Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da Iman, Banda wanka a tsundumata a ruwa, suna tsaye ya saka Nurse ta kwatanta musu yanda za’a ringa wanke mata jikin shima ba kullum ba musamman yanayin garin sanyi ya kankama.

Sannan ya dora musu da bayanin in so samu ne mamanta kadai zata ringa daukarta kar a jagwalgwalata su tabbatar kuma ko yaushe tana cikin dumi kar ake fitar da ita cikin iska ko sanyi a kula da kayan da za’a ringa saka mata kuma.
Sallama sukayi suka tafi bayan ya basu ranar da zasu dawo ganin likita.

Bashir be yadda ma an dauke ta a hannu ba cikin Baby carrier daya siyo tundaga lagos ya sakata ya dauka Addah ta hau salati da salallami wai ya saka ya a kwando to duk bala’in sa dai ko mayu ne su se ya basu yar in sunje gida tunda ba da ita ze ringa yawo ba,

shida be tankata ba. Seda ya ajiyeta dakyau ya maqala belt din ko ina sannan ya shige ya tada mota har sukaje gida kuwa Addah bata saduda ba se sababi takeyi.

A gidan ma suna zuwa da kansa ya bata feeder ta fara sha dan bottle feeding suke yi kafin ya bawa Amirah taci gaba da bata yana tsaye, seda ya tabbatar tasha yanda ya kamata ya dagata kamar kwan da baya so ya fashe ya sakata a kafada tayi gyatsa kafin ya kwantar da ita a dan gadonta. Seda ya dauketa hoto a wayar sa sannan ya juya.

Kallo daya yayiwa Amirah dake doka uban Murmushi saboda ganin irin tattali da kulawar da yake nunawa yarinyar, ta san yanzu ko Albarkacin Iman seta qara matsayi a zuciyarsa shi kuwa gogan tsaki ya buga ya fice daga dakin dan haushinta yake ji.

Yana fita Addah da jama’arta suka duru daki ganin Baby, kamar me tattaro kaya ta zura hannu zata cukumota Amirah kuwa tayi caraf ta riqe tana cewa “Haba Addah bakiji me likita yace bane shine zaki kawo mata wannan cafkar ai seki ballata”.

Suka kwashi salati ita da jama’arta kafin ta fara masifa tana cewa “Eh lallai yanzu na yarda ba iya Bashir ne tanbadaddenba harda ke, yo in banda tanbada ni uwarki zaki hana na dauketa har ni zaki gayawa kar a karya miki ya, to da ban haihu ba yau se nayi kuka kiji da jinki seda na haifi Goma na binne takwas gaku nan biyu a raye harke ma kinyi yar kanki zaki nunamun sanabe da iyayi”.

Inna Gaji ce ta ceci Amirah tace “Ba haka bane Fattu yanzu dai barta mu kalla daga haka dan Allah abunda in muna da tsahon rai watarana da qafarta zata taka ta hau jikin duk wanda take so” haka aka lallaba Addah kowa ya leqa yarinya dake baccinta masha Allah kyakykyawa da ita kowa se yace ta kwaso kaman nin yayan Ma’u.

Addah dai bata haqura ba seda ta daukota Amirah na kumbura baki tana komai,
“Oh ni Fatu wannan abu kamar yar kyanwa, kwanta karna manta Dan mutum ne nayi jifa dashi” ta fada tana maida yar cikin Gadonta kafin ta harari Amirah data cika baki da iska tayi qwafa ta fita daga dakin.

Bashir kuwa yana fita Part din Ma’u ya bude ya shiga, ya zuqi qamshin da a gurinta kadai ya sanshi dan gidanta na nan dana Lagos qanshi su daya duk kuwa da bata ciki ya rigada ya kama Gurin se a sannan ya tuna dakin masu jegon ma daya shiga kodan Air freshener beji ba bare Turaren wuta.

Wanka ya farayi ya yi sallar Isha da shafa’i da wuturi sannan ya shiga kitchen ko ze samu abinda ze ci tunda can basu bashi ba. ya yi sa’a kuwa cikin Freezer ya samu farfesun kayan ciki dama mutuminsa ne nan da nan ya dumma ya dauki bread ya hada tea ya fara ci. Seda ya kusa cinye wa naman suna ya fado masa a rai, kunsan mutuminku ko kura Albarka nan da nan ya qarasa cinyewa ya dauki waya ya dannawa Amirah kira dan baya so ya koma su hadu da Addah.

Amirah na cikin waya da Tailor data bawa dinki dan tuni ta kai musanyen lace din da aka sako mata na barka ta karbo wani ta bada dinki da sauran kayan da zatayi amfani dasu a lokacin ma tailor yana gaya mata ya gama ne gobe ze kawo ya karbi bakance din kudinsa, ganin kiran Bashir yasa ta cewa Tailor tana zuwa ta amsa wayar da fatan Allah sa Zancen sunan ze mata.

“Kizo ina son ganin ki, ki taho mun da nawa kason Naman” ya fada a taqaice. Seda cikinta ya bada qulululu dan bata taba zaton ze tambaya ba. Tas suka rabe naman nan ko gutsiren hanji beyi saura ba ita yanzu me zata ce masa?

Ai kuwa beci ta manta ba aduk sanda Anty Asma’u ta haihu kasawa yake ya tsare se an cire masa nasa kason, tana kuma yawan jin Asma’un na qorafin daga baya se ya biyo wanda aka aje mata ya cinye ta rasa wane irin so Bashir yakewa Nama a rayuwarsa dukda gashi yanzu ita sun hada sun lamushe.

Haka ta zari mayafin ta ta fita tana taraddadin me zata ce masa, a qofa taci karo da Addah ta dawo daga raka baqin ta.
“Ke kuma ina zaki fita a daren nan da danyen jego” ta fada tana kallon ta ganin ta da mayafi.

“Yaya Bashir ne yake kirana”
“Oh to se kin dawo” Addah ta fada tana rabeta zata wuce se Amirah ta ruqota tana rartaba ido.

“Ya akayi se wani qifta ido kike kamar an kama Kwarto?”

“Addah wai cewa yayi in taho masa da kason naman sa na suna” cewar Amirah.

“To se ki tafi ai” Addah ta fada tana son wucewa ciki.

“Kin manta Addah ya qare fa babu ko diddiga yanzu me zan ce masa”

“Ke dallah matsa ki ban guri se kice masa ya qare ko kice an hada an kaiwa Nafi bashi kenan ba”.

“Addah wace Dadan kuma kin manta itama fa baki basu ba wanda aka ware musu bashi kikace a bawa su Hajia Salamatu ba da suka Zo barka kika ce ta rabawa yan group dinku?”.

Se Addah tayi kasaqe tace “haka ne kuma fa, tab di amma fa mu ma munyi gwari wallahi to yanzu ya za’ayi?”

“Nima ban sani ba” Amirah ta fada tana marairaicewa. Ta tabbatar laifin cinye nasa kadan ne akan idan yaji ko su Dada ba’a aikawa dashi ba.

“Kinga yanzu kije kawai in ya tambaya kice kin manta, idan ya biyo sahu ni kuma zan ce masa Muzuru sun shigo sun cinye bamu sani ba se in nuna masa duddugar bashi kenan ba, shima ai yasan dangin ku da yawa ya wani se miki rago biyu ai yayi kadan” (😳) tana gama fada tayi ciki abinta, nama dai sun cinye ba kuma a isa ace su biya ba.

Amirah kuwa jiki a mace ta shiga palour, ga abinda yake a gabanta amma ta bige da kallon qurilla taga me aka chanza a ciki i lai kuwa taga sabuwar Kantamemiyar Cinema Tv bango guda da Asma’un ta saka kana ganin muatanen ciki kamar zasu fito, sannan ta chanza Dining dinta ba na da bane ga wasu hadaddun Kwanuka akai shikansa Turkish Centre carpet din ba wancan bane kamar.

Kallonta Bashir yake ba laifi ta sace amma bata gama dawowa daidai ba ga cikinta nan haryanzu da girman sa Allah dai yasa kar tayi tumbi dan a duniya ya tsani tumbi a jikin mace kuma da Allah ya taimakeshi Ma’un sa haihuwa Biyar amma har yau bata da tumbi ko dan tana kula da jikinta ne oho?

yanda yaga Amiarn tana kalle kalle yasa ya girgiza kai kawai kafin yace “Malama ko zauna mana kin tsaya mun akai. Zama tayi kan Kujerun da suka dade da tsole mata ido ta kuma quduri niyya itama fa se ya mata irin su yanzu ko ga qarin Dining ma da TV duk irinsu take so itama a siya mata.

Sake gaishe shi tayi ya amsa hankalin sa akan Tv, jin shiru bata miqo masa komai ba ya sakashi kallonta yace “Ina naman” dan fa shi har ya dakko a exotic drink coconut and pineapple dinsa da ze hada ya kora nama seta hau kame kame tana sosa kai tace “uhm uhm daman”

Idonsa akanta yace “malama daman me kin tsaya kina wani kwana kwana in ma wani abu zaki tambayeni bani dashi ki bani namana ki tafi daman kiran da na miki kenan”.

“Ai naman ne ya qare” ta zabi da ta fada masa gaskiya kawai komai ta fan jama fanjan.

“Ya qare?” Ya tambaye ta, se daga masa kai alamar Eh dan ta kasa kuma bude bakinta saboda kallon da yake mata.

Daurewa yayi ya danne bacin ransa kafin yace “ toh kun kai gidan Dada kun bawa Ma’una nata ko?”

“Ai se tafi da rikicewa, kai ta juya masa alamar Aa cikin tsawar da seda ta zabura yace “Malama ki bude baki kiyi mun magana ko”

Jiki na rawa tace “Ni wallahi ban sani ba kasan bani da lafiya su Addah ne suka raba ban san kota kai musu ba dan ni wallahi ko yanka daya banci naman ba”.

Ya tabbatar basu bawa ko daya daga ciki ba kenan, dan haka kawai yace ta tashi taje kafin ya jawo wayarsa ya danna kiran Dada yana saita fushinsa. Bayan ta daga suka gaisa, tambayarta yayi an kai musu naman suna kuwa tace Aa.

“Kar kace zakayi magana Bashir nama dai Allah na tuba kullum ai muna ci, ba wani Abu kasan yan gidan su nada yawa kowa ze so a qulla masa” Dada ta fada da son kwantar masa da hankali dan tasan Bashir da Nama.

Seda yayi kokawa da bacin ransa kafin yace “Amma Dada raguna har biyu manya ne fa ba wai qanana ba su soya su cinye ko yanka daya su kasa kai wa uwata idan ni da na siya banda mutunchin da zasu bani sannan ga Ma’u da yara gaba daya suna cikin gidan a soya duk su kasa basu”.

“Kadaiyi haquri” Dadan ta sake fada kafin su kayi sallama. Ransa a bace ya shiga dakinsa ya kwanta se kuma ya ja wayar ya kira Asma’u dan yau duk basuyi waya ba.

“Ran Alhaji Bashir Baban Ali ya dade” ta fada cike da nishadi dan hirar sa suke yi da Yaya Bilki ya kira. Murmushin da beyi niyya bane ya kwace masa kamar wanda ake watsawa ruwan sanyi yaji zuciyar sa na huce wa, muryarta kadai ta wanke masa bacin ran Naman suna seya gyara kwanciya yana cewa

“Ba wani nan bayan kunyi tafiyar ku ma kin manta dani inaga sena biyo ku sannan zaku dawo”

“Haba dai kwatakwata fa kwanan mu biyar yau cikin weekend muke saka ran dawowa ai” Asma’u ta fada.

“Shikenan ma kinga da kun dawo se mu wuce kawai, na gaji da zaman gwauranta kan nan”.

Dariya tayi kafin tace “oh kana Gombe kenan”

“Eh na shigo dazu, an sallamo Fatima yanzu tana gida”.
“Masha Allah Allah ya raya mata ya bata lafiya, ashe Addah aka saka”.
Da “Amin” ya amsa ya share tambayar ta ta. To me take so yace mata in dai ba son tada zaune tsaye kuma ba.

Yaran ya tambayeta tace sunyi bacci suka dan taba hira kafin sukayi sallama bayan sun gaisa da Yaya Bilkisu.

“Kinji mutuminki nace ashe Addah aka saka yayi kamar beji ba” Asma’u ta fada bayan ta ajiye wayar.

“Kema da neman magana kike wallahi me kike so to yace miki?” Cewar Yaya Bilki
“Me kuwa zece daman kinga ai ta ta uwar tafi tawa a gunsa shiyasa ya saka mata sunanta”.

“To da be saka ba dama Addini ne yace dole ayi ko kuwa da ze zama laifi” cewar Goggo da shigowarta kenan. Muqus Asma’u tayi, dan tasan idan ta tofa wata fada ne zata sha ita kam se taga kamar Goggo tafi son Bashir a kanta ma wani lokacin, bargo taja ta rufe har kanta hankali tacewa Yaya Bilki “idan ta fita ki gaya mun” jin Goggo ta ci gaba da magana.

Seda Goggon ta fita kuwa ta bude tana cewa “Ita Goggo bata san takaicin da ake qullawa mutum ba tayi ta rufeshi da fada, wai fa kinji ma cewa yake idan mun koma se mu bishi mu tafi ni nama fasa tafiya Sunday din sena tabbatar ya koma tukunna. Sati uku mukayi dashi munci biyu se na qarasa sati na wallahi dan har Bauchi nake so Naje wa Alawa sannan naje Jos ma”.

“Ai kuwa da ba kwana zakiyi a Bauchin ba nima da naje Alawiyya har tayi mitar ta gaji ban taba zuwa ba” inji Yaya Bilkisu

“Kai haba dai amma baki kyauta ba wallahi ina Gombe ina Bauch” cewar Asma’u

“Ba haka bane kinsan yawan ci abin zuwan haihuwa ce to kusan tare muke haihuwa kota rigani kona rigata amma daya baya Arba’in to sedai mu hadu a gida”.

“Eh to hakane”. Hira suka ci gaba dayi kafin sukayi bacci.

A Gombe kuwa washe gari Bashir ga haushin cinye masa nama gana tambayar kudi da Amirah tazo ta fara masa da sassafe, buyagin gaske yai mata ya faffada mata maganganu son ransa qarshe ta fita tana kuka da dana sanin zuwan daman Qawarta Husna ce ta tsara mata yanda zataje ta same shi gashi babu biyan buqata se baqin ciki ta kwaso tana shiga dakin ta kuma ta tarar da Addah ta cika baho da ruwan zafi ta tube Iman tana shirin tsumbulata tai mata wanka.

Da mugun gudu Amirah ta tare ta hannun ta ya shiga cikin ruwan da sauri ta cire jin zafin ruwan ta yayimi towel ta nade Iman tana kallon Addah data saki baki da Hanci tana kallonta itama.

“Dan ubanki saboda zan mata wanka shine kika buga wannan tsallen kamar wata yar ball kika kwace ta? So kike a bar ya mace ba wanka kusan sati biyu da haihuwa tayi warin qashi To wallahi ba da ni ba dole a wanke mata dattin mahaifa”.

Ita dai Amira bata kula ta ba, se jijjiga Iman da ke dan kukan da ko muryar ba’aji dakyau take dan ta firgita, jin Addah bazatayi shiri ba yasa tace “wai Addah baki ji me likita yace bane gaskiya idan ba zaki mata irin yanda yace ayi ba ki bar wankan kawai zan nunawa Inna Gaji ta ringa mata. Haka kawai idan wani abun ya sameta ai nice da Asara kuma ji ruwan da kika saka kamar wanda zaki fige kaza”.

Salati Addah ta debo ta dire kafin ta shiga auno mata ashar tana cewa “kiji mun yar banza ni kike shatawa layi akan wannan magen dan bazance mutum ba to kinyi da yar halak in na sake taba ta kice shegiya nake” ta mike tana gyara zani tana ci gaba da banbaminta.

Inna Gaji da shigowarta kenan ta tambayi ba’asi Amiran ta mayar mata seta dubi Addah tace

“Wallahi Fatu kin fiya tada zaune tsaye in ba haka tunda ga abinda likita yace se kibi na dan lokaci ne ko cewa akayi zata dawwama ba wankan ne se ki mata yanda suka ce.

Yanzu kizo ki zunduma musu ya a ruwa bayan naji ance tana da munoniya wani abu ya faru kinsan dai wannan sirikin naki manta komai zeyi wallahi har ni nan da babu ruwa na qila se yayi qarar mu ai wannan ruwan yayi yawa...kaii” maganar ta katse bayan data tsumbula hannu a ruwan, seta kalli Addah ido waje tace

Fatu kice kisan kai kika shirya wannan ruwan ko uwarta bata wanka da me zafinsa shine zaki jefa wannan tatsitsiyar yar a ciki? To nidai inaga watan tafiyata gida ya kama dan bazan iya zuwa polisteshan bada sutotimen ba”.

Addah da tayi tsilli tsilli dakyar tace “nifa ji nayi jikin ba kwari shine nake so na gasata jikinta ya hade amma tunda banyi abin kirki ba shikenan kuda kuka iya se ku mata” fuu tayi waje.
Wunin ranar haka ta yini mita duk wanda yazo seta gaya masa abinda Amirah tayi mata kuma dai kowa ita yake bawa laifi.

Ganin dai dagaske Bashir baze bada kudin taro ba Addah ta shiga ta fita da abinda Baban Amirah da yan uwanta suka hada da bashin Jama’a duk ta ganganda za’ayi bikin suna. Kayan abinci dama ba matsala bane sunyi akan na Store dinta za’a diba ayi komai.

Kaji kawai zasu siya se ruwa da lemo da kayan snacks se kuma kayan rabo da Amirah ta nace se tayi dan har ta kira me hoto yazo ya dauki Baby wanda za’a saka ajikin Jaka da Memo. Duk shirin nan basu gayawa Dada ba tunda tace bada yawunta ba balle Bashir da ya rantse ya kuma rantsewa baza’ayi ba shiyasa ma suka tsaida ranar Laraba bayan ya tafi litinan sannan zasuyi sunan.

Allah kaimu ranar suna lafiya 😂😂😂🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 17

Ranar Litinin Bashir ya tafi a ranar kuma Asma’u ta dawo dan ta tabbatar daman kafin su iso ya tafi. Da wuri suka taso dan haka sun sauka da wuri.

Gaba daya ranar baccin gajiya sukayi har zuwa washe gari talata sannan suka wartsake. Da yamma ta shirya dan tana so ta fita harta kunna motar ta amma taqi tashi tayi duk abinda zata iya amma taqiyi dole ta haqura ta kira Naziru ya zo da bakanike suka dubata yace dole seya tafi da ita gareji haka suka lallaba suka tafi se fasa fitar tayi.

Seda aka yi Sallar Isha tayi order Bolt, itada yaran suka fita, Shagonta na siyar da kayan yara sukaje dan tana so ta siyowa Baby Iman riguna, basu bata lokaci ba ta zabi masu kyau yan turkey guda uku se Shawl shima me kyau daya sannan tacewa yaran kowa ya dauki abu daya da ze kaiwa Baby Iman.

A leda aka zuba musu kowa aka bashi nasa suka juyo zuwa gida, seda ta dakko Atamfar data ajiye da zata hada musu da ita ta saka da qaramar Barimar Gold da tun cikin su Ahmad ta siyeta da aka ce mata mace ce qarshe se gashi ta haifi yan Biyu duk Maza tama manta da ita se zuwan nan ta ganta shine ta dakko ta hada musu da ita.

Yan uwan Amiran Suna zaune a palour sun baje kayan rabo ana zuzzubawa ita kuma tana daga gefe tana duba dinkunan ta ga gadon Iman a kusa da ita Asma’u sukayi sallama ita da yaran gaba daya.

A sake suka amsa musu, Amirah ta ajiye Kayan hannunta tana kallonsu, hada ido sukayi da Ma’u, seda ta murguda baki ta juya ido sannan ta gaisheta ita ko Ma’u data na ankare da duk abinda takeyi murmushi tayi kawai ta amsa mata a ranta tace “zaki gane kurenki yarinya Allah sa kiyi kuskuren zagina wata rana”.

Addah da tajiyo muryar Asma’u tai wuf ta fito daga daki, bakin kaman ze tsage saboda fara’a suka gaisa tana satar kallon Ledojin da suka shigo dasu.

“Miqo musu Yar mana Amirah kina zaune” Addah ta fada tana yiwa Amiran signa da ido, se Amiran ta daga ido ta kalleta fuskarta na nuna alamun “kin san me kike cewa kuwa” Ma’u da duk tana kallonsu tayi saurin cewa”Aa barta ma kawai bari mu qaraso mu ganta kar a jagwalgwalata”.

“Wane irin magana ne haka ke gafara da Allah ki gani se ayita wani saka ya a ke ji kamar kaza tunda tazo duniya ai dole a dauketa a haka zata saba” ta kwashe Net ta ciro Iman ta miqawa Ma’u.

Bakinta dauke da Bismillah ta karbeta cike da taka tsan tsan, masha Allah kuwa ga kamannin Farida nan a Fuskarta koda yake ai duk yaran da Bashir suke kama saboda ita macece shiyasa kamar ta da Farida tafi fitowa. Tana hannunta duk yaran suka leqata har Ahmad yana kama dan hannunta ya riqe.

“Mami muna son ta mu tafi da ita Lagos” ya fada yana wasa da hannun yarinyar, se Ma’u tayi murmushi kafin ta amsa shi Addah tayi caraf tace “Da ita zaku tafi ai Malam Amadu ko kuma in kunyi gaba zata biyo daga baya”.

Sunyi kaman minti Goma Ma’u ta miqe ta kwantar musu da ita kafin ta turawa Amirah ledar kayan tace gasu nan babu yawa a sakawa Baby nan suma yaran kowa ya dire tasa duk kowa da abinda ya tsinto mata banda Aliyu da daman shi a qofar palour ya coge bema shiga ba.

“An gode madallah” Addah da sauran Yan gurin suka fada, sukayi musu sallama ta tattara yaranta sukayi waje kamar suna jira suka shiga zazzage kayan a qasa.

“Ke Amirah kinga rigar da nake gaya miki wallahi yar dubu Ashirin da biyar dinnan kin gani ga kudinta nan ma a jiki” Nusaiba Diyar Inna Gaji ta fada dan zancen rigar da za’a sakawa babyn lokacin Shagalin suka gama take gaya mata akwai wadda tagani ta fita kunya a gurin wata qawarta har sun fara shawarwarin yanda za’a samu kudi aje a siyo se gashi Allah ya kawo mata daga sama.

Atamfar ta sake dagawa ta riqe baki tace “Amirah Embellished ce fa, bari dai muga ko qaramar ce” ta hau duba lambar Atamfa da fentin jiki seta dau sowa tana cewa

“Wallahi babbar ce, ke harda dan kunnen Gwal kai lalai matar nan dagaske take Dama Allah ya bani kishiya irin haka ai na huce takaicina se in ta haihuwa duk shekara tana kawomun kayan arziqi” Nusaiban ta fada tana ta faman daga kayan.

“Ke na taba ki da Arziqi, wannan uban kayan da kudinta ko na mijin aka siya?” Asiya yayar Amirah ta fada se Ummi da bata sa musu baki ba tayi caraf tace

“Ce miki akayi itama cima zaune ce irinku kuna zaune kuna jira se abinda miji ya dakko ya baku, toh nema takeyi tana aiki tana kasuwanci ta kayan nan ma da kika gani a shagon ta take siyarwa ga ledar nan kina gani”.

Ledar suka duba gashi nan kuwa “Asma’u Kiddies shop” a rubuce, se Nusaiba ta riqe baki tace

“Lallai kice ta kama qasa irin wannan kaya yan order kodai ma shagon ne naji ana zancen sa an ce duk Gombe Albarka ko da yake wannan iwar dukiya da aka mutu aka bar musu dole suyi ta bude gurare, jifa Salon din Yayar ta Bilkisun nan ba abinda ba’ayi na gyaran mace a gurin” Inji Asiyar,

daga nan kace nace ya kaure aka shiga fadar irin abubuwan da yan gidan su Ma’un suka kafa, kowa fadi yake suna birge shi yanda kansu yake a hade bazaka taba ganin wani abu wai shi yan ubanci a cikinsu ba.

Ran Amirah in yayi duba ya baci jin yabon da suke wa Ma’un, ta rasa a duniya dalilin da yasa Asma’u keda farin jinin mutane, duk wanda ya budi baki sedai ya fadi Alkhairinta badai sharri ba.

“Ke kanki shaida ce akan kyawawan halin Asma’u ai da mu’amarata me kyau” zuciyar ta ta raya mata. Seta ja tsaki tabbas ita sheda ce akan karamcin Anty Asma’u, tana da kyakykywar zuciya tabbas da mu’amala me kyau. Sannan sam abun hannunta be rufe mata ido ba gata da sauke kanta matuqa bazaka taba cewa ta fito daga gidan arziqi ba sedai idan ka dubi halayyarta kasan tabbas daga babban gida ta fito da suka tashi cikin Arziqi suka jiqu dashi dan haka basu dauke shi a matsayin wani abun dagawa ko da zesa suyi girman kai ba.

Tsaki ta kuma ja ganin itama ta bige da yabon Ma’un a zuciyarta, tabbas tana kishi da Asma’u da duk wata halayya ta ta. Ta kan ji dama ita ce Asma’un, bata kasance yar Babban Attajiri kamar Baban Asma’u ba kuma wannan ne kadai tasan bazata samu ba amma baya ga haka tayi Alqawarin duk abinda Ma’u ta mallaka seta seta same shi.

Tayi zurfi cikin tunaninta har bata san sun gama zuba kayan ba kowa ya fara neman makwancinsa se itama ta miqe ta dauki Iman suka shige daki suka kwanta saboda su samu tashi da wuri.

A bangaren Ma’u ma suna komawa kowa ya nemi makwanci da wuri nan da nan bacci ya dauketa dan bata ma ji jerin missed calls din da Malam Bash ya ringa jera mata ba har bakwai seda Asuba data farka. Seda tayi sallah ta kirashi, qorafi ya hauyi mata akan rashin

Please Login or Register in order to submit comment