Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yace"Baki fadamin abunda yasa kika shigomin daki ba..?
Yafada cikin Sanyin muryan Datake cike da sha"awa.
Cak ta Tsaya bata waigo ba tace"Dama..Dama.!
"Dama me.?Malama ki juyo kimin mgana ni yaro ne da zaki juyamin baya kina min mgana..!
Bata da yadda Zatayi gabanta na Duka ta Juyo Bata yadda ta Kallesa ba shi kuma Duka Shanyayyun idanuwansa ya Zuba mata.
Cikin Dakewa tace"Dama na Tambayeka yaushe ne Ka Tsaida Bikin Tarewar mu..?
Kallonta yake cikin mamaki kafin yace"Kin kosa ne..?
Da Sauri ta Dago kamar tayi kuka Tace"Wlh A,a..Su munari ne suka mtsa suna so suji saboda Shirye shiryen fa..Ni yaushe nace na kosa..!
Tafada Tana Tura baki.
Kansa ya shafa yana Fadin"Yaran nan sun cika azarbabi..To da suke Tambaya Kayan Daki zasu hada miki ko su zasu min akwatin auran ne da suke Tambaya..?
Inteesar ta marairaice Tace"Sufa Saboda Events din da zasu shirya ne..!
Kasan kuma hakan na Bukatar Tsare Tsare..!
Imran ya Hade Fuska yana Fadin"Event..? A bikin waye zasu yi Event din..?
Yafada yana wani Kara Dakuna Fuska.
Inteesar tayi narai narai kafin tace"Bikin Tarewar fa..!
Tabe baki yayi yana Fadin"an gama mai wuyar Tunda aka Daura auran..Ba wani shanshanci kuma dazai biyo baya in nagama Shirina ni da kaina zan Daukeki mu tafi bana son Hayaniya da wata mgana Ok..!
Inteesar ai mamaki ya Kasheta bata samu Damar mgana ba ya cigaba da Fadin"Kuma ma Wa yace a zo a Tambayeni..?meyasa baku kira Daada ko su Daddy ko Abba ba..Kun Rainani ko..?ke kuma mara wayau kece yar aike ko..?da sun sani sun Tare ni da kansu..!
Inteesar tace"Ai Daddy ne yace kai zaka Tsaida Date din
Imran na Dariya yace"Nagodema Daddy..Ki Fada musu nan da Next year lokacin nima na Tara kudi sosai Kema kinga Lokacin kin Shirya tunda ai yanzu kin ce baki kosa ba..?
Inteesar takallesa Kafin ta kauda kai Lokaci Daya Tana Tura Baki yana Danne Dariyansa yace"Eyye ni kike Tura ma baki..?
Ai bata ma bari ya kara mgana ba ta Fice da Sauri ya Rakata da Dariya aransa yana Fadin"Yaran fa basu da Hankali so suke su min bidia a bikina...Ashe kuwa zan karya yarinya..!
Daki ta koma ta iske Munari na Charting nan ta zauna ta Fadamata Abunda Ya Imu yace Munari tace"Bari zan kira Ya Sagir muyi mgana..yasin Bazamu yardaba sai munyi Bidian da baya so..In yaki ma Daada zamu hadasa ko da su Abba..!
Inteesar tace"Gaskiya..Shifa yarda yake so dagani sai shi ba biki ba komai fa..Kamar wata mara Galihu..!
Munari tace"Bafa zai sabu ba yadda mukaci Burin bikin nan sai fa an sha Hidima iya Hidima Amaryan Oga Imu..!
Dariya suka saka gabadayansu kafin su cigaba da Hiransu sama sama.

****

Washegari Abba ya wuce Kaduna Motar Haya yabi,Ba"a riga an samomai Direban da zai rika Tukasa ba Tunda shi Tuki yanzu ai sai dai su Yusuf,Ya"yan nashi basu so ya hau Motar Haya ba yace ba komai Bai kuma yadda ya Fadamusu zasu je Abuja ba Yusif Daya tambayesa yace Zai je Wajen Baffa Mustpaha ne Imran kuma bayanan sun dai yi sallama da Abba Kafin ya wuce wajen aiki.
Yusuf da su Munari suka kai Abba Tasha sai da Motarsu ta tashi Daganan ya Biya ya kaisu makaranta Shikuma ya wuce wajen aiki.
Wajen karfe 11am na Safe Abba ya isa Daddy yazo ya Dauke anan Tashar kawo Daman yasan da zuwansa.
Suna zuwa gida Umma ta gabatar musu da Breakfast suka karya already daman Basheer ya siya musu tiket din Jirgi gobe karfe 6am na Safe zasu Wuce Abuja Gidan Baffa Kabiru..
Bayan sun gama karyawan Daddy yaja Abba suka Fice yakaisa Shagunansa ya gani ya saka albarka Har gidan su Umma sai da sukaje suka gaida Inno da Mallam Babba.
Sai La"aar suka Dawo gida sun iske Anty Hauwa tazo ta kawo musu Dambun Shinkafa Dayaji Zogala da gyada sukayi ta ci suna Saka mata albarka,Ga Lafiyayyan Zobon Data Hade musu dashi da Sanyayyan kayan Marmari,Tunda Basheer ya Fadamata Abba yazo shine tazo gaisheshi ita dasu Abidin.
Bayan sun gama suka baje afalo suna hira kan Abunda ya shafesu har kan mganar Tarewar Inteesar Da Abba yayi mgana Daddy yace Mgana tana Wurin Imran ko gobe yace Inteesar ta Tare bai da Damuwa Abba yace to in ya koma zai kirasa yaji saboda kada su Dauki Lokaci Daada tace sun yi Watsai da mganarta.
Nan Abba ya kwana shida Dan"uwansa Daki Daya suka kusa Raba Dare suna Hira irin tasu ta yan"uwa gari na Waye suka shiga Jirgin kasa sai Abuja Karfe 9am na Safe suka sauka Daganan suka Nemi Tashar Taxi sai gidan Baffa Kabiru Dake Maitama Abuja.














*Shakira..*
3/26/22, 22:59 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�21*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*

Gida ba kowa sai yan aiki Mami Asma"u Tana gidansu tun Ranar Umaima ta tafi makaranta Baffa Kabiru kuma ya tafi Office.
Dayake yan aikin sun sansu gama kama nan,Kuma Daddy na yawan suwa Abba ne ya Dade bai zo ba Tun kafin barinsu gida yasa nan da nan suka shiga dasu babban Falon gidan Kafin kace kwabo sun cika gabansu da kayan Ciye Ciye da Shaye shaye.
Daddy ne ya Kira Baffa Kabiru a waya ya sanar dashi gasu acikin Gidansa yayi matukar mamaki sai dai bai Tsaya bata Lokaci ba ya Hado ina inasa ya taho gida.
Lokacin Daya shigo Falon Yaga yan"uwansa Zaune suna Jiransa bai kawo cewa sun ji Labarin Rabuwarsu da Asma"u ba ya zata sun jisa Shuru ne suka Biyo Sahunsa da kuma Tattauna abunda ya Faru a Dukku.
Kunya ta Hana Baffa Kabiru iya kallon Cikin Idanuwansu sanda ya kariso Gabansu ya basu hannu Dukkansu suka Sarke Musabaha.
Sai ga Baffa Kabiru ya Duka gaban yan"uwansa yana Hawaye yana Sharan kwallah yana Rokonsu Gafara yana Fadin"Ku yafemin yan"uwana..Ku yafemin Duk da nasan Ni din mai Tarin Laifi ne..Bai chanchanta ku yafemin ba na Zama babban Banza wanda bai rike yan"uwansa da Amana ba,ku yafemin Wlh kunya da Nadama ne suka Hanani nemanku ammh na yanke Shawaran ko baku zo ba gobe na Shirya Tafiya Dukku na Duka na Roki Daada gafara kan Laifin dana aikata mata ko ta yafemin Allah ya Duba Lamarina..!
Yafada yana Goge kwallah Abba da Daddy jikinsu yayi Sanyi sosai suka Mike atare suka Rikosa Suka Hadu suka Rumgume shi suma Kamar su yi Kwallar Saboda Tsausayinsa Jini jini ne duk inda naka yake komai Lalacewarsa naka ne.
Daddy ke fadin"Haba ya kabiru ka Daina kuka..Bai kamata ba..Wlh mu bamu Taba Rikon ka ba..Daada ma bata Rike ka ba Fushi ne na Dan Lokaci kuma Zata sauko da yardan Allah..Muma kafarka kafarmu zuwa Dukku Bazamu samu Salama ba sai Dan"uwanmu ya Daidaita da Mahaifiyarmu ko ba Haka ba Ya Malami..?
Abba ya gyada kai yana Fadin"Tabbas hakane..Duk da akwai Dalilin daya kawomu ammh shima wannan yana daga Cikin Babban Dalilin zuwan mu..!
Baffa Kabiru ya Dago yana kallonsu kafin yace"Nagode muku sosai..Malami musammann kai ka yafemin nafi kowa sabamaka..Ammh Insha Allahu na gane inda na Kuskure Da yardan Allah zan gyara ZAmu je gaban Daada Zan Roketa gafara na kuma mata alkawarin ko Bayan Ranta Bazan bari Zumuncin mu ya Rabe ba mun Zama Tsintsiya Daya madaurinta Daya..!
Yafada cikin son Tabbatar da mganarsa,Daddy da Abba suka Rike Hannunsa Cikin Jin Dadi suka Hada baki Wajen Fadin"Insha Allahu..!
Daganan suka koma suka Zazzauna,Daganan suka yi Breakfast Harda Baffa Kabiru domin shima bai karyan ba ya Fita duk ya zama wani iri kamar bashi ba Daurewa kawai yake ammh Tabbas Rabuwa da Asma"un ya Tabasa.
Sai da suka Natsa kana Daddy ya gyara Zama yana kallon Baffa Kabiru lokaci Daya yana Fadin"Wani Labari mukaji mara dadin ji Ya kabiru..?
Ya kallesa Cikin mamaki kafin yace"Wani Labari kuma Kuka ji Mustapha..?
Daddy yace"Shekaranjiya Da Daddare Yar Wajenka Umaima ta Kirani a waya Tana kuka Take fadin kun yi yar Hatsaniya da Asma"u Karshe dai Har da Saki..!
Baffa Kabiru ya sauke ajiyar Zuciya yace"Eh..Ashe ta Kiraka..!
Daddy yace"Eh Data kirani Gaskiya Hankalina ya tashi..Sai na Kira ya Malami mukayi mgana,muka Tsaida mgana kan cewa yau zamu zo mu ji Ta yaya haka ya Faru..? Mu kuma baka Hakuri komai ya Faru ya wuce Zuciya bata da kashi kayi Hakuri ka maidata Dakinta Ko Domin Darajan ya"yanku bazasu ji Dadin hakan ta Faru a Tsakaninku ba..!
Abba ya karbe da cewa"Kuma in Rai ya baci ai Hankali ke Nemosa Mustapha..Duk in akayi Hakuri sai komai ya wuce Watarana sai Labari..Kuma ku ba yara bane kun Girma bai kamata hakan na Shiga Tsakanimku ba ya kabiru..!
Baffa Kabiru na jinsu kansa na kasa Sai da suka gama kana ya Dago Kansa yana Fadin"Duk naji bayanan ku..Buh kuyi Hakuri Zama Tsakanina da Asma"u ya kare in har bata gyara Halinta ta gane tayi ba Daidai ba..!
Daddy yace"Ai ya Kabiru hakuri zakayi a Hankali kana nuna mata Har Ta gane..!
Baffa Kabiru yace"Kayya ai bazata taba ganewa ba..Da kuke cewa na maidata kunsan abunda ta aikata..?bayan cin Zarafin Datayi ma Daada a Dukku a gaban i...!
Daddy ya Dakatar Dashi Da Fadin"Kayi Shuru Kawai Ya Kabiru ba sai ka Fadamana abunda ya Faru ba wannan Sirrinka ne Tsakaninka da matarka kuma Sulhu muka zo nema ba Tada mgana ba Don Allah kayi hakuri ka maidata ita kanta Daada in taji haka bazataji Dadi ba ga ya"yanku Taya zasu Fuskanci wannan Raunin..?kuma an riga an zama Daya Ku da zaku yi ma wasu Fada Yaya..! Bai kamata ba don Allah kayi Hakuri ka Maida komai ba komai ba ka Maidata Dakinta ko Saboda Darajan Daada da ya"yanku da alfarman da mu yan"uwanka muka Nema don Allah..!
Abba ya jinjina kai yana Fadin"Kuma zama ba Mata haka ai bai Dace ba..Ko ni Saboda Mutuwa ce da kuma Rashin Kwanciyar Hankali ammh ai cikar Namiji Shine Matarsa don Allah kabar Tuna baya ka yi Hakuri ka maidata Dakinta..!
Baffa Kabiru ya Sauke Numfashi kafin yace"Zan maidata ne saboda Darajan Daada da kuma Kimarku da kuka baro Ayyukanku kuka zo har Gida Domin nuna Damuwarku akaina..Nagode kwarai Allah ya bar Zumunci..!
Suka amsa da Ameen Cikin Jin Dadi Daddy yace"To baka ce ka maidata ba..?
Baffa Kabiru yace"Ni kabiru na maida Matata Asma"u na janye Sakin Dake Tsakaninmu.Ba Shikenan ba..!
Abba da Daddy suka yi Dariya suna Fadin"Alhamdulillah..!
Baffa Kabiru ya ce"Na maidata ammh da Sharadin bazan Gayamata na maidata ba Har sai ita da kanta tayi Nadaman abunda ta aikata na Nemi mu Daidaita sai na Fadamata na Maidata ammh ko nan da shekara nawa ne in bata yi Nadama ba ni kuma bazan nemeta ba..!
Suka jinjuna kai atare kafin Daddy yace"Insha Allahu ba Matsala ai Barrister ta barrister ne Zaku nemi juna in kuka Huce..!
Ya karishe Fada yana Dariya Abba na Tayashi Baffa Kabiru Mirmishi kadai yayi bai ce komai ba.
Abba ne yace"Ina Sajida take ne..?munyi mgana da Daada tace min ta Dawo Daga Dukku..?
Baffa Kabiru ya Muskusta yana Fadin"Daga Dukkun bata dawo gida ba Makaranta ta wuce Direct,ba kowa agidan nan Asma'u Tun Ranar da abun ya Faru Mahaifinta Juctice Tafida ya aiko da Direba aka Tafi da ita Khamis ma Ranar Monday yabi Jirgi ya koma bakin aikinsa..!
Cikin Tsausayawa suke Kallonsa Abubuwa sun Taru sun yimai yawa sosai.
Daddy ne ya fara baki bshi Tare da Lallashi Abba dai ya kasa mgana Sabida yana jin kunyar abunda Imran ya aikata na Sakin Sajida sai dai bawa bai isa ya ja da Hukuncin Allah ba.
Daddy ya kada kai yana Fadin"Nadade ina jin Labarin Rikewar Boko Da akidan Banzan Justice Tafida ban kara yarda ba sai yau Sabani ya Shiga Tsakanin Yarka da Mijinta ammh bai Kira yaji Neman ba"asi ba kawai ya Turo Direba an Dauketa me hakan ke Nufi..?
Baffa Kabiru yace"Ai bazai Taba kirana ba..Shi a kidansa bazai Turasasani na maidata kan Ra"ayina ba itama bazai mtsa mata kan hakan ba acewarsa sanda muka Hadu muka Kulla Soyayya muka Aminta da juna bai Sani ba kuma muka yadda da Ra"ayin auran junanmu yanzu kuma da Hakan ta Faru Ra"ayinmu ne Justice Tafida yana da akidan Bin Ra"ayin Kowa baya kutse Cikin Ra"ayin Wani ko da Ya"yansa ne na Cikin shine suna da wannan Right din..!
Daddy da Abba suka jinjina kai,ba su ce komai ba Domin abun ya wuce suyi mgana Aran Abba yana Fadin Dole Asma"u Ta zama yar gaban kanta ta Hadu da Uban mai Bin Ra"ayin kowa da Ra"ayi mai kyau da mara kyau Daddy kuwa Tir da Tarin Ilimi yake Ilimin da bazai amfani Mutum ba.
Nan fa suka Bude Hira Kala Kala su tabo Chan su Tabo chan,Har mganar Samun aikin Abba sai da sukayi Baffa Kabiru yana nuna jin Dadinsa sosai Sallar Azahar ya tadasu bayan sun je sun Dawo su ka kara zaman Hira yaushe gamo suna ta Tabo Labarin baya Tun Lokacin Gwarzon Mahaifinsu nada rai suna Tuna abubuwan da suka Faru alokacin Tuni Baffa Kabiru ya saki Jiki Cikin yan"uwansa Kamar bai da wata Damuwa.
Sai da Umaima ta Dawo makaranta Daga su Abba taji Dadi sosai ta Dinga Murnan Mami Zata dawo.
Allah Sarki Mami Asma"u tana chan Cikin Damuwa da abun kunya Domin Gotai gotai da ita Sakin aure a gareta abun kunya ne in wani yaji Labari zai zama abun Dariya a gareta.
Koda yan"uwanta suka zo gidan suka ganta bata yarda ta Furta Kalmar Sakinta akayi ba nuna musu tayi Tazo ta Huta ne ba wanda ya yarda da ita Taya ya Zata baro Gidan Mijinta Tace Tazo Gida Hutu da wani dai mgana,Hajiya Turai ma taki ce musu komai ballatana Justice da ba Ruwansa da Shiga abunda ba"a Saka sa ba,Indai ba Asma"u ta Fada ba shi baza"aji komai Daga Bakinsa ba.
Batare da Shawara da kowa ba Hajiya Turai tace ma Asma"u ta Dakatar da Shigar da karan nan Saboda ceton Auranta ita kanta Barazanace ammh Asma"u fa ba yarinya bace akwai Tarin Kalubale ta Zauna gabanta Tana Zawarci ba gaddama ba Musu Mami ta Kira Brr.Zailani tace a Dakatar da komai Shi kuma bai kawo abun har takai ga Rabuwa ba ya Zata Brr Kabiru yayi ma abun Tufkan Hanci ne bai san ya bama Mami Red card ne wanda ya Girgixata da Girmanta an Saketa abunda Tun Lokaci Tana da kuruciya bai Faru da ita ba,Ta tsinema Daada acikin Ranta yafi a Kirga Domin har lokacin bata Fahimci bata kyauta ba gani Take Duk Daada ce ta ja komai kuma itace silan Mutuwar auranta,Ego dinta da son kanta yasa ta kasa Zama ta Fahimci matsalan Daga Wajenta yake,Sakin ya Dameta gani take kamar Abun kunya Aji kamarta ace Mijinta ya Saketa ko kawayenta sai sun Rainata
Sajidan ma Datake Fada akanta ta Gujeta ta Zabi Dangin Ubanta akanta bayan Sakin Wulakancin da Kabiru yayi mata tayi ta Kiran Sajidan bata Dauki Wayanta ba daga Karshe ma Sai ta Ratayeta kwata kwata ma ta Daina Samunta Khamis ma bata samunsa Kwata kwata a waya Umaima ce kadai take Kiranta Umaima kuma yarinya ce bata san komai ba,gabadaya taji kamar ta Rasa komai ya"yanta da bata da kamarsu batasa tare da ita Ta kara jin Ta Tsani Daada tana ganin Duk itace Silan komai.
Sai da Umaima ta Fadamata Sajida na School kana Hankalinta ya kwanta,Sannan ta Gudura aranta Bazata nemeta ba ai ita Uwa take gareta komai lalacewarta Tana nan a Mtsayinta na Uwa Zata Tsaya tagani Shin Sajidan ta Sauya wata Uwar ce Bayan ita..
Umaiman duk sanda sukayi Waya ta Dinga Fadin Plz Mami Come Back itama Sai tace ba Laifina bane Umaima a kunnenki kikaji Ubanku ya Sakeni yace nabarmai Gida,Har Fadama Daddy da Umaima Tayi ta Sanar da Mami Asma"u aranta tace Dole yazo ya bani Hakuri Haka Umaima na Dawo makaranta ta gansu ta Kira Mamin ta Fadamata kanta ya Fashe ta Fadama Hajiya Turai wacce tace"Ai daman na sani Kabiru baazai iya Rayuwa baki ba..Allah yasa su kwaso Kafafuwansu nan gida sai nayi musu Fata fata kafin na yarda ki koma mu Zaimaida Kananun mutane..!
Ita kuma Mami Sai Mirmishin Mugunta take yi Tana Tunanin yadda Mustapaha da Malami da shi kanshi Kabirun zasu Duka suna bata Hakurin ta koma ma Dan"uwansu sai Ta Rama Wulakanci da Tozarcin da suka mata Musamman ma Mustapha Daya Dauki yarsa ya aurama Imran bai ma Tsaya Jimamin Sakin kaskascin da akayi ma yarta ba Da Umma data bata mamaki Wlh ita taga Kalar kowa a wannan Dangin Bata taba Tsammanin Umma Zata yarda a bama Imran auran yarta ba ta Dauka saboda ita da Sajida ita ta mike tace A"a in ta kama sai dai Imran din ya Maida Sajidan ko kuma ya Fita Waje ya auri wata badai acikin Dangi ba.
Sai dai tayi ta Zaman Jiran gawan Shanu Har Washegari Shuru bata ga Kowa ba ta ta kiran Umaima bata Samu ba Tatafi makaranta Sai da ta Dawo Dataga Kiran Mamin Dayawa Bayan ta Kirata take Tambayanta ina Baffaninta..?
Umaima ta Tabbatar mata tun da Safe suka kama Hanyar Dukku Harda Dad dinsu Mami Asma"u sai taji jikinta sanyi Jin Tunaninta bai zama Daidai ba Ko Hajiya Turai dataji sun Tafi Dukku Jikinta yayi sanyi ada ta Hango Daidatawar Komai,Taso ne itama ta Wulakanta Kabiru kamar yadda ya Tozarta mata y'a sai dai hakan bai samu ba ba Baffa Kabiru ba su Abba sai Mami Asma"u ta koma Tana neman ma kanta Mafita ammh Har Lokacin batayi nadama ba Tana ganin koma meya faru ita aka Cuta..!

*****

Daada sai da tayi kwallah da Taga Zaratan ya"yanta nata agabanta Bata Zata ba sai dai ta gansu kwatsam Baffa Kabiru ya zube gabanta yana kuka yana Rokonta gafara Daman Wlh Aranar ta yafemai komai ita bata Rikesa ba Bacinrai ne ta Rumgume sa Tana Fadin ta yafemai Duniya da Lahira.
Da kansa ya Fadama Daada Hukuncin Daya Dauka kan Asma"u bai Fadamata Sa"insansu ba yadai Fadamata ta shigar da Complain Zatayi kararsu,Shiyasa ya Saketa Daada bata ji Dadi ba sosai tayi mai Fada ta kuma ce Maza maza ya maida Matarsa Dakinta nan yake Fada mata Zuwansu Abba da jiya da Abunda ya kawosu da yadda suka Shawo kansa ya Maidata Dakinta da Sharadin Daya Saka mata.
Daada taji Dadi Farinciki ya Cikata ya"yanta sun Hada kansu ta Dinga Saka Musu albarka su da Zuru"ansu Ta ce kuma Sharadin Baffa Kabiru yayi Daidai gwara ya Rabu da Asma"u Tayi Hankali da kanta ammh in yayi Saurin Dawowa da ita Zata ga ta isa ne kuma Mtsayinta yakaine.
Daada Ranar Tare da ya"yanta taci Abinci Cikin Soyayya da kauna Tana Sharan Kwallar Tunawa da Marigayi Hamisu Dukku Allah ya jikan Maza Domin Tabbas Mazaje sun kwanta Dama.
Kiran Sallar azahar ya tadasu Daga gaban Daada suka tafi masallaci su kai Sallah suka Dawo suka iske Daada na Sallah bata idar ba nan suka Zazzauna suna cigaba da Hiransu Cikin Hiran ne Baffa Kabiru ya kalli su Abba yana Fadin"Malami Mustpaha nace ba..?ina mganar Tarewan ya"yana ya aka kwana ne Imran da mai sunan Daada..!?
Ya fada yana kallonsu Daddy da Abba suka Kalli juna cikin jin Dadi Lalle Ya Kabiru ya Sauya..!
Abba yace"Mustpaha yacemin wai Mganata tana Hannun Imran..Ammh ai naga Daada ce Zata yanke Lokacin ko..?
Daada Data Shafa adduarta bayan ta idar da Sallah ta juyo Cikin Fara"a Tana Fadin"A"a mgana bata Hannuna ai na gama nawa Tun a wanchan karon na Sanar daku ku zaku Tsara Komai nace dai ayi Biki na al"ada na Fulani ku bama Kowani bangare Dama ni ina nan Dukku bana bukatar kowa sai dai aturomin ita Mai sunan Tawa kafin Tarewar ina son ganinta..!
Suka Jinjina kai Dukkansu kafin Daddy yace"Insha Allahu Daada Zata zo..Dayake Text suke yi a makaranta kuma ina jin da sun gama sai Jarabawar Second Semester..!
Abba yace"Eh hakane ma naji suna Fada ita da mai sunan Autan Daada Munari..!
Baffa Kabiru yace"To ai sai mu Tsaida Lokaci ko .?me ake jira ai anyi mai Wahalar tunda aka Daura auran gwara ayi komai Cikin Lokaci Ta tare Dakin Mijinta mun gama Dasu sai muji da Sauran yaran namu gama Babbansu nan Malami kaima aure Zan maka..!
Gabadayansu Dariya su ka saka Harda Daada Abba na shafa kansa yace""Haba dai Yaya ina ni ina aure Tsofai Tsofai dani ko Daada.?
Ai ma barma yaranmu..!
Baffa Kabiru yace"Ban yarda ba..Daada ki Zama Shaida in akwai Wacce Daga barayinki kika ga ta Dace muyi mgana zan Biya Sadaki da komai kabar cewa ka Tsufa yadda kake din nan sai ka auri yarinya Danya Sharaf da ita Wlh..!
Dariya suka kara sawa Gabadayansu Abba na Fadin"A"a Allah ya Rabani da abun kunyar auro Sa"ar Munari..!
Daada dai Dariya Kawai take yi Ranta Kamar Farar Takarda Saboda Farinciki.
Baffa Kabiru ne ya kauda mganar da Cewa"Ina jinku..Ya kuke ganin Za"ayi..?
Daddy yace"Ni mun yi mgana da Ya Malami nace mgana tana Hannun Imran ya tambayesa yaushe yake son Tarewar? Tunda shine Mijin kuma Dukkan Hakki na kansa ne ni ina da a Shawaratace da an Bari nan da Wata Hudu zuwa Biyar Tunda bai dade da Fara aiki ba yanzu kan Lokacin komai ya Daidaita sai a Shirya Bikin Tariya ga Ya Malami ma Monday zai Fara shiga office shima kan Lokaci abubuwa sun Daidaita itama Inteesar sun gama Jarabawa sun shiga Level 2..!
Daada Nadaga gefe tace"Mustapah yayi Tsawo..nifa so nake kafin na Mutu na Fara goyan ya"yan Jikokina abayana..!
Baffa Kabiru yace"Zaki goya da yardan Allah Daada ba Mtsala indai kan Kudi kake wannan mganar Mustapha ba Ruwanka kaida Malami ni nine nan Uban ango kuma Uban Amarya na Daukin Nauyin Siyama Imran Gidan da zai zauna da Kayan lefe ita kuma Inteesar Kamfanin Marhaba Zata zo ta kawata mata Gidanta da yardan Allah ni nawa Bangaran kenan a Mtsayina na Uba..!
Ai Abba da Daddy sun kasa mgana Daada ce tace"Allahu akbar..Allah ya jikan Mahaifinku..Allah yasa ya Huta..Ka kyauta kabiru..Sai yau ka Nuna min ko bayan Raina kai Uba ne ga Duka kannenka da ya"yansu Allah yayi muku albarka..!
Suka amsa da Ameen dukkansu.
Abba yace"Imran nada gida Bankin Daya Fara aiki dasu sun basa Gida Da Mota Kyauta..Ya kabiru Abubuwan zasu maka yawa..!
Baffa Kabiru yace"Bakomai kada na karajin wani cikin ku yace wai Abun zai min yawa don Uba yayi ma ya"yansa Wani abu Laifi ne..?
Ko kuwa ku in kumma Sajida ko Umaima wani abu a Mtsayinku na Iyayensu zan ce wani abu ne..?
Gabadayansu suka girgizamai kai.
Shi kuma sai ya Kada kai yana Fadin"To kada ku kara Cewa komai..Yanzu abunda Za"ayi kai Malami kiramana Imran din muji yaushe yake son Tarewar..?
Abba bai yi gaddama ya Fito da Wayarsa ya Lalubo Lambar Imran ya Kirasa sai da ta gama Ringing bai Dauka ba kana ya Biyo bayan Kiran Abba din..
Abba ya saka a wayar a amsa kuwwa Suka gaisa da Imran Dake Cikin Office dinsa yana Tsaka da aiki duk da ya Kusa tashi Karfe 3pm na Rana zai koma Gida.
Abba yace"Imran yaushe ne kake Tunanin ya kamata Inteesar ta tare a Dakinta..?
Imran ya Dakata da Latsa Computer Dake gabansa kafin yace"Abba meyasa kowa ke Tambayana ne..?Haka itama yaran nan su Munari suka Turo ta Tana min mgana na Dauka ku zaku yanke Lokacin..!
Abba yace"Eh duk da haka kaima aji Ra"ayinka da Lokacin Daka ke so..!
Imran yayi Shuru yana wani Tunani kafin yace"Abba Kuna Tare da Daddy ne..?
Abba yace"Eh Harda Baffanka Kabiru muna Dukku gaban Daada..!
Imran ya karkace kai aransa yace na gano komai wato su Abba sun je Daidaita Daada da Baffa Kabiru ne
Yamutsa Fuska yayi kafin yace"Ni fa Abba bani da ta cewa..I think ba wani abu ko duk abunda kuka yanke is ok..!
Abba yace"Kada ka damu ka Dai Fadi Lokacin..Ga ma Baffanku nan yace shine Uban ango da Amarya Hatta Lefe ya Dauke maka..!
Imran ya Zaro ido Cikin Mamaki kafin yace"Ni din..!
Abba yace"Kwarai da gaske Haka yace..!
Imran bai samu Zarafin mgana ba Baffa Kabiru ya karbi wayar Hannun Abba yana Fadin"Son..Baffan ka ne Time kawai zaka Fadi Lokacin da ka ga yayi maka daidai..Baka da Mtsala ko Katin gayyata ban ce ka Bugo ba ni Dakaina zan yi komai Lokacin kawai muke son ji..!
Imran yayi kasake yana ganin abun mamaki kamar a mafarki sai dai bai yi Saurin Saki ba Saboda bai gama Tabbatar da abunda Zuciyarsa ke Fadamasa ba.
Cikin Dan Kaushinsa yace"Da ka barshi Zan yi komai da kaina Insha Allahu..!
Baffa Kabiru bai Damu ba Daman yasan Za"ayi haka shiyasa yayi Mirmishi kafin yace"Ba ruwanka Nauyin Uba Daya Rataya akaina zan Sauke Lokaci kawai nake so naji..!
Imran bai da ta tace illah ya Muskuta yana Fadin"Karshen wannan Watan a Think is
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment