Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Dake Dariya ya Shige Dakinsa da Haushin Inteesar ta Kauda kai taki yarda su hada ido wai itana nan taji Haushi ne ko..?
Karamin Tsaki yaja yana jin Takaichi ya Riga yagama Shirinsa gobe sai Dukku waya ya Dauka ya Turama Intee Sako.

"Yayi miki kyau Tunda nine kike Turama baki kina kauda kai baki san ganina..!

Ba Dadewa ta bashi amsa da Cewa

"Eh din..Gobe zakaje kaga Amaryanka ina Ruwanka dani..!

Sai da ya waro ido Daya ga mganarta Dariya ta kamsa Yarinyar nan ta gama Rainasa cikin gatse yace mta

"Kamar kin sami ta Abuja zan sauka ko kina da sako wajen Amaryan tawa..?

Ya tura mata Sakon yana ta Dariya Har yana jin Sautinta yasan ya gama Kunno yar shagwaban kamar ya sani Dataga sakonsa sai da Zuciyarta ta Buga Saboda Takaichi da Kishi Cikin Tura Haushi ta Turamai.

"Ka gaisheta..Ango mijin Amarya..In kaga Nawa Mijin ka isar mai da Sakon i Miss Him Khamis Kabir Dukku nake nufi.."

Ai sai nata yafi Zafi Daya sakon nan kamar yayi Bindiga kiranta yayi taki Dauka sai yaji kamar Zuciyarsa Zata Fito Saboda Kishi Wai Mijinta..? Lalle nema to ba sai ya zama mijin nata ya gani ba haka yake ta Fada yana Sakin Tsaki.
Itama chan bangaranta haka tayi ta jan Tsaki tana kunkuni ita kadai Daga Karshe ma barin Falon Tayi,Ta shige Ba wanda ya Lura da yanayinta sai Munari ga Dariya ga Tsausayi..
Tana shiga Daki Ta Fada kan gadi ta saka kuka ranta na kuna Afili ta Furta"To ni ina ruwana ya ma je su Tare tare achan babu Abunda ya Dameni..!
Take Fada Cikin tura Haushi Lokaci Daya ga Hawaye Munari shigowarta kenan taji Abunda Intee ke fada Ssi ta bata Tsausayi bata nuna mata taji ba ta Basar ammh Tana Lura da ita bata wani samu barci ba Bini bini ta juya ta saki Tsaki shi kanshi Imran din Rabi da Rabi ne barcin nasa kowa ya kwana da Takaicin kowa.








*Shakira*
3/22/22, 23:15 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�12*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*


Da garin Allah ya waye saboda ita da Safe yazo ya Tsaya a Haraban gidan Saboda yasan suna da makaranta yau da safe so yake ya ganta kafin ya tafi.
Sai dai duk yadda yaso Inteesar da suka Fito ya yusuf zai kai su kafin ya wuce wajen aiki bata yarda ta Hada ido dashi ba,Duk yadda yayi kokarin haka yaga Idanuwanta sun tasa alamun Tasha kuka jiya da Dadaddre..
Munari ce kadai ta gaisheshi Inteesar kuwa Mota ta shige Fuskarta ba Fara"a ko kadan ta maida ma kanta wani gefe Ran Imu ya sosu yaji ba Dadi yau shine Intee bata son ganin Fuskarsa abun is so painfull acikin Ransa.
Ya yusuf ne Daya fito ya gansa Tsaye Jikin Mashin dinsa ya Hade Hannuwansa Saman Kirjinsa kamar ko yaushe Kallonsa yayi yana Fadin"Yaushe zaka wuce ne..?
Kai Tsaye Imran yace"Yanzu..!
Yafada Kan Sa tsaye Kuma Duka Kallonsa naga Inteesar wacce ta maida kanta gefe batama yarda ta Dago ba ballatana su hada ido ba duk da ta Lura ita yake kallo kuma jikinta ya bata Wadandan Kafaffun Idanuwansa suna kanta ne.
Ya yusuf yayi sakake yana kallonsa Kafin yace"Yanzu..?kuma kake Tsaye anan ba wani Shirin Tafiya..?
Imran gajiya ma yayi da mganar Yusuf ya barsa yaji da abunda ke gabansa mana bai ce mai komai ba ya Taka zuwa Cikin Falon ko waige Yusuf ya Bisa da kallo kafin ya Tabe bakinsa sai alokacin Inteesar tabi bayansa da kallo Cikin Samun Sukuni da Salamar Dake Tattare da ganinsa din Munari na Gefenta Tana Lura da Komai acikin Ranta tace Allah Sarki Soyayyah..
Yusuf shima Shigowa Motar yayi ya Kunnata yayi Riverse suka Fice Daga Haraban gidan.

Suna Tafiya ba Dadewa Imran ya Fito Cikin Shirin Tafiya yayi shigar Riga da Wando Rigar Fara ce mai Dogon Hannu Tana da Layin Baki ajikinta Sai Wandon Jikinsa baki ya kamasa daga kasa Kadan kafarsa sanye Cikin Bakin Takalmi Sawu Ciki na Fatar Damisa,Ahannunsa na Hagu sanye da bakin agogon Fata na Kamfanin Rado Kan nashi yasha gyara,Bayansa ya Rataye da Jakarsa baka ta baya kamar ta yan makaranta Bawani Kure adaka yayi ba ammh ko sau Daya ka kallesa sai ka kara kallonsa Cikar Zatinsa baiwa ce Daga Allah kwarjinsa da Kyansa kuma Hallitace ta Ubangiji Duk Takamar mace da Kudinta da Iliminta in Imran ya Tsaya a gabanta ya Kalleta ido Cikin ido sai taji ta Raina kanta da Duk Abunda ta mallaka Maza kuma yan"uwansa Dole in suka kallesa sai sun kara kallansa sun kuma Tabbatar ma kansu Babban Goro sai magogin karfe.
Ko afitowar da yayi Abba Dake kan Dining yana karyawa Sai da ya Dago ya kallesa acikin ransa yana Kirari ga Allah mai gagara Misali da ya Hallici Imran a yadda yake,Safiya ma Dake Zaune afalo bayan ta Rako Yusuf ne ta Jabe anan tana Hutawa ta kasa karisawa Shashenta Cikinta har ya Fito Domin ya Shiga watansa na Biyar,Itama Dake Zaune sai da ta kallesa ta kuma Jinjina Kwarjinsa Ya gaisheta ta amsa mai Cikin Sakin Fuska yana gaisheta Wani Lokacin In suka Hadu Gab da gab ammh fa baya Binta ya gaisheta in sun hadu shima din yana Cikin Mood mai Dadi in Ransa na bace kuwa baya bi ma ta kan kowa.

Wajen Abba ya karisa ya dan Rankwafa ya gaisheshi Abba ya amsa Cikin Sakin Fuska yana Fadin'Bakon Daada..badai har an fito ba..?
Imran na Shafa keyarsa yace"Na fito Abba..!
Abba yace"To haka zaka tafi baka ci komai ba..?
Imran ya Girgiza kansa yana Fadin"A"a Abba bana cin wani abu in zan yi doguwar Tafiya..!
Abba ya jinjina kai kafin ya kallesa yana Fadin"To kana da kudi a Hannunka ne..,?
Imran yadan yi Mirmishi kafin yace"Kada ka damu Abba..!
Abba yace"Dole na Damu mana..Zaka gane gidan kuwa..?kadai kula da kanka kaji ko in baka gane ba ka kirani!
Imran da ya Murmusa sai da kyakyawan Fararan Hakoransa suka Bayyana ya Mike yana Fadin"Abba am not a Boy fa..?Nasan abunda nake yi..Zan kiraka da Zarar na isa Dukku ku gaisa da Daada..!
Abba yace"Shikenan Allah ya kaika Lafiya Daman mun yi mgana da ita da Safe bam ma gayamata zaka zo ba..Nasan Zataji Dadin ganinka..!
Kai Imran ya Kada bai yi mgana ba suka kara yin Sallama da Abba ya Fice bayan ya Fadaamai Sagir zai kaisa Tasha da mashin dinsa Zai bar mai Mashin din a wajensa har ya Dawo Abba yace hakan yayi nan ya fice Abba da Safiya suka bisa da Faten isa Lafiya.
Yana Fitowa ya Hau mashinsa ya Fice Daga Gidan Iro megadi ya bisa da Allah ya Kiyaye Daman sunyi Waya da Sagir Tun jiya da Daddare,kuma da Safan nan sun yi mgana yana Kofar gida yana Jiransa,yana zuwa Sagir ya Karbi Tukin Mashin din Imran ya Dawo baya ya zauna suka tafi Tasha koda da sukaje Motar Gombe suka Tarar ta kusa cika Sai Imran yace bari ya Hauta in yaje Gombe sai ya Hau Mota ta karisa dashi Dukku.
Akwai kudi a Hannunsa Sauran kudinsa Bankinsa ya Ciresu Saboda Tafiyar nan,20k ya Cire ya bar 10k agida Saboda akwai abunda zai yi dasu in ya dawo 10k ya Sako a Aljihu Saboda Tafiyar nan
Kafin Motan ta karisa cika suka Tsaya nan Gaban Motan suna Mgana Sagir ya kallesa yana Fadin"To ita Inteesar din tasan zaka tafi Dukku Saboda ita..?
Imran ya bata rai Cikin bayyanar Bacin Ransa yana Fadin"Ita Datake Fushi Dani..!.
Sagir ya kallesa cikin Mamaki kafin yace"Fushi to me kayi mata..?
Imran ya mele baki ya fara bama Sagir Labarin abunda ya Faru ya Karishe da Fadin"Kaji fa wai yarinyar nan ni zata Rubuto ma wai khamis Mijinta..?ni fa ta rainani yarinyar nan Naji dama sanda take fadin haka tana kusa dani na Daki bakinta sai yayi Jini nan gaba zatasan me zata rika gayamin Tunda ni ba sa"an wasanta bane..!
Yafada Cikin bayyana jin Haushinsa Sagir kuwa Dariya ta kamashi Har da Dukawa Imran ya Bisa da kallon Takaichi yana fadin"Kai fa Banza ne..!
Sagir ya Dago Daga Dariyan Dayake yi yana Fadin"Ban ga Laifinta bafa..wayace kace Sajida Amaryarka..? Ashe ba Dade ai kuma ta baka amsarka Daidai da mganarka..Wow..wannan Salom Soyayyar taku ta fara Burgeni kuna son juna ammh Dukkan ku baku sani ba,Inteesar Tana sonka Shiyasa take Kishin Sajida kamar yadda kake Kishin Khamis..!
Yafada yana kara Sakin Dariya kallonsa Imran yake Cikin Nazarin mganarsa Cikin mamaki yace"Itama Tana Sona..?
Sagir ya gyada kai yana Fadin"Am Very Sure..Itama Tana sonka kamar yadda kake sonta..!
Shuru Imran yayi bai yi mgana ba yana Jujjya mganar Sagir Cikin Dakuna Fuska yace"Ni ai ba sonta nake yi ba!
Sagir ya kallesa yana Dariya yace"Allah ko..?
Imran ya Hararesa yana Fadin"Kai wai a ina kasan Soyayya ma haka Daka ke fadin cewa ina sonta tana sona da karfin Gwiwanka ko ka taba Soyayya ne ban sani ba.,?
Sagir yace"Ni ba irin ka bace..ina shiga Social media ina Hulda da abokai ina Karance karance nasan abubuwa da yawa kan soyayyah ammh ni ban Taba soyayyah ba sai dai irin na yarinta..!
Imran ya saki karamin Tsaki yana Fadin"Shirme kenan..Ni ko na yarinta ma ban yi ba..!
Sagir zai yi mgana kenan akace Mota ta Cika a Hado kudin Mota Dole ya Dakata Imran ya bada Kudim Mota ya Shiga Gidan gaba Key din mashin din Daman yana Hannun Sagir nan yace ma ya riketa a wajensa Har ya Dawo Sagir bai bar tashan ba,Sai da Motar su Imran tatashi Kana ya bar Wajen Cikin kewar Imran din.
Sai da suka Dauki Hanya kana ya Lalubo Wayarsa ya Danna ma Inteesar Kira ammh bata Dauka ba Koda baya son nuna Damuwarsa Dole Damuwar ta bayyana Sako ya Tura mata.

"Zan yi doguwar Tafiya ba Allah ya Kiyaye Hanya..?

Haka ya Tura mata bai saka Ran Zata bshi amsa ba san sai ga Sakonta daman Lokacin Daya Kira suna Lecture ne.

"Allah ya kiyaye Hanya..'
Daga haka bata kara ba,Sai da ya Murmusa daya ga Sakonta ganinsa kawai yayi yana Rubuta mata.

"I miss u....!

Ya tura mata bai kuma damu daman Data bashi amsa ba kamar yadda itama Data gani kamar yana gabanta ta Turamai baki tana fadin"Ba wani nam..Kai da zakaje wajen Wata..!
Ranta kuna yake in ta tuna haka sai dai bata isa ta kankare kalmar Sajida matar Imran bane.

Tunda suka Fara Tafiyar har suka kai bai yi mgana da kowa ba amotar duk da na kusa dashi da Direba da wasu a baya sai Hiran yadda Harkan Tsaro ya Tabarbare sukeyi a kasar nan namu ya Takura matuka da Hayaniyarsu sai dai ba yadda Zai yi bai Tofa bakinsa ba an Tsaya wasu sun siya Ruwa da abubuwan ci na saman Hanya ammh ko Shi ko abunda ba"a so bai siya ba,Har na Kusa dashi ya Siya Buredi da Ruwa yamai Tayi ya Girgiza kai Sunyi Gudu soaai koda 12pm na Rana tayi suna garin Gombe Daganan ya Hau Mota zuwa Dukku Goro kadai ya Tsaya a gombe ya siyama Daada Tunda tana ci sama sama.
Daya saura na Rana ya iso Dukku Daada na cikin Dakinta taji Baba Asabe nayi ma Imran maraba mamaki ya kamata lokacin Dataji sunansa Bata yarda ba ta Zata bataji Daidai bane Alwala ta Dauro tana Kokarin Tada Salla Imran ya shigo Dakinta da Sallamarsa Cikin Kaushunsa Koda yaushe.
Takalmin kafarsa ya Tsaya ya Cire nan Kofar Dakinta kafin ya kariso baki ta Saki Tana kallonsa Cikin mamakin ganinsa Shi kuma gabanta ya karisa Fuskarsa bata bayyana Fara"a Sosai ba sai dai ya Saki Ransa ba kamar yadda ya Saba ba,Har gabanta ya karisa cikin Dan yakensa yace"Daada..!
Daada data kasa mgana ta shafa kansa Daya dan rankwafa agabanta yana gaisheta tace"Kai nake gani ko kuwa Idanuwana ne suka Fara Rauni ne..!
Mirmishi yayi kafin yace"Nine Daada..!
Daada Farinciki ya kamata ta kamasa suka Zauna saman Darduman Data Shimfida bakinta Har kunne Tana Fadin"Masha Allah Sannu da zuwa yanzu kake tafe Imrana? Ya wajen Malami da sauran yan"uwamka ko ba daga gida kake ba domin munyi mgana da Mahaifin naka da Safe bai ce min kana Tafe ba..!
Yana Sauke Jakar Bayansa yake Fadin"Daga gida nake Daada..Wannan Tafiyar ta takanas ta kano Taki ce Daada..!
Yafada yana Kallonta Cikin Jin Dadin yadda yaga Tana Murna da ganinsa Cikin Jin Dadinta tace"Kai..Aikuwa naji Dadi sosai ka kyauta..Yau ina Zuwaira Allah ya jikanta tazo taga  yau da kafarka ka tako zuwa Dukku Domin ka Dubani..,!
Kai ya kada yayi kafin yace"Allah ya jikansu da Rahma..!
Daada ta amsa da Ameen daidai Lokacin Baba aasabe ta shigo mai da Faranti shake da Ruwa da ababen sha,Suka gaisa sama sama ta Fice Ruwa kadai ya Tsiyaya yasha,Kafin ya Ciro goron Daya siyama Daada a aljihunsa ya mika mata ta Karba Tana ta Godiya da saka albarka kamar ya bata Duniya Duk sai yaji Tsausayinta ya kara kamashi ba,tun yau ba yasan Daada Tana matukar kaunarsa Soyayyar Datake yi ma Abba ne ya Shafesa.
Mikewa yayi Dauke da Jakarsa yana Fadin"Daada yi sallar ki..Nima bari naje nayi wanka nayi Sallar na Dawo wajenki nazo akwai mganar da nikeso mu Tattauna..!
Daada na Mirmishin Farinciki Tace"Shikenan ina jiranka..!
Daga haka ya Fice Dakin da suka Sauka shi da Sagir wanchan karon nan ya sauka yayi wanka ya Sauya kaya Saboda duk yaji kayan sun Damesa Karamin Wando ya saka 3Quater,da Wata karamar riga yayi Sallah kafin ya Dawo dakin Daada Baba asabe ta jera abinci mai Rai da lafiyan nan ya Zauna gaban Daada Tare sukaci abinci White rice da Miyar kaza Bai wani ci da yawa ba Daadan ma haka Kunun aya dai yasha da yawa suna yi suna Hira sama sama Sai da suka gama Imran ya Kira Abba ya Bama Daada sukayi mgana.
Sai da suka Natsu Daada nacin goron da Imran ya kawo mata ta kalleshi yana Zaune gabanta yadan Kishigida Daga Jikin gadonta tace"To ina Sauraranka Jikana..Allah yasa kan mganar Tarewar Sajida ne adakinta yau da nayi Farincikin da ban taba yi ba..!
Imran kallonta kawai yayi bai yi mgana sai chan ya Mike Zaune Dakyau ya gyara Zama yana kallon Daada kafin yace"Ita ai Tun Washegarin Ranar da aka Dauramna Aure na gama da babinta..,!
Daada ta Kalleshi Cikin Tsoro kafin tace"Bangane ba..?
Dan Mirmishin Saman lebe yayi kafin yace"Manta da wannan mganar Zamu yita Daga baya..Yanzu dai kan mganar yarinyar nan ne ta kawo ni Daada...plz zan Roke ki kada ki aura mata wannan yaron basu dace da juna ba Infact ma bata sonshi kada ki kware ta kamar yadda kika kwareni..!
Yafada kai Tsaye yana Kallonta Daada Tayi Sagale tana Bin Imran da kallo Tana auna Wasu abuubuwa acikin Ranta,
Cikin Karin Haske data ke so Daga Wajensa tace"Wata yarinya kenan..?kuma dame na kwareka..?
Imran kai Tsaye yace"Inteesar mana Daada..Da yaron nan na wajen Baffa Kabiru wachan zuwan namu kina cewa ya nemi yardanta..,!
Daada tana kara Nazarinsa tace"To menene mtsalan Imrana..!
Imran ya Dakuna Fuska yana Fadin"Mtsala Daya Daada bata son sa kuma bai dace da ita ba..!
Daada ta dade shuru batayi mgana ba ganin haka yasa Imran ya Rike duka Hannayenta yana Fadin"Daada kada ki yarda da mganarsa..Wlh inteesar bata sonsa koda yazo yace miki wani abu karya yake yi..kada ki Saurareshi..,!
Daada ta Sauke Numfashi Tana Fadin"Naji bata sonshi..To wa take so..,?
Imran ya tabe baki yana Fadin"Ni bansani ba abunda kawai na sani bata sonshi kuma amtsayina na Dan"uwanta bazan so hakan ya kwareta ba..!
Daada ta Kallesa ido Cikin ido kafon tace"Kai kake sonta kenan shiyasa kace kada na yarda da mganar mai sunan megidana Hamisu..?
Abazata yaji mganar da Sauri ya Kalleta yana Nazarin mganarta meyasa Daada itama tace ko yana son Inteesar ne Hade rai yayi yana Fadin"Nifa ba sonta nake yi ba..Ni fa ban ma sani ba ko ina sonta ko bana sonta..!
Daada Tayi mirmishin su na manya akallah dai a shekarunta Zata iya gano Inda Imran ya dosa domin ta ma Lura Shi kanshi baisan yana son Inteesar din ba Zuciyartsa ke jansa yana aikata wasu abubuwan baisani ba.
Saboda ta kara Tabbatar da Zarginta ta gyara Zama Tana fadin"Naji bata son Khamis kai ma baka sonta..To na yarda da mganarka ature mganar khamis daman akwai wani yaro dan kawata Aina"u tuni take son mu Hada Zuru"a da ita sai nayi mata mgana yaje ya ganta su Sasanta nasan Zasu Daidaita..,!
Ai kamar Daada ta Zubamai Wuta haka yaji mganar nata,Kallonta yake kai tsaye yana jin Zuciyarsa na suya Daada na Lura dashi Tana Dariya acikin Ranta.
Bata rai yayi yana Fadin"A"a daada baza"ayi haka ba gaskiya..!
Kai Tsaye tace"To ya za"ayi.?ko kana da wanda za"a hadasun ne nifa bana son na Mutu ban aurar da duka jikokina ba Daga Mazan har matan..!
Imran yayi shuru yana wani Tunani Kafin kai Tsaye ya kalli Daada yana Fadin"Ni zan aureta Daada shikenan..!
Daada ta saki Dariya aranta tace Dan kwal uba kama Dawo Hanya ne..
Kai Tsaye tacemai"Sajidan fa..?kasan bazaka Hada jini Daya kishi ba ko..!?
Tabe baki yayi yana Fadin"Daada matso kiji..!
Kunnenta ta kawo ya rada mata mganar da baisan kome yace mata ba Naga dai Daada ta Zaro ido Tana kallonsa kafin tace"Innalillahi wa"inna Ilaihirraju"un Imrana meyasa kayi hakan..?
Batare da Shakka ba yace"Saboda Hakan kadai ne mafita Daada..Kiyi Hakuri ban iya cika Miki Burinki ba..Ammh ki bani Auran Inteesar na miki alkawarin bazan baki kunya ba..!
Daada Cikin jimami tace"A"a itama ai baka sonta bazan baka ita a maimaita abunda ya Faru ba..!
Da Sauri yace"Bazai faru ba Daada..Nifa ina son ganinta kusa dani ban Tsaneta ba..Kinga ai zan iya Zama da ita ko..!?
Yafada batare ma Daya sani ba Daada Tayi Shuru batayi mgana ta shiga wani Tunani,acikin Ranta bata isa tace ma Imran A",a ba kodomin ta gyara Kuskuranta na baya na Auramai Sajida Domin gyara Zumunci sai dai abubuwa sun Faru marasa Dadi.maimakon Zumuncin ya gyaru sai abubuwa suka Lalace a mganganun Imran ta Lura yana son Inteesar wannan ne karo na Farko Daya nemi wami abu a wajenta bazata hansa ba Tunda ya kasa Rike abunda ke Ransa yazo ya gayamata kuma Tabbas Zatayi amfani da wannan Damar ta nuna ma Mami Asma"u kuskuranta ta kuma Nuna ma Kabiri sakacin da ya aikata,
Duk da abunda Imran ya aikata bataji Dadinsa ba Da Sajida da Inteeaar duka nata ne,Sai dai gwara hakan gwara ayi abunda za"ace gwara da akayi da Abunda Daga baya za"a zo ana nadama ita kanta Daga wannan Datayi bazata kara aikata irin wannan Kuskuran ba.

Daada na chan na Nazarinta ita kadai Imran ma nayin nasa shi fa a Tunaninsa zai yi Taimako ne Tunda Inteesar bata son khamis bazai bari a aura mata shi ba,Kuma bazai yarda Daada ta kawo wani ba Shiyasa yace Zai aureta ba domin ya yarda da mganarsu na cewa ko yana sonta bane baiyi Beleving kan wannan abun ba.
Daada ta Sauke Numfashi Tana Fadin"Zan yi mgana kan auranka da Inteesar kuma bamai Tada mgana ta..Sai dai kaima ina so kamin wani abu Guda Daya..!
Kallonta yake yi bai yi mgana ba Daada ta gyara ZAma Tana Fadin"Da Farko Dole zaka Dawo Imran din ka Dana sani..Ka daina shan Taba ka koma aiki ka zama Mutum wanda zai iya Rike mace saboda Nauyi ne zai Hau kanka Ina so don Allah ka Dawo Rayuwarka ta baya komai yayi Tsanani Saukin sa na wajen Allah indai zakamin wannan alfarman nayi maka alkawarin Karshen Wata Zan kira kowa da kowa kuma baza"a Watse ba sai da auranka da Inteesar da yardan Allah..!
Kamar Daada tayimai gafara haka yaji Cikin Farimcikinsa Daya kasa Boyuwa yace"Insha Allahu Daada..!
Daada taji Dadi sosai ta Rika sakamai albarka Kiran La"asar ya tadasu ya tafi yayi sallah Daya dawo ya shiga ya kwanta yana Barcin gajiya bai tashi ba sai gabda mangariba Ya tashi yaje yayi salla ya Dawo barcin yammah Cikin kunci ya tashi ga kuma Fushin Inteesar bata Kirasa ba sai shima ya Shareta.
Da Daddare sun sha Hira Daada Shi kanshi yana ta mamakin kansa ko Saboda Rabi Hirar Daada ke yinsa kuma Duka Labarkn Anni ce shiyasa yake jin Dadin Hirar kuma bama Haka ba Zuwansa Dukku yazomai da Sauyi sosai yaji Dadin zuwansa Wajen Kakarsa sai alokacin yake jin Dadin da Sauran mutane ke ji in suka zo wajen kakkaninsu bai taba Samun kusanci da Daada ba sai wannan karon.
Washegari daya tashi da Safe yaga Kiran waya da bakuwar lamba ba adadi,ga Sako yayi mamakin wanda ya Kirasa,sai dai sakon Daya gani ya bashi amsa Sajida ce.
Tsaki yaja yayi Bloking dinta ya Share Sakon nata Domin baya Bukatar Wata mu'amala da ita bashi da akala da ita
Ita kuma Daman Umaima ta saka Ta Tambayan mata Munari ita kuma ta Turo ma Umaiman ta Tura mata,Shine ta Dinga Kiransa bai Dauka ba ta Turamai sako Daga baya ta Dinga Kira bai shiga ba ta Fahimci ya Kulleta ne Tayi kuka sosai kamar Ranta Zai Fita kuma ta Dora Bleeminng din komai kam Mami Tama ganin koma menene ya Faru itace Sila,Shiyasa bayan sun gama Test tayi zamanta a Hostel bata Dawo gida ba saboda Haushin Mami Asma"u take ji.

Sai ga Imran dayaje Dukku da Niyyar kwana Daya ya shantake har kwana Biyu sai dai Ranar Lahadi da Safe Bankin GTB, Reshen Jahar kano suka Turomai sakon suna son ganinsa Karfe 8:00am na safe tayimai a Office din Manaja Ranar Monday abaya bai Damu ba da aikin ba,ammh yanzu ya Damu ko Saboda mganar Daada,Khalil ya kira ya gayamai sun Dade suna mgana yana bashi Shawarwari da Kwarin gwiwa kafin suyi sallama alokacin yayi shirin Tafiya Kano da shirnsa ma ya shiga Dakin Daada yayi mata sallama Tana ta mamakin Tafiya ba Shiri yace mata wani abu ne ya taso.
Kamar kar yatafi haka Daada taji shima haka sai dai ba yarda zatayi haka sukayi sallama karfe 12, yana gombe,Daganan ya Hau Motar kano sun samu Goslow a hanya da kuma Wahalan Mai yasa basu shigo da Wuri ba sai bayan mangariba suka Shigo kano.sai dai su Abba suka gansa kamar Daga sama.


*Naji Sauki Sosai...Nagode da addu"o'inku..Allah ya bar Zumunci Ameen..*



*Shakira*
3/22/22, 23:15 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�13*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*

Ganinsa Kamar daga sama bai sa wani ya Tambayesa Dalilinsa ba,Sanin halinsa shiyasa ba wanda ya Damu daya cemai wani abu ko Abba ya saka ma Ransa ya gaji da zaman Dukkun ne Shiyasa Lokaci Daya yaji dawowa gida,ba wanda ya kawo Tunanin wani abu,Shima baice ma kowa komai ba so yake sai komai ya tabbata ya bama Abba da Yaya Yusuf a big Suprise.
Inteesar da Munari suna gidan Tunda Mama bata dawo ba,Bai bi ma ta kanta ba saboda Ransa ya baci da abunda tayimai Yayi Doguwar Tafiya ko ta Kirashi Taji lafiya ya sauka Shiyasa yayi shigewarsa Daki bayan ya barsu afalo tare da su Abba Ko kallonta ma bai yarda yayi ba ita kuwa Tana kallonsa Cikin wani Shaukin Dake Fitowa daga kasan Ranta.
Wanka yayi ya sauya kaya yayi Sallar mangariba,sannan ya fita yaje Kitchen ya Hada Tea ya Fito Dauke da Mug din kan Dinning ya zauna yasha Abunsa Inteesar da duke zaune afalon Tana ta satar kallonsa sai kuma Taga ko kallonta ma bai yi ba yana shan Tea dinsa yana Nazarin abubuwan da zai Faru gobe shiyasa yana gamawa ya mike ya Fice Daga Falon Inteesar ta Bisa da kallon kauna.
Masallaci ya nufa,Saboda yaji kamar an Tada sallah Su Abba ma sun tafi tun Dazu,koda yaje Raka"a Biyu ya samu Sauran sai da ya Rama yana cikin Masallacin Abba da Ya yusuf suka Fice Sai Sagir ne ya Jirasa ya idar suka Fito tare.
Akofar gidan su Sagir din suka Tsaya Sagir na Tambayansa ya sukayi da Daada bai gayamai ba yadai cemai komai lafiyalau Key din mashinsa ya amsa,yace ma Sagir gobe da Safe akwai inda Zashi ganin Imran din bai gayamai inda zashi ba yasa Shima bai Tambaya ba,Ba Dadewa sukayi Sallama Sagir ya Fada shagonsa Shima Imran din ya wuce gida.
Da wuri ya kwanta Saboda akwai Gajiya ajikinsa Har ya kwanta ya Tuna da Inteesar karamin Tsaki yaja kawai Mikewa zaune yayi ya Dauko Wayarsa ya Kirata alokacin bai da Riga Dagashi sai Boxer Imran ko ana Sanyi baya shiri da Zafi kwatakwata
Wayar ta shiga sai dai bata Dade Tana Ringing ba yaji
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment