani abu naji kamar yana min yawo ajikina..!
Karamin Tsaki yaja yana Fadin"Mtswww..!
Yafada yana Kokarin Daidata kansa Zata koma ta Zauna yace"Kinga koma Daki ki sauya wannan kayan.baki da Hankali ne..?kina mace kina yawo da wannan kayan acikin gida..!
Inteesar ta Tura baki Tana Fadin"To ai gidan Mijina ne ba Haramun bane..!
Idanuwansa ya kankance yana Fadin"Eh ba Haramin bane Shedanu ake gudu..Ki rika Suturta Jikinki..,!
Inteesar Dariya ke cinta ganin yadda ya Fittike yana Fada kamar wani Laifi Tayi so take ta samu Sarari ta Saki Dariyanta Son Ranta yasa ta Mike batare da tayi mgana ba ta Wuce Zuwa Dakinta Da kallo ya Bita Cikin Kokarin Matse Kafarsa Dayajin wani abu na Shirin Zubomai kamar ma Fa yana jin wani Zur zur ne ya rasa ma gane kansa.
Ai yana ganin ta shige ya Mike yana duba kansa Ajiyar rai ya Sauke ganin yadda gaban Wandonsa ya Kumbura kansa ya Dafe yana Fadin"Meke shirin Faruwa Dani ne..?
Yake Fada kafin yayi karamin Tsaki ya Kwashi kayansa zuwa Cikin Daki Alwala ya sake Domin ta Baci ta Farkon
Sallar Isha"i yayi aransa yana Fadin Zaman falo ya Haramta garesa in yana son ya Tsira da Mutumcinsa in ba so yake Inteesar tayi Wansharere da adekon Mutumcin nashi ba.
Ita kuwa Inteesar tana Shiga Dakinta ta Zauna sai Dariya take kwasa sai da ta Duka harda rike Ciki a Fili tace"Yau ina ma Munari na nan..?taga Mazuran idon da yayanta yake yi gaya Manyan kaya a wajen karamar yarinya..!
Sai da ta ci Dariyanta ta Koshi kana ta Tashi Da alwalanta baki ta Kuskure ta zo Tayi Sallah da Hijabin Sallar ta Fita Falo Taga Wayam a Ranta tace"Zan Biyo ka har Dakin ne Mijina..!
Kayan Dining din ta kwashe zuwa Kitchen ta Daureye wanda suka bata Kwanukan Sauran Naman ta Saka Cikin fridge da duka sauran abincin Kafin ta baro Kitchen din.
Daki ta koma ta Sake shiga wanka Tana Fitowa ta Tsane jikinta ta Fara Bin Kowani Kusurwa na Jikinta da Turaren Humran da Umma
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment