Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

din Tabara kawai sukayi tayi Kafin su Fito tare suka Shafa ma juna Mai suka ka kuma koma suka Kwanta suna Nane da juna Adaran dai bai kara ba ammh da Asuba bayan sun gama Sallar asuba sai da Imran ya kara kafi Siga Dadi.
Haka Rayuwarsu ta Cigaba da Tafiya Imran shi haka Salon nashi Soyayyar take mai Zafi ce sosai,bai iya Fadinta abaki sai dai a aikace Inteesar Tana ganin Abu Salo Salo A aikace ta Zama yar gata Wajen Imran ta kuma kara yardan ma kanta Shi din na Dabam kamar yadda yake na Dabam acikin Ranta..
Inteesar Ta ji Dadin Hutun Makarantar da suka samu Saboda yadda suka samu Ishashen Lokacin da suka Murje amarcinsu Imran bai so ma suka koma ba Hutun Wajen Wata Daya da kwanaki kana suka koma makaranta,Kudin Rigistration din su Ita da munari duka shi ya Biya musu na Shiga Aji Biyu,ba yadda ya iya ne kamar yace abar karatun Tunda da suka koma Lectures sosai sukeyi sai Yammah suke dawowa shi yake zuwa Watarana ya Daukosu ita da Munari ya Fara kai Munari gida kafin su wuce Wani Lokacin kuma kusan atare suke Dawowa Gabadaya dan kiban datayi na amarci Duk ta fara ramewa Ga gajiyan makaranta in ta dawo ga Girki da Laluran Miji Imran ba Daga kafa ya Saukar da gajiyan Dare ya Saukar da ta asuba to yata iya yasan Lagonta ko Ta Hanasa sai ya Lallabata ya ji Dadinsa ba ruwansa.

*****

*After 2 Month*

Bayan Wata Biyu da Daidatawar abubuwa Tsakanin Inteesar da Munari Daada ta Zame a bandaki Tayi Gocewar Kashi da sai da aka Dangantata da asibiti,Hankalin iyalanta ya tashi sosai da duka Jikokinta,gabadaya kowa da kowa sai fa sa yaje saboda jin Halin da Daada ke Ciki,ga Jikin Tsufa ga Kashi ya Tabu Baffa Kabiru da Abba da Daddy tun da abun ya Faru suka bar komai nasu suka Tafi Chan An gyara Kafar Kwananta Hudu aka Sallamota su Goggo Maimunatu ne tare da ita,Jikokinta duk sun zo su Sadam da su Sa"id ya su ya Basheer Ya Yusuf ma yaje Imran dai sai Weekend suka Tafi da Inteeear lokacin Harta su Abba sun koma Goggo Bintalo ne ke Zaune da ita Har Lokacin.
Daada kamar bakinta zai yge Saboda Murnan ganin Inteesar da Imran Cikin Farimciki da annushuwa Daman abunda take Fata kenan tayima Allah godiya ta kuma kara Godemai da ya Hada kan Iyalanta Waje Daya Kwana Daya sukayi suka Juya Inna Bintalo kam ga Gulma abakinta ba wajen Fada Tunda Mami Asma"u da Rayuwa ta gama ma kullin Goro ta Daina Daukan Wayanta Tun bayan Bikin Imran da Inteesar Data Kirata Tayi mata Tas tace kada ta kara Nemanta indai ba Alheri Zata Fadamata ba in kuma ba Daidaita abubuwa Zatayi ba ta barta da Halin Datake Ciki Tundaga Lokacin bata kara Sauraran Inna Bintalo ba.
Mami Asma"u ta gama ganin Rayuwa ta kuma Sarewa da al"amarin ta Tabbatar ma kanta ta riga ta rasa komai,ita ba Miji ba ya"ya ba Khamis ma bata samunsa kwata kwata awaya Sajida kuma ta Zama sauran Cutar Namiji Baffa Kabiru ya gama Toshe duk Wata Hanyar da zasu hadu ballatana ta saka ran in suka Hadu yaga Yadda ta koma zai Tsausayamata ta Rame ta Fige kamar ba Mami Asma"u in lissafinta yayi Daidai Tama Fita Iddanta Kenan Aure ya Haramta Tsakaninta da Kabiru sai in har ya Sake yarda an Daura musu aure gashi Tun tana Boye abun har ya bayyana yan"uwanta sun gane Sakinta Mijinta yayi mgana har wajen abokan aikinta ana ganinta ana Gulmaanta a kawayenta ma duka sun samu Labari Harda wadanda suka Tareta suka mata mgana Mami Asma"u Wlh ta yarda Duka Kuskuranta ne ammh bata san ya Zata gyara abunda ta Riga Ta gama batawa ba.
Bata da wata Hanya Hatta Hajiya Turai ta Sare tace Mami ta Kira Baffa Kabiru ta basa Hakuri Mami kunya ya Sata kasa Kiransa sai dai ta bama Umaima Sako ita kuma Data Fadamai bai ce komai ba Saboda ai bata gama Nadama ba In ta yi Nadaman da gaske Tasan yadda Zata gyara komai,Shi kanshi baya Cikin Natsuwarsa kan Rashin Sanin Halin da Khamis yake ciki,Yaso yaje tun sanda sukayi mgana da Imran sai dai wani Case ne ya Rikesa yasa ya kasa Tafiya yana so sai sun yi Covering din komai Tukunnah ya Shirya yaje Har Chan Anambara ya gani ko Lafiya..?shiyasa ya Share Mamin Asma"u yasani akwai Watarana da Zata gane Duka abubuawn Data aikata kanta suka Dawo,Shiyasa ya Kyaleta sai Ta Fahimci Kuskuranta da kanta.


Su Inteesar na Tsaka da Karatu Anty Hauwan Ya Basheer ya Ta Haihu Ya mace Murna wajen Inteesar ba"a gama sai dai Murnanta ta koma Ciki Tunda sai ana gobe suna Imran ya bari suka tafi Tare da Anty Safiya da itama Cikinta Haihuwa ko yau ko gobe da Munari da Anty Aneesa da Fareesatu da Hafsa,suka Tafi Kaduna suna shima din Inteesar sai da Abba ya Saka baki ya barta tayi kwana Biyu,Yarinya Takwaran Inteesar ne Domin taci sunan Maryama ne kuma Itama Inteesar za"a rika Kiranta ai ko Auta Tayi bajinta ita Goganta Imran sun Siyama Mejego da Baby kaya na alfarma,Domin duk wacce taci sunan Inteesar abar karramawarsa ce a zuwan su suna ne kowa yake jin Labarin Soyayyar Hafsah da Sagir da na Munari da Khalil kuma kowa yayi Na"am Tunda Sagir yaje Dutse sau Biyu,kuma ya Sa"id yayi Na"am Dashi Shi Sagir din bai gayama Imran ba Shi Sa"id din shi ya Kira Imran din sukayi mgana Anan ne yaji Sagir din yaje har Dutse Imran aransa yace Uhm da gaske Yaron nan yake Shiyasa yadda bai Gayamai yaje ba Shima bai Numamai ba Kowa yaji Abun sai yace Hadin ya kayatar Ita ma Munari Khalil din yana nan tafe Kafin Iyayensa su suzo shima ya gabatar da mganar awajensu Dr.Isa Ali Argungu
A kuma Lokacin ne aka kara Tattauna Lamarin Mami Asma"u da Baffa Kabiru,Tunda Labari ya bayyana acikin Dangi Auransu ya Mutu kowa sai Fadi yake ai mganinta keman Taga Karshenta goggo maimunatu bata zo ba ammh ya"yanta su Zainab da Karima sun je Daga Kwana Biyu sai ga yan suna da kwana Hudu Imran ransa ya Baci Inteesar sai ta Saki jiki ta Rama mai Kwanakin da bata nan ya Kwashi Dadinsa Shine yasa ya Dan Hakura Kadan Daga baya kuma sai da yayi mata Fadan nan nasa ta gama Tura Bakinta ta Hakura tunda itace bata da gaskiya.
Tsakanin Haihuwan Anty Hauwa da Anty Safiya Kwana Hamsin ne Itama Allah ya Sauketa Lafiya a asibitim Murtala,Danta Namiji kyakyawa mai kama da Imran kamar shine Ubansa yana Kama na Jini da Mahaifinsa da Mahaifiyarsa.
Haihuwan nan Kamar wani karin Haske ne a wannan Gidan Tun a asibiti Yusuf yayi mai Huduba da Imran,Masha Allah Imran baki yaki Rufuwa Ya Yusuf yamai Takwara Yaji Dadin har yakasa Boye Murnansa Inteesar sai rawan kafa Take Takwaran Gwarzonta Anty Saratu ke Tare da Anty Safiyan har suka Dawo Gida Mama Ya yusuf ya kira Tazo sukaje asibiti tare,Suna Dawowa Gida ta Saka Ruwan Zafi tayima Maijego wanka Ta kuma Gyara mai sunan Imran,nan da man gida ya Cika da Dangin Anty Safiya Abba kuma baki yaki Rufuwa Anyi jika Daddy da Baffa Kabiru sun kira sun yi barka da Fatan Alheri.
Tunda akayi Haihuwan Inteesar chan take wuni Sai Dare Imran ke Daukanta su koma Gida,da sun Dawo Makaranta nan suke yada Zango,Alhaji Alhassan da kansa yazo Har gida yayi barka ya bama mejego 50k Amtsayinsa na Uba bayan kuma akwatin Kayan Daya shako Cike da kayan Bby da Na uwar,Alhaji Alhassan ya Riga ya gama yin Nadama ya Zama Mutumin kwarai yana so ya gyara Halinsa ya Roki Hajiya Mero Gafara ita da Danginta da nashi Dangin.
Inteesar Taci Darajan mai sunan Imran da kuma Darajan Ya Yusuf yasa Imran ya Sakarmata kafa sosai tana Wuninta agidan,Shima amtsayinsa na Wanda Jariri yaci sunansa yayi rawan gani Shima akwati guda yayi na kayan yaro Inteesar kuma ta siya mai Jego atamfofi.
Anyi suna Taro sosai an tashi Lafiya Mama ita ke zuwa Tana ma Safiya wanka da Imran junior safe da yammah Mommy Taji Dadin haka Daman ta Fara Tunanin wacce zata Zauna da Safiyan sai ga Mama Abba ma Kyautar Dubu 100ya yi ma Jikansa na Farko Duniya kuma mai sunan Dansa Gabadaya Ahalin Daada sun Hadu Hatta da inna maimunatu sunzo sunan da su Inna Bintalo,kuma sai da sukayi kwana Biyu kana suka koma,Raguna uku Yusuf ya yanka ma takwaran Imran an sha Shagali sosai kam sai Fatan Allah ya Raya Imran karami.
Bayan suna kuwa Inteesar ta Gayama Aya Zakinta Domin Imran sai da ya Famshe kwanakinsa Inteeear ta Jigata sosai a Hannunsa Sai ta Fara Hadamai da kuka da magiya yake kyaleta Tunda yanzu ta Fara Zama Raguwa Tun Sunan Anty Hauwa bata jinta Daidaita Tunda suka Tare bata Taba Jini agidan ba sai dai Kafin Tarewar ne tayi period,Bata Dauka komai ba Saboda yana mata haka Shiyasa bata Damu ba,sai bayan sunan ne na Anty Safiya ta Fara Zazzabi da Amai Ta Rame duk ta Tsurr har da kwanciya asibiti lokacin da aka Tabbatar da Inteesar nada Cikin Wattani biyu da wani abu Murna wajen Imran kamar Zai Shide bai Taba Zaton Watarana zai Zama Baba ba sai gashi da kanshi ya Kira Sagir da Khalil ya Fada musu ya Kusa Zama Baba suna nan a yara Su kuma sukacemai Suna kan Hanya da yardan Allah
Samuwar Cikin Inteesar ya Zaga Dangi Har kunnen Daada,Sai Jin Dadi Take Tana saka albarka,Inteesar kuma Cikimta mai Laulayi ne ga makaranta Dole Munari ta koma Gidan Tana Taimakamata Tana ganin Abu Su Ya Imu asan ya"ya Wato na wasu ne bai Damu dasu ba ya Damu da nashi Tana kallon Rayuwa yadda Inteesar ke Zuba Shagwabanta Dama gata mai Raki Baban Urborn kuma na Tarairayanta,kuma bai jin kunyar Munari Ko ajikinsa ammh da sun Hadu ya Hade rai yana Hura Hanci Munari tace aranta Daman ai nasan Watarana Mace Zata sauya ya Imu ko bai gama Dawowa Daidai ba Watarana in ya zama uba zai dawo Daidai yanzu ma Shan Taba ya Ragesa Saboda Intee abun ya Zame mai jiki ne yasa yake sha asati sau Daya wani Lokacin balle yanzu Data samu wannan Cikin Inteesar ta kara Lalacewa Tsurfa kala kala batacin komai Daga Goriba sai tuwo sai su Fante da sauransu Imran shine da baisan Hanyar kasuwa ba ya sani yanzu Tunda zai zama Baba Munari kuma ke ta Wahala da tsurfan Inteesar Umma Daman dataji Labari tace Imran ya shiga Uku Daddy na Dariya yace ai Daman sun Hadu da sun Dace ne Dagashi har Inteesar din.
Allah ya Taimaki Inteesar basu Fara Test da wuri ba sai da tadan samu kanta Kana Munari ta koma Gida Bayan sun gama Test suka fara Jarabwwa Lokacin Laulayin yayi Sauki aman ya Tsaya suka samu hutu na Sati uku Imran yaji Dadin haka ta koma Gida tana Hutawa.

******

Baffa Kabiru ya samu zuwa Anambara Har gidan Khamis inda yake Zaune gidansa Daya mallaka Halak malak,Halin da Baffa yaga Khamis sai ya Dawo Abuja yana kuka da Idanuwansa yana Durama Mami Asma"u Allah ya isa.
Yaje yaga Khamis ya Kazance ya koma Cikin Wata Rayuwa,Shaye shaye ga Shan Giya shi yaci Uban Taba,harda Wiwi yana sha,ga Harkan mata Koda Baffa Kabiru ya isa gidan cikin maye ya iskesa ya Tara Kasumaba Duk yayi kazanta Harda mace ya gani agidan,Baffa Kabiru kuka Shabe Shabe Bai iya kwana agarim ba,Har ya baro garin Khamis baya Cikin Hayyacinsa bai san ma yazo ba tun a Garin ya Daga Waya ya Kira Mami Lokacin Tana Hanya Zata Dawo makaranar su Sajida da aka Kirata Bata da Lafiya har an kwantar da ita a Clinic din makaranta Tayi kuka sosai Data ga Halin da Sajida Take Ciki sai dai Sajidan ta nuna ma Mamin Ulcer ce ke Damunta Saboda Tana Zama da yunwa ba komai ba ta Boyemata yadda Take Tarin jini wani Lokacin Achan makaranta ta wuni sai da Taga Sajida ta koma Hostel Tayi Tayi ta Bita Gida Taki ta Fake da Sun kusa Fara Jarabawa Bata so tayi Loosing abunda bata sani ba Mami Taje ta Duba result din Sajidam sai da taji Tsoro ta kuma Tabbatar ma kamta Sajidan Rabuwanta da Imran ya tabata Gabadaya Tayi kasa sosai G dinta Low,Kowa kuma yasan Sajida da Kokari ammh Yanzu Har an yi mata Warning din Kora Daga Deparmnt Mami Asma'u ta baro makaranta cikin wannan Damuwar Tana Tafe tana Driving Tana kuka Har ta kusa Bugama wani Mota ya leko yana ta Zagimta Dayasan Halin Datake ciki Da bai Tsayama bi ta kanta ba Da yayi mata Uzuri.
Bata kai ga isa gida ba Kiran Baffa Kabiru ya shigo wayarta karo na Farko Bayan Abunda ya Faru Wata Shida Cikin na bakwai.
Da farko ta Zata gizo idonta ke mata Har ta katse bata Dauka ba sai da ya kara Kira kana ta Zabura Tana Dauka Tana Sharan Hawaye sai Fuskarta ta Cika da Alhini da Kuka Data barke da shi bayan jin Abunda Baffa Kabiru yake Fadamata Cikin Kaushin Murya"Asma"u me zan ce miki..?in nace na barki da Allah Kamar nayi miki adalci Gwara na Miki Allah ya Isa Allah ya isa Asma"u ko naji Sanyi a Raina Kin Zama Silar Tsarwata Rayuwar ya"yana da bani da kowa sai su..kin ta aibanta Imran kina Kiransa Mai Shaye Shaye Dan iska To Shi Taba Kadai yake sha D'anki gashi chan yana Kora Giya da Wiwi yana Budema Mata Rayuwarss gabadaya kinga Illah aibata D'an wani da Mugun bakin ki ya kamaki me zaki ce..?Kin Ruguzama Sajida Duka Rayuwarta Kin saka Tayi Sallama da Farincikinta In ban yi miki Allah ya isa ba Me zan ce miki..?
Wlh bazan yafe miki ba Asma"u yadda Kika sani kuka Insha Allahu kema sai kinyi mafiyin nawa..!
Ko Cewarta bai jira ba ya Datse Kiransa yabar Mami da kuka Allah yasa Kafin ta amsa Wayar sai da Ta Faka Motar agefen Hanya da Allah kadai yasan Irin Hadarin da Xata Hada kanta ta Hade da Sitiyarin Motar Tana kuka kukan Wurjajan kamar Mahaukaciya afili Take Fadin"Ai nama Fara Kuka Kabiru..Na Dade ina kuka kai ne baka sani ba..Kaicona Ni Asma"u na Kashe Kaina da kaina na Illata Duka Rayuwar ya"yana ba Auran ba Farincikina ya"yana Innalillahi Wa"inna Ilaihirraju"un haka ta Ke Fada Tana Dafe kanta Datake jin yana Barazanar Fashewa Lokaci Daya Tana gunjin kuka.
Dakyar ta iya Rarrafawa Ta Tada Motar Zuwa gida aharaban gidan Da tasamu ta isa Dakyar bata iya Fitowa Da kanta acikin Mota ba sai dai Fito da ita akayi Jiri Take gani Hajiya Turai ta Firgita da ganin Mamin Aranar sai da Likitansu yazo ya Dubata ya Dauramata Drip tana kwance Tana Fadin"Kaico na..Kaico na ni Asma"u..Ya"yana mijina..!
Haka take ta Fada tana Kuka Hajiya Turai Jikinta ya gama yin Sanyin Ta Fita Taje wajen Justice tace ya Kira Kabiru ya Rokeshi yazo su Daidaita da Asma"u yace bazai Kirasa ya Tursasa ba Sanda yake bama Asma"u baki ai bata Jisa ba Shi ba Ruwansa abunda ta Zabama kanta kenan.





*Shakira...*
3/30/22, 20:57 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�30*


*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*

Asma"u ta rasa ta ina Zata farama Hajiyarsu bayanin abunda ya Faru Kunya take ji ita kanta in ta Tuna Kabiru yayi mata Allah ya isa ya Fada ya kara Fada Allah ya isa bai yafe mata ba Ta ina Zata Fara wazata Tunkara da zai saurareta Ballatana ya Fahimceta duk inda taje itace akasa Bata da gaskiya tabi son Ranta da son kanta Eh mana gaskiya ne Tana da son kamta mana in ba Domin haka ba da ta Duba Ya"yanta da Mijinta ta ijiye son Ranta da Tabi Ra"ayi da duka Muradan Mijinta da ya"yanta Kaiconta haka take ta Fada Tana kuka kamar Zatayi hauka.
Hajiya Turai ta Damu kwarai da gaske ganin haka yasa ta samu Mami Asma"u tana kwance bayan kwana Biyu Da kiran da Kabiru yayi mata Gabadaya ta Fige ta rame Ita kanta tasan bata da lafiya Jiri take gani in ta Mike duk da mgungunar Likita ammh Saboda bata cikin Kwamciyar Hankali ko sau Daya mganin bai mata amfani ba Batama sha sai Hajiya tazo ta mtsamata to gani take ko ta sha bai da amfanin Halin Datake ciki Mgani bazai Lafar da komai ba bazai Hana Wutar Nadama da kuskuran Data aikata ci acikin Zuciyarta ba.
Kwance ta sameta yaraf kamar ko yaushe kamar kayan wanki gabadaya Jikinta ya gama saki kamar mai Cutar Shanyewar barin jiki ba na barin Jiki bane na Mutuwar Zuciya ne
Kuka Take na Boye dana Sarari hawaye sun riga sun gama Samun Matsungguni akan Fuskarta Kukan Zucci kuwa Shi take kwana Tana wuni Tanayi,batare da tasan Hanyar da Zata Dakatar da hakan ba
Har Hajiya Turai ta shigo ta Zauna gefen gado kusa da Mami Asma"u bata sani ba ta Riga tayi Zurfi Cikin Tunanin Daya Zameta abun yi akoda yaushe Zafafan Hawaye suna Kwaranyomata.
Hajiya Turai Ta Kira sunanta Har yafi sau uku bata jita ba sai da ta Tabata kadan Tare da Girgizata Lokaci Daya Kafin tayi Firgigit ta dawo Cikin Hayyacinta daga Zurfaffan Tunanin Data Fada idonta ya sauka akan Hajiyarsu Saurin Share kwallah Tayi kafin ta yunkura ta mike Tana Fadin"Hajiyarmu yaushe kika shigo..?
Hajiya Turai tace"Ina Zaki san na Shigo kin Shiga Cikin Tunanin ki na Fama..?sau nawa zan Fada miki wannan Tunanin da kike yi da kukan nan bashi bane Mafita ba,Likita ya Fada miki ki Daina yawan Tunani da Damuwa saboda Jininki ya Hau sosai..!
Mami batace komai ba illah kanta Data sadda kasa Hawayenta na Diga har kan Cinyarta,Kafin tace"Ya zan yi Hajiya..?kukan shi kadai ne mafita na Na Rasa komai na Rasa aurena na Rasa Ya"yana da Duka Martabana Hajiya ya zan yi..! tafada tana Kara Sautin kukanta
Hajiya Turai kai Tsaye tace"Akwai mafita ki nemi Kabiru ki basa Hakuri ku Daidaita kanku..In ya"yanku suka ga haka suma Hankulansu zai kwanta..Nasan nima nayi kuskurre a Mtsayina ta uwa gareki ban Fadamiki Gaskiya ba sai na rika Zugaki Har Kika Tafkan wannan Kuskuran nima sai Daga baya na Fahimci Bamu kyauta ba Dagani har ke shiyasa nake so ki gyara Kuskuran ki ki same sa ki basa Hakuri ya maidake Dakin ki Daga baya sai komai ya Biyo baya..!
Mami Tasaki Mirmishin Dayafi kuka Ciwo kafin tace"Ai bazai Saurareni ba Hajiya..Gabadaya Tun bayan Faruwar lamarin Ya yanke duk wata Hanya da zai sa mu hadu..Bazai taba Saurarata ba Hajiya na Rantse..!
Hajiya Tayi shuru kafin tace"To ya za"ayi kenan..?
Gashi kuma Justice yace bazai Kira sa ba..!
Mami Asma"u batace komai ba ta koma Ta kwanta Tana jan majinan kuka,Hajiya Turai ta girgiza kai kafin Ta tashi ta Fice Cikin Nadaman Gudummuwar Data bata Wajen Kashe ma yarta aure da Lalata gabadaya Mafarkinta Tabbas itace sila in da a mtsayin ta na Uwa ga Asma"u ta bi Hanyar daya Dace da duk haka bai Faru ba Mami kuwa kuka kawai take Tana Tunanin mafita haka take Wuni ta Kwana cikin Daki bata Fita Tana Tunanin mafita da yadda Zata gyara Abunda ta bata....
Tayi ta Kiran Lambar khamis bata Samesa ba Ta Kira Wayar Sajida ta shiga ammh bata Dauka ba,sai Daga baya ta Kirata Daga yanayin Muryanta tasan bata da lafiya ammh sai tace mata taji Sauki Mami batabari Sajidan ta gane bata da Lafiya ba sai ta Boye mata adaran Jiya Ta samoma kanta mafita Batare da ta Yi shawara da kowa ba ita kadai ta Bata kuma ita kadai Zata gyara.
Bata cikin karfin jiki Jiri ma take gani Ta Riga Tama Direban da zai Tukata mgana Tun Safe ta Shirya ba wani Shiri Tayi ba Kamar ba Asma"u yar gayu ba Tuni Gilashin idonta ya kama gabansa ma bata san isalinsa ba Tana ta kanta ne Figai Figai da ita ta Fito Ta Samu Hajiya Turai ta Fadamata Zata je wani Waje sai yammah Zata dawo.
Hajiya Turai ta kalleta sai dai batayi mgana ba ta mata Fatan Dawowa Lafiya.
Daganan ta Fice Direba ya Tukata suna Fita tace mai Dukku Zataje ba Musu ya Take Mota suka Dau Hanya ta Riga ta gama Neman ma kanta Mafita Zuwa dukku shine Mafitanta zataje ta Duka har kasa Ta bama Daada Hakuri ba domin Kabiru ya maidata Dakinta ba ko Zata ga Haske a Rayuwarta Sajida tana Halin cutar da taki barin Ma a Dubata ballatana agane meke Damunta ga Khamis ya koma Wani iri,Irin yadda take aibata ya"yan wasu Kai innalillahi rayuwa ta Juya mata baya bazata iya ita Kadai ba Wlh bazata iya ba wannan Nauyin yayi mata yawa Tabbas bazata iya ba.
Har suka isa Dukku Mami Asma"u na kuka Hawayenta basu Tsaya ba lokacin da Baba Asabe ta shigo Dakin Daada Tana Fada mata zuwan Mami Asma"u din bata gama mamaki ba sai da Taga Mami Asma"u din Tsoron Allah ya kara kama Daada da Tsoron Duniya ganin yadda Mami ta koma Daada Sai Tayi kwallah Lokacin da Mami Asma"u ta Zube agabanta ta duka ta Dafa kafarta tana kuka Tana bata Hakuri Tana Fadamata irin Halin Datake ciki da Halin da Sajida ke Ciki da Halin da Baffa Kabiru yaje yaga Khamis aciki Mami Asma"u na Kuka hawayenta na Diga saman Kafafun Daada Dake Zaune take Fadin"Ki yafemin Daaada..Wlh nayi Nadama..Na Fahimci Abunda na aikatane duka suka Dawo kaina Daada Wlh bazan iya ba nayi Rauni nayi Laushin da bazan iya Daukan abubuwanan ba ni kadai Daada Kabiru ya Kirani yamin Allah yasa isa kan Ya"yansa Daada ina zan Saka kaina..?Wlh hakkin ku ne keda Imran da Malami da su Mustapaha da kukan da na Sakaki shine yake Bibiyata ban yi Tunanun kema kamar Uwa kike gareni ba ko Tsinemin kikayi sai na Bi Duniya..Don Allah da Zatin Allah Daada Kiyi Hakuri ki yafemin..!
Daada Kwallah sai da ta Cikamata ido Ta saka Hannu ta Dago Mami Asma"u Data Durkushe gabanta Tana kuka Hawaye Shabe shabe hannu Daada ta Saka Ta Share mata Hawaye Tana Fadin"Wlh ban ta ba Rike ki araina ba Asma"u na yafe miki..Kuma suma zasu yafe miki..Ai tunda kin gane Kuskuranki bawanda zai ki karban Tubanki..Kabiru bai Fadamin Halin Daya je ya Samu Khamis ba Bansani ba..Ammh Zan Kirasa baza"a Zura ido ba su hadu shi da yan"uwansa suje su Taho Dashi Damuwace tasa ya shiga Halin Daya shiga ammh da Izinin Lahi Komai zai koma Daidai ki Daina kuka bakomai Insha Allahu..!
Mami Asma"u na goge kwallarta Tana Fadin"Bayan Damuwa harda Silar Bakina Daada nayi ta aibata Imrana Ina Kiransa da sunayej banza..yau gashi Duka sun Tabbata kan Da"ana Daada Sakayyace Allah ne ya kamani Kaico na..!
Tafada Tana Kara Saka Kuka Daada na Lallashinta Cikin Zuciyarta Tana Tsausayin Kabiru Lokaci Daya Kaddara ta Fadamai Allah Sarki yana chan cikin wannan kunar ga Asma"u Yadda ta koma Ko da wannan ka kallah Zaka Gane Allah shine gagara Misali.
Bata yadda ta Fadama Mami Har Lokacin ita Matar Baffa bane sai dai ta Lallasheta ta kuma mata alkawarin Zatayi magana da Baffa Kabiru Sajida kuma zata dawo gida Domin asan meke Damunta Mami Asma"u bata jima sosai a Dukku ba Hankalinta ya kwanta jin Daada bata Riketa aranta ba Dakyar ta Tsaya taci abinci Sama Sama Tayi ma Daada sallama Direba ya Juya da ita,Daada ta bita da kallon Tsausayi.
Tana Tafiya ta saka Baba Asabe ta Kira mata Baffa Kabiru Dake chan yana Faman Kokuwa da Zuciyarsa shi kanshi Tun bayan Dawowarsa Anambara Da ganin Halin da Tilon Dansa ke ciki bai da Cikakken Lafiya yayi kuka har ya Gode Allah kwakwalwarsa Ta toshe yarasa Tunanin ma me zai yi..?ballatana ya Samu Mafita Lokacin Daada ke Fadamai zuwan Asma"u bai ji mamaki ba sai dai bai Zata Zata karaya haka Cikin Sauki ba ya Dauka Bata gama ganin komai ba yanzu ta Fara gani nuna ma Daada yayi karya Take duka kukan Munafunci ne Daga baya kenan bayan ta gama Lalata komai..?shi yanzu yadda zai Dawo da Rayuwar Khamis kamar baya yake Tunani Tunda Taje ta Fadama Daada komai,Daada tace maza ya Kira yan"uwansa aje a taho da Khamis
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment