Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

hannunsa ya Duba yaga lokacin Sallah ya kusa Daman ya Dauro alwala cema Sagir yayi alwala su tafi masallaci ba Musu ya tashi yaje yayi alwala suka Fita Tare koda suka fita duka mazan suna Waje suna alwala har da su Abba ya Hadu da Mami Asma"u a Falo bai ko kalli barayinta ba,Dariya yake cikin Ransa Domin har yana Hango irin yadda Zatayi in taji Hukunci da ya yanke akanta da ita da yarta.
Gabadayansu suka Dumguma zuwa masallaci sai da suka Tsaya aka Tada sallar tunda sunje da wuri bayan sun idar suka nufo gida.
Imran da shi da Sagir suna Baya sai Daga baya suka Shigo gidan Tun Daga Nesa ya Hango Sajida Tana Tsaye ko da bai sani ba yana da Tabbaci shi take jira zatayi mgana dashi Sanye take da wani material mai Santsi Dingin Doguwar riga ta yane kanta da karamin Bakim Vail kafarta Cikin takalmi baki sawu ciki a Fuskarta ta Rame sosai Idanuwanta duk sun Sauya Launi
Sagir na ganinta ya Zunguri Imran yana Fadin"Ga Amaryan ka nan..!
Ko kallonsa Imran bai yi ba sai ma kara Tamke Fuska da yayi kamar bai Taba Dariya ba Har suka kariso kusa da ita Sagir na Shirin Dakatawa Imran ya wuce Kamar ma bai ganta ba ganin haka yasa Sajidan da gabanta ke Fadi Saboda yadda Imran din yayi mata Kwarjini tace"ina yini..!
Imran yajita ammh yayi kamar bai jita ba ya cigaba da Tafiyarsa Sagir Daya ga haka ya Daga Murya yana Fadin"Imu tana gaisheka fa..Don Allah ka Tssya..!
Da kamar bazai Tsaya sai Wata Zuciyar tace ka Tsaya ai ba wani Sauran Rina Dake Tsakaninku.
Cak ya Tsaya Lokaci Daya yana juyowa Hannuwansa ya Haarde Saman Kirjinsa yana kallon Sagir irin gashi na Tsaya sai yaya..?
Sagir ne ganin haka yasa ya Kalli Sajida da kanta ke kasa jikinta ma ya fara rawa tana ta wasa da Kwalliyar Jikin Rigarta.
Ya sanyaya Murya yarinyar ta bashi Tsausayi saboda yasan wacce Zata iya gaba da gaba da Imu ba karamar Jaruma bace
Yace"Ki je ki sameshi in ba haka ba zai Tafi abunsa..!
Daga haka ya wuceta da sauri kusa da Imran ya karisa daidai kunnensa yayi mai Rada"Plz ka saki Ranka She is ur Wife..!
Sanda Sagir ya fadi haka sai yaji kamar ya Mangaresa da mari,sai kuma yayi Fuska kawai ya kara Hade rai ko kadan ba annuri ballatana Samun sukuni agame dashi Sagir dai Ciki ya shige yana Fatan kada Allah yasa Imran ya zabgama yarinyar nan Rashin Mutumcinsa.
Gajiya yayi da tsayuwa ganin Ta na nan Tsaye bata ma tako ba,juyawa yayi niyyar tafiya sai gata ta kariso Salau Salau kamar mara kuzari aransa yace ji ta kamar wata ta Allah.
Kanta na kasa bata son Hada ido dashi Tace"Ina yini..!
Tafada Lokaci Daya gabanta na Faduwa,Saboda bata son kallonsa kwayan idonsa yana bata tsoro matuka yana saka taji duk wani Comfident dinta ya tafi indai tana gabansa gabanta sai Fadi yake in da Zai lura har rawan jiki dana Baki take yi alokaci Daya.
Kallonta yake Daga sama Har kasa so yayi ya sakin mata Tsaki sai kuma ya fasa cikin Dauke kai da Dakuna Fuska yace"Lafiya..!
Yafada yana kallon Fuskarta acikin Ransa yace irin Fuskar uwarta ya"yan nagada ba na haya ba.
Gajiya yayi da tsayuwa yasa yace"Ammh kinsan dai ba wasa tsakanina Dake da zaki Tsaidani ki tasani agaba kuma kiki mgana ko..?
Yafada cikin Kaushinsa kamar ko yaushe.
Jim haka yasa ta kara Sadda kanta Tana Fadin"Dama..Dama!
Wani Haushi ya kamashi yace"Dama What..?ke kinga ni ina da abunyi yanzuma Da kika ga na Tsaya Wlh ba wai domin darajanki bane ke har kin Isa..? Ba macen data isa ta sani ni Imran nayi abunda ban yi niyya ba Darajan Abokina kikaci..So in baki da Fada on my..!
Bata bari ya karisa ba,Tunda taji mganarsa Cikin Kaushinsa kafin tace"Dama ina ta Kiranka a waya ne baka Dauka ba Daga baya kuma sai na Daina Samun ka..!
Karamin Tsaki yaja kai Tsaye yace"Nayi Blooking dinki ne..!
Batasan Sadda ta Dago rinannun Idanuwanta Tana kallonsa ba Cikin mamakin kalamansa Duk da tasan dai Ya kulleta ne ammh bata Zata zai iya gayamata haka ido Cikin ido ba.
Ganin irin kallon Datake yimai ne yasa ya Daga mata gira guda Daya yana Fadin"Yes..Saboda bana son Wata mu"amala ta shiga Tsakanina Dake Infact ma bamu da wata alaqa..!
Bai bata Zarafin mgana ba ya cigaba da Fadin"Nasan zuciyarki na Fada miki ba an Daura mana aure ba..? Auran Dan iska dan Shaye shaye bai Dace da Sajida Kabir Dukku ba Diyar Lauyoyi jikar Lauyoyi Diyar na gada ba na Haya ba..To u better wake up..kinga kuwa ni ban Dace dake ba..Ke ba Matata bace bamu da wata akala!
Gabadaya kalamansa sun rikitata Bata san Sadda ta dago kanta Tana kallonsa ba sanda yace ita ba Matarsa bace Kara Dakuna Fuska yayi kafin yace"Eh nace bamu da akala ko muna Dashi ne? Nasan zaki ce to ko ba aure ai ni yar"uwarka ce u ara mad in kikayi Tunanin haka akaina ni Imran Wlh wanda keyi dani sai ma naga Dama Zanyi Dashi acikin Dangi ballatana Wanda basan da wanzuwarsu ba So plz and plz ki Rabu dani kada ki kara Kirana am not ur mate kada ki kara Kirana In baka ba Haka zaki san Oder Side dina!
Tsaki yaja mai karfi yana Fadin"Rubbiish kawai..!
Daga haka ya juya ya shige cikin Gida,da kallo ta Bisa Hawayen da suka cika mata ido suka zubo mata masu Zafi da Tsananin kaunar Imran Kuka Take so ta fashe dashi ammh Zuciyarta ta Chuse waje Daya Meyasa yace ita ba Matarsa bace ko ya saketa ne?
Saurin dafe kanta Tayi jin ya sara mata da wannan Karamin Tunanin a Fili ta Furta"A"a bazai taba sakina ba..Bazai sakeni ba bazai sabama mganar Baffa data Daada ba..Wlh ina sonsa inajin kamar in na Rasashi Zam iya Mutuwa..!
Take Fada tana Sharan Hawayenta kamar Wata Tattabiya soyyaya Ta sakata Zatayi hauka kafin ta Dibi Sauri Zuwa Cikin Gida.
Tana shiga Taga ana ta cin Abinci Mami Asma"u dake Faman nemanta ta Tsareta da ido Cikin Tuhuma Tana fadin"Ina kika shiga Tun dazu..!?
Cikin kame kame tace"Na fita amsa waya ne Mami..!
Tafada Tana kallon Imran Dake kusa da Yusuf suna cin Alalan da Baba asabe Tayi a Filet Daya,Ko barayin Datake bai kallah ba kansa na kasa ya bada natsuwasan kan abun ke gabansa.
Hararanta Mami Asma"u tayi Tana Fadin"Waya ko..? Ita kuma wannan ta waye..?
Tafada Tana Daga mata wayarta da ta barta gefen Mami Asma"u din bata sani ba.
Kanta ta Sadda kasa batace komai ba Hankalin kowa baya kansu Ba wanda ma yabi ta kansu su Abba suna Dakin Daada achan suke cin nasu abincin.
Mami Asma"u kure Sajida da ido take yi,Tana Nazarin wani abu acikin Ranta Taga shigowar Imran kuma ba Dadewa Taga Sajida ta shigo Allah yasa ba ajinta ta Zubar taje tayi mai mgana ba in ko hakane da sai taci Uban Sajida in ta kuskura tayi mata wannan Shirmen.
Abinci tace tazo taci bata cikin good Mood yasa tace bazata ci ba wucewarta Tayi Dakin da suka Sauka ita da Mami Asma"u ranta duk ba Dadi Mami Asma"u ta bita da wani kallon yarinyar nan Tana Hauka ne..?
Ba a dauki Lokaci ba kowa ya gama cin Abincinsa nan mazan suka Zauna suna Hirarsu Imu ma na cikin su sai dai baya mgana Sai dai yana jinsu kawai in abun mgana ce aka Sako sa sai da ya gyada kai ko ya Rage Daure Fuskar Wayace a hannunsa Mgana suke da Intee Tana mai shagwaban gida ba kowa duk ba Dadi tana Missing dinsa,Sakar mai da kasala Take duk da ba Waya suke ba Massages ne bai biye mata yace ta wuce taje ta Dauki Littafanta Tafara Karatu baya son Shirme.
Suna nan Zaune sai ga su Abba sun Fito Dukkansu sun taso Tsohuwa Daada agaba Tana Tafe sanye da Hijabi mai ruwan kasa,Bai da Tsawo sosai Carbi ne a Hannunta tana ja Inna Bintalo da Inna Maimuna suna Kafada kafada da ita sun sakata a Tsakiya.
Kan kujera suka Taimaka mata ta Zauna Gabadayansu suka Zauna a kasa Umma Dake saman kujera ta Sauko ta zauna akasa,Daman Mazan duk suna Malale zaune ne saman Cafet din Daya malale Falon.
Mami Asma"u dai Bata sauko ba sai ma kara gyara Zama datayi akan kujeran ta kara gyara Zaman Siririn Gilashin Dake idanuwamta Khamis na gefenta a kasa yazauna wajen Kafafunta.
Tuni Falom yayi Tsit sai Sautim Muryoyin su Sa"id da suke ma Daada Barka da Fitowa amsawa take cikin kulawa,Tana Bin Kowa da kallo Daya bayan Daya sai ta sauke kallonta kan Mami Asma"u wani abu na cin Ranta Uhm Lokaci yayi da Asma"u zata gane Kuskuranta Juyawa tayi Tana kallon Baffa Kabiru kafin tace"Ina Sajida..?banganta ba ko bada ita kuka zo ba..?
Kai ya girgiza mata kafin ma yace Wani abu Mami Asma"u ta yi Caraf tace"Da ita muka zo mana Daada..Yanzu ta shiga ciki..!
Daada ta gyada kai kafin tace"Jeki kirata..Domin wannan Haduwar ta Shafeta sosai..!
Mirmishin Saman baki Mami Tayi Damam ai tasan mganar Sajidan da wannan Tsagerin yaron nan Lalle kuwa yau Zata nuna ikonta a Mtsayinta na uwa,Sai ta ja Imran a kasan Kafarta bai isa yaja da ita ba.
Tana shiga Dakin ta iske Sajida kwance Tana Hawaye jin muryanta a saman kanta ne yasa tayi Saurin Share Hawayenta ta mike Zaune tana kokarin Kauda idonta kada Mamin Ta gano Halin Datake ciki.
Kallon Tsab Mami Tayi mata kafin Tace"Wai Sajida kukan Uban me kike yi ne Tun dazu..?
Sajida tace"Kuka kuma..? Ni ban yi kuka ba Mami..?
Tafada tana kokarin mikewa ta kaucema Kaifaffun Idanuwan Mami Asma'u Daga gano yanayinta.
Mami Ta wani kalleta a karkace kafin tace"Kina Zaton ban san kukam me kike yi bane..? Uhm yaro man kaza..Dazu fitan da kikayi wajen Dan iskan yaron nan kikaje..!
Sajida ta Dago kanta cikin mamaki ta Bude baki Zatayi mgana Mami Ta Dakatar da ita lokaci Daya Tana Daga mata Hannu tana Fadin"To bari kiji na Fada miki in ma Kina kokarin Saukowa ne ki yarda da auransa Cikin Sauki ni Asma"u uwarki ban yarda ba ko Zan amince da wannan auran ba yanzu ba sai na ja Yaron nan akasan Kafata ya duka yana kuka yana Bani Hakurin Rashin Da"ar da yayi min sannan kuma yana kuka yana Rokon na bashi ke sannan zan iya yarda ma ki Zauna dashi ammh in ba haka ba Duk wacce Za"ayi sai dai ayi bazan bari ki Zauna da wannan Dan iskan yaron ba.!.
Tafada cikin son Tabbatar da mganarta bata damu da yanayin Sajidan ba ta Fice Tana Fadin"Ki fito Daada na kiranki..!
Sajida Kuka ya kwace mata Mami bata son Imu shine Rayuwarta ba Wani irin so mai Tsanani ne ya kamata alokaci Daya tana jin kamar Zata Mutu in ta rasashi Wata Zuciyar tace to ke sai ki bari ki rasashi..Ina bazata taba bari haka ya Faru ba Imran mijinta ne kuma Dole tayikomai Saboda ta Dauwama Dashi Wannan karon zata Dakatar da Mami Zata Fadamata gaskiya She Love Imran Tana matukar sonshi kuma Zata Zauna dashi a duk yadda yake so ta kyaleta don Allah kada ta Shiga Rayuwarta ta lalata mata
Tiolet ta shiga ta wanko Fuskarts tazo ta Tsane da mayafinta kana ta Fito Falom ita ake ta jira ba"a Fara Taron ba Tana Zama gefen Dan"uwanta Daada ta kalli Yusuf Tana Fadin"Yusufa Bude mana Taron da addu"a.."
Ba musu ya gyara zama ya Bude Taron da addu"a aka shafa sannan Daada tayi gyaran murya ta Fara mgana..!
"Da farko dai ina yi ma Duka ya"yana da jikokina da suka Taru anan wajen barka da zuwa..nasan kun baro duka Tarun ayyukan ku ka amsa kirana Naji Dadin haka Allah ya saka Muku da mafificin Alheri ya raya muku Zuru"a ya baku ya"ya wadanda zasu ji kan ku kamar yadda kuke jin kaina..!
Gabadaya aka amsa mata da Ameen Ameen.
Kafin ta dan yi shiru kafin ta Cigaba Cikin muryan tsufa"Dalilin Dayasa nace ina son ganinku duka da wasu Daga cikin yayenku Mgana ce Daya zuwa Biyu..na farko mgana ne kan Imranu gashi chan Dan Wajen Malami sai Sajida Yar wajen Kabiru..Kafin naje gaba a mganata kowa anan wajen ya Shaida Auran dana saka aka daura shi Wata Daya Daya gabata a garin nan tsakanin Imranu da ita Sajidan ko..?
Kowa ya gyada kai alamun hakane Daada tana Jan Casbahanta tacigaba da Fadin"Alhamdulillah kuma kowa anan yasan abubuwan da suka yi ta Faruwa bayan an Daura auran da kafin a Daura Inda Asma"u gatanan matar Kabiru ta rika nuna rashin Amincewarta tare da Diban albarka kala kala ammh duk na kauda kai bam ce komai ba Saboda bai kamata nayi mgana alokacin ba Kuma ni miye nawa..?ko me zan ce tunda agaban Mijinta ne Gashi nan kabiru bai Tsawarta mata ba kenan shima ya yarda da duka abunda ta Zauna akai bai so hadin Zumunci Tsakanin jininsa da jinin Abubakar ba..!
Tafada Tana dan Sauke Numfashi Kowa afalon yayi shiru yana Sauraranta Baffa Kabiru ya dago kansa ya kare kansa Daada ta wurgamai wani kallon Da Dole yayi Shuru da bakinsa Mami Asma"u kuwa na gefe Kafa Daya kan Daya tana karkadawa alamun tana jiran kowa wanda yace kule sai tacemai Chass..!
Daada ta cigaba da Fadin"a lokacin da nayi Tunanin wannan Hadin har ga Allah Zuciyata Daya ina ganin cewa hakan shi Zai kara mana Dangom Zumunci da son junanmu sai Daga baya na gane nayi kuskure kuma nayo Hadi inda bai kamata ba na manta Asma"u ita ke jan Ragamar Rayuwar gidan Kabiru tamkar itace mijin shine Matar baya iya Zartar da mgana sai abunda tace,Sannan ko mganace ta Dangi bazai iya mgana ba sai da yawunta ko da amincewarta Shiyasa data nuna bata amince ba shima ya Goyi bayanta..To Alhamdulillah na Taraku ne anan saboda na gyara Kuskurena..Mustapha ina son ka bama Danka Imranu auran Diyarka Maryama mai sunana ba sai gobe ba yau din nake son adaura wannan auran indai kaima ka amince saboda ina Tsoron nuna isata akan ku Alhalin ban isa ba!
Gabadaya Falon sai kallo ya koma Wajen Daada ita kuma ko ajikinta Sagir ya kalli Imran alamun How comes,shi kuma ya Dagamai gira Khamis da yayi mutuwar Zaune ya Dago yana kallon Daada lokaci Daya ya koma yana kallon Imran wanda ya Cije mai baki ya Dagamai girarsa Duka Biyu irin kaga nawa ikon..?to yaya Zata zama takan ne..?
Gabadaya kowa sai mamakin Daada yake yi,Yusuf ya kalli Imran ganin ko ajikinsa ya juya yana kallon Abba da Daddy da suma suke kallon Daada aransu suna Tunanin Riikicin Tsufa ya Fara Taba Daada.
Daddy ne ya bude baki zai yi mgana Abba ya girgizamai kai,Baffa Kabiru kuwa bai ce komai ba Domin ya kasa Dora komai akan Mizani..
Sajida kuwa allah ne kadai yasan Halin da Zuciyarta take ciki gani take kamar ta Kurmance bataji Da kyau ba Mami Asma"u kuma mamakin yadda Zaton ta ya sauya take yi anya Daada nada Hankali kuwa..?
Abba ne ya Dago yana kallon Daada Cikin Sanyin murya yace"Daada bawai ina ja da mganarki bane..ko kin manta cewa Imran ya auri Sajida kuma Inteesar Shakikiya ce ga Sajida Daada duk da ba Haram bane ammh ana barin Halas ko dom kunya..!
Karamin Mirmishi Daada ta saki kafin Tace"Na sani..Ina sane da komai..Ai ba aure Tsakanin Imranu da Sajida a yanzu..!
Gabadaya mamaki ya hana kowa Mgana Inna Maimunatu ce tace a wannan karon"Daada bamu gane kan mganarki ba..!
Daada ta Dago ido Tana Fadin"Ku juya amsarku Wajen Imranu..Kai Imranu gayamusu abunda kazo ka Fadamin..!
Imran ba wani Tsoro ko Fargaba ya Dago kansa yana kallon yadda gabadaya Idanuwa suka koma kansa Ya gyara Zama yana kallon Idanuwan Mami Asma"u da Sajida da ya kusa Fadowa saboda Firgici da Tsoro.
Cikin Kaushin sa yace"Na saki Sajida Tun Washegarin Ranar da aka Daura mana Aure da ita..!
Ya fada kai tsaye Lokaci Daya yana Fito da wata Takardan a Aljihun Wandonsa ya mikama Yusuf Dake kusa Dashi Wanda yayi Jagale yana Bin Imran din da kallon mamaki.
Kalamansa sun Daki kowa afalon banda Daada Data san mganar.
Ammh Firgicin yafi bayyana kan Fuskar Baffa Kabiru,Mami Asma"u da Sajida wadanda Tsabar Rudani ko Motsi sun kasa.
Daada ta Umarci Yusuf ya Warware Takardan ya karanta afili kowa yaji Cikin Sanyi jiki ya Bude Takarda ga Hand Writting din Imran nan ya Rattaba Rubutun kamar haka.

*Ni imran Abubakar Malami na Saki Matata Sajida kabir Saki Daya Saboda bana sonta kuma bana som na cigaba da Zama da auranta na kwari kaina Daman chan Nayi Biyayya ne kan Mganar Abba Daya Gindayamin Umarni Sai dai Umarnin Auran kadai ya bani ba Umarnin kada nayi Sakin ba..Allah ya bata wani mijin Agaba wanda baya Shaye shaye daidai da ita..*

Kowa sai Shuru ba bakin mgana Musamman Abba da Daddy da suke kallon juna cikin Tarradadi,Abba Imran yake kallo Ransa na kuna da Baci sai dai ya Tabbata ko kashesa zai yi bazai Taba Sauya Ra"ayi ba sai yanzu ya gane cewa Shurun da Imran din yayi Lalle ya shammacesa.
Daada ta Umarci Yusuf daya miko mata Tadardan ya mike ya kaimata ta karba Lokaci Daya tana Mikama Baffa Kabiru da gabadaya Bacin Ran wannan Tozarcin da Imran yayi mai ya Lullubesa.
Mikamai Tayi Ya karba Cikin wani yanayi kafin yayi mgana ta Rigasa da cewa"karbi Takardan Sakin Sajida..Ka mikama Matarka..Tayi hakuri Bisa Rashin Daidai da muka mata tun Farko Daman tace indai Tana Raye ba wanda ya isa ya Tabbatar da wannan auran to gashinan Imranu din ya Yanke komai shiyasa dayazo ya gayamin ban damu ba Duk da naji Ciwon Abun sai dai hakan yayimin Daidai Tunda dai an yi muku abunda kuke so Ba Damuwa in wani yaki ka da wuni wani da kwana Zai soka Ga Mustapha nan na Roki alfarman ya aura masa yarsa in shima kuma bai Amince ba Wlh bazan ce Dole sai an Bi Umarni na ba..!
Tafada Idanuwanta na kawo kwallah Gabadaya sai jikin kowa sanyi Wato Daada Ranta ya baci da Baffa Kabiru da Matarsa sai yau take Dafasu Cikin Ruwan sanyi.
Baffa Kabiru ya ji bakinsa yayi nauyi yama kasa mgana Kamar zai yi mgana sai ya kasa Daada ta kalli Daddy tana Fadin"ka amince ko baka Amince ba..?Salaha kema kina da Hakki kan wannan mganar..?
Khamis Da yaga Wankin Hula zai kaisa ga Dare yayi Zaraf zai yi mgana Daada ta Dakatar dashi da Fadin"Kada kace komai..Inteesar tace bata sonka agaban kowa da kowa saboda haka baxan mata Dole ba..Ni Maryama na Riga na Cire bakina kan ya"yam Kabiru Duk Abunda iyayenku suka Zaba muku Daidai ne..!
Kansa ya Sadda Hawaye sun cikamai ido ya kasa mgana Daada ta Dawo da kallonta kan Daddy tana Fadon"Ko kaima bazaka bashin ba..?
Da Sauri Daddy yace"Ni na isa Daada..? Na amince Dari bisa Dari Imrana kamar Da yake a wajena Dashi da Basheer da Inteesar Wlh basu da maraba..Mganar Salaha kuma bata da Mtsala Daada ita din mai Umarni da duka Mganata ce ko mganarki..!
Yafada aransa yana jin Dadi duk da Sakin da imran yayi ma Sajida bai ji Dadi ba ammh yau kadai zai Rama mganar Mami Asma"u Datace Daada Tayi sonkai Dayake mgana shi Zai iya bashi yarsa ce to yau Zata gani kuma Za"ayi agaban idonta.
Umma ma baki ta Bude Tana Fadin"Daada ni ban taba ja da mganarki ba..Imran Mutun ne kamar Kowa Ina Taya autata Murnan Samun Gwarzon Namiji kamarsa..!
Tafada cikin som Turama Mami Asma"u Haushi Wacce take Zaune ita da yarta kamar Mutum mutum.
Daada ta saki kayattacen Mirmishi Tana Fadin"Masha Allah naji Dadin haka..!
Baffa Kabiru ta kallah kafin tace"Bayan Sallar La"asar nake son ku Daura auran..!
Khamis ya zaraf Cikin kunar rai yace"Daada kiyi Adalci mana..Taya Zaki aura mata wanda baya sonta kuma Da kikace tace bata sona shi tace Tana sonsa ne..!
Daada bata nuna Damuwa ba tace"Mustapha Kiramim Maryama ka Tambayeta Zaka aura mata Dan"uwanta Imran abunda muka ji Daga gareta dashi Zanyi Amfani..So nake na goge kalmar Rashin aldacin da ya"yan Baffa Kabiru ke jifana dashi su da iyayensu.
Ba wanda yayi motsi Daddy ya Dauko Waya ya Kira Inteesar ta shiga ta Fara Ringing da Bugawar zuciyar wasu Sajida Mami da Khamis Imran kuwa ko ajikinsa bai Damu ba yasan ko Intee ta amsa ko bata amsa ba shike da Nasara yau din nan.








*Shakira*
3/23/22, 21:51 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�16*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*


Inteesar da Munari suna baje a Falo a kan Cafet din Daya yi ma Falon kwanya Littafansu suka baje suna karatu Saboda test din da zasu fara Ranar Monday da farko Hirar su suke sha Da Anty Safiya bama su fara karatun ba sai da Imran yace mata Taje tayi karatu kana ta mtsama Munari ta Dauko musu Littafan suka Fara
Hankalinsu ya tafi kan abunda ke gabansu bama su ji kiran Wayar Inteesar da Daddy ke yi ba sai da ta katse ya sake kira kana Munari taji ta Dauko Wayar tana Fadin"Besty kinga Daddy nata kira bamu ji ba..!
Inteesar na Duke da Biro a Hannunta Tana Rubutu cikin wani karamin Littafi kai Tsaye tace"Dauka Sakata a Speaker!
Ba musu munari ta Daga Kiran ta sakata a amsa kuwwa ta ijiyeta anan Tsakiyarsu dukkansu suka Hada baki Wajen gaida Daddy bayan yayi Sallama.
Daddy ya amsa cikin Sauri yana kallon Daada Data kafesa da ido Cikin Gyara Zama da mgana mai muhimmanci Daddy yace"Intee kina jina Dakyau..?
Cikin Mirmishi tace"Yes My Hero Dad
!Tafada cikin barkwancin da suka Saba Daddy bai biye mata ba yace"Tambayarki zan yi kuma ina so ki Fadamin gaskiya kin ji Intee..!
Daga ita Har Munari sai da suka Dakata da Abunda suke yi suna sauraran Daddy Intee cikin Wani yanayi Lokaci Daya gabanta na Faduwa tace"Insha Allahu Daddy..!
Kai Tsaye yace mata"Daada ce ta Umarceni da bama Dan"uwanki Imran auranki..Ammh na Tambayeki ko kin Amince da hakan..?
Daga ita Har Munari ido suka Fiddo Waje Cikin mamakin kalaman Daddy Intee Sai taji kamar bataji da kyau ba Tana Kifta ido kamar yana gabanta Tace"Daddy me kace...? Wani Dan"uwan nawa..? Ya imu..?
Tafada cikin rawan baki Lokaci Daya Tana kallon Munari Data Washe baki Tsantsan Farinciki ya Cika mata Zuciya na ganin wannan Ranar Intee da Ya Imu as a couple Boyayyiyar Soyayya Zata bayyana kanta don Ubanta ko taki ko ta so.
Inteesar kuwa yanayin Datake ciki Allah ne kadai zai iya Fassara yanayin Sai kuma Ma"abota soyayya yayinda sukaji Labarin mallakan Abun da suke so Zuciyarta ta cika da Haske Farincikin da bata Taba Zato ba ko Tsammani Ya Imu fa shi zai zama Mijinta kai Daada ta Biyasheta Mijinta fa Ya imu..?
Gabadaya bata son idanuwanta ya cika da kwallah ba sai da suka Zubo Munari ta zungureta alamun Tayi mgana Daddy naji,Domin kowa yayi Shuru Daga chan bangaran ana jiran amaar Inteesar Daada kuwa bata Damu ba Tana da kyakyawan yakinin ba Macen data kai Macen da Zataki Imranu karyanta shi kuwa Imu sai da aka Kirata ya samu Faduwar gaba To yanzu in tace bata son sa fa? Sai Daada ta aura ma Khamis ita Tuni yaji Duhu ya mamayemai ganinsa Wata Zuciyar tace ka manta Sagir yace Tana sonka,Kuma in bata sonka meyasa take Fushi Dakai saboda kace zakaje Wajen Sajida?
Daddy ne dayaji Shurun yayi yawa yayi gyaran Murya shima acikin Ransa yana da Full Confident Intee Tana Ra"ayin Imran kodaga yadda Take yawan yin Zencensa Lokaci Bayan Lokaci Umma ma addu"a take acikin Ranta Allah yasa Inteesar ta amsa Domin wannan Hanyar ne kadai Zasu maidama Mami Asma"u martani Sannan ita ai tayi ma Intee sha"awar Yaron Tsayayyen Namiji dazai iya Rike gidansa a kowani Hali Sannan ta Hango Dacewarsu Tun ba yau ba kowa sai addu"an ta amsa yake yi barim ma Yaya Yusuf Sagir dai yasan Komai ma zai tafi kamar yadda yake Fata Inna Bintalo ne kadai Ranta a Hade Tunda yar Fadan Mami Asma"u ce wacce Ke Zaune kawai kamar kankara ya Daskarar da ita Sajida na gefenta Tana Rafzan kuka Khamis kuma kansa na kasa Idanuwansa sun yi jajir ya rasa ma a wata Duniya yake.
Munari nata Zungurin Intee tayi mgana Taki yi tama kasa cewa komai kunya da Farimciki sun Lullubeta Dadday yace"Inteesar ke fa muke jira da Abunda kika ce zamu yi amfani..,!
Inteesar ta kasa mgana kunya take ji Munari na ganin haka tayi Zaraf tace"Daddy bazata iya mgana
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment