Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Daya yana Lakuce mata yacw"Mrning How was ur Nite..?
Safiya tace"Lilsisy kin Tashi Lafiya..?
Munari tace"Lafiya Lau Anty Safiya..Ya yusuf Yanzu Abba ke Tambayanku..!
Yusuf yace"yanzu Wajensa Zamu Shiga..ya karya..?
Kai ta gyada mai kafin tace"Eh yau kunun Gyada nayi mana Sai na Soya Dankali..Yanzu na gama bashi yasha na bashi mgani Sauri nake tayi Yaya Zan Shiga makaranta 8am muke da Karatu..!.
Yusuf yace"Sannu da kokari..Bazaki jirani na Sauke ki ba..?
Agogon Fatan Dake Hannunta Ta Kallah Kafin tace"A"a Ya Yusuf bari na Tafi in na Tsaya jiranka Zan makara..!
Bai mata Musu ba ya Ciro 1k Cikin Aljihun Wandonsa ya Mikamata yana Fadin"Take Care..!
Ta karba Tana Fadin"Tanque Ya Yusuf..Anty Safiya Bye..!.Tafada Tana Daga mata Hannu,Hannun itama Safiyan ta Dagamata Tana Fadin"Sai kin Dawo ki kula da kanki..!
Mirmishi Tayi musu kafin ta Fice su kuma suka Shiga Dakin Abba suka Iskeshi yana Zaune kan gado yana Tunani Kasa suka Zauna suka Gaisheshi ya amsa yana Saka musu albakar.
Yusuf ya Kalli Abba yana Fadin"Ya karfin Jikin Abba..?Hope dai ba Wata Mtsala..!
Abba ya Girgizq kai kafin yace"Ina Samun Sauki..!.
Atare Shi da Safiya suka amsa da Allah ya kara Lafiya Kafin Yusuf ya Muskuta yana Fadama Abba Shawarwn da Safiya ta kawo Abba ya Dade kansa na Kasa kafin ya Dago ya Murmusa yana Fadin"Cikamakon Mutum Shine Samun Mace ta Gari...NAgode sosai yata..Kuma nayi Miki alkawarin Zan baki Kowani Hadin kai Domin Tamkar Munari nake kallonki..Sannan ni kaina Ina son na Warke Ko Domin na Koma ga Yan"uwana da Mahaifiyata..Itace araina Domin In har ina da Rai akwai Hakkinta Daya Rataya a Wuyana..!
Yusuf ya kalli Safiya itama ta Kallesa suka Gyada kai atare Kan Safiya na kasa Tace"Insha Allahu Zaka Samu Lafiya Kamar baka Taba wannan Laluran ba. !
Abba yace"Allah ya amsa..!.
Suka amsa da Ameen sun Dade Zaune Abba yana ta Tambayan Safiya matakin Karatunta Tana Fadamai sai ga Abba na Hirar Karatu da Safiya Data gayamai Fannin Data Karanta yake Fadamata abaya Daman yace in bai Zama Malami ba zai zama Masanin Na"ura ne .
Sai ga Yusuf Farinciki yaki barinsa Ransa Har sukayi ma Abba Sallama suka Fice,Su Biyu Suka yi Breakfast Saman Dining sunayi suna Hira Bayan Sun gama Safiya ta Rakashi Har Haraban gidan bata koma ba sai da Taga Fitar sa Daga Gidan kana ta Koma Cikin Gidan.
Dakin Barcinsu ta koma ta gyara Shi Tsaf kana ta koma ta Tatttara Abunda suka Bata Daga Dining zuwa Kitchen Tana ganin yanayin Kitchen din bai Wani Samun gyara Saboda Munari ce Ita kadai kuma Saboda makaranta Bata Samun Lokacin kanta Ballatana ta Tsabtace Kitchen din
Ga kwanukan Wanke wanke nan Kamar sun fi na kwana Biyu Munari bata samu Damar wankewa ba,Nan Safiya ta Zage ta wanke komai ta maidaahi a Muhallinsa,Ta kuma Share Kitchen din ta Gogeshi Tas ya Fara Kyalli,Ta leka Store Taga akwai komai na Bukatar Girki na Gidan Masu Rufin asiri Ta gyara Store din Shima ta Duba Fridge Shima Shake da Abubuwan amfani bata san Sadda tace Masha Allah ba Domin Komai akwai Babu Abunda kuma Zata Nema Yusuf bai waasa da Cefane Duk Sati,Tasio tamai mganar Cefanen sai Kuma Ta fasa Domin bata san yasan Zata Fara Girki yau din ta tabbata Zai Hanatane..
Bayan ta gama da Kitchen din ta Fito Falo Shima ta gyarashi ta Dauko Abun Shara ta Share ta goge ko"ina Haushinta Daya ko Dan Turaran Wuta Bata Dashi,Sai taji kamar Tayi kuka Sai kuma ta Daure,Ammh Zata Fadama Mommy Abubuwan Data keso Ta Siyamata in sunje da yusuf Sai Ta Taho Daahi kafin Abubuwa su Daidaita.
Daki ta koma ta Dauki Wayarta Da Niyar Kiran Mommy sai kuma Taga Kiranta sai Tabi Bayan kiran Har ta kusa Katsewa Kana Mommy ta Dauka Suka Gaisa Safiya tace"Mommy ina Falo ne na bar wayar a daki nazo Naga Kiran ki.. !
Mommy tace"Tasleem ce ta kiraki..Sai da na Hanata..Yanzu kuma Direba ya tafi kaita Makaranta..!
Safiya tace"Allah Sarki Tasleem..!
Mommy tace"Da kinga bazaki iya Zama ba Safiya ki kirani kinji ko Ni Dakaina Zan zo na Tafi Dake..!
Safiya tace"Bafa komai Mommy..!
Mommy ta Sauke Numfashi Tana Fadin"Shikenan nima yau Zan je gida na Gayama su Baba abunda ya Faru Bazqn iya Kyale Mahaifinku ba Safiya Kada ya ga yayi yaji Dadi ya maimaita akan Tasleem kuma..!
Safiya tayi Shuru kafin tace"Kiyi Hakuri Mommy..!
Mommy tace"Sai na Dauki mataki..Kiyi ma Shuru Kawai..ya mganar Kayan Daki da abubuwan Da kike so ki Rubutomin komai ta Waya ki Turomin Fatana ya Tanadi Muhallin da Zamu saka Miki kayan Duk ga yadda Auran ya kasance..!
Safiya sai ta Kasa cema Mommy Yusuf yace a barshi sai kawai tace Mata"Kibari nazo Mommy Zamu yi mgana..Domin yace in aka kwana Biyu Zamu zo mu Gaisheku..!
Mommy tace"Shikenan..!
Daga Haka sukayi Sallama
Daganan bata zauna ba ta Fita Zuwa Falo Bayan ta Duba Lokaci 9am ta kusa ya kamata ta Shiga ta Duba Abba koda ta Shiga Sai Taga baya Dakin Data Saurara sai taji karar Ruwa yana Wanka kenan sai ta Fito Falo Ta Zauna tana jira Shuru ita Kadai ga Tv ammh kuma da alamu ma ba"a Taba Hadata ba,Batayi mamaki ba ammh Zata Saka Yusuf ya Hadata Saboda Shima kallon yana Rage Damuwa ko da Tashar Wa"azi ce tafi a rika Zama Shuru.
Sai da ta Kwashe Minti Talatin Kana ta koma Dakin Abba ta iske shi tsaye yana Saka Botirin rigar Shaddar Dake Jikinsa Sai dai Bai saka Wandon Shaddar ba Wata ya saka yayi gamin Gambiza kenan.
Tana Shigowa da Sallama ya Waigo yana amsa mata Cikin Sakin Fuska.
Kanta na kasa Tace"Barka da Hutawa Abba..!
Abba yace"Yauwa yata..Sai dai Gidan Duk ba kowa sub barki ke kadai ko..? Sai Imurana Kuma Dashi ba Babu Duk Daya na Tabbata har yanzu bai fiti ba..!
Safiya tace"La bakomai Abba..Dama na Shigo na Dubaka ne..Nace ko Zaka Fito Falo yau ka Huta Kafin anjuma..!?
Abba ya Murmusa Kafin Yace"Nagode yata..Naji Dadin hakan ni kaina Nagaji da Zama Waje Daya muje..!
Kanta ta Sadda kasa kafin Tace"Amh..Abba Kayan ba iri Daya bane. !
Sai da ta Fada ya Duba ya ganu kai kawai ya Girgiza Kafin yace"Kinga ba Domin kin yi mgana ban Ma Lura ba..!
Bata Damu ba tace"Bakomai Abba...In ba Damuwa bari na Duba maka wandon Rigar ko..!
Yace"Yauwa to Dubomin ni Duk idona ma ya Cinye Saboda Rashin Ganin Hasken Waje..!
Tana Bude Wardrope din Tace"Zai Washe Da yardan Allah Abba..!
Cikin Farimciki yace Allah, yasa bata Wahala ba ta gano Wando ta Daukomai ya karba Sai ita kuma ta Fice Bayan ta Daukan mai Matashi,Falo ta koma ta Sakamai Matashin Saman kujera mai Cin Mutum Biyu,ta Shiga Kitchen ta Daukomai Ruwa da Kofi tazo ta Jawo Karamin Table zuwa gaban Kujera Ta rasa Ma Zata Dauko ma Abba ya Daukemai Hankali Sai ta Tuna Taga karamin Qur"ani acikin Dirowar Yuauf da Sauri taje ta Dauko Ta yanke Shawaran Zata kira Yusuf yazo da Jaridun Datayimai mgana Jiya.
Tana Fitowa Abba Shima na Fitowa Mirmishi yayi mata itama ta maidamai Yau Rana Daya yana jin kansa Kamar bashi ba,Bai Taba Fitowa ya Zauna afalon nan ba Tun Dawowarsu Gidan koda yaushe yana Cikin Daki in baya kwance yana Zaune yana Tunani.
Sai da ya Zauna kana ya Rika sakama Safiya albarka tana amsawa ta Tsiyayamai Ruwa ta mikamai yasha Kadan ya Miko mata Tana Karba Tana Fadim"Abba badai kajin Barci ko..?
Abba yace"Gaskiya yau ban ji Barci ba..Ko Saboda na baro Katifar Dake Rinjayana Barcin ne..?
Ya karishe Cikin Zolaya Kanta ta Sunkuyar Tana Mirmishi sai ta Mikamai karamin Qur"anin Tana Fadin"Kada ka Zauna Shuru Abba..Saboda Tunani marasa kyau..Ka karanta iya Abunda ya Sauwaka Zan kira Yusuf nacemai ya Taho Maka da Jaridu ka Rika karantawa kana Sanin Abunda Duniya take ciki..!
Abba ya saka Hannu Biyu ya karba Hawaye sun kawo Idanuwansa yace"Barkallahu Fiki..Nagode..!
Yafada yana jin Rauni ya bayyanamai Domin bazai iya Tuna Ranar Karshe Daya yi Karatu ba Lalle Mace agida Shine gida Matukar Bata kuwa sai a Hankali.
Gefw ta koma ta Zauna akasan Cafet Abba yayi ta koma Kujera Taki sai ya Kyaleta Bude Qur"anin yayi ya Faraa Dubawa,Duk da Raunin Idanuwansa sukayi Qur"ani na Dabam ne,Ballatana ai yana da Hadda akansa nan da nan ya Bude Suratul Yusuf ya Fara Karantawa a Hankali Safiya na gefe Tana Kallonsa Cikin Tsausayi ganin Lokaci Bayan Lokaci yana Share Kwallar da suke Cikamai ido..

Acikin Wannan Halin Imran ya Fito Daga Dakinsa Sanye da Jallabiya baka,daga alamu kuma Tashinsa keman Sigarin sa ne ya kare,Sannan kuma Dole yaga Sagir Domin yagayamai Yar gidan Wacece Wannan Mara Mutumcin yarinyar,Sai kuma Fitowarsa yaci karo da Abun mamaki Abba ne Zaune afalo yana Karatu.?
Gani yayi kamqr bai gani Daidai ba Sau ya kara Matsowa yana Mutsike Idanuwansa Still Dai Abu Daya yake gani Safiya ce ta Ganshi Da Sauri Tace"Ina kwana..!
Sai alokacin ya ganta Kallo Daya yayi nata ya kauda kai Shi ai bacin Ran Daya Kwana Daahi Jiya yasa yama manta da Yusuf da wata Amaryansa ma,asaman Lebensa ya amsa mata da Lafiya lau,Kusa da Abba ya Karisa ya Zauna yana kallonsa ganin haka yasa Abba ya Dakata da Karatun ya Dago yana Kallonsa Imran Cikin Mamaki yace"Abba ...Abba Kai ne..!?
Abba ya Murmusa kafin yace"Na"am..Nine Imran..!
Yafada Lokaci Daya yana Dafa Kafadansa Saboda Murna Imran baisa Sadda ya Rumgumesa ba yana Fadin"Plz Abba..Come Back..We Need Dr.Abubukar Malami Back..Wanda Ke Tsaye Ga kafafunsa Saboda Ahalinsa  ba Abubakar Malami ba Wanda Ya koma Yusud da Imran ne masu Kula Dashi ba..!
Abba ya Murmusa kafin ya Buga Bayan Imran alamun Lallashi Lokaci Daya ya Dagosa yana Fadin"Insha Allahu..komai Zai Zama Tarihi Tunda My Son yayi Dacen Samun Mace Tagari..ita tace na Fito Falo na Huta ta kuma Bani Qur"ani tace nayi Karatu..!
Abba ya Fada yana Nuna Safiya da kanta ke kasa..!
Imran ya murmusa kafin ya Mike yana Fadin"She do alot to us..Tanque so Much..!
Batace komai ba sai ta murmusa aranta Tana Tuna Hirarsu da Munari.
Abba ya kallah Kafin yace"Abba ka Cigaba da Karatunka..Bari na Je nan kasa Wajen Sagir..!
Abba ya gyada kai kafin yace"Sannan kuma Zaka Siyo Sigari ko..!?
Imran ya Waigo yana kallon Abba Kamar bazai ce komai ba sai kuma yace"Eh Abba..Ammh Zan yi kokarin na Rage shanta Saboda kai..!
Abba ya girgiza kai yace"Imran...Imran To Nagode..!
Bai kara mgana ba ya sakai ya Fice Daga Safiya Har Abba suka Bisa da kallo Abba yana kallota yana Fadin"Ni na Haifeshi ammh Wani Lokacin yana Matukar min kwarjini..Rashin Tsoronsa da Gaskiyansa Wani Lokacin Suna kara Sakani naji yana Burgeni da shiga raina..!
Safiya Batayi mamaki ba Tunda Munari ta gayamata Yusuf ma ya mata Bayani Abba bai nemi Jin ta bakinta ba yace"Allah ka kara Shiryamin ya"yana..!
Safiya ta amsa da Ameen acikin Ranta Shi kuma Abba ya Cigaba da Karatunsa Yana jin Wata Natsuwa na Shigarsa Natsuwarsa da Tun Bayan Rasuwar su Anni bai kara Samun irinta ba sai yau.



*Ina godiya Masoyana da Tarin kaunarku ga wannan Labarin Allah ya saka da alheri WhatApps fans dina Duka ina ganin Sharhinku ina kuma Godiya sai yan Wattpadian Kuma ina ganin Voting dinku da Comments dinku ina Matukar godiya Allah ya saka da alheri Allah kuma ya bar Zumunci Ameen..*





*Shakira...*
3/22/22, 23:04 - Ummi Tandama😇: *GIDAN MU..!*
_(Our House)_
*Book 1*

*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janafty❤️*



           *🅿?15*

"Da kafarsa ya gangara zuwa Gidansu Sagir din Bai tsaya ma Daukan Mashin Din nashi ba domin kwana Biyu yafi jin dadin Tafiya da kafarsa fiye da ko yaushe,kwana Biyu bai Fita Jogging ba yana jin Jikinsa wani iri Shiyasa yake Treeking da kafarsa Wani Lokacin.
Sai da yazo Kofar gidansu Sagir din yaja ya tsaya,Kuma ya leka Shagon ya Hangi Sagir kan keke yana ta Dinki Hankalinsa na kan Abunda yake yi,Bai ma Lura Da masu Shigowa da masu fita ba yau Dagashi sai Yaronsa Daya Sauran basu Riga sun zo ba shine ma yaga Lekowan Imran din ganin ya koma Shiyasa baima Sagir din mgana ba.
Waya Imran ya Lalubo Cikin Aljihun Jallabiyansa ya Lalubo Lambar Sagir ya Dokamai kira yana Tsaka Da Dinki Wayarsa Dake ajiye gefensa ta Dauki Neman agaji Ta Wutsiyar ido ya Juya yaga mai kiran Imran ne bai Daga ba Sai da yakai karshen Inda ya Fara Dinkawa kana ya dakata ya Daga Kiran Yana Fadin"Ya akayi ne..?
Imran Dake waje yace"Bansani ba..Mallam ka Fito gani a Kofar Shagon ka..!
Sagir ya Dakuna Fuska kamar Imran na Ganinsa yace"To kai meye ya Hanaka Shigowa..? Ka Shigo mana Ina Dinki ne ba Zaune nake ba kamar kai..!
Imran yace"Ban ga Daman Shigowa bane..Kuma Dake min Gorin Zaman banza Ka samo min aikin yin ne kaga nace bazan yi ba..?
Sagir Dayaji Haka ya Mike yana Fadin"Ta kwana Gidan Sauki Indai aiki ne Ina dashi..Bari na Fito..!
Yafada Lokaci daya yana Katse Kiran Yaronsa yayi ma mgana kafin ya Fita ya Iske Imran din Tsaye ya Tusa Duka Hannayensa Cikin Aljihun Jallabiyansa
Yana Jiransa yayi mamakin ganinsa yau baya Busa Hayaki Shiyasa yana Zuwa yace"yau Watarana Abokina yazo baya Shan Sigari..?
Imran ya kallesa kamar bazai yi mgana ba sai Chan yace"Zan Busata kuwa..Ta karemin ne jiya Cikin Dare..Yanzu kafin na Shiga Gida Zan Siya..!
Sagir ya kada kai kafin yace"Don Allah Ka Daina Shan Sigari..Wlh Sam Shanta bai Dace Dakai ba ko alama..!.
Batare Daya Kallesa ba yace"Daman masu Shanta din ta Dace dasu ne..?
Sagir yace"Eh gsakiya Majority din masu Shanta Zaka ga sun Dace da Shanta Din ammh kai Fa kalleka Daga Sama Har kasa Duk da bansan komai akan ka ba na Tabbata kayi Ilimi mai Zurfi Tundaga na Zamani har na Boko Wanda bai ma Zauna Dakai ba Zai Fahimci U are a Luky Ballatana ni da na sanka Gaskiya Shan Sigari bata Dace Dakai ba Abokina Don Allah ka Daina Shanta Sam bana jin Dadi..Kalli bakin ka Har ya Fara Baki..!
Imran yayi Shuru yana kallon Sagir Allah Sarki zai Rage shan Sigari ko Domin Abba da Sagir sun Damu Dashi kwarai Kuma Shi Mutun ne Da baya Juyama masu kaunarsa Baya Kota Halin Kaka sai ya Rama musu Alherinsu gareshi..!
Ganin yayi Shuru yasa Sagir ya Dafa Kafadarsa yana Fadin'Kayi hakuri in mgana ta bata maka rai..Ina son Naga rayuwarka Ta Dawo Tamkar yadda kowa ke Rayuwa ne..Am sorry..!
Imran ya Saki Mirmishinsa kafin yace"Bakamin komai ba..Zan yi kokari na Rage shanta ko Saboda kai da Abba..Ku din wasu Mutane ne masu Muhimmanci a Rayuwata bazan bari Rashin jina da Taurin kai na ya Bata Muku Rai ba..Ammh kasan sai a Hankali..Kamar yadda na Koyi Shanta Rana Tsaka Haka zan zo Rana Tsaka Kaga na Daina Shanta kwakwata..!.
Cikin Farinciki Sagir yace"kai naji Dadi..Allah ya amsa..Ammh wai a ina ka Koyi iya Shanta ne..? Kwarewarka fa yasa na Fara Tunanin Any ba Kwalejin masu Shan Sigarin ka Shiga ka Samu Kwarewa ba..?
Wannan karan Sai da Fararan Hakoransa suka Bayyana Saboda Dariya Wanda ba kasafai ake ganinsu ba Dukan Kafadan Sagir yayi yana Fadin"Ashe kai Dan iska ne..?
Sagir na Dariya yace"Yaushe na Tashi Daga Banzan..?
Imran yace"Duka kai ne...ga ka Banza ga ka D'an Iska Daman ai Telan Mata ai Dan iska ne..!
Sagir ya Harareshi yace"Haka Dai Kace..Miya Hada Telan mata da Iskanci..!
Imran yace"Baka na Gwadasu ba..Ranar fa ina ganinka Kasa Abun gwajinka kana gwada wata yarinya..!
Ya karishe Fada Cikin Zolaya Lokaci Daya kuma Fadin yarinyar Dayayi sai ya Tuna da Abunda ya kawosa nan da nan ya Hade rai Shi Sagir bai ma Lura ba Dariya ya Kwashe Dashi yana Fadin"Ashe Shurun Shurun nan naka Mugun Dan saka ido ne kai a Fakaice..Wlh bana Gwada kowacce Mace sai dai ki kawo Measurement dinki,Wacce kaganta Yaro na ne yake Gwadata bani ba ta mtsa sai an gwadata ne ammh Ni kowa ya sani bana Gwada mace Saboda Kiyaye Addini da Mutumcina..!
Imran bai cemai komai ganin haka yasa ya Dagi kafadansa yana Fadin"Yauwa kace na sama maka aiki ko..?
Kai Tsaye Imran Daya Kagara mganar ta Kare yace"Eh..!
Sagir yaji Dadi nan da nan yace"To kazo na samar maka aikin yi..Kazo zan Koyamaka Daukan Measurement Din Duk Macen Data Dake son sai an Gwadata ga Measurement Imran nan bata da Damuwa..!
Wani Kallo ya Jefama Sagir kafin yace"Kutumar Uba ne..Wlh nafi karfin Wata mace ta Tsaya na gwadata..Baka Tashi bani aikin ba indai hakane..!
Sagir na Dariya yace"Da gaske kake kenan..?
To kazo Gobe sai muga da Abunda Zamu Fara Ni dai kaga Wajen Sana"ata Dinki ne kuma Alhamdulillah Dashi Nake Rufama Kaina asiri Da Mama..!
Imran ya Kada kai kafin"Dakyau..!
Sagir ya Bude baki zai yi mgana kenan Imran yace"Who is She..?
Sagir yaji kamar bai jisa ba Cikin mamaki yace"She naji kace..wa..?ita wacce Zaka fara gwajin a kanta..!?
Karamin Tsaki Imran Yaja kafin yace"Kai fa Banza ne..Wannan Yarinyar ta Jiya Data Kalleni ta Kiramin Tsarin Shedan sannan ta Toshemin Hanci ta Tofar da Miyau Don Ubanta Wari nake ko kuwa Tsabar Raini ne ko Wulakanci..!?
Sagir daya Manta da Abunda ya Faru Tsakaninsu da Inteesar Jiya sai yanzu da Imran din ya Tunamai gabansa ya Fadi Cikin Mamaki yace"Wai Daman baka manta ba..?
Imran ya kara Hade Ransa yana Fadin"Ta ina Zan manta..? Aini bana manta Cin fuska ko Raini..Ni Imran ba Wanda mace Karama irin wannan yarinyar Zata Raina bane..Ka Fadamin Wata Mara Mutumcin ce So nake na Koyamata Hankali in ta Takamarta Rashin kunya Nine Zan Gyara mata Zama..!Kila Cikin yan iskan matan nan ne masu Zuwa kawo Maka Dinki ko..?
Sagir Yayi Saurin Cewa"A"a Wlh..Don Allah kayi Hakuri Bata sani bane..Kuma Bata san Warin Sigari ne baka gani ba..Wlh sai da Tayi amai fa..!
Shekeke Imran yake kallonsa kafin yace"Oh Daman Duk kana Sane da Abunda ya Faru kenan..?
Sagir yace"Eh Nidai Sorry on Behalf on Her..Kanwatace fa..Diyar kanwar Mama ce Inna Salaha ta Kaduna Shekaranjiya iyayenta suka Kawota Wajen Mama suka Damka Amanarta awajenta Karatu Ta Fara nan Jami"ar Bayero.!
Kamar Imran bazai yi mgana ba sai Chan yace"Naji Dadin cewa ma kanwarka Ce..Zan fi Cimata Mutumci Dakyau..Ai ni Yayanta don Ubanta Kuma ka Fadamata Kada ta yarda mu Hadu Duk Ranar da muka Hadu sai na Toshe Bakinta na Dura mata Hayakin Sigarin sai na Tabbatar Daya Shiga Cikinta,In Aman kayan Cikinta Zatayi Sai dai Tayi..Hukuncin Toshe Hanci Agaban Imran kenan..!
Yana Gama Fadin haka ya Wuce ya Fara Tafiya Cikin Sassafarsa Na koda Yaushe Sagir ya saki baki yana Kallonsa Kafin ya Sauke Numfashi yana Fadin"Inteesar Ta Taro ma kanta Macth bata da yan wasa..Kayyasa..!
Daga haka ya juya ya koma Cikin Shagosa ya Tuna Yadda Imran ya Tsani yana Shan Sigari a toshemai Hanci ko Dashi ne sai sun Hau Sama sun Fado Koma miye bazai bari ma Su Kara Haduwa da Inteesar ba yasan Halin Imran bai da Mantuwa Akan Abunda akayimai.
Koda Imran ya koma Gida ya Iske Abba ya Gama Karatun Qur"anin suna ta Hira da Safiya kamar sun Shekara da Haduwa yana ta Bata Labarin Yanayin Jami"ar Lagos da yanayin Karatunsa Dayake suna Hira ne kan Jami"o"i
Bai ce musu komai ba ya Shige Dakinsa Ammh Tabbas yana Cikin Farimcikin ganin Abba ahaka kan gado ya zauna afili yana Fadin"Abba ba Mahaukaci bane..Abba da Hankalinsa Baffa Kabiru..!
Yafada Lokaci Daya yanajin Suyan Tuna Wasu kalaman da akan Jefe Abbansu dashi na kalmar Mahaukaci.
Wanka ya Shiga bayan ya Fito ya Shafamai Ya saka wani karamin Wando bai ko Saka riga ba,Ya Hau gado yan jin Zuciyarsa Ta Danyi Sanyi Tunda yabama Sagir Sako ya Tabbata kuma Zai gargadeta Bai damu da yadda suke ba Shi Raini ne baya so kuma Ko Munari ce tamai Haukan nan Sai ta gane bata da wayau ballatana Wata Chan Dabam
Yayi alkawarin sai  ya koyamata Hankali,Ya gama Lura Rashin kunya ce da Iyayi na yaran da suka Shiga Jami"a ba Bayero take ba Ko Duka Jami"ar Duniyace akanta Tunda ta Shiga Gonarsa He will Teach Her a Lesson a Big lesson din da Bazata manta ba.
Saboda bacin rai ma yasa ya manta bai Siyo sigarin sa ba Tsaki kuwa yajasa yafi a kirga saboda Haushi.

Safiya kuwa suna Cikin Hira da Abba Barci ya kwasheshi sai ta Kyaleshi ya Huta Daman barcin yana da kyau Sai ta Fada Kitchen taga Abunda Zata Dafa ta iske Nikakken kayan Miya a Cikin Fridge sai ta Dauko tace bari Tayi White rice da Miyar Kaza Tunda Taga akwai kazan Har da Ganyen Kabeji,nan da nan ta kunna Gas Din Duka Guda Biyu ta Dauko Tukunyar ta Fara aiki Cikin Natsuwa da Kwarewa aranta Tana Sakama Mommy Albarka Data Koyamata Aikim mata da yau Da aure ya kawota Wannan Ahalin da suke Bukatar Taimakonta bata san yadda Zatayi ba.
Tana Cikin Aikin ne Taji Abba na kiranta da Sauri ta Dauraye Hannayenta ta Fito Tana amsawa Abba ya Kalleta Lokacin Daya mike Zaune yana Fadin"Barci ne ashe ya Kwasheni.?
Safiya tace"Eh Abba..Nace ai gwara ka Huta Saboda mgungunka ne Akwai na Barci..!
Abba ya kalleta kafin yace"Badai wani aikin kike ba Daugther...?
Safiya ta Dukar Dakai tana Fadin"Ba wani aiki bane Abba abiincin da Za"aci nake Dafawa Munari taje makaranta In ta Dawo ta gaji kuma Ai Zaka ta zama da yunwa ne kai da kake Shan mgunguna..!
Abba ya Girgiza kai yana Fadin"A"a gaskiya Dana sani bazan bari kiyi wani aiki ba..Jiya fa aka kawoki gida nan..Sam bai kamata ba Da baki Damu Dani ba ko Tea sai ki bani nasha..Nasan yusuf bazai shigo hakanan ba..!
Mirmishi kawai tayi tace"Bakomai Abba..Miye amfanina na..? Indai ka Daukeni Tamkar Munari to ka samun Albaeka kawai..!
Cikin kada kai yace"Shikenan Daugther Allah yayi miki Albarka Allah ya jikanki Kamar yadda kike jin kaina..!
Cike da Farinciiki ta amsa da Ameen Kafin tace"Bari na koma na karisa Abba..!
Ya amsa mata da To shikenan afito Lafiya,Cikin Sauri ta koma ta Cigaba da aikinta Cikin Kwarewa.
Cikin Lokaci ta kamallah Daidai Lokacin Dataji ana ta kiran Sallar Azahar Aranta ta kudiri Niyyar Dawo da Farincikin wannan Ahalin,Ta Lura Daga Yusuf din Har Imran din ba wanda ke Zuwa Masallaci Bin Jam"i,Da sun Shigo Shikenan Ballatana su Rika Tafiya da Abba Gaskiya Hakan bai kamata ba,Suna Musulmai Ya zama Wajibi su Rika Sallar Cikin Jam"i Zata Gayama Yusuf Gasikiya su gyara Sallarsu.
Sai da ta kamallah komai ta Juye komai a Flask,ta yanka Ganyen sai dai Bata Hada ba ta bari sai Zuwa anjuma,bata bar Kitchen din ba sai da Ta Goge komai sai Ta Fito Taga Abba Baya Falo Kila ya Shiga Ciki yayi alwala ne itama sai ta Shiga Daki ta Fada Tiolet Tayi wanka Saboda Girkin Datayi Tazo ta Sauya kaya Dole zata gayama Mommy A hada mata kayanta Waje Daya in sukaje ita da Yusuf Zata Taho da Abunta wata Doguwar Riga ta Samu ta saka Kirar Armani ta Saka Mayafinta Ta Tada Sallah Tana Cikin Sallar ne taji Abba na Knooking Din Kofa Lokaci Daya yana Kiran sunan Imran Tanaji yazo ya Bude Abba na Mgana bataji me yake Fade ba sai taji Abba na Buga mata Kofa Lokacin ta Sallame sai tazo ta Bude Abba ta Gani Harda Hulansa da Casbaha yayi mata Mirmishi yana Fadin"Daugther na taso Imran nace ya Rakani Massalaci Shima mu Fara Salla Cikin Jam"i Kamar yadda kikace..!
Safiya ta Fadada Mirmishinta kafin Tace"Ka kyauta Abba..Adawo Lafiya..!
Tafada Tana Hangen Imran Din Daya Sanya Wata riga sai dai ya Sauya Wando Dogo ya Sanyo karo na Farko da Abba zai Fita da Kafarsa Tun Bayan Dawowaarsu kano gwarama Imran yana Tsayawa masallacin kusa da Gidansu Sagir yayi Sallah in dai yana Waje in ya Shigo kuma Shikenan Ammh yau da Abba ya Bukaci Haka sai yaji Shima Zakwadin Abun Acikin Ransa ya kuma Kuduri Niyyar Daga yau Dagashi Har Abba da Yusuf indai suna Gida Masallacin Kusa da Gidan su Sagir zasu Rika zuwa Sallah acikon Ransa yana Kara Taya Yusuf Murna Na Samun mace irin Safiya aransa yana Ayyana Bata Dauko halin Tsohon najadun uban ta ba.
Har suka Fice Bakin Safiya yaki rufuwa Waya ta Dauka zata Kira Yusuf Saima taga Kiransa Da yawa ya Kirata Kila Tana Kitchen ne,Nan da nan tabi bayan kiran sai dai bai Daga ba sai ta kyakeshi sai Zuwa Chan ya Kirata ta Daga Cikin Farinciki yana ma Tambayanta ina ta Shigene ita kuma Saboda Murna tana Fadamai Abba yau ya Fita masallaci Shi da Imran Yusuf Yana Office dinsa kenan Shima Dawowarsa Daga masallacin Ma"aikatansu kenan yakai goshinsa kasa yana Jeromaa Allah Godiya Farinciki Sai da yayi kwallah yama kasa Mgana Cikin Muryan Sanyi da Farinciki yake Fadin"Tanque...Tanque so Much Babe na..Allah yayi miki albarka Shigowarki Gidanmu Haske ne..Daga yau kin tashi Daga Babe na kin Koma Noor!
Cikin jin Dadi tace"Nagode My Dear..In zaka Dawo ka Taho da Jaridun da Littafan da mukayi mgana..!
Yace"Insha Allahu..Mai zan Taho Miki Dashi..?
Da Sauri tace"Bana Bukatar komai Illah Son ganin ka Dawo Cikin Koshin Lafiya..!
Cikin Annuri
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment