Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ka koya bah" ya fadama kanshi murya can kasa.




⚜B.W.AπŸ–Š
⚜BRILLIANT WRITERS ASSOπŸ–Š




πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’
BOYAYYEN KUDIRI.

πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’
πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’


Story,editing by
NOBLE JUDGE,
Writing KHALEESI.


5⃣3βƒ£βž•5⃣4⃣


Dedicated to
⚜Brilliant writers associationπŸ–Š

I miss you guys lots, ina fata komai na lyf dinku na tafiya daidai, Allah ya amsa maku du'ain ku na khairi ya kareku daga sharrin makiyan ku,

AMIN.✌

Fans din littafin nan nayi kewar nishadantar daku, but rayuwa sai a hankali, ina baran Addu'a daga gareku, na Allah ya amsa min du'aina,

Kuma ina mai maku fatan Alkhairi, Allah ya baku abinda kuke nema,
Amin,❀


"But, amma?"
Ta turo baki tana binshi a baya

"Amma meh smoochsy pooh" shima yayi yadda tayi,

Bata rai tayi tana niyyan komawa daki,

"Ai cewa nayi zaki je gda bance yau bah" ya dafota suka sauka daga mattatakalan dake tsakiyar gidan,

"Ni fah har na shirya kayana kuma na gaya mah mama na yau zan zo"
Saida ya saki baki,

"Jiya jiya fah mukayi maganar zuwa gdan, da daddare kuma, yaushe kika samu daman gaya mata"

Tasa hannu ta zagaye kugunshi,

"Yau da safe manah, ba kai kanata bacci bah"

Tun kafin su karasa falo ta bada space tsakanin su,

"Waya damu ballanta ya lura da abinda mukeyi" bata bashi ansa bah,

Amma suna shiga falo idon Mom a kansu,

'Ita ta damu kuma zata lura'
Ta gaishe dasu kafin ta samu wuri ta zauna gefen Hajia,

"Meh wannan yakeyi anan?" Sai lokacin itama ta lura dashi,

Wani mutum bature, marar tsawo sosai,

"Good morning Sir, Mrs Mas'ud here ta kirani, tace kana bukatar services dinah"

Mom yace a dan gajiye,

"Mom tunda nazo nan na saba yin abubuwa da kaina, bana bukatar yayi ta bina"

Mom bata daga kai ta kalleshi bah sai wayarta da take latsa wa,

Suna hada ido tayimai dan karamin murmushi

"Sorry" ta motsin bakinshi ta gane abinda yace

"Ba komai" suna cikin yima juna smiling Mom tayi gyaran murya,
Natsuwa tayi ta fara kalla ko ina banda inda suke,

"Ehsaas ina da reputation da nake bukatar maintaining,

A matsayina na co- owner din enterprises dinmu, kuma mahaifiyar ka,
Beh kamata aga kana yin komai da kanka bah, most especially a office,

Kana rage ma kanka karfi a idon competitors da yan sa ido"

Ajiyar zuciya yayi sannan ya zauna kusa da ita, ya dora hannu saman nata,

"Mom kin san i don't care with what people think,

But na damu da abinda ma'aikatan mu suke tunani akaina,

Zasu fi ganin girma na in bana barking orders but inayi da kaina,

And"

Hannu ta daga mai kafin tace wani abu

"Okay zanje da P.A office duk da nafi son yin komai da kaina,

Amma da Husna zanje"

'Oh oh oh, no no no no Ehsaas, zaka sani a matsala da safen nan, ya ilahi'

A ranta dafe kanta tayi,

"Kaga tunanin da bana so kanayi,

So low, taya zaka tafi da ita a matsayin P.A dinka, kanata ruining reputation dinmu"
Ta koma hausa

"Farko ka aureta, yanxu kuma zaka kaita office kaje ka nuna mah mutane sauran wanin daka aura,

Ki tabbata beh tafi dake inda mutane masu ji da kansu suke bah"

Tana karasawa ta mike ta bar wurin

"Ehsaas meh kakeyi anan har yanxu, kayi sauri ka bita,

Bata ji dadi bah fah, gani takeyi kayi mata shi yasa ka daina bata mahimmanci kuma kake mata musu,

Gsky kaje ka bata hakuri, muje manah"

Wani irin kallo yake mata har tana ji a ranta yasan ba haka mahaifiyar shi tace bah,

"Ehsaas manah, koh karya nakeyi" tayi fuska tausayi harda dora hannu saman kirji, irin ni

"No Husna am sorry, tnk u"

Yana tashi ta dukar da kanta tana shirin barin hawayen su tsiyayo,

Sai ji tayi an dafata, murmushi tayi ma Hajia dan ta manta da tana nan zaune,

"Ki kara hakuri Asma'u, komai ze wuce in shaa Allah,

Kuma kiyi min uxuri in kinga bana kwabarta in tanayi maki wani abu,

Kina ganin uba ze iya hana danshi shan taba, bayan shima sha yakeyi"

"Meh ze hana,kawai dai shima uban daina sha ya kamata yayi"

Hajia tayi murmushi meh hade da hmmmm,

"Bari inje Hajia" tana mikewa sai gashi da saurin shi,

"Cutie pie, zo muje" ya jata zuwa sama,

"Gobe zamu je gda" murna har a idanunta saida ya nuna

" tunda gobe Sunday sai muje mu dawo" ta bata fuska,

"Ranar zamuje mu dawo" yace yes a hankali,

Girgixa kai tayi,
"Ni sai bayan sallah nakeso in dawo"turn dinshi ne na fiddo idanu waje

"Bayan sallah!" itama saida taji kunya ta dukar da kai,

"Husna har bayan sallah, wata nawa kenan" daga yadda yake magana tason baze yadda da hakan bah,

"Saura sati biyu da yan kwana ki fah" yace NO ya tafi ya barta a nan tsaye,

"Ehsaas" ta bi bayan shi tana kiran shi,

"Yi hakuri toh, kwana nawa zanyi"
Ta tsaya gaban shi tana kallon shi,

"Ni so nake muje mu dawo tare Husna, bana son kina yin nesa dani koh dan"

"Toh koh dan 7 days ne manah, pls"
Goshinsu a hade yake girgixa mata kai

"Pls sati daya kawai" ya kara cewa NO

"Toh kwana nawa zanyi"
Yatsu biyu ya daga mata
"2days kawai" tayi baya tana fada,

a hankali ya daga mata kai yana janta zuwa dakin mahaifiyar shi,

"Mom tace zataje shopping, shine nace ku tafi tare sai kiyi masu Mama tsaraba"

Saura kiris ta furta bazata je bah,

Kyaleshi tayi ya kaita har dakin Mom,

Yana da kyau ka kyautata mah dangin mijinka, tunda kaima kanaso ya kula da naka,

Ballantana shi da tun kafin suyi aure yake ina zesa ina ze aza da iyayenta,

"Mom gata, kuje kuyi having fun, zanyi kewar ku, bari in je lambu wurin Dad, bye wifey"

Ta juya gareshi zatace mai bye, peck ya mata a gaban Mom kafin ya rada mata abu a kunne

"I love you" sannan ya tafi,

"Bazan iya zama dake bah Asma'u,

No I can't let you stay" ta zari gyalenta da bag,

"Maganata ya kamata yaji, basai kince bah tukunna yayi,

Wannan so da kaunar da yake nuna maki duk nawa ne, amma ya karkata su zuwa ke,

Bazan bari sai abu yayi nisa kafin in nemi abinyi bah,

Bazan zauna ina ji ina gani a sake rabani da abinda nawa ne bah ni kadai,
Ehsaas dana ne, ni kadai ke iya sashi farin ciki kuma in share mai hawaye,

You got that"

Ba tambaya bace bah amma saida ta ansa

"Clearly Mom" bangaje ta tayi ta wuce

Laifin wani ya shafe ni, tace a ranta,

"Kinga tsiyar tasu koh Umma, yanxu jibeta dan Allah"

Tayi fiki fiki da ido tana kallon kanta, meh tayi ba daidai bah,

"Ki kula da kyau, daya daga cikin abinda yasa nace baki dace da dana bah kenan,

Kullum ya zamana a shirye kike, ko ina za a iya zuwa dake, but kalle ki, yanxu sai kin bata min lokaci wajen shiryawa,

Kuma bazaki bacemin bah sai kinga karshen masifar tawa"

Ai bata bari ta rufe baki bah ta ruga a guje, binciken kaya ta fara yi,

Riga da skirt ne jikinta na atamfa, ita niyyarta ta daura hijab dinta, wahadas,

Amma yanxu ance batayi bah,

Wani gown ta fiddo cikin kayan da Hajia ta zaban mata na lefe,

Blue ne kalar sararin samaniya, sai falmara meh tsawo yellow meh haske sosai, kaman cream color,gyalen mah blue ne ta yafa dan kar a jirata sai batayi rolling bah,

"Ugh, da sauki dai"
Sai mun dawo tace mah Hajia kafin ta daga kafa dan kar tayi laifi in aka rigata isa wurin mota,


"Ya kiketa bina a baya, koh babu abinda zaki siya ne"

Hadiyar miyau tayi sannan tayi nuni da kayan dake hannunta,

Da kyar take ganin hanya mah, saboda tsirin da sukayi,

"Oh! Kece keta bina a baya shi yasa naxata masu aikin wurin ne" Tace kafin ta hada yatsunta sukayi kara,

"Basu kayan" ta wuce ta barta nan tsaye, ana karban kayan sai ta koma baya,

Taga abubuwa dayawa da suka daukan mata ido, abubuwan da zata so ace ta mallaka,

Babu abinda ta dauka gudun kar aga ta zake


"Kin gama" tace Eh, duk da bata tsaya saurarenta bah tayi gaba,

Gaban mota dama ta zauna, Mom na baya, suna shiga cikin gdan ta tsere dakin su, dan kaman a saman kaya take cikin mota da kuma mall din da sukaje,


"Meh kika siyo cutie pie"

Ahmmmmm tace kafin ta dan sosa keya,

"Ni banga wani abu da yayi min bah a shop din, kila gobe kan hanya in siya masu wani abu"



Bayan an sha ruwa kowa na shirin zuwa masallaci ita kuma ta hau shirya kayanta, dama bah sallah takeyi bah, kawai dai ta kama bakinta neh,


"Muje Husna, in muka dawo sai in tayaki" ya tsaya sa buttons din hannun rigar shi,

Kullum tare suke fita zuwa masallaci, kuma ya jirata in an idar sai su dawo tare,

"Yau na gaji, kaje kawai" okay yace yana tafiya,

Juyowa yayi kaman lokacin yaji abinda tace da kyau,

Ya dade tsaye a wurin bata mah lura bah

"Asma'u" taji gabanta ya fadi, baya kiranta da Asma'u sai in yana so tasan ba wasa yake bah,

"Yau bakiyi azumi bah, true or false" kaman tace tayi kuma sai ta ce Aa

"Kuma bakici komai bah duk yau" ta daga mai kai a hankali,

Yau manya idanu data zuba mai basu sassauta mai zuciyarshi bah,

Bude bakinshi aka kabbara sallah, abinda ya ceceta daga koh mah meh zece

"In na dawo" ajiyar zuciya tayi bayan ya tafi, sannan ta cigaba da shirin ta,


"Asma'u" da sauri ta amsa tana aje aikin da takeyi, sannan ta mike tsaye,

"Muje dakina"

Duk daga kafa saita nemi tsari daga sharrin shaidan kuma sai bugun zuciyarta ya linku,

"Kalli wadan nan kayan ki zaban man gudu biyar"

Alhamdulillah tace a ranta ba wani abu nayi bah,

bin lace da atamfar dake kan kujera tayi da kallo,
Ba daukan lokaci ta zabo wadanda suka fi yi mata kyau,

"Kin iya zabe kam" sannan ta nuna mata shadda harda wasu yadika masu kyau,

"Suma zabi guda biyar"

Da fari ta fara kafin ta nufi sauran kalolin da sukayi mata,

"Sasu a leda, in kin je kice ina gaishe dasu" sakin baki tayi tana mamakin wannan kyauta,

"Nagode sosai Mom, Mungode Allah ya saka da Alkhairi ya kara budi"

Har kasa ta tsugunna tana mata godiya,

"Meye abin godiya anan, ai mu bamu da rowa koh san abin duniya,

Bakaman ku bah" rufe ido tayi tace dama tasan da wani BOYAYYEN KUDIRI tayi hakan, dan taci ma iyayenta mutunci

"Kai talaka na cin banza, da dukiyar mu suke ci, sha , kuma su suturta kansu, akayi aure koh gara babu,

Kuma kinzo kin zauna daga ci sai kashi,

Wannan ai jin dadi ne zama irin ku koh"

Shiru tayi batace uffan bah har saida ta gama sannan ta sake yi mata godiya kafin ta tafi dakinsu,

Saman gado ta zauna da kayan saman cinyarta, shafasu takeyi tana bin kowani zane da yatsanta,

Digar hawaye saman kayan ya tsayar da ita,

So take ta fayyace yadda take ji a ranta a wannan lokacin, kaman ta kwala ihu, ta bayyana mah duka duniya zafin dake cikin ranta,

Kayan ta aje gefen gado, sannan ta dauko diary dinta,

Abinda yafi ci mata rai ta rubuta,

*iyayena sun so hado ni da duk abinda ake kai mah amarya a gdan aurenta,

Babu abinda mahaifiyata bata hada bah,

Ni nace ze zama banna neh dan bazamuyi amfani dashi bah, kuma Hajia saida ta ce basa bukatar akawo ni da komai,

Koh mah meh ya biyo baya ni na jawo ma iyayena bayin Allah,

Allah yasa hakan xe faru, shi yasa na manta da inda za'a kaini, na shafa'a har na jawo manah kaskanci da wulakanci *

Kasa cigaba da rubutun tayi ta fara share hawayen dake bin kuncinta,
Karshe ture littafin tayi gefe ta bar idanunta suyi aikin su,

" Husna " share hawayenta tayi tana kokarin hana kanta sheshekar kukan dake fitowa,

"Husna, meye wannan" ya mika hannu ze dauki diary dinta,

Da sauri ta dauki book din ta rungume, tana yin haka kawai ta cigaba da kukanta, batayi kokarin tsayawa bah,

"Husna!" Yana kokarin tabata ta juya mai baya,

Saman gadon ya hau yana kokarin dagato, amma yana tabata ta matsa da sauri kaman garwashi ne hannun shi,

"Asma'u meye hakan" yana kara kai hannu ze tabata ta sauka daga gadon baki daya,

Daure diary din tayi da igiyarshi, tanayi tana sabon kukan da ta kasa tsayarwa,

Zaune yayi saman gado yana kallon ta, kayanta ta hada tsaf sannan ta mike ta shiga bandaki tayi wanka da kuma alwallar bacci,

"Wifey, zan iya sanin abinda ya saki kuka" wani shehseka ya zo mata da saida tayi ta jan numfashi, jikinta gabaki daya kyarma yakeyi,

"Husna dan Allah ki tallafa min ta hanyar fadamin abinda ke damunki"

Yana dora hannu saman kafadar ta, tayi saurin hankadewa,

"So kike in kwanta a haka ina jin kukan " ya fincikota yana kokarin mannata da jikinshi,
Sai sabon kuka data fashe dashi tana fizgewa daga rikon dayayi mata,

"Ni gdan mu nakeso na tafi, duk laifin ka ne koh ma menene" ta fada da hausa, kara janta yake zuwa jikinshi,

"Ssshhhhh, am here babu abinda zan bari ya sameki in shaa Allah"

Bayan boriΓ± nata ya lafa ta koma ajiyar zuciya,

Cikin kankanin lokaci bacci yayi gaba da ita,

Da asubah kuma tana farkawa shima ya tashi,

"Yau baka tashi da tsakar dare bah"

Yana zaune saman prayer mat, tazo ta jera mai abincin sahur dinshi,

"Banyi bacci da wuri bah"

Zuba mai tayi sannan ta koma gefe abinta,
Dama ba cin abinci takeyi bah lokacin sahur, saidai ta sha ruwa meh dan dumi data sa lemon tsami koh cucumber a ciki,

"Yau bazaki yini da yunwa ba koh" ya tsaya kallonta yana jiran amsa,

"Ai yau gda zanje koh" ji yayi wani abu ya tokaremai a makoshi, abincin ya fita ranshi,

Mikewa yayi ya bar dakin,

Fidda numfashi tayi tana dafe kanta, ta dade nan tsugunne kafin tasa aka kwashe kayan,

Nan kasa ta kwanta har gari ya fara haske, sannan ta tashi ta shirya tana zaman jiran shi ya dawo,

Wani kukan taci ta koshi da har past 1 beh dawo bah, tana kwance a daki ta jiyo dariya da kuma magana cikin babban murya,

Sai lokacin ta bar dakin su ta nufi stairs,

"Am sorry na daina" kuma sai ya kara fashewa da dariya,

Lekawa tayi daga inda take tsaye, tana ganin yadda yake ta fara tun karar wurin,

Fadan da taji Mom nayi mai ya hanata karasawa, Dad kuma dariya kawai yake yana kallon shi,

"Am sorry Mom"
Tsaki ta buga
"Sorry for yourself, sai ka zauna jinya har sunburn din ya washe" ta kara wani tsaki,

"Karki damu madam, a shirye nazo, inada sunscreen a nan"

A falon dakinsu ta zauna zaman jiranshi har ya shigo,

"Husna" yana murmushi ya rumtse idanu saboda zafin daya ji daga yin magana,

Jikinshi duk yayi wani jaa, kuma ya dan tashi ,

"Cikin rana na zauna, na manta kuma ban shafa sun screen bah, shi yasa zafin ranan yayi min haka"

"Kawo in shafa maka" rigar shi ya cire bayan ya mika mata maganin,

Ita kuma tabi duk inda yayi ja ta shafa mai maganin,

Tana cikin yin haka ne wani tunani yazo mata,

"Ka dade a nan koh" ya daga mata
Kai
"Na kusan yin shekara" ta tsaya da shafa mai tana kallon shi,

"Kana sane ka bari jikin ka yayi haka" tsit yayi kaman ruwa ya cinye shi,

"Magani na kenan dana auri mata meh wayau"

Da yaga bata biyemai bah sai yayi gyaran murya,

"Abinda kawai naga zan iya yi kenan daze sa ki tsaya, har in samu ki fadamin abinda ya saki kuka jiya"

Girgixa kai tayi ta cigaba da shafa mai a fuska da saman wuyan shi,

"Da kace min karki tafi daya wadatar, basai kaje kayi wannan abin bah"

Ta fada da lebe cije, haushi da bacin ran da takeji ya linku,

"Am sorry wifey, nasan in na hanaki tafiya bazaki ji dadi bah,
Kuma bana so ki tsane ni saboda hakan"

Dungura mai maganin tayi zata tafi,

"Meh nakeyi bah daidai bah Husna, jiya nazo na sameki kina kuka,
Yau mah saida kikayi kuka,
Kuma a haka kikeso in kyale ki ki bar gdan nan, batare da nasan abinda ke damunki bah"

Dama ta riga da ta juya mai baya, dan haka tayi magana ba tareda ta juyo bah,

"Na fasa tafiyan mah"
Ta taka a sannu ta bar mai dakin.


Beyi mamaki bah data cigaba da kula dashi har ya warke, amma taki sakin fuska dashi,

Shi yasa ya yanke shawaran barinta taje gda, kila in ta dawo hankalinta har ta iya fadamai abinda ke damunta,


"Badai baza kiyi eid tare damu bah"
Kafin tace wani abu ya rigata,

"No Granny MA anan zatayi sallah manah, kwana biyu kawai zatayi,
Koh?" Ya tambayeta murya can kasa

"Anan zanyi sallah"
Ta bada ansa irin tashi,

Jin jina kai yayi yana yabama shawarar daya zaba,

Gashi tun kafin taje ta dawo har ta fara fara'a kuma ta fito tayi magana da mutane bata zauna ita kadai a daki bah,

"2days kawai koh" ya sake fada bayan ya rakota zuwa wurin mota,
Daga mai kai tayi hade da dan siririn murmushi,

"Okay, ki gaishe da kowa kinji, lukman ze tsaya a Zaria har sai zaki dawo sai yaje ya dauke ki"

Ta sake daga mai kai da sauri,

"Husna" ya hada goshin su wuri daya

"Da azumi a bakin ki yau" ta daga mai kai,

"Banda zama da yunwa pls" tace mai toh,

Da kyar ya kyaleta ta shiga mota,
Wani dadi takeji ya mamayeta, sai washe baki take tayi ita kadai,


Akan hanya ta tsaya ta siya masu tsarabar data dace dasu da kuma watan da ake ciki,

Tana shiga gdansu tayi karo da Ma'u

"Ke meh kikeyi anan?" Duka Ma'u ta kai mata
"Yar duniya, kice min din kina hanya in zo kuma ki tambaye ni meh ya kawoni"

Dariya tayi data dade batayi irin shi bah,
Da gudu ta shiga gda tana murna, duk wanda ta gani sai ta rungumeshi kaman zata karya,

"Anya namecy kina azumi kuwa, wannan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment