Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

sakamai albarka Mami Asma"u sai Hararansa take gani take duk wannan abubuwan Dayake yi na Munafunci ne,Ta kalli mijinta Dayayi Shuru bai ce komai ba ita hakan yayi mata Daidai Kada ya ce komai Suje su karata,Gabadaya zuwansu Dukku ba Alheri bane a wajenta Gabadaya Ranta yana bace ne,Allah Allah take Su bar Dukku kamar tana kan kaya.
Daada bata yarda Taron nan ya Watse ba sai da Ta Saka Khamis da Imran suka Nemi yafiyan juna Bayan tayi ma Imran Fadan Kai ma Khamis hannu Da yayi har suka Fara kokawa ta saka Sunyi musabaha da junansu Azuciyar khamis yaji komai ya wuce ammh banda Imran Da abun ke cikin Ransa.
Koda Taron ya tashi Zuciyar kowa ba Dadi,Inteesar da su munari suka Kule Cikin Dakin duk Tambayan duniyan nan sunyi ma Inteesar taki yadda ta Fada musu komai Dole suka kyaleta.
Mami Asma"u kuwa ita da ya"yanta Tayi ta ma Khamis Fada kamar ta Dakesa sai da Baffa Kabiru ya tsawarta mata kana tyi shuru Sajida na gefe ita da Umaima Mami Asma"u ta Umarce su da su hada kayansu gobe da Sassafe zasu Dauki Hanyar Abuja
Har garin Allah ya waye Zuciyiyon kowa ba Dadi suna ta shirin komawa Inda suka Fito,Mami Asma"u da ya"yanta kamar suna kan kaya ko Breakafsat bata yarda sun Tsaya sunyi ba Ta mtsama Baffa Kabiru yayi sallama da Daada da Sauran yan"uwansa suka mika Hanya ko Sajida da Daada tace ta bari su gana da Imran bata bari ba ta Tarata suka Shige Mota sai da suka bar Dukku Taji ta Samu natsuwa kadan.
Daga Su Mami Asma"u Sai Inna Maimunatu ita da ya"yanta suka Wuce Bauchi,Sai Hamidan Inna Bintalo itama ta wuce katsina Sai Sa"id mutanen Dutse suma suka Dauki Hanya da Hafsah da suka yi kamar suyi kuka ita da Munari da inteesar Su Abba ne kusan karshen Tafiya Domin sai da Daddy daya Basheer da Umma suka mika bayan sun bar musu Inteesar zasu koma kano da ita saboda makaranta.
Suna wucewa suma sukayi Shirin Tafiya Imran dai Tun Abunda ya Faru jiya bai kara ma kowa mgana ba kamar Wanda aka Dinkemai baki Sagir har gaya gaji damai mgana ya kyalesa Kowa yayi sallama da yan"uwa banda shi,Ko Daada bai ma Sallama ba gani yake duk itace ta jamai wannan Bacin rai baima son ganinta Haraban gidan ya Fita yana Rataye da Jakarsa yana cika yana batsewa.
Abba tare da Sadam Zasu mika Tunda duka kano zasu nufa,Sadam da Imran Dake gefensa agaba Matarsa Aneesa da ya"yansu Waleed da Waleeda sai Sagir suka Fara Mikawa sai Yusuf Dake driving Abba na Gidan gaba,Sai Munari da Inteesar da Anty Safiya Dake gidan baya Imran yana ganinsu yace bazai shiga Motar ba ya gwammace ya shiga ta Sadam ba ya son ya Zauna kusa da Inteeaar Baya son ganin kwanyan idanuwanta kallonta kadai kasala yake sakamar so yake yayi yaki da koma meke Damunsa bazai bari a Fahimci Rauninsa ba.
Su Imran su suka fara yin gaba kuma sun Riga su Abba isa kano,Har Gida Sadam yakai sa har sai da yadan Jira su Abba suka kariso kana sukayi sallama ya kama Hanyar gidansa Dauke da matarsa da ya"yansa.
Tuni imran ya shige Cikin Gida ya Fada Dakinsa ya maida koda Sagir bai shiga ba Daganan yayi ma su Abba Sallama ya wuce gida Domin ya Shaida Mama, Dawowarsu Inteesar bata Bisa ba Tunda itama yanzu Gidan su Munari kamar gidansu yake Munari tabi Zuwa Dakinta gabadayansu duk sun gaji ammh Inteesar Rabin Hankakinta na kan Imran Data gansa wani iri Har Sako ta Turamai kuma yagani bai bata amsa ba gabanta Fadi yake tana Fatan Allah yasa Fushin Khamis bai shafe ta ba.
Sai da sukayi wanka suka yi salla suka Huta kana munari da Inteesar suka shiga suka sama musi Abunda zasu ci.
Zuwa Dare kuma Kowa ya isa Gidansa Lafiya.
Ta wayar Yusuf Abba ya Kira Baffa Kabiru da Daddy yayi musu ban gajiya Harda Inna Maimunatu itama ta isa gida Lafiya Inna Bintalo Tana Dukku sai gobe zata koma ita.
Daddy da Abba sun Dade suna Tattaunawa kan Tafiya Lagos Sati mai Zuwa da yardan Allah Rayuwa Zata Inganta Ranar da Daddare Mama Sagir ya Rakota tazo ma Abba Murna da ban gajiya,Taga kowa banda Imran wanda tunda ya shiga Dakinsa bai Fito ba ko Sallah aciki yayi abunsa Da Mama Zata tafi ta Dunga ma Inteesar tsiyan Taga Gidan Abbanta Ta gujeta Inteesar na Dariya tace gobe Zata dawo Munari ta Daka Tsalle tace kafarta kafarta Abba yace ko"ina suka zauna Duka Gida ne shi bai da mtsala.
Washegari da Safe Yusuf ya Tafi aiki Munari da Inteesar suka shiga makaranta saboda ana ta Karatu an Wucesu Safiya kadai ce agida Tana aiki sai Abba Imran na Daki sau Daya ya Fito da Safe ya Hada Tea yasha yagaida Abba ya Dauki Ruwa ya koma Cikin Daki.
Da wuri Yusuf ya Dawo Daga Wajen aiki ya Siyoma Abba Sabuwar waya Saboda ya fara amfani da ita Abba yaji Dadi ya Dinga sakama Yusuf albarka suma su Munari sai yammah suka Dawo Daganan wajen Mama suka Sauka Munari ta Kira Ya Yusuf ta Fadamai yace bakomai.










*Janafty*
3/22/22, 23:14 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�9*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*


*After 1 week*
Kimanin Sati Daya kenan da zuwansu Dukku,Imran har zuwa wannan Lokacin bai warware ba Ya daina ma kowa mgana Abba ne kadai daya zama Dolensa yake Fitowa ya gaishesa da Safe,duk da kowa ya sanshi da Rashin son shiga jama"a ammh wannan karon abun nashi ya Taba zuciyar wadanda ke tare dashi,ganin ko Masallaci ya daina zuwa na kusa da Gidan su Sagir sai ya koma zuwa wani karamin masallaci na chan gaban gidansu Tunda suka Dawo Daga Dukku ba wanda yaji kalma Daya Daga Bakinsa bayan gaisuwa.
Abun ya damu Yusuf har sai da yayi ma Abba mgana Domin har ga Allah shima yaga baiken Daada akan wannan Hadin a yadda Imran yake Gudanar da Rayuwarsa auran Hadi bai Dace dashi ba kuma bai Chanchanta dashi ba.
Kamata yayi ya samu wacce yake so tana sonsa ahakan Za"a samu Riba kan Riban abunda ake nema ammh a yanzu da kunci ya kara Dabaibaye Rayuwarsa zai iya koma Fiye ma Imran din da suka sani abaya,Shan Taba kila Har ya Fara kora wasu kayan Mayen in ya Damuwa tayimai yawa Har acikin Ransa bai da yadda Zai yi ne ammh Tabbas Hadin nan na Daada ko alama bai kwantamai ba Duk da Sajidan bata da wani aibu sai dai A kallo Daya da yayi mata yasan bazata iya Zama da Imran ba bata dace dashi ba.
Abba Dayaji bayanan Yusuf shi kanshi ya gamsu kuma Daman yana Cikin Damuwar haka din ne sai dai bai bari Yusuf din ya Fahimceshi ba Sai ya nunamai ya kyalesa babu Abunda zai faru dashi Fushi yake na wani Lokaci in Abun ya sakesa zai Wartsake,Ya nuna ma Yusuf kada ya sake ya Tari Imran da wata mgana Saboda bayaso kuma abubuwa su Dawo baya Yasan Halin Imran ciki da Waje shi ya Haifesa ya kuma Tabbata shine kadai weekness din Imran in ba shi ba bai ga wanda ya isa ya Rika Lamkwasasa yadda yaga Dama ba Shi kanshi yana jin Tsausayinsa sai dai Abun nan da Hausawa kan Fadi kaki naka Duniya tasoshi hakan da yake yi Shine Daidai in Imran ya gane yana Tsausayinshi to zai yi amfani da wannam Damar yayi abunda yake so Shi kuma bazai barsa ba Yana da Sanyin Hali yana son Mahaifiyarsa da ya kwashe Fin shekaru uku bai sata a ido ba karon Farko bayan sun Hadu ta bada Unarni kan Abunda ya Haifa bai isa ya Taka wannan Umarnin ba ko shi baya Taka Umarnin Daada ballatana Abunda ya Haifa Shiyasa Daga shi Har yusuf suka Zura Mai ido Bawanda yace mai kala kamar yadda Shima bai damu yace dasu wani abu ba..
Ammh acikin Ransu suna Fata damai addu"an Allah ya sassautamai koma Miye ke Damunsa acikin Zuciyarsa.
Bayan Abba da Ya yusuf Inteesar ma tana Cikin Damuwa wannan yanayin da Imran ke Ciki Tunda suka Dawo bai kara yarda sun hadu ba Tayi ta Turamai sako zai gani zai karanta bazai bata amsa ba,Datagaji sai ta Fara Kiransa nan ma sai ta gaji da Ringing bazai dauka ba Daga karshe sai ya Kashe wayarsa Inteesar ta shiga Damuwa sosai na Rashin Sanin Halin Dayake ciki ga Karatun makaranta yayi Zafi sai ta fara Rama atsaye gata Daman ba wani kauri ba,Duk yadda taso su hadu hakan bai samu ba Zasu kwana su Wuni acikin Gidan nan ko Gilmawarsa bata isa ta gani ba Tunda suna Raba Raba ne,Yau su kwana a nan gidan Gobe gidan Mama saboda ta Saba da Inteesar tafiyarta zai saka ta ji Kadaici ya Dameta shiyasa suke Raba Raba ita da Munari da suka kara Shakuwa kamar wasu yan Biyu Daya bai iya Boyema Daya abu sai dai Inteesar ta Boyena Munari Damuwarta kan Imran ko dataga Tana ta Ramewa Data mata mgana sai ta ce saboda Stress din Karatu ne.
Inteesar Zuciyarta Zafi take tana da Raunin Data kasa Daukan Lamarin Imran yana bata Wahala batare data san Dalili ba Zuciyarta na Zafi Wani Lokaci Jikinta ya Dauki Dumi Zata iya Jure komai banda Fushin Imran Dafi ne gareta Ta zauna Tayi ta kuka ita Kadai in abun ya Dameta sai kuma Daga baya tayi wani Tunanin Kila ya Daina kula tane saboda Sajida yayi auransa me zai yi da ita yanzu..? Inteesar batasan Soyayya ba Domin bata taba yi ba ballatana ta gane itace ta mata Mugun kamu sannan bata karance karance Social median ma Bata wani Dameta ba,shiyasa ta gaza Fahimtar wani Hali take Ciki kamar yadda Ego din Imran yaki bari ya Fahimci Inteesar ta gama Mamaye Zuciyarsa da gangan Jikinsa ta yadda bazai iya Gudanar da komai acikin wannan Rayuwar ba sai da ita.
Abunda Inteesar bata sani ba Imran yafi ta Shiga Damuwa ya fita Wahala akanta,Sai dai shi Namiji ne kuma Shi din bamai Rauni ne bane ko Rauninsa ya bayyana baya yadda wani na Kusa Dashi ya Fahimta.
Atsakanin nan yadda yake azabtuwa da Rashin ganin Inteesar ko Abunda Daada tayimai baya Damunsa Saboda yagama da wannan Shafin Tuni Ransa ne yake bace tun Dawowarsu Daga yaji bayason kowa kusa dashi yafi son ya zauna shi kadai Daga shi sai Busa Hayakinsa,Bai taba Tunanin Rashin ganin Inteesar zai zama Cuta garesa ba sai alokacin,Fushi yake da ita Fushi mai Tsanani Saboda In ya Runtse idonsa ganinta yake Khamis rike a Hannunta sannan kuma yana Tuna kalamansa na ita din tashi ce in ya Tuna Hakan sai yaji har ita bayason gani kwata kwata..
Yana ganin Sakonta kuma yana karantawa Domin sune suka Zamemai Tamkar Rigakafin Samun Saukin Wutar da Zuciyarsa ke ciki,In bata Turo ba Wuni zai yi yana Duba Wayarsa yana sakin Tsaki in bata Turo ba Haka zai ta maimata sakonta na Baya wani yayi Mirmishi wani yaji Haushi,in kuma ta Turo ya Dinga maimaitawa kenan kamar yadda yarinyar ta damu dashi matuka Sakonta Duka iri Daya ne.

"Ya imu kana lafiya ko..?

"Kaci abinci..? Don allah ka Rika cin Abinci bana so ka zauna da yunwa.."

"Fatana dai ba rashin Walwalarka Laifi nayi maka ba ko?

"Ya imu plz am sorry in wani Laifi nayi maka kada ka Hora kanka da Zaman kadaici.."

"Ok..Naji..Plz kada rika shan Sigari..bana son watarana na Rasaka I miss u.."

Iraren sakonta kenan sakon da sukasa Nishadi,Suke Debemai kewa Cikin Satin Dayan da yayi yana Boye mata kanshi,Ko Sagir bai kara yarda sun Hadu ba Tun bayan Dawowarsu ya Kirasa a waya yaki Dagaewa Kila Shima Fushi yayi bai kara Kiransa ba kuma bai nemesa ba Shima yafi son haka,Yafi so ya gama Da Kansa Tukunna kafim yazo kuma yaji da Damuwar wasu kuma.

******
*Abuja*

Labarin mutanen Abuja Hajiya Mami da ya"yanta wanda tunda suka koma bata barsu sun zauna Lafiya ba haka take ta fada Tana fadin Baffa Kabiru yayi Shuru Danginsa sun ci Zarafinta ita da ya"yanta tayi ikirarin wlh Sai ta Raba auran Sajida da Imran yarta bazata taba zama da Dan"iska ba.
Baffa Kabiru dai bai ce mata komai ba Khamis ne ke bata baki shima ta Hada dashi ta Balbale tare da Gargadi mai Girma kada ta karajin mganar Inteesar a bakinsa bata kaunar wannan Hadin kwata kwata,Ita ce nan Mahaifiyarsa ita Zata zabamai da matar Daya dace da shi.
Anan gabar kan Baffa Kabiru yayi mgana yace mata kada ta shiga Hurumin da banata ya yadda Imran bai Dace da Sajida ba,Ammh Inteesar bata da wani aibun da Zatace Khamis bazai aureta ba Kuma Diyar Mustapha ce suna da kyakyawan alaqan Jini da yan"uwanta da bazai ji Kyashin Hada Zuru"a dashi ba.
Mami Asma"u na jin haka ta Daka Tsalle tace bazai sabu ba bazata bari su hade mata kai shi da Danginsa ba,Sajida an mata auran kaskascin Auran da bazata iya Daga baki ta Fadeshi Cikin Dangi ba Ta tabbata masu mata Dariya suna da yawa sannan kuma shima Khamis din sai ya kara Zama nasu ta gama Wahala Dashi ya kawo yanzu sai ya zama Surikin Mustpaha da Salaha ita ta Zama yar kallo kenan bata yarda ba bata Amince ba kuma ba wai tace yarinyar nada Illah bane kawai Hadin ne bai mataba bata Ra"ayi kuma Tunda aka mata fim Karfi kan Sajida wannan karon bazata kara yarda ba.
Baffa Kabiru dai bai biye mata ba Sanin Halinta sai ya kyaleta,Sai ta koma kan Khamis tajamai kunne sosai na kada ya sake taji wata mgana kan Inteesar ta kara tashi Daliln Dayasa yaji Zaman Abujan ya isheshi kwana Biyu yayi ya koma Anambara Sai dai kafin Tafiyarsa sun yi mgana da Baffa Kabiru sosai ya bashi Daman Indai yana son Inteesar ya Nemi soyayya da yardanta yayi mai alkwarkn zai shigemai gaba sai ya aureta da wannan kwarin gwiwan ya koma Bakin aikinsa da yakinin zai samo kan Inteesar da yardanta Tunda Dad ya shigemai gaba Mami ba Damuwarsa bane in ta gama bambaminta shikenan.

Bangaran Sajida Mami Asma"u ta dawo kanta ganin Khamis ya koma bakin aikinsa,Ta riga ta kudura ma Ranta Tsarwatsa auran nan kuma ta Lashi Tokobin sai ta Wulakanta Imran Tana Fatan ya tako kafarsa zuwa Gidanta sai ya Raina kansa.
Tattara Sajida tayi tace ta koma makaranta Zasu fara Test,Daman A Hostel take zaune sai dai bayan 2 weeks take Dawowa Gida tayi weekend wani Lokacin har Sati ma Tana Dawowa Gida sai in Sun Fara Test ne ko jarabawa take zama acikin makaranta sosai wannan karon Mami bata ma barta tayi Tunanin makomarta ba ta Tarkatata makaranta da kanta ta kaita ta maidata bayan ta mata Fadan ta Cire komai acikin Ranta tayi Facing din Karatunta kamar wani abu bai Faru ba Sannan ta Gargade ta kada ta Sake ta fadama wani an mata aurre..Domin kaskanci ne sosai wani yaji wannan Labarin Sai ayi mata Dariya.
Sajida a makaranta bazatace ga Halin Datake ciki ba,Zuciyarta da Duka Tunaninta suna wajen Mijinta Imran ne bata San ta wata Hanya zata bi ta samesa ba,Ba mgana take da kowa ba Acikin Dangi ballatana ta saka ran Zata samu ko wajen wata ne,Bata kuma da lambar Munari Umaima ce ke dashi kuma tana gida bata san kuma ta Kirata Mami taji Labari ita ko bata Dama ta gana da Mijin nata ba"ayi ba abubuwa suka zo suka Faru ba Dadi ita dai koma Menene bazata yarda Mami ta rabata da Imran ba Tana son shi tana Kaunarsa ya Dace da Duka Zabinta bata damu da Hallayarsa ba shi take so kuma bata Damu da Rashin Jituwansu da Mami ba Ballatana Ya Khamis ba yare Daya take Fahimta Shine Son Imran mijinta Har wani alfahari take da hakan kuma bazata jura ko Ganin wani ya Shiga Tsakaninta da abunda take so ba, koda Mamin ne da kanta.
Haka take Sukuku bata da wani Karkashi Allah ne ma ya Taimaketa Kwakwalwarta naja shiyasa ta iya Tabuka wani abu a Test din da sukeyi ammh Rabin Hankalinta da komai nata suna ga Imran ne duka Mafarkinta nashi ne.
Ta bari ne su gama Test ta dawo gida Sai ta san yadda tayi ta mallaki lambarsa su rika mgana Kila jin Muryansa zai Rage mata wani Radadin ba ruwanta dashi bai Nemeta ba,ita din zata Nemesa saboda Shi din Mijinta ne nata ita kadai.

*******
*Kano..*

Yau ta kama Jumma"a ne a masallacin Jumma"a suka Hade tsakanin Sagir da Imran,Daman nan suke Sallar Jumma"a Shida Sagir,Abba kuma na chan Tsallaken Gadon kaya yake zuwa ,Tun ana Huduba Imran ya iso masallacin,shiyasa ya samu Shiga Cikin masallacin aka gama Huduba aka Tada Sallar sai da aka idar irin Tururuwan Fitowana nan sukaci karo da juna.
Tsayawa sukayi suna kallon kallon juna Sagir na sanye Cikin Sabuwar Shaddansa Fara Dinkin zamnii na Riga da wando Da Hulansa Zanna Bukar,sai Dardumansa Dake hannunsa yayi kyau sosai kuruciyarsa ta kara Bayyana da Samartakansa..
Yayinda Imran ke sanye da Jallabiya mai Ruwan madara,bata da tsawo sosai sai ya Hada da wani bakin Wando kafarsa Cikin Takalminsa Sawu Ciki na Fatar damisa,kansa ba Hula sai dai yasha gyara Hannunsa kuma Agogon Fata ne baki na Fatar Damisa fuskarnan ko kadan ba Fara"a Ya wani Kara Dakuna Fuska da suka Hadu da Sagir.
Sagir bai damu ba Mirmishi yayi mai Lokaci Daya yana bashi Hannu alamun Musabaha bai yi gaddama ba ya mikamai suka gaisa Daganan suka jera har Wajen masallacin Mutane nata Xirga Zirga tafiya masu ababan Hawa nayi masu Tafiyar kasa nayi.
Sagir ya kalli Imran yana Fadin"Kazo da Mashin ne..?
Ko tankasa Imran bai yi ba Hanyarsa ya Dauka ya Fara Tafiya wanda hakan da yayi shi ya bama Sagir amsa sa bai Hakura ba ya taka ya Bisa suka Fara Jerawa Suna Tafiya Kafada da kafada ammh ba wanda ya kara ma wani mgana sai Sagir ne ya kallesa yana Fadin"Na kiraka baka Dauka ba..Hala wayarka Ta lalace ne..?domin naga baka Biyo baya ba..?
Imran ya wani kara Tamke Fuska Hannuns Daya Cikin Aljihun Jallabiyansa kamar bazai yi mgana ba sai chan yace"Bata lalace ba..Kawai bana Ra"ayin mgana Dakai ne..!
Sagir na Dariya yace"Nagane..Daman mai Amarya Danyan Sharaf irin Sajida ina zai yi ra"ayin mgana Damu..!
Kamar ya watsamai Wuta haka yaji mganarsa Da ace ba domin suna Bakin Titi bane da sai ya Daki bakin Sagir ya Fitar da jini sai dai yaci Daraja Daya suna Cikin Mutane ne da yau ya gane Kuransa na gayamai wannan mganar.
Kala bai kara cemai ba Sai ma kara Hade Rai da yayi yana wani Bude Hanci ganin ya kunnosa yasa Sagir bai kara mgana ba sai Kunshe Dariyansa yake yi.
Haka suka rika Tafiya kamar kurame har suka kariso kofar Gidan su Sagir din wanda yayi ya shiga ya gaida Mama yace bazai shiga ba kuma Shima Sagir din bazai shiga Gidan ba yanzu Sagir ya Tsaya yana kallon Ikon Allah ga Shagonsa yaronsa Auwal ya Rufe sun tafi masallaci Da alamun ya Rigasu dawowa.
Bai ce komai ba ya gyara Tsayuwa suna Tsaye kafada da kafada suna Bin Hanya da kallo kamar masu kirga wani Abu.
Ta bangaran Imran ba haka abun yake yau yaji ya gaza Inteesar kadai yake son gani,in bai ganta ba ji yake kamar zai iya Mutuwa gashi ta Daina Kiransa kwana Biyi bai ga Sakonta ba Ko ta Daina Damuwa dashi ne..?
Juyawa yayi yana kallon Kofar gidan Mama Tun jiya bai ji Motsinta ita da Munari agidan ba,kila Gidan Mama suka kwana kuma yau har yabar Gida bai gansu ba Abba da Anty Safiya ya bari agida Yusuf na wajen aiki.
Kallon Kofar gidan yake kamar yana so yaga Inteesar din ta Fito Sagir Dake Lura dashi Tun dazu ya Juyo yana kallonsa Cikin Nazarinsa kafin yace"wai wakake nema ne sai kallon Waje Daya kake yi..?Nace kuma kazo mu shiga kace A"a..!
Imran bai ce komai ba sai ma Mtsawa Da yayi gefe ya Fito da wayarsa Dake Cikin Aljihu Sagir na gefe Hannunsa Saman Kirjinsa yana kallon ikon Allah Cike da Nazarin Imran din.
Sako ya Tura mata saboda yana son yaji ko Tana ina ne..?

'"Kina ina ne.."?

Haka kurum ya Turamata ya koma yana Jiran Tsammanin amsarta Sai dai Har wajen Shudewar Mintina Goma bai jita ba sai kallon Wayar yake yana Sakin Siririn Tsaki wata Zuciyar na Fadamai kila Fushi Take yi Dakai tana Kiranka baka Dauka Ransa ya kara baci Wato ita ce ma Zatayi Fushi ita bata ga abunda tayimai ba ko?
Kwafa yayi kawai yana kokarin Daidaita kansa Sagir Dake lura dashi ya matso kusa dashi yana Fadin"Wa kake ta kira ne haka..? Ko yaki Dauka ne naga sai Tsaki kake ja kai kadai..ko Amarya ce taki Dauka tana ja ma Ango aji..!
Ya karisa Fada yana yar Dariya wani banzan Kallo Imran ya Bisa Dashi kafin ya maida wayarsa aljihun Jallbiyan Dake jikinsa Kokarin Dunkule hannu yake yakai ma Sagir din Wani Naushin da Kila sai Bakinsa ya Zubda Hakora Lura da Hakan da yayi ne yasa yamtsa da Sauri yana Fadin"Daga mgana..? Allah ya Huci Ran angon Sajida ya Dade..!
Yake Fada yana Dariyan ganin yadda Fuskar Imran din tayi saboda Haushi Kwafa yaja kafin yace"Banza Dan saka ido..Ai daka Tssya Daka gane Ango yau..!
Yafada yana kara Sakin wani Tsakin ya koma gefe wayarsa ya kara Fiddowa Shuru bai ga Sakon Inteesar ba Ransa sai ya kara baci,Ga Sagir Sai Dariya yake yi mai Banza Dashi yayi bai bi ta kansa ba Duk da Sunan Sajidan Dayake ambata kamar ya Juya ya Watsamai mari da ashariya haka yake ji.
Sagir ganin Imran din bai kula sa ba sai ya Daina ya Matso kusa dashi ganinsa sai Bini Bini ya Duba Waya yana Sakin Tsaki ya Fahimco wani abu na Damunsa Cikin Lallami yace"Meke Damunka Imu..?na lura dakai kamar Miskilancin naka yau yafi na koyaushe..!
Imran yayi kamar bai jisa ba Sai chan yace"Ina Ruwanka..?
Sagir ya kada kai yana Fadin"Au Daga Tambaya..? Nima Allah karamin da nake kokarin jin Damuwarka kaga Tafiyama ka Dade damuwar bata Kashe ka ba Tunda kai baka son Abun Arziki ba..!
Yafada Lokaci Daya yana wucewa Shagonsa ya shige Daman Tun dazu suna Tsaye su Auwal din suka Dawo suka zo suka Bude shagon da kallo ya Bisa shifa bama Sagir ne agabansa ba..Damuwar Dayake ciki tafi karfin ya Tsaya yana bi ta kansa wanda yasan anjuma nan zasu Shirya kansu.
Ganin Shuru Shuru bai jita ba yasa ya yanke Shawaran Kiranta Duk da baya son Kiran nata ammh Zuciyarsa ta Rinjayi gangar Jikinsa Daya kasa Hana kanshi Sai dai ya gansa kawai yana Kiranta,Zuciyarsa Bugawa take da Sauri da Sauri so yake ji Muryanta ko ya Samu Salama,Sai dai me yana Kiran nata ta shiga yaji Call Waiting ma"ana Tana amfani da wayar kenan Wani Rugugin bala"i Imran yaji sun Saukomai acikin kansa Har wani Jiri Jiri yake gani bai Katse Kiran ba Sai da ta yanke da kanta,Kansa ya Dafe yana jin wani Daci Daga kasan Ransa Wato ma Tana ganin Sakonsa Tayi banza Dashi..? Da ganga taki kulasa..?kan Bala"i bata san Waye Imran ba Ya zama Dole Abunda yake so ayimai in kuma akaki yimai ba Zaman Lafiya.
Wani Tunanine ya shiga kansa Kodai da wannan Banzan gayen take waya ne..? Domin ai yaji Daada ta bashi Umarnin ya Nemi yardanta in ta Amince shikenan Tuna Haka da yayi sai da Idanuwansa suka Sauya Launi Kirjinsa ya Fara tashi yana komawa da wani bakin Kishi da shi kanshi baisan yana da shi ba Tana Waya dashi Shine tayi banza Dani..Ina Bata isa ba..Shima khamis din bai isa ba Inteesar bazata taba Zama nashi ba Har Abada.

Abunda bai sani ba Sakon Daya Turama Inteesar ba ita ta gani ba Munari ce,Domin yau din da Safe suka Shiga School shima Assigment suka yi Submitting,suka Dawo gidan Mama suka kwana Daman bayan sun Dawo kuma suka yi Girki,Da Niyyar da sun gama zasu je gidan su Munari,To bayan sun gama ne Duka aikin su ne Mama tana Falo ta samu Barci Saman kujera ita kuma Inteesar ta shiga wanka Munari tace bazatayi wanka ba sai anjuma Tunda Tayi da Safe Inteesar tace sai ta karayi bazata iya Fita hakanan ba Tayi kaurin Kitchen
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment