Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

abu..?
Da sauri ya Girgizamata kai kafin yace"Wannan ma is ok Daada Zan ci.!
Kai ta gyadamai Lokaci Daya Tana kara Nazarinsa Juya Cokalin yake yi Sai ya Dauki Lokaci kafin ya karaci yanayi yana kallon Wayarsa Zuciyarsa ta fara Zafin ganin bai ga sakonta ba,atsawon Mintina Hudu kafin yaji Sakonta ya shigo da Sauri ya Dauka ya Duba.

"Nasha Tea Ya imu..!

Da Sauri ya Rubuta mata Amsa da cewa"No..Do as i say Inteesar!!!..Kinsan bana son gaddama ko..?

Ya turamata kafin ya ijiye wayar Yana Sauke Numfashi.
Daga bangaran Inteeear kuma ganin Sakon Imu yasa Dole ta mike sanin Halinsa kada tayi laifi Dogon Hijabin Hafsah ta saka Ja,mai hannu Dama karamar Rigace ajikinta mai kama da Shimi shiyasa ta saka Dogon Hijabi,Allah yasa Munari ta tasheta Tayi sallar Isha"i ta matsa mata ta sha Tea.
Cikin Tafiyar kasala ta fito daga Cikin Dakin zuwa Falo lokacin data Fito ma Wasu sun gama cin abinci wasu ne basu gama ba Tukunnah,Tana yin sallama acikin Falon idanuwan Khamis ya fada kanta ya wani Kuramata Ido kamar zai lasheta,Imran ma ganinta yasa yaji sanyi shi kallo Daya yayi mata bai kara ba ya waske yaji dadi tanajin mganarsa,Bai ma lura da kallon da Khamis ke Binta dashi ba.
Ta gansa sai dai tayi kamar bata gansa ba ko barayinsa bata kallah ba Wajen su Abba ta nufa ta duka ta gaishesu suka amsa mata suna Tambayanta ya jiki ta amsa musu da sauki,Daddy ya Dafa kanta yana Tambayanta ya jikinta ta amsa mai cikin Shagwaba kamar ta Kwanta ajikinsa sai dai ba Hali tashi tayi ta koma wajensu Umma Tana gaida su goggo Maimunatu,ita kadai ta amsa mata cikin Sakin Fuska banda Goggo Bintalo Sama sama dai bata damu ba ta Lafe jikin Umma,Umma ta Tureta tana Fadin ta dagata Shagwabe afuska Tayi goggo Maimunatu nayi musu Dariya Daga Khamis har Imran kallonsa na kanta shi khamis irin kallon nan ne ma marasa aji yayinda Imran yake kallonta ta kasan Idanuwansa wanda ba wanda zai Fahimci yana kallonta ne.
Tashi tayi ta koma Wajen su Anty Safiya inda suke Hira dasu Munari Kafin taje ta gaida Daada Wanda Imran ke gefenta,Lamgwabe tayi jikin Daada Tana mata Shagwaba Daada na tambayanta jikinta ta amsa tana kallon Imran wamda ya Dauke kansa kamar bai ganta ba.
Daada ta Umarce da akwashe kwanunka da aka gama cin Abinci nan da nan kuwa su Munari suka Mike dasu Anty Safiya suka Tattara komai suka maida Kitchen Munari da Hafsah da Umaima suka Share Wajen suka Goge.
Daada ta Umarce ya"yanta su Matso kusa da"ita Inteesar tatashi ta koma Cikin su Munari yayinda Imran ya koma Chan karshen kusa da Sagir bai da yarda zai yi ya gudu saboda Daada bayaso yayi abunda zai bata mata rai.
Sai da kowa ya natsu kana Daada ta fara da Sallama ta Umarci Sadam daya Bude Taron da addu"a ya Bude aka Shafa Daada ba wani Dogon bayani tayi ba Abba ta bama Daada ya bama Kowa Labarin inda suka Shiga bayan barinsu Lagos.
Abba bai yi Nauyin baki ba ya gyara Zama ya shiga bada Labarin Abunda ya sani na Komawarsu kano daga Bakin ya"yansa dayasha ji da kuma Wanda ya sani ya Karishe da Fadin"Ya"yana sune garkuwata sune Duniyata..Musamman ma Yusuf gashi nan dan albarka ya Dauki Ragama da Nauyin daya kamata ni zan dauka ya kula dani..Ya kula da Kannensa Munari da Imran,ya Dauke komai a Wuyansa Imran ma ba"a barsa abaya ba Yana da kwanjin Kula da Ahalinsa Babu Abunda Zance musu sai Godiya da Fatan Allah ya basu masu Rama musu..!
Yafada cikin sadda kai Lokaci Daya aka amsa da Ameen.
Kafin Abba ya Dago ya cigaba da Fadin"Daada kiyi hakuri ki yafemin keda Sauran yan'uwana..Har ga Allah ba"a san raina Suka yanke wannan Hukuncin ba Lokacin bani da lafiya Sanda na Dawo Cikin hayyacina babu abunda zan iyayi saboda Ina neman Lafiyata ne kafin komai..!
Daada ta jinjina kai Tana Fadin"Bakomi Malami ban taba Rikon ka acikin Raina ba Tsakanina Dakai sai addu"a da Fatan Alheri..Ba kuma Laifinka bane ba kuma Laifin su Imrama bane Laifin Yan"uwanka ne da suka kasa Fahimtarka Musamman ma Kabiru..!
Tafada Tana nuna Baffa Kabiru Wanda ya Dago yana kallonta Hakama Ya"yansa da Matarsa suka Dago suma kallon Daada.
Cikin Muryan Tsufa ta Cigaba da Fadin"Da basu  rika ganin Laifinka ba..da duk haka bata faru ba..Da sun jaka ajiki da duk haka bata faru ba..Ammh tunda kaga ka dawo Alhamdulillah kuma sun gane kuskuransu..Yanzu kai kabiru da Mustpaha ku juya ku bama Dan"uwanku Hakuri..!
Abba zai yi mgana Daada ta Hanashi Tana Fadin"Ku bashi Hakuri..nace..!
Daddy ne ya fara mgana inda ya kalli Abba yana bashi Hakuri Abba ya girgiza kai yana Fadin"Bakomai Mustpaha Wlh bantaba Kullatanku ba..!
Baffa Kabiru kamar bazai yi mgana ba Mami Asma"u sai Hararan Daada take yi Sajida ma ranta duk ya baci gani take kamar Daada ta Dizga Dad dinsu gaban Mutane bai isa ya Tsallake Umarnin Daada ba ya juya yana bama Abba Hakuri ya girgizamai kai yana Fadin"Wlh ko daya ban taba Rike hakan Araina ba..!
Daada ta murmusa Tana Fadin"Naji dadin jin haka..Daman fa"idan haka ku hada kanku Waje daya ne..Naji dadi sosai Allah ya kara Hada kanku..yayi muku albarka Gabadayanku ku da Zuru"anku..!
Dukkansu suka amsa da Ameen
Abba ya gyara Zama yana Fadin"Daada ina son na gayamiki wani abu kada ki gani kice ban Fadamiki ba..!
Da mamaki Daada ke fadin"Meya faru Malami..!?
Abba juyawa yayi yana kallon Imran Wanda kamsa ke kasa kamar baya jin Abunda ke Faruwa nan kuwa yana jin komai,Maida kallonsa yayi kan Daada kafin yace"Faruwar abunda ya Faru ya Sauya Imran sosai..har Sigari ma yana sha..Sai dai nasan Tunda komai ya Daidaita zai daina sha da Izinin Lahi..!
Shuru falon yayi Imran kuwa ko Dago kai baima yi ba,Kamar ma bai ji ba Haka ya nuna,Mami Asma"u ta tabe baki tace"Ai wanda ya fara ShayeShaye..Da wahala kaga ya iya barinta..!
Tafada kai Atsaye ba wanda yabi ta kanta Sajida kuwa Gabanta ne ya Fadi Imran ke Shaye shaye..? Gabanta ya kara Faduwa ta fara Wurga idnuwansa nemansa Cikin Falon sai chan ta Hangosa kansa na kasa ta na kara Nazarinsa taga Yayi mata kama da mai Shaye shaye ko A"a..? Sai dai bata ga wata alama ba.
Inteesar kuwa Mami Asma"u ta kallan Tana Mamakinta ita meyasa bata kama Girmanta ne..!
Daada kuwa Mirmishi tayi kafin tace"Ai ya gayamin ma Malami Dazu da safe..!
Gabadaya kowa ya Kalleta Cikin  mamaki kai ta gyada tana kallon Imran kafin yace"Eh da kansa ya Fadamin..Halinsa iri dayane da na Mahaifinku Alkali baya karya komai zai Fada iya gaskiyansa kenan..Bakomai Allah yayi mana mganin komai..!
Suka amsa da Ameen Tabe baki Mami Asma"u tayi ba Haka taso ba taso ne Daada tayi fada sosai.ta zageshi sosai ta kuma ji ta tsaneshi sai dai hakan bai samu ba Daada ta nuna ko ajikinta ma.
Imran kuwa yana Duke dan Mirmishi kawai yayi bai ce komai ba acikin Ransa yana auna wasu abubuwa.
Kwatsan yaji Daada tace"bayan haka akwai wani abu da nike son gabatarwa..Wanda na zauna na yanke Hukunci ni kadai da Zuciyata Kuma ba Shawara bace Umarni nake so na baku koda shi kadai ne abu na Karshe da zan gudanar ina da Rayuwa..!
Kowa Hankalinsa ya maida kanta Domin karin bayani.
Daada ta gyara Zama Kafin ta Cigaba da fadin"Mustpha,Malami da kai Kabiru kune Maza manya..Ina son ku Hada Auran Imran Dan wajen Malami Da Sajida yar Wajen Baffa Kabiru Saboda Dalilina na kara Hada kanku ya"yana da Jikokina waje daya..!
Gabadaya Falon sai da kowa yaji mganar Daada kamar Daga sama Baffa Kabiru ya zaro ido yana kallon Daada Abba kuwa Daddy ya juya ya kallah Shima shi yake kallo cike da mamaki.
Zuciyoyi uku kuma sun Buga Lokaci Daya Zuciyar Imran data Sajida sai ta Inteesar wacce ta kwalalo ido Tana kallon Imran wanda ya Dago kansa Cikin mamaki yana kallon Daada yayinda Sajida ta rasa gane yanayinta Farinciki ko bakinciki.
Munari da Hafsah suka kalli juna cikin mamaki haka su Yusuf su kansu mganar tazo musu a bazata.
Inna Maimuna kuwa jinjina abun take ita da Umma suna Hango Tashin Tashina kan wannan mganar.
Mami Asma"u kuwa kamar ma bataji Daidai ba Idanuwanta kan Daada kafin tace"Sajida fa kikace Daada..?
Wata Sajidan..?
Daada kai Tsaye ta kalleta Tana Fadin"Wata Sajida kika sani..? Sajida dai Yar wajenki Asma"u..!
Ai da sauri Mami Asma"u ta Zabura ta Mike Cikin Hargowa take fadin"Na Rantse da Allah Daada bazai sabu ba..Arasa wa za"a bama Dan Shaye Shaye Tsageri fitsararre mara kunya sai Ya"ta..?
Ina wannan mganar bama mai yuyuwa bace Sajida bazata taba auran Dan iska ba wanda baida Sana"a sai Shaye Shaye..!
Tafada Cikin bacin rai Lokaci Daya tana Tada Jijiyan Wuya da nuna Rashin yardanta kan mganar.





*Kuyi Hakuri Don Allah yau nayi Fama Da rashin Chaji ne,Bamu da wuta nakai wayata Chaji ban karbo akan Lokaci ba afuwan..*






*Shakira*
3/22/22, 23:14 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�5*


*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*

Mamakin Mami Asma"u ya kama Ilahiran wadanda ke cikin Falon,Barin ma Abba da Daddy da suka ga yadda Mami Asma"u take nuna Hannu tana so taja da mganar Daada wanda ko su basu isa su ja da Umarninta ba.
Imran manyan Idanuwansa ya Zubamata da suka Fara Chanza Launi Saboda bacin rai bai ce komai ba sai dai ya kara Ware idanuwansa kan Yarinyar da Daada takira da Sajida Duk da bai san ko itace ba a mganar Mami Asma"u ya tabbatar da Zarginsa sai akaci sa"a itama Sajidan shi take kallo da dukkan Tunaninta Shima sai Lokacin yake kare mata kallo Cikin kaskanci da bacin rai Billahil Azim Ko Dauramai wannan yarinyar akayi a Kafarsa sai ya kwance ko mata sun kare a Duniya babu abunda zai yi da ita ballatana Har Uwarta ta Nemi gayamai mganar Banza Daada kamar Tayi kuskure ne Wajen Fadan suna.
Sagir kuwa Tsabar mamaki ya kasa mgana Shi da Yuauf Imran kadai suke kallo suna Fatan kada wani Hargitsi ya Faru a wannan zaman sun sansa sun san Halinsa bayason ka Shiga Harkansa ka batamai rai yanzu zaku samu mtsala.
Khamis kuwa bai ce komai ba Ammh Shi kansa Hadin ai bai yi ba ina Sajida ina wannan Muradadden Mutumin wanda baisan yan"uwansa ba sai dai yana da Tarbiya bai saka baki cikin mganar da ba nasa ba.
Inteesar gabadaya Jikinta taji yana Rawa Zuciyarta na Bugawa Fat!Fat.Kamar wacce tayi Gudun Fanfalaki Kanta ya Fara wani Sarawa da Karfi Har Jikinta na kasa Daukanta Daga inda take Zaune Hannun Munari ta Damke Lokaci Daya tana Runtse Idanuwanta ta sauke kan Imran wanda ya Kauda kansa Daga kallon Sajida yana maidawa wani barayin yana Kokuwa da bacin Ransa ne bayaso Ransa ya baci ya Hargitsa wajen Wanda kuma ya Tabbata bazai ma kowa Dadi ba.
Munari da Hafsah cike da mamaki suke Bin Inteesar da kallo wacce ke Hada Uban gumi duk da Sanyin Fanka da A.c dake cikin Falon ammh bai isheta ba Lokaci daya Jikinta sai karkawa yake yi Har suna jin haka a Hannuwansu data Damke cikin nata.
Cikin Firgicin da suke ciki Munari tace"Intee meya faru..?Ciwon kan ne ya tashi..?
Haka suka Shiga Jera mata Tambaya Ita da Hafsah sai dai ita kanta Baxata iya Fasaara Halin data Shiga ba Tun Lokacin da Taji Daada tana Fadin Umarninta ne Imran ya auri Sajida Taji komai nata ya Tsaya Cak ta kasa gane gaba ballatana baya.
Cikin wannan Halin ne Muryan Inna Maimunatu ya Karade falon Inda ta Mike Cikin bacin rai Tana Fadin"Haba Asma"u ai banzata Tsaurin Idanuwanki yakai Har Daada tayi mgana ko gama Sauke Numfashi batayi ba ki mike kice bazai sabu ba..In kin manta bari na Tuna Miki Daada Uwa take ga Yaya Kabiru kuma Kaka take wajen Sajida kamar yadda kike da Iko da ita muma muna dashi..kuma Dangin Uba sune Kan gaba Wajen zaba ma ya"yansu Mazajen da suka Dace dasu ba ke ba..!
Ta Karishe Fada Cikin bayyana bacin Ranta da yadda Daman take Cike da Mami Asma"u da Raininta.
Mami Asma"u da idanuwanta suka Rufe ta Fara Tafa Hannu Tana Fadin"Eyye Ahhye..Wato saboda ba yarki bace shiyasa kikacewa haka..?in adalci ne meyasa sai yata..! Ba yar Muatpaha ba yar wajenki..Ko ba yar Wajen Binta Dole sai yata.?oh saboda kowannenku anan yasan Zafin nashi kuma Ko Mahaukaci nasan abu mai kyau da Nagarta,Shiyasa ba wacce Zataso a Dauki yarta a Hadata da Mai Shaye Shaye kuma Dan iska..!
Daddy ne yaji abun ya isheshi yana Daga Zaune ya Daka ma Mami Asma"u yana Fadin"Ya isa haka Asma"u..!
Jin haka yasa ta tasomai Tana Fadin"Ba zan yi shrun ba..?Saboda kada na Fadi gaskiya ko..?To wlh ba wanda ya isa ya Dinkemin baki sai nayi mgana In adalci ne ka Dauki Inteesar ka basa mana Sai ka Shiga maganar in kana so na Rufe bakina nasan kuma adalci ne za"ayi anan Wajen ba son kai ba..!
Tafada Tana kallon Daada Datake kallonta batayi mamaki ba Sai dai Tana kara Nazarin Wasu Hallayar Asma"u da ta dade da karantarsu,sai dai bata taba Nuna mata agabanta ba sai yau.
Kowa mamakinta ya cikasa da mamakin yadda take Fadar mgana son Ranta Baffa Kabiru ya kasa Dakatar da ita Daddy ya kallesa Cikin Takaichin ganin yayi Shuru ko Uffan baice ba Ballatana ya Dakatar da ita Cikin bacin rai ya Maida kallonsa kan Mami Asma"u yana Fadin"Wlh Tallahi ba Domin Umarnin Daada bane da yau na Nuna Miki iyakarki Asma"u Da yau na Nuna Miki Da Imran da Inteesar duka Dayane awajena anan Wajen ba sai gobe ba zan Biyamai Sadaki a daura musu aure..sai ki jika Taki yar kisha..Domin ba ita kadai bace ya"a ki duba Fadin Falon nan Cike yake da ya"ya da jikoki Saboda ya"yanki kadai Daada bazata ji Tayi wani Maraicin Rasa Jika ba..!
Yafada cikin Bayyana Bacin Ransa Imran kuwa jin Abunda Daddy yace ne yasa dago kansa ya Kalli Barayin da Inteesar take zaune karaf kuwa suka Hada ido Itama kallonsa take Cikin zuciyarta Tana jin Wani Rauni na shigarta,Hawayenta Datake ta Tarewa suka samu nasaran Zubomata Sharr saman Kuncinta shi kuma Imran sai yaji Ransa na Suya ganin tana kuka Wato itama saboda taji ance Zata aureshi ne take kuka..? Har haka ya zama abun kyama bai sani ba..? Shi fa Imran shine Inteesar take kuka Saboda mganar Daddy..! Tuni zuciyarsa ta bayyana Rauninsa Wanda ya Dade bai bayyana ba Abun yamai Ciwo kwarai shi bai damu ba don Mami Asma"u tayi wasu mgangu akansa Daman bata ishesa kallo ba ammh Yafi jin zafin ganin Inteesar na Hawaye bai sani ba Baisan yadda Inteesar take ji bane da bai yarda ya Zargeta kan Halin da ita kanta bata san Dalilin Shigarta ba.
Mami Asma"u da kalaman Daddy suka bata Dariya ta Murmusa tana Fadin"In ka Burgeni ka Daura mai Daure da Inteesar yanzu Mustpaha..!
Daddy ya yunkura zai mike Abba ya Rikeshi ya Dago yana kallonsa sai ya Girgiza mai kai shiyasa ya koma ya Zauna yana Huci Umma Kuwa na gefe Ranta duk ya gama baci tana ganin Sakacin Barrister sai yau ta Kara Tabbatar ma kanta ya Dade da Zama Mijin tace sai abunda Asma"u ta yanke.
Inna Bintalo ne ta Tabe baki Tana Fadin"Mganar gaskiya aduba mganar Asma"u..Ko yayane..Gwara abu mai kyau da Lalala..!
Mami Asma"u na jin haka Ta ce"Yauwa Binta daman nasan ko kowa bai Fahimceni ba ke zaki Fahimceni..Ki fa Duba Sajida fa kalleta ace Rana Daya za"a Illata Rayuwarta a aura mata Mashayi Rayuwarta ta Dauwama cikin kunci da bakinciki na Har Abada..Ina bazan bari a Cuceki ba Sajida bar kuka..!
Tafada Tana kallon Sajida dake kuka Wanda ita atunaninta kukan Mganar Daada take nan kuwa bata sani ba Sajida tana kukan yadda Lokaci Daya Zuciyarta ta kamu da son Imran sai dai Tana Hango wani al'amari nan gaba.
Daada da sai yanzu Tayi mgana Baffa Kabiru ta kalla cikin Takaichi kafin tace"To sallammmane ka Dakatar da Matarka hakanan tayi iya abunda zamu iya dauka ya kuma isa haka..Ko Tayi shuru ta koma ta zauna ko ta Ficemin daga Falo bana son ganinta!
Daada ta Fada Cikin bayyana bacin Ranta Mami Asma"u ta saki baki Tana kallonta ta Bude baki Zatayi mgana Khamis ya mike yana Fadin"Mami plz..!
Yace mata yana Riko hannunta Dole ta koma ta zauna kana ya koma Wajen zamansa Baffa Kabiru kuma bai ce komai ba,Kansa ma yamaida kasa,kamar bashi a falon saboda Yasan bazai iya Dakatar da Asma"u ba Yasan tabbas tana kan gaskiyanta ne sho kanshi bai yarda da mganar Daada ba banda Rikicin Tsufa Ina Sajida ina Imran ai Tazaran akwai Nisa kamar Tazaran sama da kasa ne.
Daada ta kada kai tana Fadin"Nayi matukar mamakin yadda na bada Umarni wanda ko ya"yana basu isa suce A"a ba sai ke Asma"u kika Mike agaban ya"yana kika ce ban isa ba kuma nayi son kai banda adalci..!
Ta karishe Fada Tana Kallon Mami Asma"u datake cika tana Batsewa.
Kafin ta Cigaba da fadin"Kuma agabanka Kabiru baka iya cewa komai ba saboda abunda tayi a wajenka Daidai ne ko..?
Dagowa yayu yana Shirin mgana ta Dagamai Hannu Tana Fadin"Ba sai kace komai ba na Riga nagama Fahimtarka..Ka nuna ban isa dakai ba Matarka ita keda iko dakai..Sai dai ina so ka sani Sajida bata fi karfin Imran ba sai ma shine yafi karfinta ba Domin Rayuwa ba ita bata isa ta taka Inda ya taka ba duk takamarta kuwa..Imran yafi karfinta da Duk Abunda Uwarta take takama dashi..!
Ta karishe Fada Tana bayyana Bacin Ranta.
Mami Asma"u tasan da ita Daada take wannan mganar Khamis sai girgizamata kai yake mganar Daada tayi ma Daddy da Inna Maimunatu Da da Munari da Safiya da Yusuf da Sagir Dadi Domin Ransu kuna yake data ke jifan Imran da kalmar dan Shaye Shaye Umma ma taji Dadi sai sakin Mirmishi take yi,Inteesar kuwa Ranta kuna yake ga Cin Fuskar Mami Asma"u ga Imu ga kuma mganar Daada.
Baffa Kabiru dayaji kunya ganin Daada ta ganosa ya muskuta yana Fadin"Ba haka bane Daada..!
Da sauri Tace"In ba Haka bane meyasa kayi shuru..?in kana so na yarda Matarka ba ita keda iko dakai ba..Ka Amince da wannan Hadin nawa..Sannan ina son a Daura auran nan Kafin kowannen ku ya koma Bakin aikinsa Gobe kenan in Allah ya kaimu..!
Gabadaya aka Zurama Daada ido Gaban Baffa Kabiru ya yanke ya Fadi ya Dago yana kallon Daada ta Hade rai ba Fara"a,kansa ya maida Wajen Mami Asma"u wacce ta Girgizmai kai da Sauri Rauninta ya bayyana bazata Jure ganin an Ruguzamata Rayuwar yarta ba.
Imran kuwa kansa na kasa bai Dago ba,yana Tunanin shi yaro ne da za"ayi mai irin wannan auran..? Me Daada take daukesa ne..?mara amfani ko wanda baisan inda kasan ke mai Ciwo bane?Kamar shi Imran ba wanda ya isa ya Wulakanta shi ko yakaskastan dashi bai nunamai kuakuransa ba Karyansa zai nuna ma Mami Asma"u tayi kuakure bazai taba Auran yarta ba Har Abada.
Baffa Kabiru bai da wata Manufa bai isa ya Bijerema Umarnin Daada ba Sai da ya Sadda kasa kafin yace"Shikenan Daada..Na Amince Allah ya kaimu goben lafiya..!
Da sauri Daada ta Saki Mirmishin Farinciki Tana Fadin'Masha Allah.Kai fa Malami me kace kan mganata..?
Abba bai da tacewa kansa ya Gyada yana Fadin"Duk yadda kikayi daidai ne ni da Imran masu Bin Umarnin ki ne..!
Mami Asma"u ta Mike Cikin Hargagi tace"To wlh in shi ya amince..Ni ban Amince ba..In dai ina Numfashi bamai Aura ma Ya"ta Dan iska Dan Shaye wanda baida Sana"ar fari ballatana na baki sai shaye shaye..!
Tafada da karfi Tana Zaro idanuwanta Waje.
Imran daya gama jin iya Abunda zai ji yakai wani limit din da Bazai iya Jurewa ba ya Mike da Sauri jikinsa na Rawa Cikin Dakakkiyar Muryansa mai Cike Amo da Zati yace"Kada ki kara Kirana Dan"iska..Ko Da'n Shaye..Shaye..Don"t Try it again..Don"t Ever Try it...!
Ya karishe Fada Jijiyoyin kansa sun Mike Radau har ana ganinsu Naman Kirjinsa na sama da kasa Lokaci Daya yan Sakin Huci mai Zafi tare da Zafin Zuciya kamar yayi Bindiga haka yake jin kansa,Hannunsa Manuniya ya Daga yana nuna Mami Asma"u dashi Cikin Alamun gargadi.
Gabadaya kowa sai ya koma kallon Imran cikin Mamaki,Umma aranta tace ai gwara yayi mganinta Haka ma Inna maimunatu taji acikin Ranta.
Mami Asma"u da Ta tsaya tana kallonsa Cikin dan shakarsa Tace"In na kara fa? Me zaka iya Mara kunya Fitsararre..?
Tafada Cikin Ingili tana Jifansa da Harara,Imran dayaji ya Fara rasa Duka Controling dinsa ya Fara Takawa zuwa gaban Mami Asma"u Cikin Dakakkiyar Muryansa yace"Sai na nuna miki Halin Dan Shaye shaye..Na kuma gwada miki Halin Yan iskan da kike Fada..!
Yafada yana kallonta Ido Cikin ido babu Wani tsoro ko Shakkarta.
Taji Tsoro saboda ganin yanayinsa sai dai kasawa ba nata bane Cikin Dari dari tace"An ce maka Dan shaye shaye..? Karya akayi ba Dan Shaye Shayen bane..?
Tafada Cikin Nuna iya gaskiyarta ai batama gama Sauke Numfashi ba taji Hucin Imran gabda Fuskarta kamar Walkiya ya kariso gabanta Idanuwansa Sun Rufe baima gani Dakyau Zuciyarsa ta gama Rufewa da wani Duhu har yana Hango kansa yayi Ball da Mami Asma"u da sai ta Gamu da Bango kanta ya shafe ya Tabbata bazata taba manta dashi ba.
Sai dai ya Daga hannunsa da Niyar Tureta Abba ya Mike da Sauri Cikin Abunda bai fi kiftawan ido ba ya Dakamai Tsawa"Imran...kada ka Fara..!
Yafada cikin Tsawa da Hargagi wanda ya Firgita kowa,Mami Asma"u tayi bayan Baffa Kabiru da suka Mimmikewa Cikin mamakin Imran,Imran kuwa Cak ya Tsaya yana Sakin Huci mai Zafi idanuwansa sun Juye kamar yana cikin maye,Inteesar da Munari suka kamkame juna suka Fashe da kuka Su Sadam kuwa suma Mimmikewa sukayi cikin mamaki.
Abba cikin Sauri yace"Yusuf da Sagir ku Rukemin shi..!
Yafada a Taushashe Daada Dake Zaune bata Motsa ba Illah dan Mirmishi Data saki In Asma"u ta tabata Kabiru yayi shuru ta tabbata In tayi ma Imran bazai kyaleta ba yaron Zamani ne mai ji da kuruciya Shine Daidai da ita.
Da sauri Yusuf da Sagir suka Karisa suka Rikesa daman suna Ta tsoron kada ya balle musu,Kokarin Fizge kansa yake yi suka mai Riko sosai Yusuf ya Kallesa yana Fadin"Imu..Imran kalleni..!natsu Nace maka..!
Yafada Cikin Daga Murya,kallon Yusuf din yayi yana Budemai idanuwansa Cikin Muryansa mai cike da amo yace"Na natsu fa kace..?Kake fadamin na Natsu..? To bazan natsun ba..ka sakeni nayi mganin matar nan..Nace bana son ana batamin rai Bana so...BANA SO..!
Tunda nazo na shiga Harkan wani..? Ina kebe kaina ne saboda ina Girmama yanayina..Bana so na bata ma wani rai nima bana son wani ya batamin Tayi ta mganganu akaina Cikin son ranta..Waya Dakatar da ita..?ko wayace mata ta bari bai kamata ba? Sai ni domin nagaji nayi mgana..? Wlh billahill Azim bata san Waye Imran ba yau bazan ji mganar kowa ba indai matar nan ta kara Bude baki ta Fadi wata mganar banza akaina sai na Nuna mata Kalata sai na Nuna mata ita din ba kowan kowa bace a Wajena..!
Ya karishe Fada Cikin Tabbatar da mganarsa Khamis ne ya Isa gaban Inran Cikin Fushi daman Tun dazu yana Tsaye so yake yaga Karshen Rashin kunyar Imran din in zai iya Dukan Maminsu..? Lalle da yau yagane Shayi Ruwa ne..!
Kikam ya Tsaya gaban Imran yana Fadin"Yanzu kai in aka barka sai ka Daketa..?kasan wacece ita agareni.?mahaifiya kasan kuwa mtsayin uwa a wajen D'anta..!?da zai iya zama ya Jure Cin Zarafinta Daga wani bangara..?
Yafada Lokaci Daya yana Dukan Kirjin Imran wanda ya tsaya Kikam Shima yana kallon Khamis Cikin wani Kallo na Takaichi Karamin Tsaki yaja kafin ya kwace hannunsa a wajensu Yusuf ya Saka Hannunsa ya bambare Hannun Khamis akan kirjinsa yayi irin Wurgi da Hannunsa da Zafi sai da Yayi baya kamar zai fadi kana ya Tsaya da Kafafunsa.
Cikin Nuna sa da yatsa Imran yace"Kai yaro kauce badai kai zan yi ba..Ita din wacece..?ni ba kowa bace a wajena..Ko Baffa Kabiru dake mtsayin Yayan Mahafina bai isa ya tsaya yana gayamin mganar da wanchan matan take Fadamin ba ballatama ita ba kowan kowa ba..In kai kasan Darajan Mahaifiyarka ni kuma da bani da uwa ai nasan Darajan kaina...Kauce kabani Wuri kafin ranka ya baci..!
Ya Karishe fada Lokaci daya ya bangaje Khamis dake tsaye sai da yayi gefe kamar Zai Fadi Sagir ya Rikosa gaban Sajida dake makale jikin Umaimah ya Karisa Cikin kallon Kaskanci Tare da kare mata kallo Daga sama Har kasa kafin ya Nunata da Yatsa yana Fadin"Wannan abar ne kike
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment