Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Dariya yace"Uhm...Harfa Rakata yana yi..
Gadin ta ma yake Wato Mr imran ya Dade dai yana Son Inteesar Daga Karshe Dayaga za"ayimai Kafa sai ya Zabura ya mike ya bayyana kansa ammh fa shi adole bai yarda yana Sonta ba Cewa yake..!
Yakasa karisawa Saboda yadda Imran ke aunamai Harara ga Ihu ya Kaure a Hall din Sagir na Dariya yana Fadin"Ammh fa soyayyar tasu ta Musamman ce..Ina wasa Dake ne..? ni Sa"anki ne..?kin Raina ni ko..? Zan Sauya miki kammani Zan yi kwallo Dake..?To Amarya Inteesar Shaawaran da zan baki a mtsayinki na kanwata Sai kin yi Hakuri kin Dage da Ninka Biyayya ga Girman Miji ga na Yaya in baki yi a Hankali ba Angon naki cikin Kwanakin nan na Amarci zai iya Sauya miki kamanni Ko kuma Gidan ku ya koma Gidan Kwallo da Mutane.!
Gabadaya aka kara Saka Tafi da ihu Imran kallon Sagir kadai yake ya auna yadda zai Yi kasa kasa dashi in suka Kebe Inteesar sai Dariya take kasa kasa yana kallonta.
Sagir ya cigaba da Fadin"To kai kuma abokina sai fa ka yi hakuri..Mata fa yan Lallashi ne duk da kace kai Allah ya kyauta ka Zauna kana Lallashin Mace..!
Khalil ya Karbe abun mganar yana Fadin"Sagir nace Ranar Lallashin bata zo bane..Nace Jama"a ku Fadama Mr Imran Ranar Lallashin bata zo bane..Sanda zai shige Dimuwa yana Fadin Baby Plz mana kiyi Hakuri..!
Ya Karishe Fada yana kwaiwayon mganar Imran ai gabadaya aka Saka Dariya wasu Harda Rike ciki Kai in aka Biyema Khalil da Sagir zasu Kullan ma da Mutane Cikinsu kuma ga ba Lokaci Imran Kamar ya Fashe Sagir da Khalil sun gama Dashi Gaban yara.
Su Yusuf Dariya kamar su kwanta yana kallon Fuskar Imran yana Dariya Nasara aka Kira tazo ta bada Tarihin Amarya Daganan aka bada Lokaci akaci akasha kana aka Fito Filin Rawa Imran duk yadda yaso ya Zille sai da su Sagir suka Fito dashi suka Rika mai barin kudi shi da Inteesar da sauran Dangi aka kuma barsu su kadai su Rausaya Imran dai ko Gyada bai yi ba sai ma Inteesar data dan juya shima bai bari ba ya Rikota yana mata wani kallo Dayasa ta Dataka sai Hall ya Dau sowa da ihu Wajen yanka Cake ma abun kallo ne Imran ai Oga ne Komai nashi na Dabam ne.
Awajen Dinner ma chan na kara Hango gayyar yan GMB2BANDGROUP,da nasu Hadadden ankon Dinner din masha Allah sai Washe baki suke Daga nesa suna Daukan Intee da imu Hoto saboda suna Tsoron su karisa wajen Imu ya Fahimci Hoto suke Daukansu zasu bazama duniya yace baisan Raini zai Sauya musu kammani suna Daga gefe sun kame suna Kallo kowa Daya bayan Daya suna masu Farincikin ganin wannan Ranar da su munari da Sagir kadai suka samu Damar gaisawa sosai.
Anci an sha an sha Rawa an yi barin kudi su Inna Bintalo ana gefe atana Daukan ma Mami Asma"u Video Tana Turamata tana kara Tada mata da Hankali
Sai 11pm aka taahi Imran suka Fara Tafiya sai da suka kai Inteeear gidan Abba kana suka wuce Gidan Sadam,Suka ijiyesa Khalil da Sagir suka juya zasu Dauko su Munari ko mgana bai musu ba ganin suna Rawan kafa kan yaran zai Fada musu gaskiya su kama kansu baya son Raini.










*Shakira...*
3/28/22, 18:34 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿?24*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*


Karfe 10:00am na safe aka Sada Inteesar da kayattacen dan madaidaicin Gidanta Dake Alu Venue anan cikin garin kano,Ta samu Rakiyan Mama da Maman Nasara da Anty Uwani sai su Inna Maimunatu da su Inna Bintalo da Sauran Tawagan Matan su Basheer da na Anty Safiya da ita kanta suka Sada Inteesar har saman Kayattacen Dakin Barcinta Kan gadonta na Royal bed mai kyau da yarari wanda yaji Shimfidun alfarma sai wanda ya gani bayan sun Umarceta da Tun kafin ta shiga Gidan ta Dafa Ginin Gidan ta karanto addu"an kariya da Zaman Lafiya Acikinsa da Dukkan alherai na Har Abada.
Kafin a wuce da ita Abba yayi mata Nasiha sosai da kuma Fatan Zama Lafiya Tsakaninta da Imran ya kuma Horeta da sai tayi Hakuri Sosai sanin Halin wanda Zata Zauna dashi
An kaita da Wuri ne saboda Za"ayi Walima,Atashi karfe Biyu na Rana akwai Wadanda zasu koma Gida yau Saboda ayyukansu kamar su Khalil da su Sa"id yau zasu koma Gida.
Duk wanda yaga irin Uban Dukiyan da aka Narka a wannan gidan sai kaji yana Sakama Baffa Kabiru albarka ana Fatan Allah ya bar wannan Zumuncin Har gaban Abada,Kowa sai Santin gidan yake Kitchen kuwa shima ya kawatu matuka Umma ce ta Roki alfarman a bar mata Kitchen din Ta gyara a Mtsayinta na Uwa sai aka Barmata Lalle ta Aurar da Autarta Sai wanda ya gani Kayan abinci cike da Store wannan aikin Duka na Daddy ne Ba abincin da Babu aciki Fridge kuwa Cike da kayan Cefene wannan kuma aikin Yusuf ne yasan Waye kaninsa Careless ne sosai kan Abunda ya Shafi Cin Abinci Shiyasa ya gama da Wannan Barayin ya Tabbata Cefanen zai matukar basa Wahala.
Irin su Anty Aneesa da su Fareesatu sai Daukan Hoton Gidan suke su Munari kuwa sai Faaman Daukan Hotuna suke yi ko gajiya basa yi Kowa yana Nuna Murnansa a Fili banda yan Bakinciki irin su Inna Bintalo Har Video gidan sai da ta Dauka ta Turama Mami Asma"u Tana nuna mata Irin Kudin da Baffa Kabiru ya bar nartar kan wanda ya Saki yarsa da Inteesar din da aka yi mishi auran Tura Haushi da ita.
Mami Asma"u Tun Jiya Take kwance bata da lafiya ta gama Sarewa da al"amarin Baffa Kabiru ta gama yarda ya Juyamata baya kuma bai da Niyyar Dawowa gareta,Daada da yan"uwansa sun yi musu Farraku lokacin Dataga Hoton Imran da Inteesar Awajen Dinner sai da kwalla ta kawo mata A zahirin gaskiya Imran bai da makusa ko D'anta Khamis Wlh bazai jera kafada Dashi ba Cikin Maza Dubu Sai an Tona za"a samu kamarsa anya anya ba Gaskiya bane Tana da Sonkai.?ta so kanta da yawa yasa bata Fahimci Babban goron da Allah ya Kashe yabama yarta ba sai Rudin Duniya da hujjarta mara Tushe Ballatana makama ta Ruguza komai ta Bata komai Karshenta itace tayi Biyu babu An Saki yarta Sajida Tana chan Tana Ramewa Saboda Damuwa itama Gatanan Gotai Gotai Da ita Miji ya Saketa ta dawo Gida Zawarci Itafa bata yarda ma ta Fara Kirga kwanakin Iddarta ba gani take kamar Wasa Kabiru yake zai zo ya Dauketa su koma Gida bai Saketa ba.
Da Bintalo ta Turo mata Video gidan Tagani Batace mata komai ba ta Fara Jin Haushinta Taya zata Rika Turo Mata Abunda zai Dagamata Hankali Ita kuma ba wani mganin Matsalarta Zatayi mata ba Shiyasa ta Kashe Wayarta bata son ta Dameta da Tseguminta wanda ta Saba kuma ya Zame mata jiki gwara ita Tana Gidan Mijinta kuma ya"yanta ba wacce aka Taba Saka ta zama karamar bazawara irin y'arta Sajida,kuma duk fa aje a dawo Daada uwa take ga Bintalo kuma kabiru da su Mustapaha Shakikan yan"uwa ne gareta Duk inda akaje ita ce ke cikin Bala"i ba Bintalo ba Shiyasa ta Kashe Wayarta abunda Taji ya Isheta bata Kaunar kuma ta kara jin wani abunda zai yi barazar Tafiya da Numfashinta.
Karfe 12:00pm aka Fara Walima
Malama Juwairiya Anty Safiya ta gayyato an saka Kanofi a Haraban Gidan Duk da bai da Girma sosai an Fito da Amarya Saboda Wa"azin Walimar Aure,Masha Allah Malama ta yi Wa"azi sosai kan Hakkokin mata ga Mijinta da Hakkin miji kan mata da yadda Mu mata zamu gyara Jikinmu Tare da Shawarwari ga Amarya an Raba Snks da Key Holder da Kofuna da Memo karamin Choter,Hanky da Riguna da Jaka Duka Dauke da Tambarin IMSAR FOREVER❤️🤩 Duk wannan aikin su Munari ne Snks din kuma aikin Umma ne,naga Tarin Mutane sosai a wajen Har da gayyar GMB2BAND GROUP suma sun Hallaci Wannan Walimar Domin Tabbatar da su Team din Imsar Forever ne.
Sai Karfe 2pm aka tashi Walimar sai aka Fara shirin gyara gidan da kuma Haraman Tafiya abar Amarya a Muhallinta.
Dr Isa Ali argungu sun zo shi da Matarsa Hajiya Barira yima Abba Allah sanya alheri aure da kuma aikin Daya samu yau zasu bi Jirgin Karfe 4pm zuwa Lagos tare da D'ansu Khalil Daga Fagge Suke daman Tunda suka iso suna chan gidan Dan"uwanta Taje Dake nan Zoo Raod ta iske Duka Gidan basa nan yayan nata kadai ta gani suka gaisa duk sun Tafi Biki.
Koda suka zo Gidan Abba ma ba Kowa sai su Imran da shi kanshi Abba Duka suna Chan gidan Amarya.
Bayan sun gaisa da Abba tayimai Allah sanya Alheri tace akaita Ta Leka Gidan Amarya kafin ta wuce Yusuf ya Dauketa Amota zuwa Gidan Tana zuwa suka Hade da Anty Safiya sai suka Tsaya suna kallon juna Baki Sake Anty Safiya Tace"Goggo Barira..!
Hjiya Mero ma ta Kira sunanta itama Cikin mamaki tace"Hajiya Mero..Ikon Allah yanzu nan Da muka Fito Daga Fagge gidanku muka Fara zuwa bakwa nan sai Alhassan kadai muka iske shine muka kariso chan Gidan Dr.Malami ai makotan mu ne,abokin aikin Dr.Ne tare sukayi koyarwa nan Jami"ar Lagos kuma mun zauna ga gida ga gida a Lagos..!
Sai kallo ya koma Sama Hajiya Mero Cikin Fara"a tace"Ikon Allah..Ai Safiya Yusuf take aure..!
Hajiya Barira ta rike baki Tana Fadin"Ikon Allah..Wato auran da Goggo Tace yayima yarsa a Wulakance batare daya Fadama kowa ba ashe ma D'an Gida ta aura Yusuf Duk Tare da ya"yanmu suka tashi. Iyalan Dr.Malami nasu Nagarta ne ni nan munyi Zaman Amana da Mahaifiyarsu Marigayiya zuwaira Allah ya jikanta Khalil kuma Hala baku Hadu bane ai abokin Imran ne yana nan Tun Ranar jumma"a
Hajiya Mero tace"Hajiya yaushe zasu Shaidasa ko ni nan ai na Dade ban gansa ba ko yazo iyakarsa Fagge baya karisowa kece dai in kika zo sai kin kariso..!
Nan fa Hira ta Sarke Hajiya Barira Tace"Ai Dayake ga Karatu ga yanayin aikinsa Banki ne ba Lokacin sun gama Sayarma gwannati..!
Nan fa Aka Tsinke da Hira Anty Safiya sai Nuna Hajiya Barira take kanwar Alhaji Alhassan ce Da goggo da Wacce ta Haifeta Inna Furare Uwarsu Daya Ubansu Daya Zumunci sosai kowa da yaji yayi mamaki matuka Har Bedroom din Inteesar Mommy ta kaita ta saka Amarya albarka Sauri Take yasa Datace Zata koma Mommy tace su tafi Gabadaya suma Daman yanzusuke Shirin Tafiya yusuf na Haraban Gidan yana Jiranta sai gasu sun Fito nan yake jin Sabon Labari yana ta mamaki haka ma su Abba sukaji Wannan mamakin da suka koma Hajiya Mero kam sai jin Dadi take irin wannan Ranar take jiyema Alhaji Alhassan Ranar da zai ji kunya,Hajiya Barira da Dr.Isa Ali argugu suna bada Labarin karamccin da Mutunci irin na Abba da Duka Iyalansa suna Fadin har suka Zauna dasu na Tsawon Shekaru basu Taba Samun Mtsala ba Shiyasa ko yanzu Megadin Dake Tsaron Gidan nasu da Iyalansa DR.Isa Ali argungu ke Biyansa Duk Wata yace ma Yusuf kada ya Damu shi ya Dauke wannan,Tsakaninsa da Abba sai Godiya anyi Zaman Amana da Mutumci
Hajiya Barira da kanta ta Kira Alhaji Alhassan tana Fadamai,Dayake Daganan Filin Jirgi zasu wuce kunya da Nadama suka kara Lullube Alhaji Alhassan ya Godema Allah baya Wajen da wani idozai kalli Yusuf da Abba..?ballatana Imran Daya gama Sanin Duka Sirrinsa.
Yaji kunya sanda Hajiya Barira ke Fadamasa Marigayiya Hajiya Zuwaira Kawartace sosai har Allah ya Dauki Ranta Daga Karshe ta Sanar dashi AhalinDaya bada yarsa kyakyawan Ahali ne mai Cike da Nagarta Alhaji Alhassan dai ba baki Zufa kadai ke Ketomai har suka gama mgana yana Tunanin Allah na son shi Dayake ta Nuna mai Ishara kala kala alamace Ta ya Tubarma Allah kafin Lokaci ya Kuremai in ba Haka ba ya Gujema Ranar da Duniya zata san Halinsa na Boye sai ga Alhaji Alhassan na kuka da Idanuwansa kukan Nadama da danasani Ba shakka Imran ya Cika Mutumin Kirki mai kyaakyawan Zuciya a yadda yake kallonsa bai taba Zata Har yanzu bazai iya Tona mummmunan aikinsa ba sai gashi ko alama yaron ya nuna masa yasan Abunda yake yi alokacin Alhaji Alhassan yaji komai ya Fita kansa Nadama ta Shigesa yadaukan ma kansa Alkawarin ya Daina neman mata Har Abada yana me yin Nadama ga abunda ya aikata a baya.
Khalil kuwa baisan Wainar da ake Toyawa ba sai da ya Dawo Shima Kiransa Babansa ke tayi Lokaci ya Kusa kada su Rasa Jirgi suna chan Gidan Amarya Shi da Sagir kowa yaja Wacce ta shiga Ransa yana Fadamata Sirrin Zuciyarsa Saboda Dama Daya Take zuwa a Rayuwa.
Sagir ya gama gabatar da kansa Wajen Hafsah kuma ya samu shiga kwarai da Gaske sun karbi Lambar juna khalil ma ya gama Sace zuciyar Munari Tuni itama tayi Na"am da mganar na Khalil saboda ai ya gama Haduwa Shima,Tuni suka karbi Lambar juna Duk da kowa nadashi Imran nachan sai Kiran su yake su Hajiya Barira na Jiransa Ya Yusuf zai kai su Filin Jirgi sai da suka gama Kafa Zuciyarsu sai gasu sun Dawo sai Alokacin Hajiya Barira ke nuna mai Hajiya Mero da Anty Safiya,Tasleem ma ashe kanwarsa ce Shiyasa yaga kamar ya santa Tunda shi yama Dade Rabonsa da kano yafi Shekara Bakwai.
Imran sai Hararansu yake yi Shi da Sagir saboda wani Hade kai da yaga sunayi Da yayi mgana Sai su yi mai Chaaa,A gurguje akayi sallama gabadaya acikin masu Rakiyan Har da Imran da Sagir suka shiga Motar Imran din suka Rakasu Filin Jirgi basu Baro ba sai da Jirgin su ya tashi suka Dawo a Mota Imran ya wani Hade rai Sagir ko ta kansa bai bi ballatana ma ya Tsaya Tambayansa.
Bayan La"asar su Inna Maimunatu duk suka dawo Gidan Abba sai gobe zasu Tafi su Maman Nasara kuma Gidan Mama suka yada Zango suna sai gobe zasu tafi Su Munari suka bari agidan dsu Anty Aneesa itama Anty Safiya ta koma Data Raka Mommy da Anty Saratu Tasleem dai Tana Gidan Amarya sai an juma Zata dawo.
Su suka Hadu suka kara gyara Gidan suka Share suka Turare gidan Turaran Wuta masu kamshi da Sanyaya rai Wanda Maman Nasara tazo ma da Inteesar da yawa kala kala bayan na Jiki harda na Daki dana Turara gida..
Sai gabda mangariba suka yi Shirin Tafiya Fareesatu sun fasa Tafiya suma sai Gobe Mazajen nasu suka zo Daukansu zuwa Gidan Abba abar Amarya Ta Huta kafin Ango ya Shigo.
Inteesar da Farko bata Damu ba sai da Taga Tafiyar zasu yi da gaske kana ta Fara Kuka Tana Rike Munari Duk Dauriyan Munari Sai da tayi kukan Sabo hawaye shabe shabe aka Bambare su Daga Jikin juna aka yo Waje da Munari Hafsah ma da Tasleem da Nasara sai kuka, Harda Umaima itama Haka suka Shiga Mota suna Sharan Hawaye Inteesar kuma Ta Kudundune kan Gadonta Tana ta kuka kukan da kowacce mace take yinsa Ranar da aka Kaita Gidan Mijinta Za"a Tafi a barta.
Gashi kuma suna da Jarabawa Allah yasa Munari ta Dauko mata Wasu Li ttafai da Zata Bukata Ba mganar Amarci mganace ta Karatu kawai ba kama Hannun yaro,Sagir ma yazo Daukan su Hafsah aMotan Imran din Tunda ya iya Tuki Imran ya koya masa,Dukkansu agidan Abba sukayi Sallar mangariba aka Zauna anata Labarin Biki da maida yadda abubuwa suka Kasance Imran na Cikin Dakinsa ya kasa Tabuka komai Kewa yake jin kewa zai yi nesa da Abba da Ya Yusuf da Gidansu Daya Saba Dashi Fiye da ko"ina zai Tafi yau ya Kwana ainda bazai ji Motsin Abba ba Rauninsa yaso ya Tabasa Raunin Tuna Anni a wajensa Yau yayi aure zai Tare a Gidansa ammh Anni bata Wannan Duniya yana Tuna kalamanta Imran Duk Ranar da kayi aure ni da kaina Zan Rakaka Dakin Matarka ba Kai ne Zan bama Hakurin Zama da ita ba kai zan bata amanarka na kumace Tayi Hakuri Domin ba karamar Jaruma bace Macen da ta yadda ta aureka..
Alokacin Tabe baki kadai yake yi baya Mgana ammh yau sai da Zafafan Hawaye suka Zubomai acikin Kwarmin Idanuwansa ya Hade kansa da Gwiwa yana ta kuka kukan mai Cinrai da kewa da kaunar Uwa acikin Ransa.
Abba ne yake ta Cigiyansa kan abar Inteesar ita kadai achan Gida Sagir aka Kira kosuna Tare yace shima Nemansa yake yana ta Kiransa bai Dauka ba Yusuf ne yasan ba inda Za"a Gansa sai Cikin Dakinsa Halin Daya Samesa ne yasa ya Kira Abba Shi kanshi Abba sai da ya Fitar da kwallah Shima yayi kuka a irin wannan Ranar Allah ya jikan Zuwaira da Sauran ya"yanta Allah yasa suna Cikin Aljannah
Haka Abba ya Rungume Zaratan ya"yan nashi yana Sharan kwallah yana Lallashinsu sun yi ma yan"uwansu da Mahaifiyarsu addu"an Dacewa da Fatan Allah ya jikansu da Rahma.
Yusuf shi ya Hadama Imran Kayansa da Zai Bukata Tunda bai Dauki Hutu ba Mr Tunde da Mr Sulaiman sun yi Dashi ya Dauki Hutu yace bazai Dauka ba Duka Duka yaushe ya Fara aikin Da wannan kuma don wannan Dole suka kyalesa Har Khalil ma yamai mgana shima wannan Hujjar ya kawomai kuma shima ya yarda yace ya bari sai nan gaba sai ya Dauka sai susha Honey moon Cikin Natsuwa Lokacin itama Intee ta gama Jarabawarta ba Streess na makaranta.
Duk yadda Imran yaso kada Rauninsa ya bayyana kasawa yayi yau Rana ta Farko da kowa yaga yana kuka Ya Rumgume Abba kamar Wata Mace ba wanda bai Tsausayamai ba Abba ya Buga Kafadarsa yana Fadin"Ka Daina kuka..Jarumai kamar ka da Juriya aka sansu ba kuka ba..Kaje Ga.Matarka Allah yayi maka albarka ka Riketa Amana Kanwa take gareka Ta Kowani bangare ta Chanchanci Kulawarka..Sannan Rokona na Karshe ka Rage Zafin Rai don Allah Imran kuma ina Rokon Allah yasa wannan auran ne Sanadiyar Dukkan Wasu alherai Allah ya Zaunar daku Lafiya!
Gabadaya aka amsa da Ameen Ameen Sagir ne zai Tukasa zuwa Gidan bayan an gama Saka kayan nashi a Mota ya Shiga Gidan Gaba Sagir yayi Riverse ya Fice Daga gidan su Abba na Dagamai Hannu Yusuf bai san yana Kwallah ba sai da yaji Abba ya Saka Hannu ya Sharemai ko da Imu ya kasance bamai Hayaniya da shiga Mutane ba Akwai Shakuwa Tsakaninsu Sosai Kuma shi Sabo ai ake yima kuka Su Sa"id suna ta bama Yusuf baki suna Fadin suma fa Tare koda yaushe suka so zasu ga juna ba"a Rabu ba Har Abada.
Shi kanshi Sagir Jikinsa ya Mutu da yanayin Imran din kuma shima wannan kewar na Damunsa Bai fi Shekara uku Dayasan Imran ba Ammh Sun yi Sharing din kauna da Shakuwa a Tsakaninsu suyi Fada su Shirya ammh kuma basa iya Rabuwa da juna Ammh yau aure yakai Imran wani Mtsyin da zai bar anguwan Gabadaya sai dai Waya ko kuma in ya Lekosu shima Tuni jikinsa yayi sanyi Har suka kai Gidan ba wanda yayi ma Dan"uwansa mgana..
Gidan bamai gadi Imran ya Sauka ya Bude Get din Sagir ya Shigo Ciki Shi ya Tayasa suka Kwashe kayan zuwa Cikin Gidan Har Cikin Dayan Bedroom din da zai zama mallakin na Imran ne.
Sagir ya zauna Saman Daya Daga Cikin kujeran Falon yana Fadin"Ango ba Kazan Amarci haka zaka shigarma Amaryan taka Hannun Rabbana..!
Imran na Tsaye yana kallon Wani Barayin ya Karkace kai Idanuwansa sun kala yace"Uhm..!
Daga haka bai kara cewa komai ba Sagir ma sai bai kara cewa komai ba yana Bin Falon da kallo yace"Baffa Kabiru yayi Kokari..Allah ya Biyasa..!
Imran na Jinsa bai ce komai ba Tunaninsa ya Tafi yadda Rayuwa Zata Juyamai na Rayuwa shi da Inteesar a Inuwa Daya a mtsayin mata da Miji.
Anya zai iya Daukan wannan Nauyin..?shifa ba Daya yake da kowa ba Kansa ma bai Damu dashi ba ballatana Nauyin wata..?wata zuciyar tace mai ai ita Zatta kula Dakai kaima ai Zaka kula da ita Tunda itace kadai Zuciyarka bata manta da ita ba..!
Yana Cikin wannan Tunanin Sagir yace"kamar Tashin kuka fa nake ji aciki..?ko Inteesar ne bata Daina kukan Rabuwa dasu Munarin ba..?
Sai alokacin Imran yaji dan Tashin kuka Kofar Bedroom din Dayake Kyautata Zaton tana ciki ya sakama Ido Itama Tana kuka ne..?
Shi tasan meya sa yake kuka..?saboda yau zai kwana inda ba Yusuf ba Abba ba Munari wadanan sune Ahalinsa da baida Kamarsu duk Duniya ko"ina Yaje ya dawo Su din kamar wasu Garkuwa ne a garesa yana kukan yau ya bar Gidansu Wata Rayuwa ta kawosa Wata gabar da bai Taba Hasashe ba ko Fatanta nan kusa ba bai Taba ji aransa zai iya aure nan kusa ba sai gashi shigowar Inteesar Rayuwarsa ta sauya komai.
Sagir ne ya Katsesa Yana Fadin"Bari na Tafi..Tunda naga anko kuka kai da Amaryan taka kai kuka ita kuka..Kawai ka shiga Ciki ne ku Hada kai kuyi ta Rafzan kuka sai gobe da asuba sai ku Dakata..!
Yafada Lokaci Daya yana Mikewa Tsaye Imran ya Murmusa Lokaci Daya ya saka Kafa ya Daki Kafar Sagir yayi Gaba da Sauri yana Fadin"Bakomai na yafe Maka duk cikin Nishadin Ango ne..!
Yafada yana jin wani kewa na kamaaa sa bayaso ya waigo Hawayen Dayake ta Rikewa ya bayyana Imran ya Taka ya Bisa yana Fadin"bazaka Tsaya mu yi Sallama ba..!?
Sagir na Ficewa yana Fadin"Wani Sallama.?bayan wacce mukayi..Sai da Safe a gaida Amarya sai an kwana Biyu indawo cin Girkinta ka Fadamata tayi Hakuri haka auran yake kaima Allah ya baka Hakuri Imran Allah ya baku Zaman lafiya..!
Yafada Lokaci Daya yana Dauke Hawayen da suka Cikomai ido
Imran ya Tsaya Cak yana kallonsa juyowa yayi yana Mikamai key din Motarsa yana Fadin"Sai da safe..!
Imran ya saka Hannu ya karba yana Fadin"Zaka Samu abun hawa kuwa..?
Sagir ya Gyada kai yana Fadin"Insha Allahu..!
Imran yayi gaba yana Fadin"Muje na Taka maka!
Yafada yana Tusa Key din Motar Cikin Aljihun yadin Boyel din da Sagir yayi musu wanda suka sanya yau din Yana jin Wani abu Daga Karkashin Ransa
Sagir yabiyosa suka jera kowa na Sauke Ajiyar rai Imran acikin Ransa yana Fadin Waye Sagir a wajena..?
Sagir Dan"uwa ne kuma Abokina aminina wanda bani da kamarsa acikin Wannan Duniyan ya Zauna Dani Da Dadi ba Dadi duk abunda na Zama yau ko na Taka da Gudummuwarsa Abokina Wanda Samun Irinsa sai an Tona Inda Haka abokai suke kamar Sagir da Mutane da Dadama sun ji Dadin abota bazai Kirasa aboki ba ya Zama Bangaran Dan"uwansa da Kokarinsa akaina bazan Taba mantawa ba.
Sagir kuma Tuna Alheran Imran yake a garesa Duk da yana da Murdaddun Halaye ammh shi ya Fi kowa Fahimtarsa yana da kyakyawan Zuciya da Tunani mai kyau mai Kirki ne kuma mai Nagarta ne bai Taba Haduwa da aboki kamarsa ba ya wuce aboki ya wuce amini Shi din Dan"uwane a Wajensa
Suna wannan Sake saken suka isa Bakin Titi Cikin Sa"a Sagir ya samu mai adaidaita sai ya juya ya mikama Imran hannu sukayi musabaha yana Fadin"Ka koma ka bar Min kanwata ita kadai..Kuma Mallam ka Sauke wannan Ego din naka da wani Kukan ka agefe in ka koma ka Lallasheta Ta Daina kuka Haka ango kema kowacce Amarya sannan Tell Her sorry Kazanta Tabini Bashi Khalil gabadaya Nauyin ni ya Doramawa kuma yana kaina Zan Biya bashi..!
Imran kallonsa kawai yake bai ce komai ba sai da ya gama yace"Shirme..!
Yafada yana wani Dakuna Fuska,Sagir ya Daki Kafadarsa yana Fadin"Ko da yake na Tuna..Ranar Lallashin bata zo bane ko Imran..?
Yafada cikin Dariya Shima Imran din Dariya yake suka Rumgume juna Kowa na Dauke Hawayensa Imran ya Dago yana Jinjina Hannun Sagir lokaci Daya yana Fadin"Tanque....Nagode kwarai..Bansan da wani baki Zan gode maka ba..!
Sagir yace"Ni bana Bukatar Godiyarka mallam abu Daya zakamin..?
Imran ya Kallesa yana Fadin'menene shi..?
Sagir yace"Ka so kanwata..Ka bata Kulawa kuma don Allah kada ka bari wannan Girman kan naka ya Bata Wahala..!
Yafada yana Dunguremai kai Dariya suka saka gabadaya yana Fadin"Insha Allahu zan taimaka muku.!
Mai adaidaita ne ya gaji da jira yayi hon kana suka kara Sallama Sagir ya shiga Imram na Dagamai hannu suka Wuce kowa na Dauke kwallarsa.
Jiki ba Laka Imran ya Taka ya dawo Gidan sa yana Kallo da nazarin anguwan da kansa ya Rufe get din Kana ya taka zuwa Cikin gidan ya Kulle Kofar Falom a aransa yana Fadib"Lalle na yarda nabar gida..Imran na kulle gida..?
Sai da ya Murmusa Har zai
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment