Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

had'e da cewa

"d'an uwa kenan, badai rigima ba" d'aki tashiga ta d'auko makullin takawo masa yakarb'a tare da wucewa, da gudu junior yabi bayansa yana fad'in"

"Yayan kd wai inasu ya Bassam da Bilal,? Nayi missing d'insu da funny joke d'in da mukeyi dasu"

"Kai junior kaji tsoron Allah yau duka duka kwananku nawa da rabuwa da zakace haka?" B'ata rai yayi tare da cewa

"Ai yaya 'YAN UWANA NE shiyasa nake missing d'insu kullum" juyowa yayi tare da duk'owa daidai tsawonsa yace

"Am sorry nasan 'yan uwan kane malam junior, suna can gida nabaro lafiya klw suke suma sunyi missing d'inka sosai" yak'are maganar tare da d'an bubbuga kafad'arsa sannan yawuce abunsa, wajen Ummah shima yanufa ya aza mata rigima wai sai ankaisa wajen su Bilal,

Saida ya gama watso ruwa ya shirya sannan yakira faraaharsa data aza masa mita da rigimar yakashe wayoyinsa yanata faman rarrashi sannan ta hak'ura, seda suka sha firar soyayyarsu sannan yakira Mahmud pilot yasanar dashi Yana garin borno yanzuma haka Yana cikin gida kuma a d'akinsa sannan yafito yaci abinci, Yana kammalawa suka shiga firar yaushe rabo da ummah tana tambayarsa ya yayanta yake da can wajensu mom da batool da kuma iyalin nasa, jin bata ambaci ummi da 'yar uwar saba yasa yace

"Ummah ba dai kema fushi kike da ummi da kuma 'yar uwata ba?" Kauda kanta gefe tayi batare data amsa masa ba cike da takaicin tunawa da abunda yafaru,

"Ummah kenan, agaskiya indai hakane baki yiwa ummi adalciba, taya zakiyi tunanin cewa inhar abunda Billy tayi kuskurene zuciyarki ta aminta da cewa dasa hannun Ummi aciki, wlh yanda kikasan halin Ummi ko wani bazata tab'a iyasa 'yarta tayi masa haka ba balle ke, bai kamata ace kinkasa fahimtar taba" juyowa ummah tayi tana kallonsa tace

"Amma kasan duk wani abu da 'ya'ya keyi Saida goyon bayan iyayensu? Data nuna mata cewa bata isaba tunda ba ita tahaifikanta ba wlh dole Bilkisu tahak'ura amma saita zuba mata ido tunda taga d'ana Yana sonta kamar ransa tayi wasa da zuciyarsa, to alhamdulillah allah daya saka masa sonta kuma yabashi hak'urin rashinta tunda gashi raye bai mutu ba"

"Ashsha Ummah, ai awannan zamanin 'ya'yan sun dena saka iyyensu acikin al'amurransu sai lokacin data kwab'e masu, amma duk da haka komai yana son fahimta"

"Hmmm Mahmud kenan, kadena wahalda kanka, don bazan iya fahimtar komaiba wanda yawuce hajia aisha tanuna cewa duk abunda 'yarta keso shi za'ayi mata koda hakan nanufin wani ko waau zaau cutu acikin al amarin"

"Ba haka bane Ummah don Allah kibani dama inyi maki bayani nasan zaki fahimceni sosai, wannan zargin da zuciyarki keyi akan Ummi zaya wanke gaba d'aya pls Ummah don Allah kisaurareni"

"Shikenan ina jinka" tafad'a ranta ab'ace, cikin natsuwa yafara bata labarin duk abubuwan dake faruwa tun daga farko har k'arshe, halin da Basmah tajefa kanta aciki naganin cewa saita hak'ura da soyayyar da takeyiwa Mahmud da kuma sadaukarwa da Billy tayi mata da b'acin rai da fushin data fuskanta wajen dady da ita har umminta babu abunda yab'oye mata, daga k'arshe yace

"Mahmud, Basmah, Bilkisu duka 'YAN UWANA NE, babu wanda zan d'auka inbar wani saboda infaranta ma wani cikinsu, amma inaso kiyar da dani wlh ummah dukkanmu babu wanda yasan dalilin Bilkisu nayin haka sai jiya da Basmah takira mom tana kuka tasanar da ita saboda tafad'awa dady da Ummi sudena fushi da ita, shin Ummah kifad'a mun har yanzu Ummi mai son kantane da 'yarta, Bilkisu k'aramar yarinyace shiyasa ta iya jure wannan matsalar ita kad'ai don farantawa 'yar uwarta duba da yanda Basmah data girmeta takasa jurewa zuciyarta haka har takai ga fad'awa cikin irin wannan mugun yanayi" gaba d'aya ummah jikinta ne yayi sanyi idanuwanta cike da k'walla tace

"Allah sarki Bilkisu garin faranta zuciyar 'yar uwarta tajawo nayi abun da nasani ga tawa 'yar uwar kuma aminiyata, Mahmud nayarda da zancenka kuma natabbatar da haka don tun washe garin da aka kawo Basmah aka kwantar da ita asibiti, sai jiya aka sallamomu, kuma likita ya tabbatar mana da irin matsalar daka fad'a akan Basmah yanzu, wanda har yace tana stage d'in k'arshe yanzu da dole sai ankula da ita sosai da kuma kiyaye wasu al'amurranta amma alhamdulillah taji sauk'i yanzu sosai, tabbas duk wanda ya yanke hukunci cikin fushi yana tare da nadama ni yanzu da wud'anne idanuwa zan kalli hajiya Aisha bisa abubuwan da nayi mata"

"Shiyasa nace bai kamata alokacin kiyi fushi da itaba, tsayawa ya kamata ace kinyi kin fahimceta, amma koyanzu nasan Ummi batada matsala matuk'ar ke kinyi hak'uri to shikenan komai ya wuce" cikin kuka tace

"E'em Allah mai iko, wlh gaba d'aya yaran nan Basmah da Bilkisu duka tausayinsu nakeji, Allah yayaye masu dukkanin damuwa"

"Ameen umma damu baki d'aya" wayarsa yaciro yakira dady lokacin yana zaune palourn Ummi don tun jiya daya fita yadawo bayada wajen zama sai nan don ranakun girkin tane, ita kuma ko kallon inda yake batayi balle yasa ran zata tanka masa, abincima idan tagama akan dining take aje masa ta tura su Bilal sufad'a masa gashican ta kaimasa, haka zai tashi yaje can ya wani cika plates ya cinye hadda k'ari suk don tagani taji dad'i amma tayi kamar bata san yanayi ba, bugu d'aya ya d'auka had'e da cewa

"Assalamualaikum, my son"

"Na'am dady barka da rana, an wuni lafiya?"

"Lpy klw my son, yau Ina kashige ban ganeka ba da safe, kuma nayita kiran wayoyinka ba'a samu?"

"Afuwan dady ina borno naje gaidasu ummah Dan nan indubo maka 'yarka da jiki" wani irin farincikine ya lullub'e dady da Allah yabashi d'an dake iya wakiltarsa har acikin zuciya, domin tun jiya yakwana da tunanin Basmah aransa duk dako sunyi waya yajita lafiya klw amma sai yayi sha'awar inama zai samu damar zuwa koya aika adubo masa ita tunda ba'a wani dad'e da kaitaba balle yace yaje, yana kallon kamar yin haka akwai kunya aciki, sai gashi kamar ya shiga zuciyarsa har ya aikata hakan,

"Masha Allah my son, Allah yayi maka albarka, to yakasamu 'yar uwar tawa da kuma taka" yafad'a cikin wani irin shauk'i dake nuna Yana cikin farinciki

"Lafiya klw dady gama Umman ku gaisa" nan yamik'a mata waya suka gaisa tare da sake biya abunda kefaruwa, nan dady yake sanar da Umma abunda yayiwa Ummi tare da rok'onta akan don Allah yana so ta lallasarmashi ita kozata hak'ura.

"Tirk'ashi ai yaya duk kanwar ja ce, wlh nima yanzu haka cike nake da dana sanin abunda nayi mata, bansan ta Inama zanfara bata hak'uri kaidai kasan yanda zaka lallab'a abukka tahak'ura" da haka auka gama wayar Mahmud yakarb'a tare da cewa

"Dady idan kana tare dasu mom ko Ummi kabanisu" ai kamar jira dady yakeyi yace

"Ina zuwa my son jira in kirawo maka ummin" hanu yasa ya dad'e speaker wayarsa yana faman kiran Ummi,

"Oum Bilqis yo sauri mana, d'anki keson yin magana dake" har taso tak'yalesa sai kuma taje takarb'i wayar a hannunsa, binta yayi da wani irin shu'umin kallo yana murmushi ita kuma tabasar tayi kamar bata ganesa ba.

"Hell" tafad'a lokacin data kara wayar akunne,

"Hello Ummi ina wuni?" Fad'ad'a murmushinta tayi kamar ba itaba sannan ta amsa masa da

"Lafiya klw babana, ya gida ya 'yatah take? Injin dai duk kuna lafiya ko?"

"Lafiya klw Ummi ina borno fa?"

"Haba Allah sarki, ya ka isko umman taku da Basmah suma suna lfiya ko?"

"Lafiya lau Ummi"

"Masha Allah, babana wannan tafiyako sanarwa babu gaahi inada sak'on da zaka jewa Basmah dashi ai daka kaimata"

"Wlh Ummi kawai naji bari dai inzo in dubasu, amma ayi hak'uri tunda anriga angama"

"To shikenan, kagaishe mana dasu, suk da dai laifin 'yar uwarka ya ahafeni ummanku fushi take dani"

"To Ummi ai gani kusa da ita sai kugaisa"

"A'a babana kabasshi don nasan da k'yar idan zata amsa" muryar umma taji tana cewa

"Mezai hana in amsa qawata indai har zaki iya tsayawa ki saurareni, kiyi hak'uri bansan yanda abun take ba sai yanzu da Mahmud yayimun bayani, wlh gaba d'aya nazata cewa da son ranki ta aikata haka kuma kika k'yaleta shiyasa raina yab'aci" ji Ummi tayi batama San amsar da zata bataba kenan da ace bisa ra''ayin Bilkisu tafasa auren da bazatayi mata uzuri ba zataci gaba da zarginta akan ita ta aikata haka, cijewa tayi sannan tace

"Karki damu, ai duk abunda yafaru ga balbela farin tane yajawo mata" hakan da Ummi tafad'a ya tabbatarwa da Ummah cewa lallai ranta ab'ace yake kuma duk abunda tayi dagaskiyarta, dole Ummah tashiga bata hak'uri har saida ta tabbatar tahak'ura sannan takashe wayar tana ajiyar zuciya, karb'ar wayar yaya Mahmud yayi yana daria kafin yace

"Dama mai hak'uri idan aka k'uresa bai iya ba haddai ga wanda yake tsammanin bai dace ace yayi masa abu"

"Hmmm! Ai nagani, tunda muke bantab'a ganin b'acin rantaba ko zafin zuciya wlh sai yau, kai Allah dai yakaremu da sharrin shaid'an da kuma na zuciya"

"Amin ya Allah Ummah" wayar mom yakira itama yabata suka gaisa sosai mom cike da kunyar abubuwan da suka faru abaya tsakaninta da ita tace

"Don Allah hajia hafsatu muyi hak'uri da abubuwan da suka faru abaya mu manta da komai"

"Bakomai hussaina nidama banwani rik'eki araiba, kawai halinnan nakine yasa banfiye son mu'amala dake ba, kinsanni da zuciya in raina yab'aci ban iyaba, to gudun kar inb'atawa yayana rai kasa kota kanki banabi amma kema kiyi hak'uri kinji matar yaya" yak'are maganar cike da zolaya, murmushi mom tayi had'e da cewa

"Aikam dai wancan halin da kika sani gaba d'aya aminiyarki tazamo silar sauyawarsa don haka Ina fatar muyafi juna duk"

"To Allah ya yafemu baki d'aya" nan dai suka d'an tab'a fira kad'an sannan suka katse wayar abun gwanin ban sha'awa, duniya kenan babu abunda hak'uri yabari,kuma duk abunda yayi farko zaiyi k'arshe, sanadiyar shiruwar mitum d'aya acikin family kan iya samar da farin ciki mai d'orewa don haka mukasan ce masu hak'uri da 'yan uwanmu hakan zaisa duk wasu dake da raunin zuciya acikinmu rana d'aya sucanza saboda albarkar wannan hak'urin da mukayi da juna ubangiji Allah yasa mudace kuma yabarmu da 'yan uwanmu.

Godiya sosai ummah yayiwa yaya Mahmud bisa wannan k'ok'ari da yayi na daidaita tsakaninta da iyayen nasa wanda hakan ba k'aramin farinciki yasataba, ana haka saiga Mahmud pilot yashigo cikin palourn da hanzari yana fad'in Ummanah Ina d'an uwa yace yana nan ya gida ya iso, Yana rufe baki idonsa na sauka akansa, murmushinsa ya fad'ad'a had'e da qarasawa wajen yabasa hannu suka gaisa Yana fad'in

"Ango, ango, ango kasha k'amshi" murmushi yayi had'e da rungumesa sannan ya rad'a masa akunne "angwaye dai" sabod kunyar Umma da yakeji bazaya iya ramawa a fili tana jin saba, murmushin shima yayi don yafahimci hakan tare da juyawa yana gaisheda Umma dake k'ok'arin barin wajen, amsawa tayi had'e da tambayarsa ya 'yarta da jiki yace lpy klw take tana gaisheta sannan tabar wajen.

Tsokanar yaya Mahmud yafarayi wai yafara zama d'an lukuti, ashe malamar asibiti ta iya kula da miji, ai yazata majinyata da allurai da sirinjai kad'ai ta iya kula dasu ashe abun ba haka bane, mere baki yaya Mahmud yayi kafin yace

"Zauna nan, aini matata expert ce komai ta iya, inma bakabi hankali ba so soon zanzama baba inbarka nan kaga dole inzama nine yaya kai kuma ka koma k'ane"

"Eyye lallai d'an uwa bakada dama, naji bakomai ai dama tuni nazama k'anenka tunda kabani auren k'anwarka"

"Aw k'anwata bada kaiba?"

"Ina aini saidai inkirata k'anwata matata, mubar wannan zancen yasu dady, Ummi, mom da kowa ma, duk lafiya suke?"

"Lpy klw, bazaka tambayi k'anwarka takaba?"

"Wakenan?, Kasan k'annena yawa kedasu kuma babu wacce na ambata aciki balle kace nayi wariya"

"Amma ai ita ta musammance ya kamata ace katambayeta maganar gaskiya"

"To mai 'yar uwa, ya Billy dasu Batool suke? ina sunanan cikin farinciki dai ko?"

"Yes ofcourse" yabashi amsa atak'aice,

Nan suka shiga firarsu ta 'yan uwantaka dake cike da tsokana har suka gangaro akan firar rashin lafiyar Basmah, wacce yanda yaga Mahmud yanuna masa damuwarsa akan haka bak'aramin dad'i yajiba, yasan koda 'yar uwarsa bata warke duka ba zata samu farinciki sosai bisa kulawar da yake bata, daga k'arshema kai tsaye suka wuce HAIFA SPECIALIST, Suka samu tattaunawa da likitan dake kula da ita, inda yaya Mahmud yayi k'ok'arin had'asa da dr inta nagida yayi masa bayanin komai dake cikin folder d'inta tare da magungunan da take sha don ya taimaka masa wajen cigaba da kula da ita har zuwa lokacin da zata samu sauk'i sannan suka kashe wayoyin, kamar dai yanda wancan dr. Ya tabbatarwa da yaya Mahmud zata samu sauk'i tunda tasamu abunda take so zata dena shiga damuwa kuma haka zai taimaka mata sosai wajen samun lafiya matuk'ar aka kula da ita yanda yakamata kuma kuma tatsare shan magunukkanta cikin lokaci,.

Sosai yaya Mahmud yayi masa godiya sannan suka baro asibitin, gidansasuka nufa dama tuni Mahmud yakira Basmah awaya yace tashirya zai kawo mata wani surprised don dama bata san da zuwan yaya Mahmud ba, ai kuwa tayi wanka tayi 'yar simple makeup tana jiran dawowarsa, haka kurum taji ta tsinci kanta cikin farincikin da sharabonta tayishi har ta manta,

Tanajin tsayawar mota tamik'e had'e da b'uya bayan labule tana jiran isowarsa taga surprised d'in da zai bata, ai kuwa tana nan alab'e tajiyo murya har ta mutun biyu ana sallama alamun kamar bashi kad'ai yake ba, ahankali tad'aga labulen don taga shida waye kawai tahango yayanta atsaye rik'e da key d'in mota yana murmushi don yanda yaga Mahmud yanufi uwar d'akin yana tafiya ahankali kamar wanda zai kama wani abun saboda yazata tana ciki sai yarufo idanuwanta suzo taga surprise d'in daya cemata, har ya aza k'afarsa zai shiga yaji anyi ihu tabayansa tare da fitowa inda tab'uya aguje ta lak'ame yaya Mahmud tana fad'in "oyoyo yaya sannu da zuwa"

Juyowa yayi yad'an b'ata fuska tare da nufo wajen yada'an zungure mata kai yna fad'in

"Wayace kifito shikenan kin b'atamun tsari" yak'are maganar yana harararta, daga yaya Mahmud har ita dariya suka saka masa tana yimasa gwalo had'e da cewa

"To sorry yaya ai kaine bakace kada infito ba ko?"

"Basmah wai sai yaushe zaki girmane, wannan irin shagwab'a da kike yi har Ina?" Yaya Mahmud yafad'a yana tsokanarta ganin yanada tawani nanik'e masa ajiki,

Rufe ido tayi had'e da mik'ewa tanufi kitchen don kawo masa ruwa da abincin da zaici, sosai yanayin daya gata tabashi tausayi don ta rame sosai ga wani duhu da tayi saboda ciwon da tayi,

Ita kuwa tsabar farinciki yasa tadinga jido drinks da abinci tajere masa agabansa,

Dariya yayi tare da cewa "ke Basmah duk ina zankai wud'annan abubuwan" tare da karb'ar ruwan data tsiyayo masa acup ta mik'o masa,

"Kacinye duka yaya, Ina Billy da Batool suke"

"Wato su zaki fara tambaya bazaki tambayi su mom da dady ba?"

"Kai yaya zan tambayesu mana sufa 'YAN UWANA NE shiyasa wlh kullum sai nayi mafarkinsu"

"To ai yayi, innaje zan fad'amasu suma dena damun kansu akanki ke baki damu daauba sai dai 'yan uwanki"

"A'a yaya ayimun hak'uri yasu dady da Ummi da mom da aunty faraaha dasu Bassam duk suna lafiya?"

"Kowa lafiya klw Basmah ya k'arfin jiki" sinne kai tayi k'asa had'e da cewa

"Alhamdulillah naji sauk'i Ummah nakula dania sosai"

"Kai Basmah kiji tsoron Allah nifa, bana kula dake? Mahmud pilot yafad'a yana kallonta, kallonsa itama tayi tak'asan idanuwa had'e da kad'a kai tace

"Kaima kanayi sosai ma"

"Bana so tunda ummanki kad'ai kika sani" yafad'a tare da komawarsa gefe yasha toka, ala tilas yayi fushi

Ido yaya Mahmud ya zuba masa cike da tsoron Allah yana kallon abunda yakeyi kafin yaji Basmah nafad'in

"To kayi hak'uri bazan k'araba, ko yayanah" yak'are maganar tana kallon yaya Mahmud, kad'a kai Mahmud yayi tare da cewa

"To babban kobo ai sai ahak'ura tunda yaya da k'anwarsa sun bada hak'uri" dariya sukasa gaba d'aya sannan aukaci gaba da fira har lokacin Basmah na zaune kusa da yayanta kamar bataso surabu.

Kwaninsa d'aya yajuya ya koma gida cikin farincikin yanda yabaro 'yar uwarsa, yatabbata cewa yanzu tasamu natsuwa da kulawar da duk wata damuwarta zata kau, Basmah kuwa da zaitafi tasha kuka sosai haka yatafi yabar Mahmud yanata faman lallashi, dole tahak'ura amma gaba d'aya ranar yini tayi kamar batada lafiya.

Dady kuwa kullum cikin 'yan dubaru da kame kame yake amma fir Ummi tak'i saukowa saida akayi adadin kwana takwas d'in da yayi yana fushi da ita sannan tabashi fuskar da zai iya tunkararta, har takwanta da daddare sai gashi ya iskota har cikin bedroom d'inta d'auke da bargo da pillow, tana ganinsa tayi saurin rufe idanuwanta don dama tun ranar da abun yafaru ta k'auracewa part d'insa saboda fushin da yakeyi da ita gashi duk da yadena kuma yau kimanin kwana takwas ko girkinta ya zagayo bata zuwa kwancenta takeyi apart d'inta, saboda yagaji da sharesan da takeyi yasa yace yau duk fushinta anan zai kwana shiyasa ya d'auko bargonsa da pillownsa koda tace bazata kwana gado d'aya dashiba,

Sosai ya bata dariya amma saita fuske tayi kamar bacci takeyi, k'arasowa yayi ciki tare da ajiye kayan gefe sannan ya zauna bisa gadon yana kiran sunanta,

"Oum Bilkis" tak'yalesa "rabba'atul bait" nanma sharesa tayi had'e da juyar da kanta gefe,

Rasa yanda zaiyi da ita yayi kawai sai yafad'a kanta had'e da lalubo bakinta yafara kissing d'inta, k'yalesa tayi har sai da yayi abunsa yagaji don kansa sannan yatashi had'e dayin niledown agabanta yana fad'in "haba rabba'atul bait wai mekike so inyine, gaba d'aya kinsa zuciyata cikin damuwa kin dabai bayeta kin hanata sukuni, don Allah kiyi hak'uri nayi kuskure amma bazan iya cigaba da jurewa wannan fushin da kikeyi dani ba, idan kuma kikace a'a to tabbas zuciyata TNA gab da bugawa kirasani gaba d'aya tunda kindena sona"

Tashi tayi had'e da gyara rigar jikinta tana kallonsa tace

"Meye don nashareka kai da kake da mata biyu, kaje mom d'in yara yafaranta maka mana, meye abun tada hankali haka harda zancen zuciya zata buga, don Allah rufan asiri katashi kaje ka kwanta abinka nima bacci nakeji"

Hannunta yarik'o tare da d'orawa saiti zuciyarsa ta kauda kanta gefe yace

"Rabba'atul bait saurari yanayin da zuciyata keciki, zafi take kamar zata k'one don Allah kiyi hak'uri kinji, gaba d'aya fushinki yasa babu wani hasken da nake gani acikin gidannan har ma da rayuwata gaba d'aya, kiyi hak'uri kiyafemun kamar yanda kema Allah keyafe maki" juyowa tayi tana kallon k'wayar idanuwansa had'e da son gasgata abunda yake fad'i sannan ta rungumesa tace

"Irin wannan yanayin da kaji nima irinsane naji lokacin da kake fushi dani wannan zafi da k'unar da zuciyarka keyi naji fiye da haka acikin zuciyata, ni nasamu k'warin guiwar jurewane saboda inada gaskiya kai kuma kakasa ne saboda rashin adalcin da kayimun, ba lallaine ace duk wani laifin d'a za'a maida hak'k'in yinsa ga mahaifiyarsa ba, idan kuma hakane don me bazaka zargi kanka ba tunda dani har kai matsayi d'aya muke dashi awurin ka, abu Bilal komai nason bincike da kuma afuwa koda ace kabincika katabbatar dasa hannuna bai kamata kayi fushi dani ba, afuwa yakamata kayimun saboda watakil kuskure yasa na aikata haka amma kahau fushi dani tamkar wacce baka so" tafashe da kukan da sai yau tasamu damar yinsa

"Kiyi hak'uri in sha Allah hakan bazata sake faruwaba, kiyar da dani ina sonki sosai kuma kema sheda ce akan haka, kawai sharrin shed'an ne da kuma fushin zuciya" yak'are maganar shima had'e da rungumeta yana jin cewa bazai tab'a iya rayuwa ba idan baya tare da ita...

_Wash duk nagaji, pls afuwan wlh jiya nayi typing garin inyi copying da pasting inturo yagoge gaba d'aya nikuma danaji haushi nak'iyin wani sai yau, kuci gaba da hak'uri muna gab da kammala sa insha Allah komai yazo k'arshe_




*_ALLAH KA JIK'AN IYAYENMU👏🏻😭_*

👭❤ *'YAN UWANA NE!*❤👭
💎 _they're my relatives..!_💎


Written by: *BILLY S FARI💎*

Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*

Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*

_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_


💎Page_____93💎


Komai ya dai daita tsakanin ummi da dady yanda yakamata, sun manta da komai sun koma bawa junansu kulawa fiyema da yanda sukeyi ada, dama ance fushin masoya hutune, haka tab'an garen zaman gidan dady komai ya dai daita kamar yanda ya dad'e yana buk'ata tsakanin mom da ummi, zamane mai cike da girmamawa da kuma tsafta sukeyi, sun ajiyar kalmar kishi agefe sun amince zasu zauna a inuwa d'aya cike da kyautatawa da kuma mutunta juna, ko wace batada burin da yafi tafaranta zuciyar mijinta, tare da yiwa 'yar uwarta uzuri da kuma kauda kai ga abubuwan da suka san cewa tabbas Allama yasan bazai iyayin adalci ba a tsakaninsu, wani irin amintaccen zamane da babu cuta acikinsa balle cutarwa, duk wanda ya shiga gidan bazai tab'a cewa zaman kiahiyoyine akeyi aciki ba, daidai gwargwado kowace na kamantawa 'yar uwarta kuma suna b'oyon hankula sosai don samun wanzuwar tabbataccen zaman lafiya, ta b'angaren dady ma yana iya k'ok'arin sa wajen kamanta yimasu adalci tare da k'ara kyautata masu bisa kwanciyar hankali da kulawar da suke bashi,

Hakama su alhaji kabiru takanas ta kano suka zauna sukayiwa kansu fad'a tare da tunanin gyara kuskuren da suka aikata abaya na cutar da matar d'an uwansu, bayan buki sukaje har gida suka nemi dady yakira masu Ummi, wanda anan gabansa suka nemeta yafuwar abunda suka yimata ashekarun baya, baranma muzammil da duk yafisu jin kunya saboda kiran da yayi mata awaya lokacin tana jinyar Billy asibiti ya zazzageta tare da cimata mutunci akan wai tarabasu da d'an uwansu ta asircesa tayanda yazab'i yayi rayuwarsa batare dasu ba, wanda hakan ba kad'an ya matuk'ar tayar mata da hankaliba amma duk da haka batace masa komaiba har yagama zazzage zazagensa yakashe wayar, sosai lokacin ranta yab'aci amma saita danne abun aranta bata tab'a fad'awa kowa ba hatta dady kuwa, cike da kunya baba ka'rami ya kalli inda take had'e da cewa

"Hajiya Aisha ina rok'on kiyi hak'uri akan zagin dana kiraki awaya nayi maki alokutan baya, nayi matuk'ar nadamar yin hakan"

Sosai dady yasha mamaki jin cewa wai muzammil d'an uwansa kefad'a da bakinsa cewa yakira matarsa awaya ya zazzageta amma daidai da rana d'aya bata tab'a fad'a masaba, juyowa yayi yana kallonta yayinda ita kuma ta d'ago kai tana kallon baba k'arami had'e da cewa

"Hak'ik'a nasha mamaki kuma naji badad'i alokacin amma inaso kasani ko kad'an ba zagin da kayimun yab'atamun raiba, shirkar da akoda yaushe kuke jifata da ita cewa na mallake maku d'an uwa na asircesa ita tafi komai k'onamun rai, akoda yaushe burina baifi infarantawa d'an uwanku raiba, banida burin da yafi inyi masa sakayya da alkhairin da zaiyi alfahari dani agobe k'iyama, amma ku gani kuke Ina cutar maku dashi, Allah shine sheda akan bantab'a had'asa da kowaba don in mallaki mijina amma nasan Ina rok'onsa daya mallakamun zuciyarsa kuma yabani hak'uri da juriyar zama dashi har iya k'arshen rayuwata, shin taya za'ace yin hakan zai zamo laifi agareni bayan Allah da kansa yace murok'esa zai amsa mana domin babu abunda yafi k'arfinsa, gashinan zaune agabanku kutambayesa shin akwai abunda narik'a wajen k'ok'arin mallake zuciyarsa face ubangijina? Idan har kun musunta haka daga wajensa narantse da ubangijina shine shedar babu wanda nake kaiwa kukana face shi amma ku kunjefeni da kalma mafi muni arayuwa wacce aduk lokacin dana tuna sai nazubar da hawaye, shin meye ribar da zanci idan na asirce maku d'an uwa bayan ba cinsa akeyiba ko sha ko kuma sutura da zan tanadawa kaina don inburge aduniya, wlh inhar sai nayi hakan zn mallakesa nafiso inmutu amatsayin baiwa cikin gidansa matuk'ar zan mutu da imanina, karku manta ku kuke da d'an uwanku, zai iya rabuwa danina har abada amma ku kuma bazai iya rabuwa da kuba"

Basu ba hatta dady Saida yaji kalamanta sun kashe masa jiki, tasowa yayi ya zauna kusa gareta tare da rik'o hannuwanta yace

"Tabbas ba'a kyauta maki ba Aisha, kuma 'yan uwana sunyi ba daidai ba, matuk'ar jin zafin abubuwan da suka faru batare da sanina ba kuma sunyimun d'aci azuciya amma ya zanyi? Karki manta su 'YAN UWANA NE da banida tamkarsu aduniya, dolene nayi hak'uri akan haka duk dako rashin jin dad'in da nayi, ba kuma wai don bana son kiba zanyi haka, A matsayina na mijinki kuma amadadin 'yan uwana, ina rok'onki akan don Allah da girmansa kiyi hak'uri kiyafe masu, sosai muzammil yayi kuskure kuma bai kyautaba, amma kiyi hak'uri bisa wannan cutarwar da akayi maki" sannan yajuyo yana kallon baba k'arami yace

"'Dan uwa maganar gaskiya baka kyauta ba, kusan kafi kowa aikata kuskure anan wajen, taya za'ace

Please Login or Register in order to submit comment