Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yace"Kin ji sanda na ce shi kadai keda Laifi Barrister Asma"u..? Cewa nayi dukkanmu munyi laifi ya sani na sani Kowa ma ya sani Tunda Daada gaban duka ya"yanmu ta fadi haka..!
Mami Asma"u ta dagamai hannu Cikin Fusata tana Fadin"Bana son jin komai Mustapha..ai ka riga ka gama mganarka Abban Sajida kaga abunda nake Fada maka ko..?ai daman na fadamaka kune kuka damu dashi shi kam bai damu ba yana nan yana Rayuwarsa Kama gani Harda dan Shaye shaye ma ya samu cikin ya"yansa..Baya bukatar kowa..Ka taso mu tafi Abuja batamana Nisa ba bayadda zan zauna ina ji ina gani ana Tozarka ba..!
Tafada Tana isa garesa Lokaci Daya ta kamo Hannunsa Shi dake tsaye ya kasa mgana saboda baida ta cewa,shi kanshi ai yasan bai kyauta ba to shima Selfish bazai barsa ya iya Daukan haka ba da kuma Ego irin nashi Daman dagashi har matar tashi They are d same.
Maimakon ya nuna mata hakan datace bai dace ba sai ya kada kai yana Fadin"Yes hakane abunda ta Fada..Daman duk abunda nake yi saboda Daada ne..Tunda kuma shima Malamin ya nuna yana bayan mganar Da"nsa bani da tacewa..Ma"u muje..!
Yafada suna Kokarin barin Falon kowa ya Bisu da kallo baki sake Abba Dai na Zaune duke da dakai bai cekomai ba Har wannan Lokacin.
Daddy ne ya mike yana Fadin"Haba Barrister ya zaka Biye mata..? Itafa macece ya kamata ka zauma mu Fahimci juna..!
Ko juyowa basu yi ba suna Shirin barin Falon Imran ya saki wata Dariyan Basawa Cikin Kaushin Muryansa yace"Ka kyake su tafi Baffa..Daman ai ba komai ya kawosu ba sai son kai irin nasu abunda kuma suka zo dominsa sun ga ba Nasara Abba bazai je ko"ina ba..!
kalamansa yasa gabadayansu Juyowa kowa sai da ya jinjina mganar Umma ta kada kai aranta tana fadin yau an samu mai daidai da Asma"u Sa"id da Sadam suka kalli juna,hakama Matansu suna ayyana Tabbas Tsaurin Idanuwan Imran sun wuce Tunaninsu.
Mami Asma"u ce ta nuna kansu tana Fadin"Mume kake kira masu son kansu..? Lalle shaye shayen ka yayi maka Rana..Tunda har kakiramu masu son kai.kuma kake Tunanin Daada ta tako kafarta ta Biyoku lalle Kwayarka bata Fadamaka daidai ba mara kunya..!
Imran ya Dakuna Fuska yana kallonta ido cikin ido Tabarsa ya zuka Hayakim ya sakesa ta Hancinsa harta Kunni cikin kallon sama da kasa yace"Ni kin ji sanda nace Daada tazo nan..? Ai ni ina girmama Daada..Ko bakomai Daada ta nuna Rauninta kan abunda ya same mu,nifa da ku nake bada Daada ba, kada kuma ki kara Kirana Mara kunya bake kika Haifeni ba mganar kwaya kuma in ma na sha ai ba da kudin Lauyoyi na siya ba ko..?
Kowa ido ya zaro da jin kalamansa Yusuf ya Dafe kansa cikin Takaichi Mami Asma"u taji ta Muzanta ta kalli Baffa Kabiru wanda yake bin Imran da kallo yana Tunanin Tsegerancin yaron zai saka ma ya iya Zaginsu kila ma Har malamin ya gagaresa Tunda gashi ya kasa mgana.
Yana neman hanata mgana ta Kwace hannunta ta fara taku zuwan gaban Imran tana nuna kanta Lokaci Daya Tana Fadin"Ni kake fadama wannan mganar..? Kasan wacece ni..?
Irin kallon sama da kasa na Rainin nan yayi mata Irin to ke din wacece cikin Gadaransa yace"To ke din Wacece..? Ai b..!
Bai karisa ba ya yaji tsawar Abba ta karade Falon cikin bacin rai yace
"Kai IMRAN...!
yafada yana Huci Huci mai zafi Tun dazu ya kasa cewa komai saboda Yasan tankwasa Imran ba abu bane mai Sauki Daman yasan tabbas sai haka ta Faru,sai dai an kawo gabar da Dole yayi mgana yana da Tabbacin da bai Tare Imran ba cemata zai yi kedin ai ba uwata bace..Zai iya Zaginta Duk mganarta yana da amsarta shi ya Haifi Imran yafi kowa sanin baya da Shayi ko Tsoro ba Asma"u ba ko Baffa Kabiru zai iya kallah yace mai ai ba Ubansa bane shi ballatana ita.
Imran ya wani kalli Abba a karkace kafin yace"Abba daka koma ka Zauna..Na dade ina sauraran mganarka ammh yau kam bazan saurareka ba..!
Yana Fadar haka ya juya wajen Mami Asma"u Lokaci daya ya saka Hannunsa ya Murje Sauran Taban Hannunsa Data rage da Wutar da komai ya saki Sauranta a kasa Hannunsa duka Biyu ya maida cikin Aljuhun wandonsa yana Fadin"Arm kika ce ma me..? Yauwa na tuna bansan ko wacece ke ba ko..? To ni ina ruwana da saninki Tunda ke ba Uw....!
Abba ya kara Dakamai Tsawa yana Fadin"Wlh in ka kara cewa Tak anan Wajen sai naci Mutumcinka imran kaji ma na Fadamaka..!
Yafada cikin kakkausan Murya yana nuna shi da yatsa.
Imran ya dago yana kallon Abba Lokaci Daya yana wani Dakuna Fuska.
Mami Asma"u tayi wiki wiki kamar mara Gaskiya Dariya kowa ke kunshewa aciki ganin yadda tayi,Basheer da Sadam suka kalli juna suna Mirmishi Inteesar kuwa sai da ta Dara Tana Rufe bakinta aranta tana godema Ya Imu yau taga mai mganin iskancin Mami Asma"u saura Diyarta Tsagera mara kunya,Hatta Umma abun yayi mata dadi kanta na kasa tana Dariya kasa kasa wato mganin Mami Asma"u sai tsageru irin su Imran Daddy na gefe bai ce tak aransa yana fadin in bata kama girmanta ba ai yaron zamani zai tayata kamawa.
Abba ya karisa wajen su Baffa Kabiru yana Fadin"Ya kabiru don Allah kuyi hakuri ku dawo..Bai kamata ka Dauki wannan abun da zafi ba..wajena kuka zo ba Wajen Imran ba kuma Imran bai isa ya hanani Abunda nayi Niyya ba..Kuma bai isa ya Raba jinin dake Tsakaninmu ba Ya kabiru..!
Baffa Kabiru ya kada kai yana Fadin"Ammh kana ji yana neman Zaginmu ni da iyalina..!
Baka iya dakatar dashi ba..?
Abba yace"Ai na Dakatar dashi Baban Sajida..kuyi hakuri..!
Kafin ma Baffa ya samu bakin mgana ta tareshi da cewa"Ka tareshi lokacin Daya gama Tozarta mu ba?
Wannan gabar Daddy ne yayi magana yana fadin"Yaya ya kamata ka Dakatar da Asma"u kan saka baki cikin mganar nan ba Huruminta bane..nan wajen fa akwai mutane kuma bataji kowa ya tanka ba..Mganace Tsakanimu iya mu nan manya bai kamata matarka tana Sako baki ba..!
Su Sa"id dake gefe suka kada kai alamun gaskiya ne.
Mami Asma"u tabi Daddy da Harara Tana Fadin"Sai nayi shuru ana cin Zarafin Mijina ko..? Ni Asma"u nasan Ciwon kaina kan Mijina da ya"yana zan iya yin komai domin sune iyalaina anan duniya..!
Daddy yace"Musan wannan kowa anan ai Ya"yan nasa da matarsa sune iyalansa kuma don su ma muke fita nema ammh bai kamata kina Tsallake in da ba Huruminki ba..!
Ta bude baki zatayi mgana Baffa ya Rike mata Hannu ammh duk da haka sai da ta Furta cikin bacin rai tace"Ammh shi Tsagerun yaron naku daya Tsoma baki sako cikin mganar kukayi..?
Daddy zai yi mgama Abba ya Hanashi ta Hanyar tareshi yana Fadin"Mustapha ba girman kabane..Kyaleta don Allah
Yaya kabiru Asma"u don Allah kuyi hakuri ku dawo ku zauna ba domin kowa ba saboda girman Allah da kuma Girman zumunci..!
Yafada yana Hada Hannayensa alaman Roko Imran Dake Tsaye yaji Haushi ya kamashi Karamin tsaki yaja kawai bai ce komai ba.
Jin haka yasa Baffa Kabiru ya kalli Mami Asma"u yana Fadin"Muje mu zauna..!
Zatayi mgana ya hanata bayan ya Girgizamata kai dole ta Bishi ya koma in da ya tashi ya zauna itama Haka sai Harare harere take yi tana waige waige,kowa yayi kamar bai ganta ba.
Suna Zama Abba ya koma ya Zauna Kafin yayi mgana Baffa Kabiru ya Rigasa da cewa"Malami Imran Shaye Shaye yake yi..?
Yafada yana kallon Abban Imran Dake gefe kamar yace"Eh ko zaka iya Daukan mataki ne..? Sai dai ba Halin mgana saboda Abba ya hanasa ammh Kallon kafa fara cikani yake ma Baffa kasa kasa Yusuf na gefensa bayaso ya bar Wajen domin Imran bazai damu da ya Zubar da Halin nashi ba.
Abba ya dan Murmusa Kafin yace"Imran baya Shaye Shaye Yaya..Taba kadai nasan yana sha..!
Baffa Kabiru yace"Taba..? Kaidai ita kagani ammh daga ganin yanayinsa bazai rasa shan kayan maye ba Allah ma ya kyauta bayashan giya..!
Yafada yana kallon Imran din daya ji kamar ya Durama Baffan Ashariya.
Abba yace"Eh bazan yi shaidansa ba..Sai dai nafi kowa sanin Imran duk cikin Ya"yana shi kadai ne bayamin karya..Yana fadin gaskiya komai Dacinta Inda yana shan wani kayan Maye bilahil azim kaji Rantsuwan musulaimai sai na fara sani..!
Baffa Kabiru ya jinjina kai bai kara mgana ba Abba ya gyara zama yana Fadin"Yanzu dai ya mganar zuwan mu Dukku gobe..Ina so naje naga Daada na roketa gafara..!
Yafada cikin wani yanayi Baffa Kabiru ya dan zakuda kafada kafin yace"Aini na gama mganata..Gobe nace daga nan mu isa Dukku bana so kowa ya Fadama Daada sai dai ta ganka kawai ammh naji Yaron ka yace bazaka je ba kila ita Daadan kake so tazo ta sameka..!
Abba ya girgiza kai yana fadin"Ban isa nace haka ba Yaya..!
Baffa Kabiru yace"D"an ka ya yanke maka Hukunci kuma baka iya cewa komai ba..!
Imran da ransa ya gama baci ya Budi baki yace"Ba Hukunci bame haka ce zata Faru ba inda zamu je..!
Abba ya Mike ransa yana Fadin"Imran..Imran me na gayamaka..?
Cikin Dakuna fuska yayi yana Fadin"Kace kada na sake mgana..!
Abba yace"Shine kuma saboda ka Rainani ka sake yin din ko..?
Imran yace"Ammh Abb..!
Rufemin baki kafin Raina ya baci na tsinke ka da mari..!
Abba ya katseshi  cikin Fusata kafin ya Cigaba da fadin"Ina Ruwanka da mganarmu.?kana sako baki cikin mganar manya yaya fa Yayana ne Uba yake gareka ya isa dani Ubanka bama kai ba..!
Imran ma kunkuni acikin ransa yana fadin Tab ni dai ba Ubana bane wlh.
Kowa yaga Motsin bakinsa Hatta Abba sai dai bai bi takai kada ya Matsa ya fada da karfi kowa yaji ya kuma san ba abu bane mai kyau ya fada ba.
Cikin Kaushin Murya Abba ya Nunashi da yatsa yana Fadin"To kul na sake jin kayi mgana anan wajen..Mganar Tafiya Dukku kuma da yardan Allah Gobe zamu tafi dukkanmu dani da kai da Yusuf da Munari da Matarsa In kaga dama kabiyomu in kaga dama kada kaje..!
Yafada cikin Fushi Imran yabudi baki yace"Fine..ni tunda bakace Dole naje ba Allah ya kiyaye hanya..!
Yana fadar haka ya juya zai koma Dakinsa Abba ya rike baki cikin mamaki kafin yace"To na fasa..Wlh sai kaje!
Imran ya Juyo cikin mamaki yana fadin"Abba..!
Yace"Eh sai ka je Umarni ne Daga ni Mahaifinka in kuma ka Sauya wani Uban ne zan gani..!
Yana gama Fadar haka ya koma Wajen Zamansa Ransa na baci.
Imran kamar zai yi mgana Ya dago ido keman suka Hada Ido Hudu da Inteesar kai ta girgizamai tana Lamgwabe kai alamun kada yace komai batajin dadin Fadan da Abba kemai yana sata jin wani iri.
Shi kuma Saboda ita bazai iya cewa komai ba Idanuwanta suna da kaifi a gareshi yasa ya juya kawai ya Shige Dakinsa ya bango kofa.
Abba ya jinjina kai kawai bai ce komai ba ya juya yana kallon Baffa Kabiru da Daddy yana Fadin"Kuyi hakuri dashi..Haka yake sai fatan Allah ya shirya..!
Ameen kawai sukce ba wanda ya kara mgana Abba ne ya mike yace su Daddy su tashi su shiga Dakinsa sa tattauna achan sauran matan kuma Safiya ta kwashi gayya zuwa Shashenta Inteesar da Munari da Hafsah suka tafi Dakinta Yusuf kuma yayi ma su Basheer jagora zuwa Dakinsa na baya.
Shi kuma sai ya yanke Shawaran kwana Dakin Imran tunda yana da Tabbacin ko giyan wake yasha bazai Tura wani Dakin Imran ba.
Shashensa ya koma ya iske Safiya ta bama Kowa wajen kwanciya Bedroom dinta ta sauke su Aneesa.
Dayan kuma ta Sauke Umma da Mami Asma"u wacce ke ta wani shan kamshi Umma dai sai dariya acikin ranta to shan kamshi me ke da yaro ya gama Tsage miki gaskiyarsa.
Imran na Kwance yana fama da Nauyin Umranin Abba bashi kuma da yarda zai yi ya Tsalleke mganar sai Mami Asma"u dayake Tunanin sai yayi mata kyakyawan zuwan da zata gane Waye shi zata kiyayesa dauka take ita wata ce..? Shi ko Baffan mijin nata ba ganinsa yake da wata kima ba ballatana ita karan kada Miya.
Yaja tsaki yafi sau ba adadi shi kadai kafin yaji Shigowar,Yusuf dago kai yaga waye zai shogomai daki sai yaga Yusuf da kayan barcinsa da Blanket da Safiya ta kawomai

Kallon Irin lafiya yabi shi dashi Shi kuma Yusuf yana ganin irin kallo yayi Fuska ya ijiye bargonsa ya shiga Tiolet ya sauya kaya ya fito ya isa gaban Madubi ya Fesa Turaran Imu yazo gefensa ya Kwanta yana fadin"Wash..Nagaji..!
Kallon mamaki Imran yabishi dashi kafin ya Mike Zaune yana Fadin"Miye haka..!?
Ina dakin matarka..?
Yusuf na kwance yace"Da baki aciki..Ko cikinsu kake so na shiga na kwanta..!
Karamin Tsaki Imran yaja kafin ya tashi ya Haye saman kujeran Dake Besdroom din ko mgama bai kara ba.
Yusuf yayi dariya ya kara Ware kafa da Jiki yana fadin'Yauwa zan sakata na Wala wlh..,!
Ya fada yana satan kallon Imu dayaji kamar ya fitar da yusuf Daga dakin shi baya kwana da wani akan gado takura yake yi juya baya yayi kawai baice komai ba Yusuf na kallonsa yana Dariya kasa kasa.










*11/03/2022*
*Janafty..*
3/22/22, 23:13 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�2*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*

Da asuba gabadaya mazan suka tafi sallar asuba a masallaci,Imran yayi ta nuku nuku har sai da suka tafi suka barsa kana ya taho daga baya daman dasu ne bayasan jerawa yusuf daya san Halin dan kayansa bai ko bi ta kansa ba ganin jiyan bai yi wani barcin kirki ba Farkawa Goma sai yaji motsin Imran yana sakin Tsaki shidai bai bi ta kansa ba ya bararraje yana ta kwasan barcinsa Hankalinsa kwance.
Da suka Hadu da Sagir a masallaci Yayi mamakin ganin Imran bai hada Sahu da Ahalinsa ba Layin baya yaje abunsa,kuma ana idar da Sallar shi ya Riga kowa ya fita,Fuskar nan a Hade kamar wanda aka aikomai da wani mumman sako da asuban Fari.
Sagir ya tsaya sun gaisa da su Abba yaga Baffa Kabiru ya kara Jinjinama kansa Lalle su Imran din yan Dangine gaba da baya.
Koda suka koma Gida Imran ya Shige Dakinsa ya kulle ya Haye gadonsa Yusuf dariya ta kamasa Daman duk Saurinsa kenan bai damu ba ya Shige Dakinsu Sadam suna Hira Abba ma Dakinsa suka Shige suka cigaba da Tattaunawa Tsakanin yan"uwan da suka Fito Daga Jini Daya sai Allah.
Mata matan kuma suma suna Sallar asuba basu koma barci ba suka Fito zuwa Kitchen Safiya da Tawagar yan matanta Inteesar,Munari da  Hafsah,Sai su Aneesa da Fareesatu da suka ce suma bazasu zauna ba,sai suka mikama Mazan nasu yaran nasu su kuma suka Fada Kitchen suka Fara Kokarin samar da abun karin safe da Wuri tunda akwai Tafiya agabansu.
Ruwan Tea suka Fara Dafawa wanda yaji Citta da kayan kamshin Shayi sai Suka Fere dankali suka soya da kwai suka kuma yi pancake,Safiya ta bada Shawaran suyi kunu da kosai Saboda su Abba nan da nan kuwa daman Tana da garin kunun da Mommy ta aiko mata dashi,suna da Sauran Nama a Fridge da kayan ciki suka Hade su sukayi Ferfesu kada su bar gidan zuwa Dukku kafin su dawo ya Lalace.
Soyan kosan ya zama na Karshe ne bayan sun gaggama komai,Safiya Da Aneesa suna tajera komai Cikin kololi ita kuma Fareesatu tana ta Jera Mug,da Filet filet da Fork iya adadin mutanen da zasu yi Amfani dashi.
Inteesar da Munari da Hafsah sune ke wajen soyan kosan,inteesar na dagachan gefe saman Cabinet din kitchen din ta Haye daga Sama Sanye take da Rigar barcin munari doguwa mai Ruwan madara,mai taushi sai dai saboda Munari tafi ta kiba sai Rigar tayi mata yawa kadan karamin mayafi ne a saman kanta ta dan Ratayeshi.
Hafsah ce ke gaban Kaskon Suya ita kuma Munari na ta faman buga Kullim kosan suna yi suna Hira Jefi Jefi.
Ba wanda yaji Shigowarsa Saboda gabadayansu Hankalinsu nakan aiyukan da sukeyi ne kuma suna Hira kuma Dayake Sallamar nashi iya Saman lebensa ne ba wanda ya Jisa.
Anty Safiya ce ta ganshi Lokacin Dayake Bude Fridge ya Dauko goran Ruwa mai Sanyi yana sanye da Jallabiya mai ruwan madara,wacce bata kai kasa ba sosai Fararan kafafuwansa masu cike da gargasa suna Waje ne.
Ganin sun Hada ido da ita yasa yace mata"Ina kwana..!
Yafada yana dan Daga idanuwansa yana Karema wadanda ke Kitchen din kallo ta kasan Idanuwansa.
Safiya tayi mirmishi Lokaci Daya Tana Fadim"Lafiya lau Imran mun tashi Lafiya..?
A saman lebensa ya amsa daidai Lokacin da suka Hada ido da Inteesar wacce ta Kuramai ido tana kallonsa cike da wani Shaukin da bata san dashi ba,Kowa ya juyo yana kallonsa ganin haka yasa Munari ta gaisheshi Hafsah ma haka su Aneesa ma suka gaisheshi ba domin ya isa ba sai Domin yana da kwarjini da cika Fuska uwa uba kuma Oga Imu ne da kansa ai baza ka jira sai ya gaisheka ba..
Tundaga gaisuwar Farko bai kara amaawa kowa ba ganin haka Inteesar taki gaisheshi,Sai ma wani lamgwabe kai datake yi tana kallonsa Shi kuma Gabansa ne ya Fadi ganin saman kirjinta yana waje ne,Kuma Rigar bata da wani kauri ga Shatin saman Nonuwanta nan ta waje Jikinsa ne yaji ya fara rawa yasa ya juya zai Bar Kitchen din dauke da goran Ruwan a Hannunsa.
Daman Inteesar tana ta gefensa ta bangaran Fita ne,ita bata sani ba yazo fita sai ta zuro kafarta ta taba mai Cinyarsa da sauri ta janye tana kallonsa kankance idanuwansa yayi yana kallonta kafin yace cikin Sanyin Murya."Ke kin raina ni ko..?kowa ya gaisheni ammh ban dake ko..?
Noke kai tayi tana yar dariya kafin tace"Ina kwana..!Mirmishi kadai yayi na gefen baki yana Ficewa Daga Kitchen din bai ce komai ba.
Yana Fita Munari da Hafsah da suka ga komai suka Juyo suna kallon Inteesar dake Dariya kasa kasa suka kalli juna suna rike baki tana juyowa suka Hada ido da ita,Ganin yadda suke kallonta yasa ta bata rai ta wani Hura Hanci Dariya suka saka Harda Tafawa ita da Munari Hafsah tayi ma Munari Rada a kunni tana Fadin"Yarinyar nan akwai munafuncin datake Boye mana..!
Hafsah tace"Barta..Kuma zasu dace da Masoya..!
Suka kara Kyalkyacewa da Dariya Inteesae ta tsargu ta Shagwabe Fuska Tana Fadin"Anty Safiya ga su Munari nan basa aikin da kika saka su suna ta Gulmana..!
Anty Safiya ta waigo Tana Fadin"Kuyi dai ku gama lokaci yana tafiya..!
Da toh suka amsa ita kuma Inteesar tana yi musu gwalo,su kuma suna ta Hararanta tana Dariya sama sama.
Cikin Lokaci suka gama komai su Inteesar suka je sukayi wanka Domin sunce bazasu iya Karyawa basu yi wanka ba,jin haka yasa suma suka Shiga Domin yin wanka suyi ma yaransu kafin su Abba su fito.
Karfe 9:00am na Safe kowa ya Hallara a Falon saboda Breakfast,An shimfida Katuwar Darduma anan Tsarkar falon su ka jera komai asamanta.
Sai da kowa ya Hallara banda Imu,Har an fara karyawan Daddy ya Dago yana kallon Yusuf kafin yace"Ina Dan"uwa yake Yusuf..?
Yusuf na Kurban Tea dinsa yace"Baffa yana Cikin dakinsa..!
Ya kada kai yana Fadin"Meyasa bai fito ya karya ba..?
Yusuf yace"Bai cika cin wani abu da Safe haka ba kila sai chan da Rana..!
Kada kai kawai yayi bai ce komai ba Mami Asma"u na gefe aranta tace gwara hakan ma Domin Tun abunda ya faru jiya Tsagerancin yaron yayi mata Tsaye a saman kanta.
Inteeesar dake gefen Hafsah zaune ta Dauko Wayarta ta Shiga Messages ta Turama Imu sako.
"Ya imu kafito kayi breakfast..!
Ba dadewa ya maido mata da amasa.
"Bana jin yunwa..am ok..!
Inteesar na ganin haka ta Turamai da Sauri.
"Saboda ka cika cikinka da Hayakin Sigari ko Ya Imu..!?
Sai da yadan jima kafin ya bata amsarta,Tama kasa cin kosan dake gabanta Hankalinta na kan wayarta.
"Eh..!
Kawai yace mata Mirmishi tayi tasan bazai mata karya ba Tunda yace Eh to yasha ne,sai ta Rubutamai.
"Kana so ka mutu ne Ya Imu..?
Da sauri ya maido mata amsa wannan karon.
"Eh in na mutu Who care..!?
Tana ganin haka sai da gabanta ya Fadi da Sauri ta Rubutamai.
"Ni mana..Zan ta kuka nadaina cin abinci har nima na mutu..!
Yana kwance ne yaga sakonta sai da ya Mike zaune yana sosa goshinsa afili ya Furta yarinyar nan akwai Rigima.
Amsa ya bata da cewa"bazaki mutu ba..!
Tana ganin haka da sauri ta maidamai da amsa.
"Zan mutu mana indai kai ma ka Mutu na daina ganinka Ya Imu..!
Sai da ya dade bai Bata amsa mata ba har ta Fara sarewa sai ga sakonsa ya Shigo
"Wayace miki zan mutu yanzu..? Oya eat ur Food bana son shagwaba am not in d mood..!
Tana ganin haka sai da tayi Mirmishi akallah dai  tasakashi yayi mgana batayi kokarin kara Turamai komai ba sanin Tunda yace baya cikin Mood din bazai kara cemata komai ba Tana kallon Wayarta Tana Mirmishi ita kadai Hafsah data Tabo Munari Tun dazu suna ta kallonta ta dago suka Hada ido Hararansu tayi kafin ta Boye Wayarta cikin karamin Hijabin Dake Jikinta,Su kuwa me zasu yi in ba Dariya ba Har sai da kowa ya Juyo yana kallonsu Daddy dake lura da Inteesar tun dazu bataci komai ba sai Danna waya take yace"Intee ijiye wayar nan ki Karya..!
Kanta a kasa tace"To Daddy..!
Lokaci daya Tana Hararan su Hafdah dake mata Dariya kasa kasa.
Basu wani bata Lokaci wajen Breakfast din ba,kowa ya tashi su Hafsah suka Tattara komai zuwa Kitchen suka fara wankewa,Su kuma su Anty Safiya suna ciki suna Shirya Tunda ance kowa ya shirya nan da 11am zasu dauki Hanya.
Suna gama wanke wanken suka Gyara Kitchen din suka koma Daki Domin Shiryawa Munari ta kalli Inteesar Tana Fadin"Intee ya zamu yi da School yau..!
Inteesar tace"Ya kuwa..? in mun dawo zamu yi covering din inda aka wucemu..!.
Munari ta gyada kai alamun gamsuwa Inteesar ta kalleta tana fadin"Sai naje gidan Mama na Dauko kayana..!
Munari tace"Basai ki saka nawa ba..!.
Inteesar tace"A"a bazan iya ba sun min yawa salon na Dinga yawo aciki..!
Hafsah ta saka Dariya ita da Munari Inteesar ta Hararesu bata kara cewa komai ba.
Sai da ta jira su Munari suka Shirya tsab Munari ta Hada kayanta cikin karamar akwati kala Biyu da kayan barci Tunda basu san yaushe zasu dawo ba Inteesar tace su hada kayansu Waje daya Shiyasa suka Dauki akwatin kayan zuwa gidan su Mama su dauko na Inteesar su tsaya ta Shirya achan Tare da Umma suka Tafi zata leka yar"uwanta.
Suna zuwa gidan Abun mamaki suka Iske Sagir shima cikin Shirinsa na Tafiya basu Shiga mamaki ba sai da sukaji Mama na fada musu Imran ne ya Kira Sagir yace su Shirya su tafi Dukku Tare.
Umma dariya kawai tayi bata da tace akan Lamarin Imran ballatana Mama.
A gurguje Inteeesar ta Shirya Cikin Riga da Sikat na wata atamfarta Codedubuwa mai kalan Blue da Fari sai tayi amfani da bakar jaka da Takalmi da mayafi baki ta Dauko Kayanta itama kala Biyu da kayan baeci sai kananun kayan da zata Bukata suka Hada kayansu Waje Daya suna Shirin fitowa Daddy ya Kira Umma yace su dawo ana Jiransu.
Dole suka Fito da Sauri Sagir ya Tsaya Shagonsa yana sallama da yaransa,Su kuma suka tafi har da Mama data Yo musu Rakiya bakin kofar gida Tana ta addu"an Allah ya Kiyaye Hanya.
Koda suka iso duk suna Haraban gidan ne,kowa cikin Shirin Tafiya Bangaram su Ya Basheer su Inteesar suka karisa suka gaishesu kana suka karisa inda su Abba ke tsaye suka gaishesu suka amsa cikin Sakin Fuska.
Sannan suka juya suna gaida Mami Asma"u dake gefe tsaye tana Latsa wayarta tana kallon Mutane ta Cikin Siririn Gilashinta,Sama sama ta amsa musu ba wanda ya Damu da ita sanin Halinta.
Aka Fara saka kaya acikin Mota Yusuf yayi Riverse da Motarsa,zuwa Inda Abba ke Tsaye yaci Shadda Fara Tazarce yayi shar dashi,Sadam daman Da safe yaje gida ya Dauko musu kaya nashi dana Aneesa da yara dukkansu sun Dauki Uzuri a wajen aikinsu yau sai Dukku.
Awajen kowa ya hallara Imran ne kadai bai fito ba Abba ya yafito Yusuf da Hannu yana zuwa yace mai"Kira min Imran..!
Yataka kenan zai koma cikin Gidan sai ga Imran ya fito Sanye cikin Riga da Wando baki da Fari na kamfanin DKNY,wandon baki ne yadan kamasa ta kasa sai wani katon bakin Booth din Takakmi sai Farar rigaraa mai kauri mai gajeren hannu Tana da Rubutu baki agaban rigan an saka GENTLY.
kansa kuma yasha gyara Dadan nan ya Zauna Daram yana Sheki Fuskarsa ba Fara"a ko kadan kamar an aiko mai da sakon mutuwa Hannunsa sanye da agogon Fata,Bayansa Rataye da wata Jaka baka irin ta matafiya inda ya saka kayansa da Abunda zai bukata Tunda Umarnin Abba ne bai isa ya Taallake ba ammh
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment