Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ku Daidaita kanku Taje ta bama Daada Hakuri is better in mu ya'yanku indai kuka Shiryan kanku..!
Kai ya kada mai kafin yace"Shikenan..!
Khamis ya Rusuna yana Fadin"Zan ga Mami kafin na wuce Dad..!
Yana Daukan Takardunsa yake Fadin"In bazaka Dade ba sai mu ijiyeka Airport kafin na wuce Office..!
Khamis ya juya yana Fadin"Yanzu zan Fito Dad..!
Yafice Uban ya Bisa da kallon Tsausayi ya Tabbata karfin Hali kawai yake yi ammh abun ya tabasa Asma"u batasan ta Ruguje Farincikin ya"yanta alokaci Daya bane,Sakarya kawai.
Takardun Hannunsa ya ke sakawa cikin Karamin Briefcase dinsa.
Knooking ya farayi yaji Shuru jin Kofar tana Bude yasa ya Tura ya shiga Lokaci Daya da Sallama.
Tana zaune kan kujeran Dreesing Mirror Tana waya shiyasa bata ma ji knooking din ba.
"Ka shirya komai..Yau nake so na shigar da Complain din Brr.Zailani..!
Iya abunda yaji kenan ya Kira Sunanta da dan karfi.
"Mami..!
Da sauri ta waigo cikin dan Tsoro jin kira Daga sama ganin shine yasa ta Sauke ajiyar Zuciya ta Mike Lokaci Daya Tana Fadin"Zan Sake kiran ka Brr.Zailani..!
Daga haka ta Datse kiran Tana kallonsa lokaci Daya Tana Fadin"Son badai har zaka wuce ba..?
Tafada tana kokarin Zama gefen gadonta.
Kallonta yake yi cikin Tsaisayinta ganin yadda tayi wani Figai Figai Cikin kwana Biyu ba gayun nan sam kamar wacce ta tashi Daga Cuta Idanuwanta duk sun kode saboda kuka da Damuwa.
Ajiyar zuciya ya Sauke kafin yace"Why Mami..? Meyasa bazaki bar mganar nan ba..? Daad zaki kai kara ko Daada ko su Baffa..?
Karamin Tsaki taja Kafin tace"Yancina Zan kwata son..Rayuwar yata suka Lalace Wlh bazan bar wannnan abu ya Tafi a banza ba ka duba ka gani Sajida Tana gayamin mgana ni Mahaifiyarta gaban kowa da kowa..? Wlh Bazan Lamunci su Rabani da y'ata ba Dukkansu zan maka su a Kotu Dad dinka naga alamun yana so ya manta da ku ya"yansa ne zai Biyema yan"uwansa to bai isa ba ko ya amince ko bai amince ba sai na shigar da Complain..!
Tafada cikin son Tabbatar da mganarta.
Khamis ya Dafe kansa yana Fadin"Mami why nace.? Inace ke kikace baki son Auran Sajida da Imran kuma yanzu komai ya kare Why kike hakane.?
Inace abunda kike so aka yi miki..?me yayi Saura..! Don Allah ki bar mganar nan ki Je ki samu Dad kuyi mgana ki basa Hakuri sannan kije har Dukku ki bama Daada Hakuri Saboda mganar Gaskiya baki kyauta ba Uwa uwace kuma ana Sauya mata ammh Mami Ki Sani ba"a Sauya uwa kamar yadda Muma kome kika mana kome kika Zama kina nan a Mtsayin Mahaifiyarmu bamu isa mu sauya ma Tuwo suna ba kuma sai in da karfin mu ya kare in muka ga wani zai Tozartaki..!
Mami Asma"u baki ta saki da Hanci Tana kallonsa kafin ta Mike Tsaye da Sauri Tana Fadin"Au Shi Kabirun ne ya aiko ka ka gayamin haka..?
Yana kokarin mgana ta Dakatar dashi da Hannu Tana Fadin"Ya isa..Basai ka kara cemin wani abu ba..Bana Bukatar jin komai Daga gareka ai ka Riga ka Fadi sakon ka Shikenan sai ka bari nima nayi mgana.!
Shuru kawai yayi yana mamakin Taurin kanta Cikin bacin rai ta Cigaba da Fadin"To in aiko ka yayi kaje ka Fadamai bazan je na bama kowa Hakuri ba Domin ban Batama kowa ba Ni ya kamata ba abama Hakuri ni da aka Lalatama Yata Future dinta Bazawara zan kirata ko Sakin Wawa..?wannan ai Cutar ma tana da yawa in shi yayi shuru ni sai nayi Shuru..? Wlh basa kaunarsa sunan yana Dan"uwansu ne da basu yi mai haka ba In shi bazai iya cewa komai ba Ni zan iya kan wannan mganar sai inda Karfina ya kare..Ni ina da kudi kuma na gaji kudi da asali Zan iya shari"a Dasu har Mahadi ya bayyana Shege ka Fasa..!
Kai ya gyada kawai kafin ya Juya yana Fadin"Mami kiyi Tunani..Ki kara Tunani abunda kika aikata bai Dace ba..kuma wanda ma zaki aikata bai Dace ba..Ina Tsoron abubuwa suxo su Lalace..!
Tsaki taja Tana Fadin"Komai ya Dade bai Lalace ba..Bazan ja da baya kan mganata ba..!
Ficewa kawai yayi ransa na kara Kunci In Mami ta aikata abunda tayi Niyya komai fa Zai Lalace wazai Dakatar da ita..?
Dad bafa bazai iya Dakatar da ita ba,Ta gama Rainasa sai dai in Justice Tafida zai kira ya Fadamawa Mahaifinta Kila in ya mata mgana Taji Hajiyarsu kuwa bama zai kirata ba Domin kamar gadon Hallayanta ne Mamin ta Dauki bama zata Dakatar da ita ba sai ma kara mata Karfin gwiwan da zatayi.
Koda ya Fito Dad na Jiransa ya shiga Mota suka Fice Umai ta Dade da wucewa makaranta a Airport suka ijiyesa kafin Baffa Kabiru ya wuce Wajen aiki Kafin Jirgin su ya tashi Khamis ya Kira Kakansa Tsohon Alkalin Alkalai na kasa Gabadaya Justice Tafida bayan sun gaisa ya Kwashe komai in Brief ya Fadamai sannan ya karishe da rikonsa kan ya Dakatar da Mami kan shigar da wannan Complain din..!
Justice Tafida ya Fahimci jikan nashi kuma yayi mai alkawarin Zai kira Mami Tazo gida ta samesa zai mata mgana Daga haka suka Rabu Lokacin ma Jirgin su ya kusa tashi sai kiran suna akeyi kashe Wayarsa yayi ya Hau kan Layi yana Tunanin in ya tafi zai Dade bai Waiwayi gida ba sai ya manta da Bacin Ransa ba zai kara Dawowa kuma wani Bacin ran ya kara adding kan nashi ba.
Koda karfe 9am na Safe yayi jirgin su ya Lula Sararin Samaniya yana Fatan Allah yasa Kakan nasa yayi wani abu In kuma bai yi ba to abubuwa fa zasu Kwabe ne,Domin yadda yaga Dad ya Shirya aikata komai kamar yadda Mami Tace baja da baya.
Ashe duk wayar nan da Justice Tafida yayi Hajiya Turai Mahaifiyar Asma"u Tana Zaune ta gama jin komai suna gama mgana ta fara Bala"i tana Fada Tana Fadin"Wlh kada kace Zaka Hanata Kwatan yancinta..Wannan ai Ya saba Sharia..auran kaskasci sukayi mata da Farko ni nan na Taushi Asma"u ta yi Hakuri da mganar kuma Shikenan yanzu sai a sakar mata yar da ko Gidan auran ma bataje ba?
Ai ko Kabiru bai Taki gaskiya ba Shi din banza waye shi?Takala dan talaka Asma"u ai ba Kalar sa bace Soyayya ce kawai da Allah ya Dora mata ammh ai Wlh ko Daya Kalan Zaren ai ba Kalan yadin bane in shi yana Tsoron yan"uwansa bazai iya mgana ba a kyalemin ya'ta ta kwaci Hakkinta amfanin Ilimin kenan!
Justice Tafida ya Murmusa kafin yace"Hajiya Turai kubi komai a Sannu..Kada kimanta Kabiru ke auranta..Sannan wannam mganace ta Danginsa fa da Mahaifiyarsa..Anya Asma"u ta taki gaskiya?Daman ai tace bata son Auran yar taata da shi yaron Dan uwwn mijin nata ba ya Saketa ba ba shikenan an muku abunda kuke so ba kuma mganar shigar da kara For What Turai..?Wlh ki shiga Hankalinki kema ki Fadama yarki Kada ta Sake ta shigar da wata kara in kuma taki ji bataki gani ba..!
Daga haka ya Dauki Farin Glass dinsa ya sanya ya Cigaba da karatun Jaridarsa yana jinta Tana ta Masifa Tana Zagin Kabiru wai dan Talaka bai da komai Mirmishin gefen baki yayi aransa yace"A"a fa Kabiru fa ba Talaka bane...Shi wani ne Mahaifinsa Har ya bar Gidan Duniya Alkali alkalai ne na Kotun musulunci kuma Talaka bai Taka wannan Mtsayin..!
Hajiya Turai Daki ta koma ta Kira Yarta Tana Fada Tana Fadin ita ta bata goyon baya Shari"a zuwa Kotun koli su bazasu ji tsoronta ba Mami Asma"u ta Fashe da kuka tana ta Fadamata irin yadda yan"uwan Baffa Kabiru suka Tozarta tare da Mahaifiyarsu Ta kare da Fadin"Hajiya Sun Rabani Da Sajida..Wlh neman zagina take saboda wannan Tsinannen yaron..!
Hajiya Turai tace"Rabu dasu duk zasu gane basu da wayau..Saki ne dai Matakin da Kabiru zai dauka na karshe ko..? To in ya fasa ya sake kin yagani in baki samu wani Babban goron Daya Takasa ba..!
Dayake Idanuwanta ya Rufe bata Fahimci Zata Tafka kuskure ba Mami Asma"u na Fadin"Wlh Hajiya..Ai daman ance Babban goro sai magogim karfe..!
Sun dade suna mgana Hajiya Turai bata Taushi Yarta ba ko Daya sai ma kara zugata Da tayi shi ya kara mata Kwarin gwiwa suna gama waya tayi wanka ta Fice a gurguje ko Karyawa batayi ba Ta fita taje Office suka Hadu da Brr. Zailani kan Tana so Ashigar da karar kai Tsaye ne Daga Kotu ta Cike Complain Form kuma ta na karan Daada ne da ya"yanta Guda Biyu Mustapha Hamisu Dukku da Abubakar Hamisu dukku..!
Abunda bata sani ba suna gama mgana da Brr.Zailani ya zagaya ya Kira Baffa Kabiru ya sanar dashi komai,Daman tun sanda Mamin Ta Kirashi kan Complain din yaji mamakin wai zata shigar da kara kan Mahaifiyar Brr. kabiru da Yan"uwansa Shiyasa ya Kirasa ya Fadamai shi kuma yace da Zarar ta Cike Complain Form ya fadamai Lokacin ne zai yi mganin Asma"u Zata ga True Colour dinsa da bata taba gani ba sai ya Koyamata Hankali Zai nuna mata ana Sauya mata ammh ba"a Sauya Uwa da yan"uwa.
Gabadaya Ransa ya gama baci yau Za"ayi ta kare Baya so ya yanke Hukunci cikin Fushi shiyasa bai Dawo Gidan ba yana son ya yanke komai a Saukake.
Yana Office Sajida ta Kirasa Tana Fadamai ta Dawo makaranta yau daga Dukku yana ta mamaki Tsausayinta ya kamashi Data gayamai a Motar Haya ta dawo ya sani itama ta Guji Gidan ne saboda Mahaifiyarsu ta gama Illata Zuciyarsu,Yaji kamar yayi mata Kwallah Fatan alheri yayi mata da kuma Nasihan ta Cire Damuwa tayi Facing din karatunta ta amsa mai da Insha Allahu.
Dukkansu sun kashe Wayar kowa Zuciyarsa ba Dadi,Baffa Kabiru kamar yayi kwallah,Kudi ya Tura mata 30k yace ta siya abunda bata dsshi
Lokacin Dataga Sakon nasa Tana libary ne tazo Karatu ba Domin Tana Fahimta ba sai domin shine Mafitanta.
Yau da Safe goggo Maimunatu ta koma Bauchi Mijinta yazo duba Daada Daganan ya wuce da ita Daman itace ke Kula da ita goggo Bintalo ba Ruwanta Ballatana Daada da Fushin Mami da Dad ya shafeta
Ta riga tasan tayi rashin Rashim Masoyin da bazata taba maida kafarsa ba,Mami Ta riga ta gama Lalatamata Farincikinta gani tayi Zaman bai da wani amfani yasa ta fara shirin Tafiya Duk bata wani jin Dadi ga Sakewar jikiga na zuciya.
Sai da tagama Shiryawa kana taje Dakin Daada Tayi mata sallama Daada Tsausayin Sajida ya kamata ta Rumgumeta tana Lallashinta da ban baki Sajida na kuka tana Rokon Daada ta yafema Dad dinta Daada tace bata Rikesa ba in ya gano kuskuransa ita Tafi kowa Murna da haka.
Ita ta bama Sajida 5k duk da tace tana da kudi tace ta kara Tunda makaranta Zata koma
Bayan Tafiyar Sajida Daada tayi kuka,Yarinyar abar Tsausayi ce Dama Dama haka bai Faru ba data Hakura da Cin Mutumcin Asma"u sai dai ai ba ita auran ke hannunta ba Wanda Auran ke hannunsa ya warware kuma bazata Tursasamai kan sai ya maida Sajidan ba, tayi alkawarin ta bar kara Tursasa kowa koda ya"yanta na Cikinta ne.






*Shakira..*
3/25/22, 22:52 - Ummi Tandama😇: *GMB2🅿�19*

*Wannan Littafin na kudi ne don Allah kada ki karanta in har kinsan baki biya ba N300 ne kachal kan wannan acct din 0552179550 Gtb ku sani ku kara Sani Mace mai aji mallakan komai nata nakeyi bata jiran abun Sata 09069067488*

Karfe 8:30pm na Dare ya shigo Gidansa,Mami Asma"u ma bata Dade da shigowa ba gidansu ta wuce Mahaifinta ya kirata awaya yace Tazo yana son ganinta Justice Tafida.
Duk da Justice Tafida yace mata ta Janye Ra"ayinta ammh bata ji ba shi kuma Dan Boko ne mai akidar Dabaya mtsama ya"yansa kan Ra"ayinsu zai gayamaka gaskiya Ruwan ka ne kayi aiki Dashi ko kar kayi aiki dashi Shi dai bazai Tursasaka Dole ba kayi Karatu kasan Daidai da akasinsa.
Hajiya Turai ce ta rika Zuga yarta ta batayi Tunanin abunda kan je ya dawo ba Mami Asma"u saboda Tana ganin kamar abun kunya ne aji wannan abun ya Faru da yarta yasa ta Roki mahaifiyarta karta Fadama kowa cikin yan'uwanta Asma"u basu da yan Uba Hajiya Turai ce kadai Matar Juctice Tafida tun auran Saurayi da Budurwa.
Da wannan Famfon Asma"u ta Dawo Gida Allah Sarki Umai ce kadai agida Daga ita sai yan aiki,shiyasa saboda Kada kadaici yayi mata yawa data yi wanka Ta sauya kaya ta Sauko kasa ta Zauna Wajen Umaima Wacce take assigmemt din da aka basu a makaranta ta Hanyar Browsing a wayarta.
Bata ce ma Mamin komai ba bayan gaisuwa saboda ba Huruminta bane Ammh Tabbas akwai Mtsala Tsakanin Mami da Dad din,Suna nan Zaune ya shigo Kallo Kallon sukayi ma juna Shida Mami Asma"u shi ya Fara Dauke kansa Umaima ce tataso Ta Rumgumesa tana yimai Welcome lokaci Daya tana karban yar karamar briefcase din Dake hannunsa ya Haura Sama tabi bayansa Mami Asma"u ta bisa da Hararan kasan ido gobe goben nan Zata je ta shigar da kara taga mai hanata
Har Dakinsa Umaima takai masa Jakar ta Fito ta barsa zai yi wanka bayan ta Fadamai tana Jiransa ya Sauko su yi Dinner.
Saboda Umaima yasa bayan yayi wanka ya saka Jallabiya ya Sauko kasa Direct Saman Dining ya Nufa Umaima na ganin haka tace ma Mami itama Ta taso,suci abinci Saboda Umai yasa ta Mike Tana wani Takun isa ta karisa Saman Dining din ta Zauna gabadayansu haka sukaci Abincin kowa na saka abunda zai Fishasheshi acikin Ransa Umaima ce kadai ke karadinta ita Kadai duka iyayen Daga Uhm sai Uhm ne Har suka gama cin Abincin kowa ya Watse Umaima Dai Dakinta ta Shige Ta karisa assigment dinta ta kwanta daman ka"idan Gidan da Wuri kowa ke shigewa ya kwanta taji ta samu natsuwa Dazu da sukayi mgana da Sajida bayan ta Dawo makranta Ita Sajidan ta Kirata sai dai yanayinta a Sanyaye yasa tasan Zarginta ya Tabbata wani abu ya Faru ko yana kan Faruwa Sun rabu da Sajida kan Umaima din zata zo ta ganta Ranar Sati a makaranta Tunda ita Sajidan tace ba zata samu Dawowa Gida Weekend ba wannan Satin.
Akallah ta samu natsuwa bada yawa ba.
Misalin Sha Daya na Dare Baffa Kabiru ya gama Duba wasu Tarkadu kan Shari"ar da suke kai ne Kana ya Mike ya Fice Daga Dakin nashi Sai da ya Fara Leka Umaima yaga tayi barci kana ya Rufomata kofa Direct Dakin Mami Asma"u ya Nufa Daman Saboda Kada Umaima taji Sa"insan da ita ne yasa ya bari sai ta kwanta barci.
Bai Tsaya ma mata Knooking ba kawai ya Tura kansa Lokaci Daya da Sallama Fitowarta Daga wanka kenan ta Saka wata doguwar Riga mai Taushi Ta barci shirin kwanciya Take yi ya shigo.
Dakata tayi da kokarin Zama kan gadon ta gyara tsayuwarta Tana kallinsa shima kallonta yake yi Cikin Wani yanayi sai dai bai Hango Nadama a Tare da ita ba yasanta Tana da Kafiya da Taurin kai,Ko a Sharia in ta samata naci bata sukuni sai Tayi Nasara.
Gyara Tsayuwa yayi Lokaci Daya yana Harde Hannunsa ya goya a bayansa Cikin Kallonta ido na ganin ido ya Fara takowa zuwa gabanta suna Tsaya suna Nazarin juna na wani Lokaci ita ta Fara kauda idonta a Kansa saboda ai Namiji ne bazata iya Juran kallon Cikin Idanuwansa ba.
Cikin dan Sanyin Murya yace"Asma"u Meyasa kika cike complain Form..?
Kai Tsaye yayi mata Tambayar yana kallonta Tana kallonsa Dan mele baki tayi Tace"Kafini Sani..!
Yana kokarin Boye bacin Ransa yace"Wa zaki kai kara..? Mahaifiyata ko yan"uwana..?
Mami Asma"u bataji wani ko Dar ba Tace"Dukkansu..Zan yi kara Domin da saka Hannunsu Rayuwar y'ata ta ragu,je in kai kayi shiru ni bazan yi Shuru ba sai na kwaci yancina..!
Bata gama Rufe baki ba ya Tare ta da Fadin"Yanci ko..?ina yancin..? Ke kisan wani abu wai shi yanci ne..?In yancin kike nema shi aka baki kin nuna bakisan auran Sajida da Alokacin na mara Miki baya saboda son da nike miki yanzu kuma an yi miki Abunda kike so kuma ya Zama abun Tozarci a wajenki..?ke wata irin macece mai son kanta Asma"u..?
Baki Tunanin kowa sai kanki.?tunda mukayi aure na Sakar miki Duka wani Dama hatta da Damar dangina Duka na baki ina bin Duka Dokokin ki kamar kice Mijin nice matar..Ina jin mganarki ina Danne Ra"ayi na Saboda na Fitata naki Ra"ayin Duka wannan abun bai isa yasa ki gane ke mai son kanki bane..?ki duba irin abunda kika aikata a Dukku Saboda na baki Dama kika cima Daada Zarafi kika Hada da yan"uwana ke baki ji kunya ba..?in nayi ma iyayanki Haka zakiji Dadi..?nace ki Duka ki bata Hakuri gaban Duka Kowa da kowa kika Nuna ban Isa Dake ba Nima ba kowan kowa bane a Wajenki,Sanadinki Daada tayi Fushi Dani kinsan Dafin Fushin Uwa kuwa Asma"u..?
Kuma Duk da Hakan bai isheki ba Sai kuma kika Bullo da wata mganar banza na zaki kai uwata da yan"uwana kotu ke gaki Ubanki Tsohon Alkali kuma ga ki Lauyar gwannati ko..?
To Shege ka Fasa Asma"u ni kuma zan nuna miki Jini yafi Ruwa kauri Uwa da yan"uwa suna gaba da kowa a wannan Duniyanan nagodema Allah Dayasa na gane kuskure tunda wuri kuma da yardan Allah Duk Zan gyara inda na kuskure ba kyalekin da nake yi bane yasa kike Wasu iskancin ba To kiyi yanzu nagani nace kiyi yanzu na gani din in ban yi mganinki ba..!
Har ya gama mgana Mami Asma"u bakinta a Bude Tana Binsa da kallon Mamaki Kafin tace"Ni yau kake Zagin Ubana Kabiru kan gaskiyata..?
Kai Tsaye yace mata"Eh an Zaga din Ashe Uba yafi Uwa ko..! Naki iyayan yan Daraja ne kuma yan gold ne ashe kina Sane nawa uwar kika Raina..!
Cikin Bacin Rai tace"Iyayena sunsan Abunda sukeyi bazasu taba aikata abunda Taka Uwar ta aikata ba...Mai son kanta kawai..!
Cikin Shima Bacin rai da Hargowa ya nunata da yatsa yana Fadin"In kika kara Fadin kalma Daya na batanci kan Daada sai na Bata Miki rai..!
Azatonta Burga yake mata sai ta gyara Tsayuwa Cikin Gatsali da Hargowa tace"In nace fa..?
Me zaka iya Kabiru..?Na Fada na kara Fada Daada Tsohuwa ce mai son kanta Mara adalc..!bata gama kai karshen mganarta ba wasu Tagwayen Maruka Dama da Hauni suka Ziyarci kuncinta Saboda Zafin marin Da Sai ta Kife saman gado
Cikin Zafin zuciya jikinsa na Rawa yake Nuna ta da yatsa yana Fadin"Kadan kika gani in har bakin ki bazai yi linzami ba..Na Rantse har ga Kika Kara fadin Tak kan Daada sai nayi miki Abunda baki Taba Tsammani ba..!
Yafada Jijiyon kansa suna tashi Saboda Bacin rai Mami Asma"u da mamaki ya Sandarvda ita Gefe Daya ga Zafin marin Daya gigita Daga zaunen Hannanunta saman kuncinta Cikin Zubar Hawaye tace"Ni ka Da ga Hannu ka mara yau Kabiru..!?
Kai ya gyada Mata yana Fadin"Wannan ma kadan nayi miki In baki iya bakin ki ba Sakarya kawai wacce bata san inda ke mata ciwo ba..!
Mami da kukan Bakinciki ya Ciyota ta Mike Cikin Hargowa da kuka taci Kwalan Baffa Kabiru Tana Fadin"Wlh baka isa ba Tunda ka mareni baka mari banza ba..Kan gaskiyata..? Ance Daada ta cika sonka Tsohuwar banZa ce i...!
Bazai iya jin Duka kalamanta ba Saboda in ya gama ji Bacin rai zai sa yayi mata Dukan Mutuwa Watsar da ita yayi a kasa cikin Fushi da Tsananin kamar ya bita ya Tattakata yake ji bai Taba Nadamar auran Wayewa da Boko ba sai yau Cikin Fitar kwallar Cin Zarafin Dayajama Daada Uwa garesa yace"Kije na SAKE KI Saki Daya Asma"u..Kibar min gida yanzu nan..kuma mganar Complain kada ki Fasa shigar da kara ni kuma Ina nan ina Jiranki Yar iskar mata kawai mara lissafi..!
Bai Tsaya Jiran Kwakwzonta ba ya Fice Daga Dakin Saboda bacin rai har Bangaje Umaima yayi bai sani ba wacce Rigiman iyayan nata ya Tada ita kuma taci kalmae Sakin da Dad ya Fadama Mami ai sai ta kasa Gaba ballatana baya,Balle taga yadda ya Fito ta Fusace sai Hawaye da kuka kafin ta Kwashu gudu zuwa Dakin Mamin nan ta ganta inda ya yasar da ita kamar irin ta shiga Shock haka Domin tayi kuri ne Hawaye suna Zubomata Shar kamar an Bude Famfo.
Gani take kamar waasa wai ita Kabiru ya ce ya saketa?Duk Abunda take yi Tana Takama da Son da yake mata baata Taba Tunanin Akwai Watarana da Kabiru zai Furta mata Kalmar Saki ba ba Burga kawai take yi Tana Tunanin bazai iya ba,Tana ganin Soyayyar Dayake mata bazai barsa ya iya Sakinta ba yanzu Daya Furtamata Sai Duniya ta Fara juyawa da ita.
Umaima ta Rungumeta Tana kuka Tana Fadin"Mami What all dis..?Dad fa naji yana Fadin ya Sake ki plz ki Fadamin wasa ne ba gaskiya bane.!
Mami Asma"u ta Zura mata ido Tana Fadin"Kema kin ji ko Umai..?Daddy ku yace wai ya Sakeni..Da gaske ya Sakeni ne..?
Umaima na Kuka tace"Mami Haka yace kema kin ji nima naji da kunnena yace ya Sakeki ki bar mai gidansa Why Mami..?meyasa kika azagi Daada.?kamar uwata take fa kema a wajenki Kada ki manta Ita ta Haifi Dad bazai Taba Jure cin Zarafinta Daga Bakin kowa ba Koda Kece kuwa!
Sai alokacin Mami Asma"u ta tabbatar da kanta komai fa daya Faru gaskiya ne Kabiru ya saketa kuma yace ta barmai Gidansa ai sai ta Rukumkume Umaima ta fashe da kuka Innalillahi me ta aikata..?
Saki Gotai gotai da ita da manya Ya"ya ta koma gida Zawarci bata Taba Dauka Haka abun yake ba Lokaci Daya Nadama ta Isketa,Mikewa Tayi Da Karfi kamar Wata Zararriya ta Rarumi Wayarta ta Doka ma Hajiyarsu Waya Umaima na gefe Tana kallonta Tana Sharan Hawaye
Lokacin da Mami ke kuka Tana Sanar da Hajiya Turai Brr.Kabiru ya Saketa Ashar ta Lailayo ta Sakar mai Dashi da Daadan gabadaya Ta Fara fadin"Yau naga aikin Fulani Daman ance Fulani akwai bakinciki da Hassada da son kai da Wauta da Rashin Lissafi eh lalle naga aikin Fulani kuwa ni Turai..Da Tsohon Daran nan zai sakar mana ke ,gotai Gotai Dake ko kunya Kabiru bai ji ba..? Ai ko bai Darajaki ya Ragamiki don Soyayyar da kika Nunamai ba ya Duba Wadanan Zaratan ya'yan da kuka Haifa in mu bazai ga Girman mu ba..!
Tafada Tana kumfar baki Mami ma sai kuka take abun ya Daketa ita kanta Hajiya Turan fa Fada ne kawai ammh Ina Zakaso D'anka da girmansa Shekaru sun ja a kore maka shi awannan Lokacin ai abun kunya ne sosai kuma ba wasu iyaye da zasu so haka ita kanta Kabirun Wlh ya bata Mamaki bata Taba Zaton zai iya Furta kalmar Saki Ga Ma"u ba Tun Daga yanayin Zamantakewarsu da yanayin Zaman auran nasu.
Justice Tafida ta Fadama Halin da ake Ciki Daman yana Zaune ne yana kallon Labarai A tashar CNN,kai kawai ya gyada kafin yace"Ki Fadamata ta shirya Direba zai zo ya Dauketa..Tunda bataji mganata ba Har takai su ga haka Is ok..Kowa yayi yadda yake so..!
Daga haka ya cigaba da Kallonsa Kafin Lokaci Daya yana Danna Wayarsa zai Kira Direban da zai Dauko Asma"u.
Hajiya Turai ta Kallesa kafin tace"Ranka ya Dade ayi haka..?Gotai gotai da Ma"u sai ta dawo gida Zaman Miji ya saketa..?
Bai mata mgana ba sai da ya gama Waya Da Direban kana ya Dago kansa bayan ya ijiye wayar yana Fadin"Sai ta zauna bayan yace tabarmai gidansa Turai..?Abunda ta Zabama kanta kenan bazan hanata ba ai ba yarinya bace She know What is Right and Wrong..Katon gidane ina dashi akwai Dakuna Kowa ya yanke ma kansa Irin Abunda ta Zamar ma kanta bazan hanasa Zama agidana ba kowa nada Righat dinsa so banga abun Damuwa ba..!
Daga haka ya dauke kansa ya Cigaba da kallonsa Ai bata kara mgana ba ta Daga Waya ta Kira Mami Asma"u tace ta Shirya ga Justice nan ya Turo Direba ya Dauketa daga haka ka Katse Kiran.
Mami Asma"u na kuka Umaima nayi Baffa Kabiru bai san sunayi ba yana Cikin Dakinsa Bai kuma yi Nadamar Abunda ya aikata ba..
Yana Daga Tsaye wajen Window yana kallon Haraban gidan Daga waje Mota ta Shigo Daga lambar Motar ya gane Daga Gidan Justice ne karamin Tsaki yaja yana jin karin wani Takaichi Sam dai ba Tsari ace kana Babba da iliminka da komai kace Bazaka Tsawata ma yaranka ba sai dai kace su ba yara bane suna da Rigaht din da Zasuyi abunda suka ga Dama,Daman fa In Boko yayi yawa wani Lokacin Har Kafirta Mutun yana yi.
Agaban Idonsa Mami Ta Fito Umaima na Riketa Tana kuka itama kukan take Tana Dauke da Karamar akwatinta,Yana Tsaye yana jiran yaga koda Umaiman zata tafi sai yaga ta shiga Mota Direba yaja sun Fice Daga Gidan Umaima ta Durkushe
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment