Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

take tana kyafci tana Girgiza jiki da kafa,Wayace a Hannunta tana ta Kiran Baffa Kabiru bai Dauka ba suna Gaban Daada,bazai iya Daukan Wayanta ba yasan Rigima ce kwance a wajen Mami Asma"u.
Inteesar Dole yasa ta Fito Falo Tunda Munari sun mtsa mata sai ta Fito,ita kuma Ranta baya mata Dadi,sannan bata son ta Hadu da Khamis yana ta Damunta da waya da Sako ko ta kansa batabi ba..
Koda ta Fito duka an hadu a falon Mazan da matan su inna maimunatu dai suna Dakin Daada su Aneesa ne dasu Anty Safiya kowacce tana Tare da mijinta sai su Munari dake Hotuna,Khamis na Dakin Mami yana bata baki har ya gama mgana kanzil batace ba,har yagaji ya Fito nan yayi Tozali da Inteesar ya kafeta da ido yana kallonta Yarinyar nan tana bashi Wahala sosai gabadaya soyayyarta ya gama kasarashi sai dai tanayin wani abu kamar bata gane ina ya Dosa ba..
Suna Hada ido ta Hada rai ta kauda kanta kamar bata ganshi ba ta Dauko wayarta tana Dannawa ba Domin tana wanu abu ba Imran take Tunani bata gansa ba wata Zuciya tace"Ina Ruwan ki kumi dashi..Yanzu ai baida Lokacinki Tunda yayi aure. !
Tuna haka yasa taji zaman Wajen ya gagareta tatashi tana Shirin Tafiya Zainab din Inna Maimunatu ta jawo tace suyi Hoto bata da yarda zatayi Dole ta tsaya Khamis kuma yana binta da kallon Sha"awa da kauna ya Nufi wajen su Basheer dake zaune suna Hira gefe kuma Matayensu Sa"id ne sun ci gayu suna ta Hira gwanin Sha"awa.
Suna ta Hotuna Kada Munari da Hafsah suji Labari,Munari ce uwar kankaba tace afito musu da Amarya suyi hoto Hafsah tasan Hali bata je ba Umaima ce taje ita dasu Hamida suka Fito da Sajidan Daga Wajen Mami Asma"u wacce ke cika tana batsewa kala bata kara Furtama kowa ba Bata so tayi mgana saboda in ta Bude baki tace wani abu zata iya Fashewa da kuka kuma Faruwar hakan kamar Imran yaci nasara akanta kenan Baffa Kabiru take jira shine Zata saukema gabadaya Bala"in Dake Cinta.
Sun Fito da Sajida nan Falo waje ya Kaure da Gudan ga Amarya su Sa"id na Dariya Yusuf da Sagir suna kallon Sajida sukace masha Allah tayi kyau matuka,Inda Imran mai Wayau ne basu ga aibun Sajida ba mace duk inda ake neman takai,Khamis yazo ya Rumgumeta ganin Inteesar a wajen Har dashi ya Dinga shiga Hoton Bakinciki ya cika Inteesar tana so ta gudu Munari ta Hanata,Ga Waleedan Anty Aneesa ta makalemata sai ta Dauketa Kallon Sajida take tana mamakin ganin ta ko Damuwa acikin Idanuwanta Fuskarta bayyana wani Damuwa ba,sun kalli juna ido Cikin ido kafin kowa ya Dauke kansa,Abunda ke bama su Inteesar da Hafsah mamaki ganin Sajida tana mgana da Munari har da mata Dariya Inteesar Ranta wani kuna yake yi wato Saboda ta auri Dan"uwanta Ita tasan Darajanta,Inda ma mutane zasu Lura Hawaye ya cika kwarmin idanuwanta Tayi saurin Sharewa kada wani ya gani.
Sun cigaba da yin Hotuna har Da su Sa"id da suka taso ana ta Family Picture,Khamis sai da yasan yadda yayi ya dawo kusa da Inteesar ya Riko Hannunta bata zata ba da Sauri ta Dago tana kallonsa Gira ya Dagamata Lokaci Daya yana marairaicemata kamar zai yi kuka kwace hannunta tayi tana Hararansa Haushi Rike mata Hannun da yayi taji Har Cikin zuciyarta.
Mtsawa tayi daga kusa dashi ta koma Kusa da Hafsah ganin munari na kusa da Sajida,wacce ke ta wurga ido tana Neman inda zata ga Imran bata gansa ba bata so kuma tayi mgana aga Zakewarta sai tayi shuru da bakinta.
Kiran Sallar La"asar da Fitowarsu Abba ya Dakatar da Hotunan suka ce mazan su fito su tafi masallaci matan kuma suma suyi sallar acikin gida.
Baffa Kabiru sai Lokacin ya Shiga Inda Mami Asma"u take tana ganin Shigowarsa Rauninta ya bayyana ta Mike ta isa gabansa Tana Fadin"Yanzu Kabir kana gani aka Daura ma yarka aure da wannan Dan iskan yaron.?Kana ji kana gani aka yi ma yarka auran kaskanci ammh ka kasa cewa komai ko Kabiru..?
Tafada tana Fashewa da kukan Takaichin Dake Cinta acikin Zuciyarta Saman kirjinsa ta fada Tana Dukansa Riketa yayi yana jin pain din Datake ji Cikin Lallashi yace"Ma"u ya zan yi..?Ni ban isa na Tsallake Umarnin Daada ba..Kada kuma ki manta Abubakar Dan"uwana ne Dana saki Nono ya kama Taya zan nuna ina gudin hada jininsa da nawa..?ya zai ji acikin Ransa..? Ammh wlh ni kaina Ma"u banso wannan Hadin ba Tunda kikaga ban yi mgana ba bani da Mafita ne acikim al"amarin..!
Ya karishe Fada yana riketa acikin jikinsa bata iya cewa komai ba sai kuka Bakimciki ya cika ta gani take Cika bakinta ya zama na banza Daada ta gama Cutar da ita cutar da bazata manta ba Har Abada.
Dakyar ya iya Lallashinta Tayi shuru da cewa bari yaje suyi salla su dawo zasu yi mgana kana ta yarda ta sakeshi ya Fice ta koma ta zauna tana Sharan kwallah jira take yazo suyi mgana Gobe goben nan bata kaunar ta kara Kwana agarin Dukku Har Daadan bata kaunar gani Zata Tarkata ya"yanta ta tafi dasu Sai taji kuma ta gani wanda ya isa yazo ya Dauki Sajidan Wlh sai dai ya gaji da auran ya Saketa tana Fatan Tsautsayi ya sa ya kwaso kafafunsa zuwa Abuja A nan ne Zata nuna mai ikon Barrister Asma"u..!
Imran sai bayan da kayi sallar La"asar kana ya Farka Daga Barcin Daya kwasheshi cikin kasala ya Mike ya Fada Tiolet ya Dauro alwala yazo ya saka Riga da wando baki da Fari,kana yayi Sallarsa acikin gida tunda an riga anyi Sallar,sai Lokacin ya Fito Daga Dakin Falon ba kowa duk suna Dakuna suna Sallah Hafsah kadai ya gani Data gaishesa Sai da ya juyo yana kallinta asaman Lebensa ya amsa kafin ya kada kai ya Fita Haraban gidan Inteesar yake son gani bai ganta ba Tun dazu din nan Daya hangota ta Boye kanta.
Yana Duba wayarsa su Basheer suka shigo gidan sun dawo Daga masaalaci
Ganin su yasa ya koma Chan gefe yayi kamar yana waya saboda bayason mgana da wani suna ba wanda yabi ta kansa Harta kuwa da Sagir suka Shiigewarsu cikin Gida sai da yaga Shigarsu kana ya Sauke Wayar Daga kunnensa ya Lalubo lambar Inteesar ya Tura mata sako.

"Kina ina ne..? Ki fito na ganki..!

Ya tura mata Ya koma ya Coge yana Jiranta,Inteesar kuwa Ta idar da Sallar kenan tana zaune kan Sallaya taji Shigowr sako Ta zata Khamis ne yasa batabi takai ba sai da mike Daga Kan Sallaya ta karisa bakin gado ta Zauna ta Dauki wayar kana taga sunan Imran har jikinta na rawa wajen Budewa abunda tagani ne ya Kara bata mata rai Baki ta Tura kamar Yana ganinta afili tace"Ina ruwanka dani..Kaje kaga matarka..!
Haka tafada Har sai da Munari Dake Zaune ta waigo tana kallonta ganin haka yasa Inteesar din ta Mike ta koma chan kusa da Tiolet ta turama Imran Sako.

"Ina daki ban ji dadi.."

Daman jiran sakonta yake yi yasa Yana Shigowa ya Duba Shuru yayi yana wani Tunani Jikinsa yayi sanyi bata da lafiya Har yanzu..!?
Haka ya Tambayi kansa da Sauri ya Tura mata sako.

"Ki fito naga yanayin jikin naki yanzu..Bana son gaddama do as i say malama..!

Ya tura mata Dataga sakonsa Sai da tayi yar dariya Imran bazai taba Sauyama ba.
Tura baki tayi kamar yana kallonta ta Turamai.

"Kana ina ne..?

Kamar yana jiranta ya Turomata.

"Ina Waje..ina jiranki..!

Ganin sakon sa yasa ta Dauki Mayafinta ta yafa Munari ta kalleta Tana Fadin"Ina zaki Kuma?
Tana yamutsa Fuska tace"Nan waje zani yanzu zan dawo..!
Hafsah da Munari suka kalli juna kafin su tafa suna fadin"In tayi wari zamu ji..!
Kallonsu tayi taja karamin Tsaki ta Fice,suka Bita da kallo suna Dariya su azaton su da Khamis suke mgana ta Messages kuma Wajensa Zataje shiyasa suke mata Dariyan sunsan komai.
Bata bi ta kansu ba ta Fice Taso ba wanda zai ga Fitarta sai dai duka suna Zaune acikin Falon Har dasu Abba Baffa Kabiru ne baya nan yana Dakin Da Mami Ta Sauka Sajida kuma tana Dakin Daada.
Wajen Daddy da Abba ta nufa ta Rankwafa ta gaida su,suka amsa mata Cikib Fara"a Abba ya Dafa kanta yana saka mata albarka Duk Khamis na Lura da ita Tun Fitowarta Mikewa Tayu tace Abba da Daddy bari ta zo yanzu zata dawo basu damu ba sanin ina Zata ba ta fice Daga Falon zuwa Haraban gidan.
Tafara Waige waigen Neman Imran kenan Khamis yasha gabanta da Sauri Har yana neman gugan Jikinta da Sauri Taja baya tana Binsa da kallo mai kama da Harara Cikin sanyinta tace"Lafiya?
Lamgwabe kai yayi yana Fadin"Kinsan ai me ya kawo ni wajen ki ko..? Look inteesar na gaji da Horan da kike min na Tabbata ke ba yarinya bace kinsan Abunda nake nufi kada mu bama junanmu Wahala..I love u Tun Ranar dana Fara ganinki sonki yana bani Wahala kuma da aure nake sonki ina so ki bani Dama mu Fahimci juna kafin iyayanmu suji mganar Daga Baya Plz.!
Ya karishe Fada yana narka mata wani irin kallo na Kauna Taso ta Yi mai Tsaki ne sai kuma ta fasa Tsuke bakinta tayi kafin tace"Ni ba yanzu zan yi Aure ba am sorry Karatu nake yi..!
Tana gama Fadin haka ta juya Zata wuce Caraf ya saka Hannunsa ya Damki Hannunta Wajen ta Waigo da Sauri gyalenta ya Zame daga saman kanta zuwa Kafadanta Gashin kanta ya bayyana wanda ke Tsife sai dai ta Nannadeshi Cikin band dinta
Juyowar da zatayi suka Hada Ido Hudu da Imran Dake Tsaye ta gefen Khamis Hannayensa goge a kirjinsa Zuciyarsa tana wani bugawa Tun Lokacin da Inteesar ta Fito ya ganta ya taka zuwa Wajenta ne sai ga Khamis yana bayansa Duk abunda ya Fada a kunnensa Bai taba jin Bakinciki ba irin na yau da Khamis yace wai yana son Inteesar yana kokarin Controling din bacin Ransa ne yaga ta juya shi kuma ya Riko mata Hannu gyalenta ya Zame gashin kanta ya Bayyana Agaban Wani katon Namijin yana kallon Hannunta Daya Rike ga kuma Mayatacen kallon Dayake Bin Inteesar dashi Kamar Zai Lasheta Tuni Imran yaji kirjinsa na Harbawa Jijiyoyin kansa sun mike Idanuwansa sun Rufe radadi ya cika Ransa na ganin wani rike da hannun Inteesar kuma yana kallon surar jikinta.









*Shakira..*
3/22/22, 23:14 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�8*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*


Khamis da baisan da wanzuwar Imran Daga bayansa ba ya shagala da kallon kyakyawan Surar Inteesar da gashin daya kwanto ta saman Goshinta ya tafi dashi har baisan Sadda ya Furta"Wow..Beatifully.!
Yafada Cikin wata Murya mai cike da Muradi mai girma.
Imran Dake bayansa wani Takaici ne ya kara kamasa Tuni naman Goshinsa ya Tattare ya koma Waje Daya Inteesar yake kallo wace ke kallonsa Cikin Wani yanayi Dayake kara Wutar bacin Ransa.
Kokarin Daidaita kansa yake shi yasa bai yi mgana ba Hannu kawai ya Saka Cak ya Dauke hannun Khamis dake Rike da Inteesar Cikin ZAfinsa har sai Da wajen yarfar da hannun Khamis yayi baya Ya fadi kasa Dabas Saboda Imran din da karfi ya Wanchakalar da Hannun nashi,Shi kuma ya saki Jikinsa ne saboda baisan Haka Zata Faru ba Shiyasa ya kasa Rike kansa Har Sai da yakai kasa.
Da mamaki ya Dago suka Hada ido da Imran Dakemai wani kallo na rainin Wayau da kaskasci.
Saurin Mikewa yayi shima Ransa ya baci Cikin Bacin rai yace"Mallam Lafiya kazo ka Tureni na Fadi kasa..?
Imran ya Kara Hade rai bai yi mgana ba Ganin haka sai Ran khamis ya Fara Tafasa yana ganin Karshen Rainin Hankali Imran ya gama Rainasa shiyasa yakarisa gabansa ya saka Hannu ya Daki Kirjinsa yana Fadin"Mallam ina mgana ka kyaleni..? Wa ya baka izinin Tabamin hannu Har kana Tureni..?
Yafada Shima Fararan Idanuwansa sun Fara Juyewa zuwa Jajaye Alluran Sojojin shima sun Fara aiki ajikinsa.
Imran Dayake Cije baki Yana kokarin Daidaita Bacin ransa yaki cewa komai illah Inteesar ya kalla wacce Ta Fara Fiki Fiki da ido tana neman yin kuka ganin Abunda ke faruwa.
Cikin Dakiyarsa yace"Ki koma Cikin Gida..!
Tsayawa tayi tana kallonsa bata tafi ba Khamis ya kalleta yana Fadin"Tatafi ina..?Ina Ruwanka da ita ai bakai ka Kirata ba..Inteesar ba inda Zaki ok..?
Yafada shima yana bata Umarni Sai kawai ta Tsaya ta kasa gaba Ballatana Baya,Ran Imran sai ya kara Baci Zuciyarsa ta Fara Tafarfasa Cikin Daka mata Tsawa yace"Nace ki bar nan..!
Yafada Cikin Dakakkiyar Muryansa Cikin Fushi Daya Tsorata Inteesar ta Juya Zata Koma Cikin Gida tana Kokarin Boye kukanta da Hannunta Bayan ta saka Mayafin jikinta Ta Rufe bakinta dashi saboda kada kukanta ya Fito Khamis na ganin haka yayi Saurin Riko Hannunta again yana Fadin"Ba inda Zataje..Zan gani in kai ka Kirata in kuma Zaman ka takeyi Acikin gidanan..Haba rainin wayau ka ya Isa haka..Kana ganin cewa tsoron ka Kowa yake ji shiyasa kake yin Abu ba"a Tanka maka..? Wlh ina Daidai da Duk Abunda kake takama dashi Inteesar ba inda Zataje sai kayi abunda Zakayi in ka Isa..!
Ya Karishe Fada Cikin Bacin Rai yana kuma Rike da Hannun Inteesar wacce take kokarin kwacewa ganin yadda Imran yake kallon Hannun nata kamar Zuciyarsa Zata Buga ya mutu gabadaya Cikin Kokarin Daidaita kansa yake fadin"Sakar mata Hannu..!
Khamis ya kallesa yana Fadin"In naki fa..?Ko kana Tsammamin zaka Dakeni ne..?
Imran ya Taune Lebensa na kasa Kafin Cikin Tsawa yace"Nace ka Sake mata Hannu Kafin Raina ya baci..Nayi maka Biji Biji anan wajen..!
Khamis ya taresa Shima Cikin Tsawa yana Fadin"Naki na saketa din kayi Abuda zakayi..Ina Ruwanka in narike mata Hannun..?Au sonta kake yi..? Lalle baka da Tunani Shaye shayenka sun gayamaka karya in ka manta bari na Tuna maka Yau aka Daura maka aure da Sajida kanwata Ko agarin gaba gaba muke ana barin Halas ko don kunya..Ko kana so baka so Inteesar mallakina ne ina sonta kuma Zan aureta ita din Tawace..!
Ya karishe Fada yana kara Riketa wannan karon harda Kafadunta duka Biyu.
Ai Imran sai yaji wani Tukikin Takaichi acikin Raina Duhu ya mamaye idanuwansa na ganin yadda Khamis ya Rike Inteesar baisan Sadda ya isa gabansa ba ya saka Hannu ya Daki Kirjinsa da Hannunsa ya Kara Bangajesa da Karfin da sai da Ya kara Faduwa duk yadda ya kara saka Karfinsa Sai da Imran yadin ya kaisa Kasa Inteesar ta ja gefe ta fashe da kuka Jikinta ya fara Imran Cikin Dakakkiyar Muryansa Ya na nuna Khamis daya yatsa yake fadin"In ka kara Saka kazamin hannun nan naka ka Tabata wlh sai ka Raina kanka..?ubanta ne kai da zaka rika Tabata duk sanda kaga Dama..?Kuma daka ke fadin Shaye shaye bai fadamin gaskiya ba da kudin tsoho ko da na Tsohuwa nake shaye shayen..? Auran kanwarka kuma ninace ina sonta..? Nace ni nace ina sonta balle kazo kana gayamin mganar banza..Har Abada wannan yarinyar bata isa Imran ya sota ba Domin bata kai wannan mtsayin ba..Kuma na Rantse da Allah daya Halliceni in ka kara Cewa Inteesar taka ce sai nayi maka Dukan Mutuwa acikin gidan nan..Bazata taba zama taka ba Har Abada..!
Ya karishe Fada yana Kumfar baki,Khamis da shima idonsa ya Rufe ya Mike jikinsa na mazari ya Fara Ture Imran yana Fadin"Kaima sonta kake yi kenan..?mallan sai ka Fadamin kishi kake yi domin na Tabata? To baka isa ba Inteesar da kamilalle ta dace ba Dan iska Sauran Shaye. shaye ba..Gashi na Riketa in baka Min Duka ba wlh baka Haifu Cikin uwa da u.!
Bai gama Rufe baki ba Yaji Saukar Naushi a bakinsa yana kokarin rike hannun inteesar yaji wannan Dukan Daya sa sai da ya Duke yana Dagowa Bakinsa ya fashe sai jini Ya duba ya gani Hankalinsa ya tashi ya mike shima yakai ma Imran duka shima abaki shima nan da nan bakinsa ya fashe ganin yadda suka Fitar ma da kansu Jini yasa Zuciyar zaratan maza ta Fara Zalzal akan kishi Batare da bata Lokaci ba suka Sarke da Mumman Dambe Kowanne yana Dukan Dan"uwansa duk inda ya Samu da Karfin da Allah ya basu..
Inteeasar ta Dora hannu asaman kanta ta kwarara ihu dayaja Hankalin Megadi Dake bakin get ya Zuro da gudu ganin abunda ke Faruwa,yana kokarin Rabasu ammh ya kasa Inteesar ganin haka yasa ta Nufi Cikin Falon gidan tana Ihun Kiran sunan Daddy da Abba.
Wanda daman duk suna zaune afalon suka fara jin Hayaniya sai ga Inteesar ta shigo tana kuka tana Haki Lokaci Daya tana Kiran sunan Abba da Daddy gabadayansu suka Mike Har wadanda ke Daki sai da suka Fito,Cikin Tashin Hankali Abba da Daddy suka Isa ga Inteesar suna Tambayanta meke faruwa Cikin Tashin Hankali..
Tana kuka Tana nuna musu waje Cikin Rawan baki take fadin"Abba...Abb..Imran..!
Hankalin Abba ya tashi ya Riketa yana Fadin"Ki natsu Inteesar Ki Fadamana me ya faru da Imran din..?
Inteesar ta girgiza kai Cikin Muryan kuka tana fadin"Abba Imran suna Fada da Khamis a waje..!
Ido kowa ya zaro Cikin kidima kafin kowa yayi waje da sauri Abba kamar zai Fadi harta su Munari ba"a barsu abaya ba Baffa Kabiru da Mami Asma"u dake cikin Daki tanamai Rigiman gobe su koma Abuja sukaji kukan Inteesar suka Fito agabansu ta Fadi suna Dambe da Khamis ai Mami Asma"u kamar ta Kife Glass din Idonta na neman ya Fadi ta Fita Haraban Gida kamar ta Kifa Saboda Razama Harta Daada sai da ta Fito Falo jin wannan al"amarin Jikokinta Guda Biyu suna Fada da junansu.
Yadda suka Fita suka iske wannan Fadan ya tashi Hankalinsu Cikin Lokaci sun jigata junansu,Khamis yana da karfnsu na Sojoji Shi ma Imran yana da karfi ga Zuciya Duka Idanuwansu sun Rufe basaaji basa gani.
Abba da kansa ya Rike Imran da karfi Shida Yusuf da Sagir da Basheer Daddy kuma da Su Sa"id suka Rirrike Khamis suna sun hada ma kansu jini da majina,Matan masu Rauni sai kuka Irinsu Munari dasu Hafsah Mami Asma"u hannu ta Dora akanta tana Ihu Tana kururuwan Fadin Imran zai kashe mata yaronta Harta Sajida sai ta Fito sai kuka Baffa Kabiru Shima yana Cikin masu rike Khamis ganin yadda yake Zillo yana neman kwace kansa.
Imram ma haka yake cida yana zillo kamar wani kadan Ruwa ammh su Abba suka Dannesa.
Daddy ne ya Daka musu tsawa yana Fadin"Kai meye haka.?Meke Damun ku ne..? Kuzo kuna Dambe kamar Wasu yara abunda kannenku zasu yi ku yi musu fada ammh ku da kanku Zaku Zauna kuna Fada da junanku..ku Sake su naga wanda ya kara Taba Dan"uwansa in ya isa..!
Ya fada Cikin Bacin Rai Sakinsu akayi suka koma suna maida Numfashi Imran ya Lakato jinin Dake gefen Bakinsa yana kallon Khamis yace Cikin Muryansa"Ba shikenan ba..Tabbas in ka kara maimaita kuskuran da kayi Wlh..Sai na Maka abunda yafi wannan..!
Yafada yana Haki Khamis din Shima Yana Hakin yana Lakatan jikin Dake gefen bakinsa yana Fadin"In kafasa..Ai basai na kara ba..Mu Cigaba mana Uban wa kike tsoronka..!
Yafada Cikin bacin rai kokarin kara Hadewa suke Mami Asma"u ta shiga Tsakaninsu Tana Fadin"Khamis zan ci Ubanka in baka bari ba..In shi bai da Tarbiya kai baka dashi ne..?
Tafada Cikin kuka Sai ya koma ya tsaya yana Maida Numfashi,Imran kuma kallon Mami Asma"u yake kamar yayi ta Dukanta sai dai ya Taushi kansa,shima Numfashin yake Saukewa.
Inteesar da Munari sun kamkame juna suna ta kuka Kowa abun baimai Dadi ba Mami Asma"u taja Hannun Khamis suka Nufi Falo Yusuf da Sagir suka kama Imran zuwa Cikin Falon Su Abba suka mara musu baya sauran ma Haka Daada na Falon tana Jiransu Ranta Duk ya baci Umarni ta bata Kowa ya nemi waje ya Zauna ya"yanta suka matsa gabanta.
Ta shiga Fada ta Inda take shiga bata nan take Fita ba Ta nemi jin ba"asin me yafaru Khamis ne ya iya maida mganar Imran kuwa kala bai ce ba yana Gefen Sagir yana Sauke Numfashin Alamun Fushin bai gama Sauka ba.
Khamis ko kunya yana Fadin Saboda ya Rike ma Inteesar hannu yasa Imran yace zai mai Duka Mami Asma"u Cikin bacin rai tace"Ya zata kaima Kanwar lasa ne da zai Latsa ka yaga Jini..D"ana Soja ne yasan Me yake yi..Kuma Daya rike mata hannu ina Ruwansa Wht is dey a taba hannu ai yar"uwansa ne bai kamata ya shiga ba Kowa anan Wajen yasan Imran bai da Gaskiya adauki mataki ko ni na Dauka bazam yarda adakeni kuma ahanani kuka ba..!
Take Fada Cikin Bacin rai ba Zato ba Tsammani Imran ya Dago Jajayen Idanuwansa yana kallonta kafin yace"Waht is dey a taba Hannunta..?Shi Ubanta ne ko Muharraminta da zai Rika taba ta duk sanda yaga Dama.?ba Soja yake ba ko Shugaban Sojojin Duniya ne in ya kara Tabata sai namai Abunda yafi wannan Sakarai kawai..!
Yafada yana cije bakinsa Cikin bayyana yadda Ransa ke kuna.
Sai kowa ya koma Binsa da kallo Umma Tayi kasake tana kallonsa Ranta yayi mata Fari domin da Farko Ranta ya baci yadda Mami Asma"u take nuna bakomai bane Abunda Khamis din ya aikata Hakama Daddy sai da ya Murmusa Abba zai yi mgana Daddy ya hanasa Domin kalaman Imran mganace mai kyau kuma yaji Dadinta Inteeear y'ace mafi soyuwa gareta Bazai so wani yaci Zarafinta ba ya Tabbata Indai Tana da Dan"uwa irin Imran bai mai iya cin Zarafinta bai Rama mata ba Hakama Ya Basheer aransa yana Mamakin Wasu Mutane meye na rike mata hannu? Har yana nuna ba wani abu ai koda take yar"uwansa hakan bai dace ba.
Sajida kuwa kallon Imran take shi baima san da ita ba,Tana Fadin acikin Zuciyarta Meyasa shi ya Rike ma Inteesar hannu jiya..?Shi din Muharraminta ne inda zata iya da sai Tayi mai wannan Tambayar sai dai bata da wannan kwarin gwiwan.
Daada ita kanta taji Dadin mganar Imran Dole ta hana Mami Asma"u mgana Tayi ma Khamis fadan Abunda yayi bai kamata ba kansa na kasa yace"Daada nifa bada wata Manufa nayi hakan ba..Ina son Inteesar..Kuma neman Damarta nakeyi ta amince na gabatar da mganarmu wajenku A tsaida mana Lokacin Aure..!
Gabadaya sai Falon ya Dau Shuru Mami Asma"u baki ta saki Cikin Takaichi Tana kallon Khamis Baffa Kabiru baice komai ba Domin kansa ya Kulle,Abba ya kalli Daddy shima ya kallesa Umma ma ta Dago Tana kallon Daddy domin taga yaya ya karbi mganar sai dai Inteesar ta bata amsa Domin Cikin kuka ta Bude baki tace bata son Khamis kuma bazata auresa ba Daddy ne ya tsawarta mata abunda bai Taba mata ba Tsawa Dole tayi shuru ta koma Tana sheshhekan kuka.
Daada ta Dade batace komai ba Sai Daga Karshe tace Khamis ya Nemi so wajen Inteesar in ta amince su basu da Mtsala saboda acikin Ranta Taana Tunanin kada ta karayin kuskuran da tayi yau dinnan na Hada Auran Imran da Sajida Saboda a abubuwa su Daidaita sai dai Tun Daga jiya zuwa yau abubuwa suna Faruwa marasa Dadi wanda suka sata ta Fara Tunanin anya batayi kuskuran Hada wannan auran ba..?Tana ganin kamar wasu abubuwan marasa Dadi zasu kara Faruwa nan gaba Shiyasa ta ce Khamis ya nemi Yarda Daga Wajen Inteesar in haka ta Faru zata fi kowa jin Dadin Jikokinta sun hada kansu.
Baffa Kabiru ya mike ya nemi Izinin Daada na komawa bakin aiki gobe tace ta bama Kowa Damar tafiya gobe in Allah ya kaimu sannan mganar Sajida da Imran kuma wannan yana Wuyan Imran din.
Mami Asma"u ta Bude baki tayi mganar Karatun yarta Tana Fadin bamai yanke ma yarta Karatu Daada tace Ai ba wanda yace zai yankemata Duka wadannan Tsaran Tsaran za"ayisu Daga baya.
Daddy ya mike yace Sati mai zuwa sun yi mgana da Daddy zasu je Lagos chan gidan da suka baro dashi da Yusuf da Imran din sannan zai Tura Cv dinsa anan Jami"ar Bayero Ko Allah zai sa za"a Dace Tunda Abba ya Nuna yafi son Zaman kano Fiye da Lagos.kowa yayi na"am da mganar Daddy saboda Abba da Sauransa Tabbas Jami"a zata amfana da iliminsa Ita da Dalibai.
Kana Daga Karshe Daddy yace Imram ma ya kawo Takardunsa yana da wani aboki Dake aiki a First bank nan Resshen kano kuma Manager ne insha Allahu komai zai yi Daidai agaban kowa da kowa nan take Imran yace shi bayaso bazai yi aiki kuma baya Bukatar Taimakom kowa Sai da Abba ya Daka mai Tsawa yace kada ya kara Mgana Dole yayi shuru.
Daada taji Dadin mganar Daddy ta Dinga
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment