Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Shi kuma sai ya kauda kai yana Danne Dariyansa yarinyar nan in ya biyemata Tabaranta Zata Rika yimai kala kala.
Ranar da suka Cika Sati Biyu da Tarewa Baffa Kabiru yazo Kano, Saboda Imran da Inteesar bai Kwana ba Aranar ya Juya bayan ya Taka har Gidan ya Cikasu da Tarin Nasihu da Fatan Alheri Imran bai Taba jin Nadamar abunda ya aikata ba Sai Ranar yaji kunya Baffa Kabiru Rana ta Farko ta kamasa anya ya Chanchanci Wannan Kyautatawar ga Baffa Kabiru..?shida ya Sakarmai ya..?
Bai Rikeka ba sai m karin kyautatawa Daya Biyo ba Imran yaji kunya saai Dai Ya yi Fuska kamar babu Abunda ya Faru Tare da Abba suka zo suka kara ganin Waje suka saka albarka.
Baffa Kabiru duk ya Rame yayi wani Iri kawai Karfin Hali ke tafe Dashi,Ga Damuwar Dayake Ciki ba Asma"u Tare dshi,Ga Khamis ba"a Samun Wayaarsa kwata kwata Ga Sajida Tana makaranta cikin Damuwa duk da bata Fito ta Fadamai ba shi ya sani wannan Raunin nata bamai Cike mata shi Sai Imran shi kuma ya Riga Yayi mata Nisa har Abada.
Wadandan Damuwan suna Ransa Kawai Karfin Hali ne da Tsabar Jaruma ke tafe Dashi yake kuma Tsaye da Kafafunsa alkawari ya Daukar ma Kansa bazai nemi Asma"u ba sai in itace ta Nemesa ba shima din Sai ya yarda da Nadamarta,ko yace bai azabtu da rashinta ba yayi karya Asma"u ai Soyayyah Ta Hadasu ba Kiyayyah ba kuma basu Taba Samun Irin wannan Babban Mtsalan ba sai wannan karom ya sani kamar yadda yake Cikin Wani Hali itama Tana Cikinsa Har kuma zuwa Lokacin bai ji Daga Justice Tafida ba Daman yasan bazai Nemesa ba Ko shi ya Nemess zai ce abunda suka yanke ma kansu Daidai ne shi bazai ce komai ba Tunda Ra"ayinsa ne.
Daga shi sai Umaima sai yan aiki suke Rayuwa Sajida basu gama Exam ba ammh yace mata da Zarar sun gama Ta dawo gida kada ma Tace Zata Zauna a makaranta ita kuma taso ta Cigaba da Zamanta a makaranta Tana Jinyar kanta ba wanda yasan Halin Datake Ciki.suna Waya da Mami Lokaci Bayan Lokaci itama Hawan ajini Duk ya Fadar da ita Karfin Halinta kawai an fa ta Fara Sarewa an Kwarari Wata na Biyu bataji Daga Kabiru ba ta Fara Saki ta Fara Zama Tana yima kanta Tunanin Ina Mafita.?shin ta ina ta Kuskure..?
Shin Tana da Son kai kamar yadda aka Fada..?tana so ta Fahimci kanta da kanta kafin ta yanke ma kanta Hakunci.
Washegarin Ranar da Baffa Kabiru yazo Ranar Monday Daga makaranta Munari ta matsama Inteesar suka Dawo Gidanta Munari ta yi mamaki Data shiga Kitchen din Inteesar ta Bude Fridge Taga Nama da Kifi har sun kankare ga abubuwan amfani nan duk bata taba amfani Dashi ba ai Batama gama mamaki ba sai da inteesar tace mata bata Fara aiki ba Daga dafa Tea shikenan take yi Munari ta Rike baki Tana Fadin"Baki Fara Girki ba..?
Inteesar ta gyadamata kai Tana Fadin"Eh ya imu bai ce na Fara ba kinsan baya cin abinci..Ni kuma kinga Gida muke wuni..,!
Munari ta Girgizakai Tana Fadin"Wlh sai yau na kara yarda kina son ya Imu ammh bakisan Halinsa ba..Shine zai ce ki Fara girki sannan ki Fara..?
Inteesar ta daga mata Kai Tana Fadin"Eh mana kawai bai ba in na Fara ina asara ga bansan kowa anguwan ba Shuru ko almajirai babu kuma Kinsan ba kyau Zubar da abinci..!
Munari ta Saki baki kawai kafin Tace"Uhm..Baki san Waye ya Imu ba..Zaki Shekara shekaruma ahaka Indai shi kike jira yace ki Fara Girki..?shi ina Ruwansa zai ma Taba Tunanin ya kamata ki Faran ne..!
Inteesar tace"Kingane..Allah kinsan bai cika Damuwa da abinci ba im na Dafa na Dinga asaransa kenan..!
Munari bata kara mgana ba Indomie ta Dafa da Hanta taci Ta hada da Lemo Bata yarda Takai Dare ba sanin Halin Imu Wlh bazai maidata Gida ba Dama Ya Yusuf ne zai ce kafarta Data kawota Ta maidata..
Munari na komawa Gida ta Kira Umma ta Fadamata Komai na Halin da Inter ke ciki Domin tasan Umma ce kadai Zata iya mata mgana taji.
Umma ta saka Salati ta Dire Wato Dai Inteesar ta auri miji Daidai da ita in Iskancin ne ya fita zaune kawai suke bamai ma wani Fada.
Ai bata bari Daddy yaji ba ta Kira Inteesar aranar ta mata Fada kaca Kaca Inteesar na Tura baki Tace ma Umma"Shifa Umma baya cin abinci Fruit yake sha kullum sai Tea kuma ai ina Dafamana..kuma bai ce min na Fara Girki ba ni..!
Umma kamar Inteesar na Kusa da ita ta kamata da Duka Zaginta Tayi kamar Tana ganinta Kafin tace"Ji Sakarci Jira Kike sai yace ki Fara..?ai kinsan Wanda kika aura Shine kike Zaune ya Kiraki yace ki Fara Girki kin Taba Dafamai kika mai Tayi yace A"a..!?
Ta girgizamata kai Tana Turl Baki Umma Tace"To banda Wawanci wai kina Zaune bakya girki ko to me kuke ci ko nace ke me kike ci..,?
Inteesar tace"Munari na ke bi zuwa Gida in mukaje Exams..Da Daddare ya Imu yaje ya Daukoni..!
Umma ta kara Saka Salati kafin ta koma Lallashi da ban baki Tana Fadin"Ki Daina zama haka Kin ji Intee yanzu kin Girma Nauyin Ciyar da Mijinki yana kanki..Duk da bayason cin Abinci in kika Girka kika Matsamai ko Saboda ke ai zai ci ko..?
Inteesar tace"Eh zai ci Umma in yaga Dama..!
Umma tace"Ki Fara Girkin ki bakomai Watarana sai Labari ai kina da komai na Cefane ko..!?
Inteesar tace akwai komai Ya Yusuf ya cika mata Fridge da Cefane,Umma aranta tace shima yasan halin kaninsa Inteesar taji Fadan Umma ta kuma Kiraa Mama tace Mata tazo ta kara jan kunnen Inteesar to bata zo ba ammh Ta mata Waya itama ta Kara mata Fada tace Insha Allahu Zata gyara sai dai ta Kira Munari ta Zageta ta ce mata Munafuka Tunda tasan ita ta Hadata da Umma Munari dai tana ta Dariya.
Washegari ta Fara Girki Ranar basu da Exams ana Saka musu Interval Sosai,Sai da Imran ya Dawo Wajen aiki ya iske tayi abinci jalop din Shinkafa da Kifi.
Mamaki ya kamashi yace waya sata girki Tana Shagwaba tace ba Umma bace ta Kirata tana mata Fadan wai bata fara Girki ba kuma ai shine bai ce ta Fara ba..!
Dariya yasha sosai ranar agaban Intee Wai Daman shi Take jira..!ai in ta barsa shifa ya manta da ma wani Girki bai kuma Taba Tunanin yace ta Fara ba sai da yaji Dadin mganar Umma ko Bakomai ai ita Macece Ranar yaci kadan dai Tunda ta Girka sai da yace ta Rika Girkawa Kadan iya Cikinta Tunda ba Lalle bane ya Rika ci kullum
Haka kuwa takeyi kadan Take Dafawa shima Ranar Datake gida in kuma ta shiga makaranta Munari take bi Gida Bata Girki Ranar Umma da kanta ta Kira Abba tace mai ya Faffataki Imran da Inteeear su daina Taremai a Gida ta kawomai Misalai Rashin Dacewar haka Harda na Rashin Girkinta tace Koda Imran yazo shi Namiji ne ita fa Mace ce kuma matarsa Saboda Haka Ta Zauna a Dakin Mijinta wannan Gantalin ta Daina shi Abba kuma ya Fahimceta yace yasan mganinsu ko Daady bata bari yaji Labarin ba tasan Halinsa ba Fahimtar komai zai yi ba


Aikuwa Abba shi da kanshi Ya gaji Daman da Ganin Inteeear da Imran suna Raba Dare a Gidansa kullum Ta dawo makaranta Chan take yada Zango shima in ya Dawo aiki yana nan Abba ya Kirasu yace su Zauna gidansu Inteesar kada ta kara Biyowa in sungama Exam ta Koma Gida shima in ya tashi aiki ya wuce Gida Imran ya Dinga Kumburi wai Abba na Koransa Abba yace Eh ya Koresa in yaji Haushi kda ya kara Dawowa
Imran yaji Haushi Tunda ga Ranar yace ma Inteeesar in taje makaranta Ta Rika Dawowa Gida,Inteesar sai Kumburi Take Imran mamaki ya kamasa Lalle yarinyar nan wato saboda ya sakarmata da Farko Tana yadda Tagama Dama shine ta Fara Rainasa ai kuwa yaFita Butunta bama Tunanin Ya Tsaya ya Lallasheta bai da wannan Lokacin.






*Shakira*
3/28/22, 21:16 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�26*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*

Inteesar kwana Biyu ta Dauka Tana Fushi da Imran kan Hanata zuwa Gidan Abba shi kuwa baima san Tanayi ba in ma Fushi ne tayi ta gama Shi baima nuna ya gane hakan ba Ballatana ta saka ran zai Lallasheta.
Kwana Biyun ko mgana batayi mai Daga gaisuwa shikenan kuma bataje Makaranta ba basu da jarabawa daman Guda biyu ya Rage musu su gama.
Abun ma nata sai ya koma basa Dariya ko Falo ta Fito da Daddare ta gansa Zaune yana aiki sai ta wani Dauke kanta ta zauna chan nesa Tana Taba wayarta ko Tana karatu Duk yana Lura da ita,bai kuma Taba nuna mata yana ma Fahimceta ba.
Bata san wani abu ba Shi ko basu yi mgana ba Ganinta kawai da Tabbacin Ita din matarsa ce wani Sinadiri ne na Farimciki da Samun Salama da Sukuni a Rayuwarsa.
Data gaji ne da kanta ta Hakura Sanin bazai Taba Sauya mgana ba Ballatana Ya Imu dai baisan ka bata rai kan yayi wani abu ya baka Hakuri ko ya Lallasheka ba.
Imran bai taba jin Labarin Soyayyar Sagir da Hafsah data Khalil Data Munari ba shi ya Dauka da aka gama Biki sun kama kansu da rawan Jikin da suka Dinga yi kan yaran sai Ranar Yaji Inteesar na mgana da Hafsah ta Waya suna Zencen mamaki ya gama kamasa aransa yana Tunanin meke Damun Sagir da Khalil ne..?
Banda Tsabar jama kai Raini ina su ina Wadanan yaran..?
Yana Zaune ne saman Kujera Sanye da karamin Wando 3Quater da Karamar Riga mai Gajeren Hannu Laptop dinsa ne a gabansa yana wani aikin da gobe Manager din Branch din Gyadi gyadi zai karba yaji suna mgana ita duk azatonta yana aikinsa baya jinta bata sani ba Duka Motsinta a idonsa ne sai dai yana komai da Taku ne kuma yana da Karfin ji kamar Maciji Daga cikin Wayar ma yana jin Abunda Hafsah take Fadi
Har suka gama waya bai yi mgana ba Inteesar Complex take sha batayi Girki ba Gogan bai Damu ba Daya Dawo Tea kadai yasha Cikinsa ya Cika.
Sai da suka gama kana ya Dago yana kallon Inteesar Dake sanye cikin Wata Riga mai Taushi tashan Iska sai dai Tana da dan Kauri kadan sai dai bata da Dogom Hannu kanta Hula ce ta Zamani ta yanmata ta Rufe kanta Dashi Kafarta Daya kan Daya ta Dora Tana shan Complex dinta.
Suna Hada ido ta Turamai baki Har da Murgudawa Ido ya Ware yana Fadin"Ni kike Harara kuma kike Turamin baki harda Murgudamin Baki Duka ni kadai..!?
Cikin Tabara tace"Ni fa badakai nake ba..!
Yana Sosa Gemunsa yace"Uhn..Kin rainani..?to bada ni kike ba dawa kike..?akwai wani agidan ne bayan ni dake..,?
Yafada yana Tsareta da Kaifaffun Idanuwansa bazata jure ba yasa ta Kauda Kai batayi mgana ba sai Chan Tace"To ba kai bane..Sai kazo ka zauna ko fa Hira bakamin ni in nayi mgana kace zan dameka da Hayaniya kana aiki ne..!
Imran na Cigaba da aikinsa yace"Yes..Ko ba aikin nake yi ba..?in na Biye miki zaki hanani aiki na ne..!
Jin haka yasa bata kara mgana ba Ta Cigaba da shan abun Dake Hannunta Shima haka sai chan yace"Wai wasu yara ne Sagir da Khalil ke soyayya dasu..?
Yafada yana Cigaba da aikinsa bai Dago ba,Inteesar Taji Hira ai sai ta Gyara Zama tana Fadin"Sagir yana son Hafsah..Shi kuma Khalil Munari..Don Allah basu Dace b..?munari tace min yace soon iyayansaa zasu zo ayi mgana Hakama Sagir..!
Mamaki ya Cikashi Cikin karin mamakin ya Dago yana Fadin"Wacece Hafsah..!?
Inteesar tace"Laa..Hafsah Autan Goggo Maimuna,wacce ke karatu nan Dutse tana zaune tare da su Ya Sa"id..!
Kai ya gyada yana Fadin"Su yaranan suke so..?yaran da yaushe aka gama Share musu majina..Khalil da Sagir sun ji Haushi basu da Girma sai na Jikinsu..!
Inteesar ta Rike baki Tana Fadin"Munarin da Hafsah ne yara Ya Imu..!,?
A karkace yace"Eh in ba yara ba manya ne..?
Inteesar tace"Tab..Age mate dina ne fa Nima kenan yarinya ce..?
Imran ya Dage gira yana Fadin"To ai kema Duka Kina Layinsu yarinya ce Baki san abunda kike yi ba..!
Yafada kai Tsaye Inteesar ta Mike Tsaye Har tana neman Ture Mug din Dake Hannunta Kan Centet Table din Dake gabansa ta Dankwar dashi Tana Fadin"Ni ce ma yarinya..?ni ce bansan Abunda nake yi ba..?
Tafada kamar zatayi kuka Imran ya Hade rai yana Kokarin Danne Dariyansa yace"Eh mana..!
Ai sai Inteesar ta Fara Buga Kafa tana Tsallen Shagwaba da kukan karya Tana Fadin"Ni Wlh ba yarinya bace..Babba ce Tunda nayi aure..!
Mirmishi yayi yana Kokarin Boye Dariyansa yana kallonta yace'"Ai wannan aikin ma da kike yi na yaran ne..Kuma kin ce ke Babba ce Tunda kin yi aure ko..?
Kai ta gyadamai Tana Jan Hanci kamar mai kukan gaske,Kansa yake Shafawa yana Fadin"Ai fa ga Babba nan..Sannu Babba..!
Yake Fada yana Dariya Inteesar an samu Waje kawai sai ta koma ta Zauna Dirshan saman Cafet ta saka kuka Baki ya saki yana kallonta Kafin ya Gimtse Fuska yana Fadin'"Lalle ma yarinyar nan Duka kike so inaganin ba Lallashi ba ko..!?
tsayawa Tayi da kukan Tana kallonsa kafin Ta waro ido Tana Fadin"Duka..?
Kai ya gyada mata yana Fadin"Eh mana nan fa ba Umma ba Daddy..Wlh kika Dameni Zanemiki jiki Zan yi.U..!
Ai bai gama mgana ba Ta Mike da Sauri ta Dauki Wayarta da Mug din Datake shan Complez suma sum Ta Shige Kitchen bata Dade ba ta Fito ko Gud Night din ma batacemai ta Shige Dakinta Dariya yayi yana Fadin"Better..!
Domin bai Shiryama Rigimarta ba a wannan Lokacin Ita batasan Tana Dagulamai lissafi bane Shiyasa take kara yin wasu abubuwan.
Abun na Ransa bai manta ba Washegari Daya Fita aiki Bayan sun tashi Lunch ya Kira Sagir yana Cemai yanzu banda Tsabar Raini da Zubar da Girma ina su ina soyayya da yaran da ko Hankalin kansu basu gama mallaka ba..?
Ga mata nan manya masu Hankali acikin Gari sai su yarda Girman ku kuna Biyema yara..!
Sagir yayi Dariya kamar me kafin yace eh sun ji shi ba yarinyar ya aura ba..?Sanda yake makale Murya yana Fadin don Allah Baby in d'an kara suna ina..?
Imran ya Rike baki yana Dariya yace"Sangiru ka zama Dan iska In kara uwar me..?
Sagir na Dariya yace"Koma miye ka sani in kuma kana son na Fada ne to..!
Imran yace"Basai ka Fadama ba kada Kasa Kunnena ya Toshe..Sangiru Allah ya Shirya ka Zama D'an iska har kana san Abunda miji da mata suke yi..
Gabadayamsu Dariya suke yi Sagir yace"Bamu sani ba sai kai Tunda kayi aure .!
Imran yace"Kai dallah..Ni fa bana son Raini sam.Kagani nan ko zan amshi Hakkina umarni zan bada kawai..Allah ya kyauta in zauna ina Wani Rage murya kamar wani Sakarai..!
Sagir yace"Uhm..Lokaci na zuwa..Lokacin da zaka gane Karuwa ba yar iska bace..!
Imran yace"Wlh yar iska ce..!
Sagir yace"A"ah fa Sana"arta take yi kada kace haka..!
Gabadayansu Dariya suke yi Daga Karshe Imu yace Wlh su nemi mai musu Best friend Allah ya kyauta yaje Cikin yara yana Bude baki da Girmansa,da komai.
Sagir yace bakomai sun ji gari da yawa maye ai baya ci kansa ba kuma ko bai zama Best friend ba ai ya Zama Babban yaya..!
Haka ya Kira Khalil yana gayamai Shima cewa yayi ai karamar yarinyar ya aura Daga Wajensa suka koya shiyasa Haka shima yace mai Bazai je Cikin yara yana mgana ba in sun neni manyan mata shikenan yana Tsausaya musu ga kayan Raini ga Dawainiya maimakon Ta Kula Dakai kai ne Zaka koma kana kula da ita Dukkansu sukace mai sun ji kuma sun gani sun gode da Shawara ji ya Zama Dole yadda ne ba Dole ba.
Khalil sai da ya bama Munari Labari batayi mamaki ba Sanin Halin Ya Imu Tace ai ita kanta Inteesar Wahalar sa Take sha Kafin ta Samu Lagonsa sai Ta yi kamar tanayi irin su kana yi ne kamar Baka yi ba irin Mazan da suke Laushi bane lokaci Daya,Ammh Zai yi Laushin In Tafiya Tayi Tafiya In ji Khalil.
Ranar Friday ta kama Zasu yi Second to d the Last Paper dinsu Sai Tafiya Hutun da zasu dawo su shiga Aji Biyu sai karfe 12pm suke da Exam gida Imran ya Barta In Lokaci yayi Zata Kulle Gida ta Hau adaidaita Tatafi makaranta Bata Tambayashi Zuwa Gidan Abba ba sai da ya Tafi Wajen aiki ta Kirashi bai Dauka ba sai ta Turamai Sako Don Allah ya barta Tabi Munari zuwa Gidan Abba.
Daya gani sai ya Shareta Aiki yayi mai yawa sai da ta kara Kiransa Sannan Mganar ta dawomai Sako ya Tura mata Cikin Gatsensa "Bana ce kada ki kara Zuwa ba..?
To ki Tafi din..!
Haka ya Tura mata ita kuma Tana ganin haka sai ta Zata ya barta ne suna gama Jarabawa tace Zata bi Munari zuwa gida Munari tace Ya Imun ya barta ne..?saboda ai aganbansu Abba yace kada su kara zuwa nan kusa Har Imran din yayi Fushi Daman Haka Abba yake so su Dauke Kafa na kwana Biyu su Zauna agidansu su kara Fahintar juna.
Sai Inteeaar tace eh ya barta Munari bata kara mgana suka tafi Abba baya nan yana cikin makaranta sai da ya dawo ya ganta Dayayi mgana Tace Imu yace tazo in ya taso aiki Zai Zo ya Dauketa Abba yayi mamaki yafa san Halin Imu bazai Huce nan kusa ba ammh dai bai ce komai ba.
Har bayan Isha"i Shuru ba Imran ba Dalilinsa kuma a ka"idarsa yana Tashi aiki Hudu zuwa Biyar na yammah in ya Tsaya wani abun ne Shida na yammah Kafin mangariba ya iso ammh Yau shuru Inteesar Tayi ta Kiransa bai Dauka ba sai idonta ya Raina Fata Munari ta Kalleta Tana Fadin"Wai Daman bai barki ba kika Taho..!
Inteesar na ta Fito da Wayarta Tana Dubo Test din da yayi mata ta Nuna ma Munari Tana Fadin"Shifa yace naje kalli ma ki gani..!
Munari ta amsa ta karanta Cikin Mamaki ta kalli Inteesar Tana Fadin"uhm..ni ban ma san me zan ce miki ba..?Kalli fa abunda yace Keji din..?shine kuma kika je din..?Allah ne kadai yasan yadda Kika Batamai rai kila don ma kene Da yau wani ne ko Wata da ya Raina kansa..!
Inteesar Idonta ya Raina Fata Tayi Shuru ta kasa mgana Munari na Kallonta sai ta bata Tsausayi ya Imu naWahalar da Inteesar ta rasa ta yadda Zata gayamata ta gane komai itama Ta Dauki Hanyar Ramawa bata karance karance bata damu davSocial media ba ballatana ta san wasu abubuwan gata kadai ta sani ita Tana Karance karancen Littafan Hausa Dana Turanci Tana kuma Mu"amala da Social media Tafi Inteesar Bude ido sosai kuma ta Fita Shiga Mutane..
Ganin ta Damu yasa Munari taje ta Fadama Abba yadda akayi Abba bai ce komai ba Daman yasan Za"a Rina Ya Yusuf na gefe yana Fadin"Shi yama yi Auran Har yau bai yi Hankali ba..?
Abba ya Daga waya ya Kirashi bai Daga Kiran ba sai da ta Katse kana ya Kira Daga baya Abba bai ma Tsaya amsa Gaisuwarsa ba yafara Fadin"kana ina..?
Imran ya Dakuna Fuska yana Tsaye a Falon gidansa Roban Ruwa Hannunsa Guda Dayan kuma yana Rike da Waya yace"Ina Gida Abba..!
Abbba yace"Ka manta da Matarka ne ka wuce gida baka zo ka Dauketa ba..?
Imran yace"kafar da ya kawota sai ya Maidota Abba..ni ai ban aikota ba..!
Abba yace"Ni kake Fadama haka Imran..?wato Kafarta ta maidota ko..!Nagode..!
Imran yadan Bude ido yana Fadin
"Abba kada ka Dauki mganar nan da Zafi..Ba dakai nake ba..Ni ban ce tazo ba ta Raina ni ne Dole ne sai abunda Take so zan yi akoda yaushe..?nace mata Kada taje bataji mgana ta ba ta Tafi ai tunda ta iya gaban kanta sai ta Dawo da kanta..!
Abba yace"Kayi mata hankali Ita yarinya ce..!
Ran Imran ya kara baci yace"In ita yarinya ne sai ni kuma Shikenan sai na Lalace akanta..?Ni Bata mata Rai zan yi bana son wasa meyasa batajin mgana ne..!
Abba yace"Kayi Hakuri kazo ka Dauketa..Yaushe Zata rika Fahimtar ka kana mata mgana Gatse gatsen ka Kwata Kwata kai Imran baka Laushi..!
Imran yace"Abba nayi Laushi Saboda ita..Bata Samu Compt Imran ba Half Ta samu..kuma na riga na Rantse ni ban Zo na Dauketa ba kuma bata isa ta Sani Kaffara ba..!
Abba ya Bude baki kafin yace"Har nima ko..!
Cikin Dakuna Fuska yace"Ni fa Abba ban ce kai ba..!
Abba ya gyada kai yana Fadin"Ka dinga dai Hakuri kai Babba ne ka Girmeta..Ka Rika Tunawa sai ka Sadda kan ka wani Lokaci ita yarinya ce akwai kuruciya Tare da ita..!
Imu Hade rai aransa yana Fadin Wato ya Sadda kai ya Zama Sakarai Allah ya Tsareshi..!
Abba yace"Yusuf zai kawota..Zan mata Fada kada ka mata wannan Hargagin naka nasan Halinka..!
Imran ok kawai yace ya Katse Kiran Ransa na baci kokarin ma Daidaita kansa yake In yace abu baya so kuma ana Damunsa akai Abba fa da kansa yace kada su dawomai Gida nan kusa Shi mutum ne Dake Daraja Kalaman mutane masu Daraja awajensa Musamman Abba Shi bama da Wata Manufa yace mata kada taje ba ya bari ne sai Abba ya nemesu da kansu suma su Rama bacin Ransa Daya daya Dawo bai ganta ba wato ke je din Taje din Sai Taga abunda zai Faru..!
Abba Fada yayi ma Inteesar Sosai Tayi Narai Narai kana Abba ya Umarci Ya Yusuf Daya maidata Gida Tace Munari Tazota Rakata Munari tace Allah ya Tsareta Ta Rakata Ya Imu ya Hada da ita,Tana ma Rokonta Kada ma a bayaninta ta Kira sunanta
Inteesar dai Tasan yau sai ta sani da Fada Ya Yusuf ya Dauketa ya kaita Gidan ya kulle gidan ta Ciki sai da Ya Yusuf ya Kirasa a waya kana ya Fito ya Bude mata bai Shigo da Motar ba Daganan yayi musu Sallama ya Juya Imran yana wani Cin mgani aransa yace Yau Inteesar ta Zama nama kenan..
Shi ya Tsaya Rufe Gidan ita kuma Tayi Sadaf Sadaf ta Shige Cikin Gidan Tana Kokarin Shiga Dakinta ya Shigo Falon Cikin Dakiyarsa yace"Zo nan..!
Cak ta Tsaya gabanta na Fadi kafin ta Juyo bata iya Dagowa ba kanta na kasa Tana wasa da adon Gyalen dake Jikinta Daga sama Har Kasa ya Kalleta Kafin yace"Sagir bai baki Sako ba..?
Kai ta girgizamai Cikin Dakuna Fuska ya Danna ma Sagir Kira ta Wayar Dake Hannunsa Buga Daya ana Biyu ya Daga Yana Fadin"Ango kasha Kamshi..!
Imran yayi Tsaki yana Fadin"mallan ina Aikin da na baka..?
Sagir yace"Wani aiki kuma da Daddaran nan..?
Imran yace"Hijabin da na baka kudi a Dinkama MARYAM..!
Sagir yace"Au na manta kasan bani ke yi ba Kasuwa nakai Wajen wani abokina yana Dinkasu kala kala bari gobe zan Tabosa naji ko ya gama Hala Baka son Tana saka Mayafi ne..?
Banga Laifinka ba kada Maxa su kalle ma yar babynka..!
Imran Tsaki yaja ya Datse Kiran Yabar Sagir da Dariya Inteesar na Gefe Tana Sauraransa Zama yayi saman Kujera ya Dora Kafa Daya kan Daya yana Sanye da Riga da Wando Fari da baki.
Kallonta yake yi yana Kokarin Daidaita kansa Cikin Kaushinsa yace"Yaushe kika Fara rainani da Har Zan ce kiyi abu kiki yi..Sai abunda kika ga Dama Zakiyi..?
Yauahe muka Fara wannan Dake..?
Ya Fada Cikin Tsawa da Daga Murya Inteesar da Tuni Idonta ya Ciko da Hawaye ta ce"Kai fa..kai fa kace naje..!
Cikin Hararanta yace"Yaushe nace kije..?cewa nayi ki je din Shine kuma Saboda Tsabar kin Raina ni sai kika je din ko..?
Inteesar na Sosan Idonta tace"Naji to kace naje kuma...!
Ransa ne ya kara baci ya daka Mata Tsawa yana Fadin"Shup up anan Wajen in kika kara mgana Kika Harzukani Zan tashi nayi kasa kasa Dake anan Wajen..!.
Jin haka yasa ta Toshe bakinta da Mayafinta Tana Hawaye bata son Fada a Rayuwarta.
Cikin Fushi yace"Bana so..Bana so..Ina mgana kina mgana Raini ne..Zaki cemin ke bakisan gatse bane..?da zaki kwashi Kafafu ki Tafi..?Kina Biyema wannan yarinyar ko..?munari Daya kuke da ita..?ke fa matar aure ce nan ne gidanki itama Chan ne gidansu Ammh baki da aiki sai Biyemata sai anyi mgana Kice Munari Munari kaza kaza..Munarin Daya kuke da ita nace..?
Yafada Cikim Tsawa ai Sai Inteesar ta Saki kukanta cikin kukan Tace"Ni bansani ba..Wlh bansan Gatse kamin ba..kana ta min Fada..Ni bana son Fada..!
Take Fada kafin ta Shige Daki da Gudu Tana kuka Baki ya Saki yana kallonta Wato ita batasan Fada..?to ya barta ta Cigaba da iskanci kenan bai Mata Fada ba,daya Daga Cikin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment